Showing 1 words to 3000 words out of 80494 words

Chapter 1 - INSAF BOOK COMPLETE BY Amnah El Yaqoub.doc

12 Sep 2025

39

??ࡱ?>?? ? ????????????? ? ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????| 2

 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?Root Entry???????? ?F? WordDocument?????0Table????????jData
???????????????????? P?f?KSKS??3v???????pp???????,?? ??DDDDDDDDF$??g*p??DD????D????D?D??DD?? ?>`??>Normal$a$KHOJPJaJ3v??20Sls???(???
?4xQ?~V????!6.?g????z??H?%?0?F?\?m??????????r? b9U?`???4?f?v???????9?Q?mb?>?????D?n?%NC?V?j@?j???"?:??h(??JN?h?w?ԡ???$?P b B! ?3 ?D [2/3, 1:06 PM] El~Yaqoub: INSAAF


Writing by:Amnah El~Yaqoub

1&2



MARUBUCIYAR :
*DANA SANI*
*BURINAH*
*WAZAN ZABA?*
*SHALELAN BABA*
*NI DAKE*
*DANGI DAYA*
*INSAAF*


Like my page on Facebook =?G?
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493




*Page Din farko nakane dan'uwa na,PRINCE ABBA BAKARYA, ubangiji Allah yabar zumunci, Amnah tana yinka sosai=??*



Dasunan Allah mai rahma mai jin qai, ya Allah yanda nafara wannan littafin lafiya, Allah kabani ikon gamawa lafiya, kuskuren da zan rubuta wanda nasani, da wanda bansaniba, Allah yayafe min, Allah ka haneni rubuta abinda zaiyi Sanadin tashin hankalin wani ko wata.


Dan girman Allah, masu doramin littafi a channel dinsu su daina, wallahi tallahi tunda nafara rubuta littafi, bantaba shan wahala irin yanda Nasha wajan rubuta labarin DANGI DAYA ba, amma abin baqin ciki ina gamawa kuka sacemin kuka doramin a channel dinku, FARAR SAQA TV wallahi idan kuka sake doramin littafi a YouTube zanyi reporting dinku a lalata channel Din, kuntara views din banza =?E? @&?, banyi littafin kudi ba banga dalilin dazaisa kunemi kudi da littafi naba, inada Damar dazan siyar dashi amma ban siyar ba,Bana saka number ta a littafi, amma acikin littafin littafin DANGI DAYA nasaka number brother na, idan kunyi masa magana zai sanar dani, yanzu de na roqeku kudaina, nagaba kuwa bazan roqeku ba.



To wannan Karon alqalamina yatafi Lagos, kuyi hakuri wannan littafin zakuci Karo da kuka,=?-? dakuma emogi d'an kadan=?L? Bazan ziga littafina ba, kakaranta kaji yanda yake da kanka >??


*A taqaice*
Labarin INSAAF labari ne da taurarin ciki suke fuskantar qalubale iri-iri, tauraron dakuma tauraruwar, kowa da irin nasa qalubalen, wanda daga qarshe zan warware muku komai insha Allah =?O?




__________
Manyan motoci ne guda biyar suke sharara gudu a babban titin dazai kaika mubi local government, Cikin jihar Adamawa, sosai suke gudu kamar sun samu titin gidansu, duka motocin guda hudu farare ne, kuma kowacce daga cikin su number motor tana dauke da sunan INSAAF, guda dayace baqar qirar Range rover take dauke da number LSR Lagos Surulere, daya daga cikin local government dake Lagos state, sosai suke gudu Bana wasaba, motocin farare biyu agaba, biyu abaya, Sai kuma baqar motar datake tsakiyarsu

Su biyu ne azaune a bayan motar shida yayansa, gaba dayansu suna sanye cikin suit wadda tayi bala'in yimusu kyau

Babban Hankalinsa Yana kan computer dake kan cinyar sa Yana typing cikin sauri, computer na qarewa kallo launin brown, amma maimakon aga sunan company computer daya qerata sainaci Karo da sunan INSAAF
Agogon dake daure a tsintsinyar hannunsa qirar Gucci ya kalla yasaki wani gajeren tsaki, sannan ya maida Hankalinsa kan abinda yake
matashin saurayin dake gefensa kyakkyawan gaske, suna mutuqar kama da juna, saide shi bekai shi shekaru ba, window dake gefensa yagama kalla bayan sunzo wucewa ta wani qauye dake kusa da Mubi, sannan ya juyo ya fuskanci dayan yace "Yaya, kasan wannan qauyen fa mukazo nida Mamy last year munraba musu zakkah, wallahi Yaya nide qauyen Yamin
, Shiru babu hayaniya, gashi lafiya muka Gama abinda yakawo mu muka tafi"

Shiru yayi Yana jiran yayan nasa yabashi amsa, amma Shiru kamar da dutse yake magana, kawai typing dinsa yake
Bata fuska yayi kalar shagwaba ya kalleshi sosai "Yaya magana fa nakema"

Batare daya kalli qauyen ba Hankalinsa Yana kan abinda yake yace masa "naji"

Shima da yaji irin amsar daya samu Sai yayi Shiru bai sake magana ba, ya rungume hannunsa a qirjinsa Yana Kallan window tare da tunanin Mamynsa, Yana fatan inama ace ta biyosu




*** ***** ***


"AMINA!"

cikin sauri tafuto daga cikin dakinta tana daura dankwali a kanta, sanye take cikin atamfa wata kod'ad'd'iya, duk da ta daura dankwali hakan bai Hana gashin kanta mai tsawo da santsi futowa ba,Allah yayi mata baiwar gashi sosai me matuqar tsawo da sheqi,wani sillallan takalmi tasaka tace "Inna gani"

"yauwa Aminatuwa 'yar albarka dauki tulun nan kisamo mana ruwa mudora abinci, Kinga yayanki baya nan, kuma wajan akwai Nisa, Dan Allah Karki tsaya shirme a hanya kinji ko"

Ahankali cikin sanyinta tace "to Inna"

Sannan ta dauki tulun tafice daga gidan batare data saka ko mayafi ba

Tana cikin tafiya tana yar waqarsu ta dandali ta hangi wata majalissa duk maza ne sunata fira suna daria,Sai masu shan rake suma sunata nishadi, mutum daya ne daga cikinsu ya hango tahowarta ya fadawa sauran, lokaci daya majalissar ta watse, tuni wajan yakoma kamar ba'a halicci mutane, mamaki ya kamata, kawai saita girgiza kanta tawuce

gidan qawarta lubabatu tashiga bakinta dauke da sallama,ta tarar dasu zaune a tsakar gida suna hira itada goggonta, lubabatu tana ganinta tace "Amina sannu da zuwa, kamar kinsan yanzu nake shirin biya miki kozakije Debo ruwa"

Itama murmushi tayi, cikin sanyin muryarta mai zaqi tace "Tona hutar dake, tashi mutafi"
Tamaida Kallan ta wajan goggo zata gaisheta, amma kafin ma tayi magana goggo tace "Ai Amina saide kije ke kadai, lubabatu tanamin aiki"

Cikin tsananin mamaki ta kalli lubabatu taga azaune taganta babu abinda take, cikin sanyin jiki tace "to goggo" sannan tajuya zata fita daga gidan

Lubabatu ta tashi zata bita, cikin tsawa goggo tace "ke!! Dawo ki zauna"

Kamar zatai kuka tace "goggo rakata zanyi kofar gida"

Cikin Kallan rashin mutunci goggo ta watsawa Amina harara, sannan tacewa lubabatu " Ai basai kin rakata Bama, da tare kuka shigo? Ba'ita kadai tashigo ba? To rakiyar ta'isa haka daga nan bakin kofa ma"

Amina tana ganin haka, tasake girgiza kanta Akaro na biyu, wani irin abu yatare mata maqoshi, kuka takeso tayi amma tahana kanta, saide manyan idanuwanta sun kada sunyi jajir, cikin sauri tafice daga gidan

Tafuto kenan daga gidan su lubabatu taga isyaku yayan lubabatu suna zaune shida abokansa kusan su biyar, isyaku Sai tsari yake, Sai zuba surutu yake suna dariya, kasancewar sa mutum mai yawan surutu, ta gabansu tazo ta wuce amma abin mamakin shine su basu guduba amma cikin sauri suka juya mata baya, ko kadan sunqi yarda su kalleta

Ahankali ta daga kanta taga yanda mutane suke gudunta, lokaci daya taji hawaye masu dumi sun silalo daga idanuwanta, wannan Karon batayi kokarin Hana kanta kuka ba, sosai take hawaye tana tafiya cikin sauri, tun tana yin kuka na hawaye harta dawo tanayinsa da sheshsheka, in banda tanada karfin hali da tuni tayi wurgi da tulun Takoma gida, amma ahakan ta daure tanufi hanyar Rafi ita kadai



*** ***** ***


Cike da qwarewa motocin suka tsaya awajan taron Bude daya daga cikin Babban Companynsu dake Mubi local government

An tsara sunan company asama mai taken....
INSAAF LTD (OIL&GAS SERVICES)

anyiwa wajan kwalliya sosai yanda ya kamata,mutane sun taru danqam awajan, su kadai ake jiran zuwansu, cikin sauri daya daga cikin Escort dinsa yabude musu bayan motar suka futo shida qaninsa
P.A dinsa Auwal ne yamatso da sauri yafara yimasa Bayani "Yallabai wannan sune takardun dazaka saka hannu bayan angama taro, sannan akwai wasu baqi da suke buqatar ganinka, akwai maganar kwangila data kawosu wajanka, dangane da wajan wannan taron kuma babu matsala, angama komai kamar yanda kabada umarni"

Adede lokacin da PA yagama Bayani, adede lokacin suka qarasa ciki, ahankali yace "Okey"
Bayan yagama jin Bayanin nasa

Bayan anbude taro da Addu'ah kuma anyi Bayani sosai Akan wannan company, Sai aka Bawa mamallakin company dama yayi nasa jawabin, bedauki wani lokaci mai tsawo Yana Bayani ba, ya damqa amanar kula, dakuma riqe wannan company a hannun qaninsa, kuma dan'uwansa, ma'ana yabashi dama ya tsaya a matsayin shugaba na wannan company

A take wajan ya dauki qaran tafi, kowa farin-ciki dauke Akan fuskar sa, mutane dayawa kuwa suna mamakin irin yanda yake qaunar wannan qanin nasa

Lokaci daya hawayen farin-ciki suka zubo masa, yadaga kansa ya kalli yayan nasa, Ahankali yace "Yaya..."

Cikin sauri yayan nasa ya dakatar dashi ta hanyar daga masa hannu, saida yagama ganawa daduk mutanan da PA dinsa yayi masa Bayani, sannan sukai shirin tafiya gida, kwata kwata zuwansu, dagama taron bedauki wani lokaci maai tsawo ba, mutane sunci sunsha sunyi hani'an, amma shi oga kwata kwata ko ruwan wajan baishaba

Daga nan basu tsaya yin komai ba, aka Bude masa Mota suka shiga, Yana zama wayarsa tafara qara, be dauka ba, saida yabari ta katse dakanta, sannan ya kirata, yanaji andauka daga daya bangaren yace "ISHRAQA"

Saida tayi murmushi sannan tace "dama kiranka nayi inji Yaya taro, dafatan komai lafiya"

Ahankali kamar mai koyon magana yace "koh?"

Dariya tayi, tace "Naga alama har yanzu fishi kake dani saboda naqi zuwa,akwai abinda yasa banzo ba"

"yayi" shine kawai abinda yace

Dan daga muryarta tayi cikin fishi tace "Wai kai Sai wani binka nake Ina baka hakuri Sai kace wani sarki Sai amsamin kake kamar bakaso d'an rainin hankali kawai, ni Sai anjima" tana fadar haka takashe wayarta

Murmushin dabai shirya yi bane ya qwace masa, har dimple dinsa ya futo sosai, cikin ransa yace "yar rainin wayo kawai" sannan ya ajiye wayar agefensa yabude computer Yana Moving wasu documents zuwa wata folder

Qanin nasa yayi sakare Yana kallansa, zai Iya cewa tunda Garin Allah ya waye babu wanda yaga murmushi afuskar yayan nasa, amma saboda Ishraqa tayi magana dashi har tayi Sanadin sakashi murmushi, shikam baisan shaquwar datake tsakanin suba, abinda yasa ni shine Ishraqa abokiyar shawarar yayan nasa ce, kuma baya boye mata komai, haka itama yasan sirrikanta dadama a matsayin su na Class Mate kawai

Ajiyar zuciya yayi, yadubi yayan nasa "Yaya Naga Alama kana cikin farin ciki saboda Anty Ishraqa takiraka, kude kuna son junanku, inama ace Nima nasamu qawa wadda zamuyi qawance da'ita haka kamar ku"

Juyowa yayi ya kalli qanin nasa, tsantsar Kallan yarinta da shirme yake masa, in banda shirme mezaisa yace suna son juna da matar datake da aure akanta, batare da yayi magana ba, ya maida Hankalinsa kan computer

Haushi ya kama qanin nasa, Dan haka Shima yayi Shiru kawai

Bayan wasu mintuna ya dago kansa tare da rufe laptop din,yasaka ta a cikin jaka sannan yarufe jakar, Ahankali yafara magana "Nagama Dora kowanne documents dawasu takardu daya danganci filaye,gidaje, gonaki, da takardun duka sauran companies na INSAAF dama sauran kadarori Akan laptop dinnan"

in banda qanin nasa Yana kusa dashi da bazai jishi ba, cikin sauri ya kalli yayan nasa "Amma Yaya kana ganin babu kuskure kuwa Akan hakan?"

Shima Kallan qanin nasa yayi cikin mamaki batare da yayi magana ba, wanne irin kuskure yake magana Akan Andora takardun komai Akan computer? Ai Yana ganin kamar hakan shine zaifi sauqi

Kafin qanin nasa ya sake magana aka yiwa motar tasu wani irin duka, arazane suka d'ago kansu suka kalli gabansu, cikin sauri driver yataka birki, hakan dayayi shiya basu Damar dukan motar ta ko'ina, gaba daya sun faffasa glass dinta

dak! dak!! gaban qanin nasa yafara faduwa,musanman dayaga gabza gabzan qartin dasuka zagaye motar tasu, lokaci daya tsoro yakamashi ya kama murdaddan dantsan hannun yayan nasa yariqe (>?#?)
Jikinsa Sai rawa yake, shikuma gogan ko kadan babu alamar tsoro a ransa, bare kagani Akan fuskarsa, shi dama yasan dole za'a rina, tunda yaga babu motocin gabansu da bayan su yasan cewa dole ansake shirya masa wata maqarqashiyar kamar yanda aka saba

Jakar laptop dinsa ya dauka cikin sauri ya ratayata ajikin sa, sannan yabude kofar motar zai fita
Qanin nasa ya sake qanqame hannunsa, tuni hawaye sun samu matsugunni Akan fuskarsa (>?#?)
Cikin kuka yafara girgiza kansa "Yaya ASIM.... karka fita, Allah zasu kasheka,Dan Allah Yaya karka fita suyima wani abu"

Batare dayace komai ba ya qwace hannunsa yafice daga motar, suna ganin futowar sa kuwa suka hau kansa da duka,babu ji babu gani,Shima yafara ramawa, driver Yana ganin yanda suke fada Shima yafuto da sauri domin temakon ubangidansa amma kafin yaqaraso daya daga cikin su yasa bindiga ya harbeshi acikinsa, nan take yace ga garinku nan (=?-?)

Wani irin karfi ne yazo masa, har yayi nasarar qwace makamin daya daga cikin su yafara yimusu wani irin mahaukacin duka dashi

Shikuwa qanin nasa dake Mota qamewa yayi azaune, tunda yake baitaba ganin harbi a zahiri ba Sai yanzu, wani irin danshi yaji a Wandonsa, wanda ya tabbatar ko tantama babu fitsari ne (>?#?)

Yajuya ya kalli yayan sa yaga yanda yake fada kamar a filin Wrestling, gaba daya Jikinsa ya dauki mazari, daya daga cikin yaran ganin Yana dukansu kuma idan sukai wasa tsaf zai musu illah, Dan haka nan take babu Bata lokaci yazaro bindigar sa yaseta shi, ji kake taaaas ya harbeshi akafardarsa

Wata irin gigitacciyar qara qanin nasa yasa, dakarfi yace "Yaya!!!"

Shikuwa Asim cak ya tsaya, lokaci daya ganinsa yafara daukewa,ya tabbatar da cewa mutanan da suke neman rayuwar sa yau sunci galaba akansa, Ahankali labbansa suka furta "Amjad"
Sannan yadaga hannunsa daqyar yayiwa qanin nasa daya Kira da suna Amjad alama yagudu, dif idanuwansa suka dauke, yazube Akan gwiwar sa, sannan yafadi awajan

Idanun Ammar sunyi jajir saboda kuka, Akan idonsa yayansa yafadi, yasan cewa yanzu kuma saura shi, cikin sauri yabude motar yafuto, bai tsaya awajanba ya kama gudu, baisan ma inda yake dosa ba

Suna ganinsa Yana gudun tsira, amma abin mamakin babu wanda yayi masa komai, asalima Dena kallansa sukai, ganin Asim a kwance kamar matattace yasa suka kwashe da wata irin dariya, su kayi kama-kama suka mai dashi cikin motar, hannunsa banda jini babu abinda yake zuba

Babban cikin su yakira waya yace "oga mungama aikinmu, yariga ya sheqa saide labarinsa"

Daga daya bangaren akai magana, sannan Yaron ya sake cewa "angama oga" daga nan yakashe wayar

Babban tafkin ruwan dake tsallaken titin wajan nan suka tura motar, babu tunanin komai suka tura motar da Asim din yake ciki cikin wannan ruwa

Suma suka hau motarsu suka tafi a dari da sittin, wajan yarage daga fassasun glass din motar, Sai jinin Asim daya zuba, dakuma gawar driver dake kwance male-male a cikin jini

Shikuwa Amjad Yana cikin gudu kwata kwata baya Kallan gabansa, saiji yayi wata Mota tayi Sama dashi, nan take yafadi awajan sumanme



*** ***** ***


Hawayen Idonta ta share Akaro na ba a dadi, mutuqar gajiya ta gaji da wannan diban ruwan, gashi yayanta baya nan, idan ta zauna ma babu abinda zatayi, Gara ta debo musu ruwan ko hakan zaisa ta ragewa kanta dinbin damuwar datake damunta
Tana qarasawa Rafin ta tsugunna da niyyar debo ruwan saitaga yayi ja, tasa hannu tana kawar dashi taga abu yaqi qarewa, tana juyawa hannun ta na dama taci Karo dashi, gabanta ne yayi mummunar faduwa, cikin sauri ta miqe tsaye ta callara wata irin qara wadda tasa cikin dajin amsawa, amma Shiru kakeji daga ita Sai kukan tsuntsaye, jikinta ne yadau ki rawa kakar-kakar, tafara ja da baya tana girgiza kanta, ganin cikakken mutum a kwance fari tass dashi tamkar bazaka masa hausa ya amsa ba, baya baya takeyi tana cewa "Ba mutum bane, wallahi aljanine" awajan tabar tulun ta kwasa aguje tayi gida, kasancewar tanada yalwar dukiyar fulani,Sai gudun datake yasa suma suke rawa

Baram! Tabude kofar gidan su tashige, tana zuwa tsakar gidan tafadi akasa
Babanta da yayanta dasuka dawo daga cin kasuwa atare suka ce "Subhanallahi..."

Amma ko kallansu batayi ba, kokarin tashi take tashige cikin dakinta, Inna ce takamota tariqeta cikin tashin hankali tace "ke Amina, menene? Keda waye? Waye yabiyo ki haka?"

Hannunta tadora Akan qirjinta datake numfashi Sama-Sama Sai haki take saboda gudun datasha, takasa basu amsa Sai Hannunta dayake rawa ta daga tana nuna musu hanyar kofar gidan





Wacece Amina? Meyasa ake gudunta?

Meyasa ake bibiyar rayuwar Asim?


Fan's ya bayan kwana biyu?












Amnah El~Yaqoub
' [2/4, 11:22 AM] El~Yaqoub: INSAAF



Writing by :Amnah El~Yaqoub




3&4

Like my page on Facebook =?G?

https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493





Babane yaje Randa yadebo mata ruwa akofi, ya tsugunna agabanta tare da meqa mata "karbi wannan Kisha"

Dasauri kuwa tashanye ruwan, amma duk da haka tana Haki, saide ba kamar nadaba, duk sun zuba mata ido suna Kallan ta, yayanta ma ya matso kusa yace "meyake faruwa qanwata? Kiyi mana Bayani mana"

Numfashinta Yana Sama Sama kadan, tace "Yaya Ammar wallahi aljanine, aljani nagani a Rafi"

Gaba dayansu su ukun suka hada baki suka ce " Aljani Amina!!"

Babanta ta kalla tace "Eh wallahi baba, zan Debi ruwa kenan naganshi, nikam shikkenan nayi gamo" ta qarasa maganar tana Dora hannun ta a kanta (=?F? @&?)

Babanta ne ya kalli yayanta yace "Ammar muje mugani, wata qila akwai abinda yake faruwa"
Cikin sauri tariqo baban "Baba karkuje, wallahi idan kukaje kuma zai Bude muku ido, karkuje baba"
Murmushin manya kawai yayi, suka nufi hanyar fita shida Ammar, Inna ma dake tsaye tace "a a Malam, ai muma bamuga ta zama ba, ya za'ai yarinya tace taga aljani kutafi kubarmu mu biyu agida, idan wani shegen ne yayi mata ture fa" (=??)
Baba yace "kumafa hakane larai, to kutashi mu tafi, idan magana tafi karfin mu Sai a fadawa mai Gari yakira masu ruqiyya ayi mata"

Inna ta yafa mayafi tabisu, itama datayi tsuru agefe cikin sauri ta tashi takama hannun Inna tariqe gam, a haka suka tafi, a hanya duk wanda yaga Amina dauke kansa yake, idan yarane kuwa saide kawai kaga sun kwasa aguje sun gudu, Abin Yana mutuqar damunta, saide tashin hankalin data gani a Rafi yafi tsaya mata Arai

Suna qarasawa kuwa tasake riqe hannun Inna,sukaja suka tsaya daga nesa, amma duk da haka saida ta buya a bayan Inna, Ahankali Ahankli take Dan leqo kanta
Baba da Yaya Ammar kuwa cikin sauri suka qarasa,Yana Nan agefen ruwan a kwance kamar yanda ta ganshi itama, baba yace "subhanallah, duba duba Ammar, ai kamar mutum nake gani"
Ammar yace "Wallahi mutum ne baba"

Bismillah sukayi sannan suka janyo shi waje,hannunsa kuwa jini ne yake zirarowa mai kauri, baba ya kalli su Amina da suke can gefe, "Larai mutum nefa, wannan yarinya da shashanci take" ya qarasa maganar Yana Kallan Amina

Inna tace "Auto, Bari mu qaraso" (=??)

Wajan suka qarasa, Amina ta zuba masa ido tana Kallan tsantsar kyan da Allah yayiwa wannan bawan Allah, Yana kwance kamar babu rai ajikinsa, amma jakar laptop dinsa tana nan ajikinsa, gashin idonsa dogaye Zara-Zara,ga wani irin saje da yayi wa fuskar sa mutuqar kyau, bashida gemu saide saje daya qara masa kyau sosai, Inna ma data ganshi saida ta tsorata, cikin ranta kuwa cewa take wannan kyan nasa ai yayi yawa

Baba yace "Ammar inaga daukansa zamuyi, mukai shi gidan maigari, duk abinda ya yanke shine daidai"

Girgiza kansa yayi "haba baba, wanne irin maigari awannan halin da yake ciki, mukai shi asbiti kawai, idan muka dawo dashi Sai akai shi gidan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login