Showing 30001 words to 33000 words out of 36278 words
Chapter 11 - Zan Fasa Kwai Part 1 Complete by Hadiza Bara'u Gidan Iko.txt
su Wanda suka ci moriyar tashi suna Nan suna juya kudi Amma dayake Dan Adam ne me yin Abu don yabo ko ganin ido sun ma manta da tsiruwar shi zumuncin zamani kawai mutane suka Rika Amma duk da haka shi Bai rike su ba duk inda Rabon yake zai fito shiyasa ya ke zaune lafiya inda Kuma hajiya ke taimaka mishi har ta Fara siyar da kaddarorin ta tana bashi kudin don ita Kam ranta ma zata iya bawa abdulkarim don yayi Mata Hidima tana Kuma addu a Allah ya kawo mishi mafita ya Kuma bude mishi kofofin arziki
Dare daya lubabatu ta soma kosawa da wannan Rayuwar ta talauci tun Bai Gane ba har aiyukan ta suka soma nuna mishi....................
[5/23, 11:35 PM] Aunty Fauzah Yar Amanah: *ZAN FASA KWAI*
*NA*
*HADIZA BARA'U GIDAN IKO*
_Hakkin Mallakar na gidan iko ne_
*Page 36*
*_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
.......... Lubabatu tamkar wadda aka zuge dare Daya ta sauya sauyi kuwa me yawa abinda ya bawa AK mamaki Amma duk da haka yayi Mata uzuri don aganin shi Dole taji Babu Dadi musamman yadda ta Saba Rayuwa cikin iko da wadata yau Kuma lamarin sai sannu
Bata fito fili ta fada mishi ba Amma ya lura da ita da take taken ta
Amma duk da haka yayi Mata hanzari don abinda ya nuna mishi kamar tagaji shine kullum cikin bacin Rai take abu kadan Kuma sai ya fusata ta Koda ko ita da yarane sai kaji tana ta antaka musu zagi abinda ta San bayaso bare duka sai ya zamo yanzu duk ta hada tanayiwa yaran sai dai ya kalla ya kauda kanshi
Idan Kuma ta hadosu shi da ita zata rufe idonta ta gurza Rashin mutunci son ranta Amma duk da hakan baya biyewa don ya San mafarin lamarin har dai wata Rana ya zaunar da ita Yana mata nasiha
"Kiyi hakuri lubabatu komai Kika gani aduniya Yana da farko da Kuma karshe. Kar wannan canjin yasa kiji aranki ko Rahamar ta Kare ko babu sauran wani Jin Dadi Nan gaba . A a yanzu ne ma lamarin zai Fara duk bawan da Kika ga an jarrabeshi matukar ya cinye jarrabawar shi to matakin nasara ne ya hau . Hska Kuma Babu Wanda zaiyi hakuri Bai cimma rabar hakurin shi ba don haka don Allah da manzon sa kiyi hakuri babun da muke ciki in Sha Allah zamu samu kanmu cikin wadata wata Rana matukar dai munyi hakuri domin Allah. Na sani ba kowane zai jurewa Rashi ba to Amma ai bawan da yayi imani yasan Dole ajarabeshi sai mu godewa Allah da ya bamu wannan jarabtar me sauki kiyi hakuri ki Kuma jure ki koma hango baya yadda kika samu Kai sai ki godewa Allah shi Kuma sai ya dubeki ke da lamarin ki.
Ta matse hawaye ba tare da tankawa nasihar sa ba inda yaji tausayin ta ya Kara kamashi
Da hakan dai ake ta gurgurawa da Dadi ba Dadi kamar dai ta dauka ko ta hakura inda ake cikin Rufin Asirin Allah wani abun mamaki Kuma ba a Kara kiranshi Kan abinda ya shafi harkar kwangila ba shima kuma Bai nemi cusa kanshi ba ya tsaya matsayin shi Yana ta laluben hanyar da Asiri zai rufu inda Allah cikin ikon shi masu zanen taswirar gidaje Kan bashi aikin zanen kasancewar shi eng Wanda ya hada har da sanin makamar zanen inda Kuma kudi ke Dan shigowa Amma ba kamar yadda aka sababa
Inda agefe Daya Kuma Kabir yayi wata irin shahara da tunbatsa akan harkar gwangila saboda ayanzu shine ke Kan kadamin shi aiki Kuma Babu nagarta haka za ayi shi agama kafin lokaci kadan ya lalace saboda an saka manuba da ha inci
Malam Ali yayi ta Kiran wayar shi Amma kememe yaki dagawa saboda ya San maganar dungo za ayi mishi inda a yau malam Ali ya bugo hanya ya iso garin Abuja duk da Bai San gidan Kabir din ba Amma akace matambayi baya Bata kasancewar shi shahararre Bai Sha wuya wurin gano gidan ba inda ya tsaya Yana karewa gidan kallo Wai gidan dan dungo ne wannan Amma ta Rayu a wani gida da bashi da maraba da kufai saboda ruwan damuna da ya kayar dashi Anna Bata samu arzikin tadawa ba Amma dubi gidan da yazo garin Abuja ya Gina tamkar yayi wurin Zama aduniya
Bama wannan ne abin ji ba irin yadda aka kirashi yazo ya samu mahaifiyar shi cikin halin ciwo da neman agaji Amma bawan Allah Nan tunda ya ufa ya tafi Bai Kara waiwayo ta ba bare yayi tunanin duba yadda ta karaji da jiki bare ya kawo Mata dauki ko agaji
Yau tsayin watanni shida Babu dungo Babu labarin ta Amma ko dai dai da Rana guda Daya Tak Bai tunawa da uwar shi na cikin neman taimako da agaji bare Kuma ya ruko wani Abu irin na jinkai da ya'yan kwarai masu neman albarka kewa tsaffin su Kai wannan wace irin SHIGA UKU da asara ce? Ubangiji ka shiryi bayinka masu Bata kasa yaran musulmi su zamowa iyayen su sanyi idaniya irin su kabiru Kam da haihuwar su wallahi gara barin su don haihuwar su batayiwa Wanda yayita Rana ba
Malam Ali ya share hawayen tausayin dungo yayiwa me gadin magana akan asanar da me gidan yayi bako
Aiko sai gashi ya fito cikin shiga ta Wanda ya samu wurin Zama a duniya Kaya masu tsada Wanda kallo daya zakayi mishi ka bashi matsayin minister ko Dan majalissa
Ganin malam Ali yasa ya ji wani Abu marar Dadi ya sauki she da ruwa da lemu inda yake tambayar shi
"Kabiru baka tambayi me jiki ba bare ka Kira kaji ya ta Kare ji?
"To ai lafiya ita ke fakuwa na San dai taji sauki..............
"Amma ko taji sauki ai tana bukatar kulawa mussamman Kai da kake dolen ta
"Kabir kayi sannu da kidan da duniya ke maka kana taka rawa Wallahi Babu komai acikin wannan Rayuwar sai rudani
Duk nasarar mutum a Rayuwa ya samota ne daga addu ar iyaye don su ke da mabudin kowace irin nasara...
"Bama abinda ya kawo Ni wurinka kenan ba don kowa ya gyara ya sani banzo don nayi maka wa azi ba sakone dungo taba Ni ta Kuma ce in isar gareka gashi Kuma Allah ya Taya min na kawo maka sai dai abin tashin hankali da saka zuciya rawa shine mun nemi dungo sama ko kasa mun rasa.....................
[5/24, 7:50 PM] Aunty Fauzah Yar Amanah: *ZAN FASA KWAI*
*NA*
*HADIZA BARA'U GIDAN IKO*
_Hakkin Mallakar na gidan iko ne_
*Page 37*
*_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
...........Arude yake kallon malam Ali Jin yace Wai Babar tashi ta bace an nemeta sama da kasa Babu ita Babu labarin ta.............
"Malam Ali ba asan inda take ba kenan?
"Abinda yake daurewa mutane Kai kenan don faruwar lamarin tamkar kiftawar ido Wai an nemi dungo Babu ita Babu dalilin ta
"Shin wani ne ya sace ta Koko guduwa tayi???..........
"Allah shine mafi sani abinda kawai na kawowa Raina shine dungo tana ganin Bata da kowa sai kanta idan ta faku idanun Al umma batayi laifi ba shiyasa don nafi zargin guduwa tayi don bakin ciki Babu abinda baya sawa...........
"Bakin cikin me malam Ali?........
"Bakin cikin ka kabiru me yuwa dungo tana kallon kanta a wadda batayi SA AR haihuwa ba don ban taba ganin Dan halak yayi irin abinda kayiwa mahaifiyar ka ba Kabir
Abu Daya Zan fada maka shine ka saurari zuwan musiba don kuwa kajawo Allah fada....
Arikice kabiru ya Mike Yana duban malam Ali da ya fada mishi gaskiya Amma ya kasa abinda zaiyi don ya yarda ya amince lallai ya jawo Allah fada
Malam Ali ya Mike Yana fadin
"Ni na koma sai Allah ya kaddaro saduwar mu idan kazo inda nake ma gaisa idan kuwa ta Kama mun hadu shima ma gaisa don ba Zan yaudari kaina cewa zaka zo gidana sada zumunci ba Toni a wa?
Da haka malam Ali ya fice ya bar Kabir da hada hudu da ukun da zasu bashi takwas
Izzatu da taji batun itama taji Babu Dadi Amma sai tace addua kawai zasuyi itace mafita
Yayinda humaira fulani taji ya kakar tata ta Bata kuka take tamkar dai izzatu ce ta Bata abinda ya Bata ran izzatu ta shiga zazzaga Mata masifa
Kwana biyu Kabir ya watsar da batun dungo inda yace duk ma inda ta SHIGA zata fito idan Kuma tayi haka ne don ta tada mishi hankali to ta tada mishi
Bai samu zarafin duba kunshin da takardar ba ya kwashe su ya watsa ciki kabit din ajiyar takardun shi
Kwana biyu ummita na zuwa kuki cafee kasa saboda Babu kudin da zatayi transport din zuwa gashi saura wata biyu ta Ida ta karbi sakamakon
Tana tafe anatse inda kamar daga sama Wilson ya hangota zata ketare titin da zai sadata da kuki cafee inda ya zuba Mata ido a yau ji yake tamkar idan baiyi Mata magana ba zaiyi Rashi na zuciyar shi sai dai kafin ya faka motar ya fito har ta shige
Ya kasa tsaye da zaune zuciyar shi na kawo mishi shawarwari akan kawai ya jira ta fito in yaso ko mayar da its gidane sai yayi Aiko ya dasa zaman jira har uku na maraice ta fito ta soma tafiya inda ya kula tamkar Bata da lafiya
Ta gota shi kadan ya ga ta dafe bishiya ta rike kanta Wanda alamu suka nuna ciwo yake Mata inda dabara ta fado mishi ya tashi motar ya karaso gareta Yana fitowa
Ya tunkaro ta ta zuba mishi ido kallo daya ta Gane shine Wanda ya tsura Mata idon Nan a country mall
Yayi Mata sallama cikin hausar shi da Bata fita Bata amsa ba ta dai dubeshi
"Sannu fa Naga kamar kina neman taimako na?......
Tayi saurin Kada mishi kanta
"No nagode zaka iya tafiya.
"Kiyi hakuri nasan inda zakije akwai nisa kizo na kaiki Naga kamar kina headache ne ......
"Nagode sosai Zan iya komawa ba damuwa...........
"Kiyi min alfarma ko ta kaiki gida ne tunda har Baki da lafiya..........
"Idan aka ganni a motarka nace me? "Ka ganka kuwa ? "Taimako wani abune da addinin mu ya koyar damu ga mabiyan sa shin kana daga mabiyan ne da zaka taimakeni?
"To duhu da haske basa tarayya a wuri Daya Dole daya ke bawa Daya wuri idan haske ya bayyana to duhu yayewa yake don haka na gode da taimakon ka gareni
"Na sani amma haka Nan naji Ina son taimakon ki tunda muma namu addinin ya koyar damu taimakon Kuma Bai saka kiyayya ga sauran addinan ba indai ba naku adfinin ya saka muku kiyayyar sauran addinan ba. Kiyi hakuri ki shigo na saukeki nayi Miki alkawarin Babu cuta tsakanin mu haka kawai nake son taimakon ki
Azahiri ita kanta tana bukatar taimakon don Jin kanta take tamkar zai tarwatse Dole ma ta nemi abinda zai kaita gida don Bata sababa ga kuma yunwa da takeji wadda idan akasa tace zata tafi to ko shakka Babu sai dai akwashe ta amika gidan don haka ta sallama ta shiga motar yaja suka iso gida ya sauketa ya Miko Mata fakitin maganin ciwon Kai me tsadar gaske ta karba tana godiya
Tun daga wannan Rana Bai Kara shiga cikin lamarin ta ba sai dai zai labe ya kalleta ya more ya koma gida inda kusan kullum sai yazo kuki internet cafee ya ganta batare da ya Bari ta ganshi ba
Hajiya sabuwa first lady matar Mr President take sanar da Mr President din maganar da ta taba fada mishi ta samowa Anwar auren diyar kawarta matar soja wato kudusiyya ta taso don haka atura mutane su nema mishi auren
Ya dubeta Yana murmushi
"Kice auren gata za ayiwa Anwar ba na fada Miki Yar gidan Kabir mashi Nima na nema mishi ba? Ta kwabe Baki da zaka yarda sai ince ka bar maganar Yar gidan Kabir mashi kudusiyya macece daya tamkar da goma.........
"Ba zanyi magana biyu ba tunda dai kema kin samo mishi wata sai ahada mishi biyu don haka itama Yar gidan Kabir mashi din sai muyi magana kawai
Wannan abin ya Bata ran haj sabuwa don tasan idan matar soja taji haka ba zata yarda ba Amma kome kenan zasu San yadda sukayi suka lalata Shirin Yar gidan Kabir din don kudusiyya kawai suke son tayi Rayuwa a gidan Anwar din baza ta tabs Zama da kishiya ba bare har ta Zama Bora
Sai dai da Anwar din ya shigo hajiya sabuwa ke mishi maganar kudusiyya da zaba mishi ita da tayi a matsayyin matar aure yayi saurin tareta.....
"Bana son ta hajiya ku barni na zabo matar da Nike so da kaina tunda Kuma zabar kanku kukayi ke da dady ba hada ku akayi ba.......
"Kayi karya ka bani kunya Wallahi Anwar Dole ne ka auri kudusiyya.....
'to shikenan haj duk abinda ya samu Yar mutane kar kiyi kuka da kowa......
Ya fice ya barta sake da Baki...............
[5/24, 7:50 PM] Aunty Fauzah Yar Amanah: *ZAN FASA KWAI*
*NA*
*HADIZA BARA'U GIDAN IKO*
_Hakkin Mallakar na gidan iko ne_
*Page 38*
*_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
........Anwar ya fito sukayi kicibus da mahaifin shi ya zube Yana rattaba mishi abinda hajiya sabuwa ta fada mishi akan Wai ta yi mishi Mata da kudusiyya wadda shi atsarin shi kudusiyya batayi mishi ba. Mr President yayi murmushi
"In Banda abinka Anwar meye na damuwa don ta zabo maka matar girma ? Nima fa nayi nufin Yi maka gata kanaji?
"Eh inaji dady.
Yauwa ai kasan gidan Alh Kabir mashi ko? Eh gaskiya kamar na sani Amma dai akwatanta min . Yayi mishi kwatance ya Kuma Gane inda ya bashi rafar dubu hamsin hamsin guda biyu ta dubu dari yace idan sun gama magana ya bada amatsayin kyauta
Ya dubi uban cikin Rashin Gane abinda yake nufi har dai ya tambaya
"Dady wa za a ba wannan kudin shi alh Kabir mashi din?
"A a kaje Zan kirashi zamuyi magana bashi zaka bawa ba ita wadda zaku yi maganar da ita zaka bawa amatsayin kyautar ka.
Ba don ya Gane ba ya taho don har ga Allah shi Bai kawo komai aranshi ba yayi nasarar Gane gidan ya Kuma tura me gadin yayi mishi sallama da alh Kabir
Atare suka iso inda Kabir kewa Anwar sannu da zuwa ya sauke shi a wurin da yake karbar Baki suka gaisa inda Anwar din yake sanar dashi dady ne ya turo shi
"Eh ai ya kirani bayan ka taho Bari in turo maka ita. Ya Mike ya bar Anwar sake da Baki Yana maimaita kalmar Bari in turo maka ita, to itawa za a turo mishi? Sai ya zuba ido kowacece itan
Fulani na zaune cikin ado da kwalliya tamkar me shiri fita party ta zubawa TV ido tana kallon India Wanda take son sanar da dadyn ta tana izuwa India don garin na burgeta sai Kuma gashi ya shigo Yana kiranta
Ta dago da sauri "gani dady
Yauwa dama bakone gareki Yana can masaukin Baki kije ku gaisa..........
"Bako Kuma dady? Ni yace maka yake nema?
Gaskiya dady bani yake nema ba sai dai in wrong address ya samu don Ni ban ba kowa address Dina ba.......
"Eh shi wannan din ma ba cewa ke Kika bashi ba Ni nace mishi yazo ku daidaita ke dai jeki idan kin dawo zamuyi magana.
Ta motse fuska don Sam acewar ta Bata ga mijin Aure a yanzu ba sai gashi Kuma ana son shigs Rayuwar ta
Tasa me aikin su talatu ta biyota da ruwa da lemu inda ta yi gaba don zuwa duba wannan marar kunyar da aka jajubo Mata
Ta taho tamkar tana Jin tausayin kasar fuskar ta murtuk Wai don kar yaga hakoranta ta shigo Babu ko sallama inda idanun su suka hadu su duka tamkar wuta taja su suka ji bugun zuciya Atare inda ta zauna tana auno mishi harara tamkar idanunta zasu fado inda talatun ta shigo dauke da tire Wanda ta jero ruwa da lemu tana Shirin ajewa humaira ta doko Mata tsawa.....
"Koma da ruwan Nan talatu wannan ba bako bane abokin Adawa ne.....
Talatu tayi dabar dabar don Bata fahimta ba inda kuma humaira ta Kuma daka Mata tsawar
"Nace ki koma dashi ko bakiji ba?
Da sauri talatu ta dauki tiren ta koma ciki inda ta fusknce shi shima Yana mamaki abinda suke nufi da turoshi inda atake ya gano gatan da dadyn yace yayi nufin yi mishi har yayi murmushi don yasan ba zasu taba daidaita wa da wannan marar mutuncin ba
Murmushin shi ya Bata haushi. "Au harma na Zama abin dariya agareka ?
"Uban me kazo yi agidan mu? Ko Nan ma kazo ne don ka sake bawa Yan sanda damar su kulle Ni ? Ta fada tana Kada kafa alamar masifa na Shirin tashi
Ya Kuma yin murmushi Wanda ke kuleta da haushi da takaici
"Kiyi hakuri Ranki ya dade............
"Kai bari fa in gaya maka dama inajiran Allah yasake hadamu don in Rama abinda kayi min
To Ni nan da kake gani wallahi uban kuturu ma ya Yi kadan bare na makaho da ba gani yake ba duk uban da ya daure maka.....
Ya gaji da Jin zagin da take mishi don Babu abinda ya tsana a Rayuwar shi irin zagi don haka ya cire hannu ya tsinke ta da Mari Marin da sai da taga giccin koriyar wuta
"Nafi karfin zagi agareki ko Zan zagu ba dai ga irin ki ba jahila marar tsinkaye wallahi ba Irina Mata ke zagi ba nafi zagi ga irinki dabba dake Kuma in har kece ake Shirin abinda aka shirya zanyi maraba da hakan ko don in koya Miki tarbiyar da uwarki Bata koya Miki ba
Ya Mike afusace ya watso Mata kudin da dadyn ya bashi ya Bata
"Gasu Nan ki kaiwa