Showing 27001 words to 30000 words out of 36278 words

Chapter 10 - Zan Fasa Kwai Part 1 Complete by Hadiza Bara'u Gidan Iko.txt

sauri ta toshe hanci tana tofar da yawu
"Haba gambo meye haka zaka shigo min da wannan shegiyar tabar me warin Kashin jaki? Don Allah koma waje ka zuke abinka ko dadin me kukeji acikin zukar hayaki hayakinma irin wannan da ko dadin Shaka Babu?..........."yi hakuri hajiya kan ne in Babu hayaki fanko ne Rayuwa ta in Babu mandular Nan akwai damuwa har Rashin lafiya nake kwantawa idan ban busa ta ba


Ya murtsuke sauran ya saka aljihunshi
"Yauwa to haka dai yafi don har kaina ya soma juyawa Nima ka sakani kwalewar Dole


"Yauwa hajiya Ashe akasi aka samu wurin aiki?
"Ai shiyasa nafi yarda da aikin ka yanzu Yaya za ayi kenan?


Ki bar komai a hannu na hajjya Ina me tabbatar Miki Nan da Rana irin ta yau wancan mutumin ya SHIGA UKU ke dai ku tanadi kudi don kin San Ni bana tare da tsautsayi ko kuskure bare wani Abu Wai shi sabani.......


"Karka damu gambo idan aiki yayi kyau ma za a biyaka kudi lunki uku Kai dai baje basirar ka kayi aiki me shegen zafi don ka samu sallama me kyau....


"Angama hajiya bani sati guda Daya kacal zakiji mugun albishir da haka sukayi sallama ya fito ya Kama gabanshi inda izzatu ta Kira Kabir take sanar dashi yadda sukayi da gambo mafiyas yace yayi daidai Kuma zai biya gambon lunki hudu ma ko biyar matukar dai aikin shi yayi sanadin fakuwar eng AK


Cikar satin da gambo mafiyas ya diba yayi daidai da kammaluwar aikin shi inda ya Kira Kabir yace yaje wurin hukuma ya sanar da akwai wani da yake kisan yaran mutane yau ya kashe wata yarinya ya sako a motar shi don haka su tashi Jami ansu da binciken motocin mutane ta haka ne tarkon zai Kama eng AK.


Aikuwa atake Kabir mashi kashe arna ya Kira wayar D P O ya sanar dashi abinda gambo mafiyas ya sanar dashi inda Kuma suka tashi Jami ansu aka soma checking point Wanda duk motar da zataje ko tazo sai me ita ya fito ya bude but sun caje komai kafin su bashi izinin tafiya


Bawan Allah eng abdukarim ya taho batare da sanin mugun qullin da aka hada mishi ba ya taho inda ya iske dogon layin na checking point Wanda ake ta bincike motoci shima ya bi layi batare da sanin shi ake son ganin baya ba ba Kuma Wai idan yajuya zaiyi tafiya ba. A a ganin baya na har abada inda ake son kasa ta rufe idanun shi................


Ubangiji kayi Mana sutura kar ka Bari makiya suga bayanmu 🤔
[5/22, 7:24 PM] Aunty Fauzah Yar Amanah: *ZAN FASA KWAI*




*NA*


*HADIZA BARA'U GIDAN IKO*




_Hakkin Mallakar na gidan iko ne_




*Page 33*


*_____________________________________*


*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation


*_____________________________________*








........Sannu ahankali akazo Kan eng AK Wanda ke kallon yadda ake binciken motocin mutane har akazo gareshi


"Ranka ya Dade muna son duba cikin motarka idan Babu damuwa.......


"A a Babu komai yallabai Bismillah ya fito Yana daga musu cikin motar suka bincike ba su samu komai ba sukace ya bude musu but


Ya kewayo ya soma kokarin bude but din Amma wani abun mamaki tamkar an sakawa but din kwado yayi yayi ya bude Amma yaki buduwa yayi iyakar kokarin shi Amma but ya ki buduwa ya dubi Dan sandan Yana sharce zufa
"Ranka ya Dade wallahi yaki buduwa karfen nasara kenan ban fa Dade da budeshi ba Amma yanzu da yake so ake ya bude yaki da zaku yarda sai ince muku babu komai aciki.............


"A a ranka ya Dade a dai bude don Rana tsaka aka tashe mu aikin Nan ..............
Ya Miko mishi key din motar


"Karbi to ka gwada kagani Ni dai na gaji gaskiya,
Dan sandan ya karbi key din ya soma kokarin gwada tashi sa ar inda ya turza sosai kafin yayi nasarar bude but din cikin sa a Kuma ya hango wani Abu me kama da jini na bin wani tsumma dake kudun dune yajawo shi ya warware inda yaga wani Abu me kama da hannun mutum inda kafar mutum ta fado Kuma wani Abu ya fado me kama da kokon Kan mutum


Eng AK ya zaro idanu Yana mamakin yadda wannan alamarin ke Shirin faruwa ta Yaya akayi wannan abin ya shigo motar shi


Inda Dan sandan yake kallon eng abdukarim da mamakin wannan abinda da ya samu acikin motar inda daga can baya Kuma cikin masu jiran go slow Kabir masi ya fito daga tashi motar ya karaso wurin inda shima yaga abinda ake mamakin gani amotar abdulkarim


"Wai abdulkarim Kaine da part din mutum a mota? Eh lallai da gaske kake har da tsafi kake hadawa shiyasa ka shiga gabana to Allah ya shirye ka ya fada Yana murmushi ya koma motar shi Yana kallo aka fidda motar eng abdukarim aka saka Mata key aka kulle shi Kuma aka wuce dashi sashen da zai bincike shi yayin da Yan sandan suka ci gaba da bincike motocin mutane


Da wata irin dariya Kabir ya SHIGA gida inda izzatu ta tarbeshi tana tambayar dariyar Nan ta lafiya ce?


"Ki tayani dariya don ya akan idona Dan banzan can AK ya shiga hannu shigar da ba zai taba fita a yanzu ba. Kai lallai na yabawa gambo mafiyas akan wannan aikin nashi Dole ne in mishi biya me kyau,


Izzatu ta kyalkyale da dariya tana fadin nasan gambo mafiyas ya fi da haka Amma ya akayi har hakan ta faru?


"Nima ban San yadda gambon ya shirya wannan makircin ba ya dai kirani ya fada min abinda Zan sanar da Jami an tsaro na Kuma fada musu sai gashi akan idona aka damke Dan banza da kafafun mutane har da hannu da kokon Kai
Amma Bari in Kira gambo mafiyas din yazo ya karbi kudin shi kuma inji yadda ya shirya wannan makircin
Ya dauko wayar shi ya Kira gambo ya ce yazo yanzu
Ai kuwa ba a rufe awa guda ba sai ga gambo mafiyas


Kabir ya daga mishi hannu alamar jinjina inda gambon ke murmushi
"Me gida kaga aiki ne Hala?
"Naga aiki gambo don akan idona aka damke Dan banza da kafafun mutane har da hannu da kokon Kai ya akayi ka shirya mishi hakan?


"Ai me gida na Dade ina binshi sannu ahankali har na samu sa ar ya bude but din na fakaici idon shi na saka mishi hannu da kafar shiyasa nace ka sanar da hukuma don ta fara binciken motocin ta yadda Za a kamashi kaga idan aka samu wannan abin a motar shi Dole za a shiga bincike kaga daga Nan sai sunan shi ya baci har ya Kai Babu me kallon shi bare sunan shi ya motsa


Izzatu da Kabir suka tafawa gambo mafiyas akan makircin shi Kabir kuwa ya bashi kudi masu yawa ya Kuma ce zai neme shi matukar wani zai yi mishi shigar sauri irin na ak to yanzu ne zai Kira shi don yayi mishi maganin shi da haka sukayi sallama gambo ya wuce Yana murna izzatu da Kabir ma suka wuni farin ciki sun jefa Rayuwar bawan Allah cikin garari....................
[5/22, 7:24 PM] Aunty Fauzah Yar Amanah: *ZAN FASA KWAI*




*NA*


*HADIZA BARA'U GIDAN IKO*




_Hakkin Mallakar na gidan iko ne_




*Page 34*




*_____________________________________*


*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation


*_____________________________________*








..........Bincike tamkar za a binciko yadda uwa tayi ciki har ta haife lamarin da yazo mishi da wani irin rudani har yakasa Gane inda mafita take bayan ta Allah


Yasha tambayoyi har na tashin hankali inda lamarin ya koma hannun C I D inda kuma suka rikeshi Wai sai sunyi bincike agidan shi


Wayarshi ma kasheta akayi don kar ya Kira wani ko wani ya kirashi,


Lubabatu da sukayi dashi ba zai wuce shida na maraice ba gashi har takwas da Rabi tayi mamakin abinda ya tsaidashi don ta San baya son yayi sallar magruba a waje
Ta jawo wayar ta ta doka mishi Kira Amma abin haushi matar Nan me zakin muryar tsiya na sanar da ita sai dai ta sake Kira lokaci na gaba yanzu Wai ba za a samu layin ba


Haka tayi ta jaraba Kiran wayar shi Amma ta kasa samun shi Dole ta hakura ba Kuma hakura tayi ba tunanin abinda ya tsaidashi da kuma Rashin samun wayar shi don tasan ba lafiya ba don ta San wayar shi Yana da caji


Ummita ta shigo Mami Ina Abba ya shige yau har yanzu Bai dawo ba?
"To Ni kuwa ina Zan sani ummita? Gaba na dai na faduwa don na fara tunanin ba lafiya ba............


"Mami bara na Kira wayarshi naji inda ya tsaya................
"Wayarshi Bata shiga na Kira na kasa samun shi Ubangiji yasa dai lafiya.


Hankali ya kasa kwanciya inda ummita tace zata Kira haj mama taji ko ta San inda abban ya shiga Amma lubabatu ta ce ta saurara tukuna
Sai dai har Sha dayan dare Babu wani Abu ko da na samun wayar shi ne Dole lubabatu ta Kira wayar haj Mama wadda har ta fara bacci ta jiyo karar waya ta farka tana tambayar lubabatu lafiya kuwa?


"Hajiya AK ne har yanzu Bai dawo ba Kuma duka layikan shi arufe shine ko ya fada Miki zaije wani wuri?


"Inna lillahi wa Inna ilaihir Raju un Wallahi lubabatu bai fada min ko zaiyi tafiya ba Kuma kince duka layi kanshi basa aiki ? Eh wallahi hajiya Amma Bari na Kira abokin shi zayyan ko ya san inda yaje da haka lubabatu tayiwa haj mama sallama ta Kira wayar zayyan din take tambayar shi ko yaji AK din zaije wani wuri Amma ya sanar da ita Bai sani ba Rabon shi dashi tun la asar.


Hankalin lubabatu da ummita ya tashi matuka gaya har dai bacci ya gagari idon su suka kwana salla suna fadawa me babbar rumfa me iko akan komai me tassarufin Al amura haka suka kusa kwana zaune inda Mubarak da Ahmed da Fatima ke ta sharar bacci abinsu saboda yarinta da kuruciya


Wayewar garin na laraba yazo musu da wani irin tashin hankali domin ko Jami ai ne daga hukumar bincike ta C I D suka diro gidan eng abdukarim inda lubabatu ta rude da Ganin su suka Fara yi Mata bayani


"Karki damu hajiya tambayoyi ne kawai Zaki amsa Mana da Kuma binciken da zamuyi agidan Nan saboda an Kama me gidan Nan da part part din mitane amota................


",Inna lillahi wa Inna ilaihir Raju un hasbunallahu wa Ni imal wakil Allahumma ajirni fee musibaty haza wa ahalufnee khairan minha.


"Abdulkarim din ne akewa wannan zargin? Ubangiji ka bashi mafita da mafitar ka........
"Kar ki damu hajiya bincike muke tukuna ba Wai an tabbatar ba abinda kawai muke so shine ki bamu hadin Kai mu gudanar da binciken komai zai daidaita da yardar Allah,
Ta share hawayenta da habar hijabinta ta soma amsa masu duk tambayoyin su har suka Kare suka shiga bincike gidan shima Allah da ikon shi ko wata kakkaifar wuka Basu samu ba da haka suka kammala sukayi Mata sallama bayan sun sanar da ita Yana hannunku


Kuka ummita keyi tamkar zata hadiye zuciyar ta inda lubabatu ma ta ke nata kukan sai yaran ma suka dauki kukan Babu Wanda yayi kokarin rarrashin wani inda Kuma haj mama ta taho gidan don taji ko AK din ya dawo don itama ta nemi wayar shi yafi akirga Amma Bata sameshi ba sai ta iske iyalan gidan sunata rizgar kuka


Hankalin ta ya tashi inda lubabatu tayi shiru tana korawa hajiyar bayani abinda ya gigita hajiya Mama itama ta fashe da nata kukan sai da kyar lubabatu ta rarrashe ta inda tace ta bari yanzu zasuje su ganshi


Suka hada mishi kayan kalaci suka tafi su duka inda hajiya Mama ke ta sharar hawaye inda suka taho har da talai itama hawayen takeyi


Sai dai duk yadda suka so ganin abdulkarim din lamarin ya ci tura Wai ba zasu ganshi yanzu ba sai dai ko Nan gaba an dai karbi abincin an Kai mishi Amma ganin shi sunce ba yanzu ba
Kuka hajiya Mama take tana rokon su su taimaka Mata ko hango shi ne tayi in ba zatayi magana dashi ba to su nuna Mata shi ta hango lafiyar shi..................
[5/23, 11:35 PM] Aunty Fauzah Yar Amanah: *ZAN FASA KWAI*




*NA*


*HADIZA BARA'U GIDAN IKO*




_Hakkin Mallakar na gidan iko ne_




*Page 35*




*_____________________________________*


*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation


*_____________________________________*








.........Kukan da hajiya Mama keyi ne yaba wani Jami I tausayi inda yake girmama girman kaunar uwa ga danta lallai duk Wanda Bai kyautatawa iyayen shi ba shine asararre duniya da lahira


Don haka sai ya ce abude musu su shiga aikuwa hajiya Mama tayi ta saka mishi albarka Inda yace ai albarkar ku muke nema mama duniya da lahira


Suka shigs inda suka samu AK lafiya kalau sai dai zaman wuri Daya kawai ne damuwar


Ummita ta makale shi tana kuka lubabatu da hajiya ma kuka suke inda yake ta Basu hakuri akan yadda kaddara ke saukowa bawa babu zato bare tsammani Kuma da anyi hakuri sai komai ya wuce .


Mubarak da Ahmed da Fatima ma rungume shi sukayi inda hajiya ke tambayar yadda abin ya faro ya Kuma sanar da ita kaf abinda ya faru.


"Ubangiji ya fidda ka kunya abdulkarim yau duniya wani baya so ko silifas ka sauya bare Kuma Ubangiji ya daukaka ka shikenan sai ashiga hassada da bin mutum ta karkashin kasa Amma Babu komai inda ADDU A ta zatayi tasiri akanka to Babu Ranar da zaka tozarta Kuma da ikon Allah kayi gaba gaban da ba za a iya cimma ka ba.............


Wani Jami I ya shigo yake sanar dasu Wai lokacin da aka Basu ya wuce sai dai suyi hakuri sai wani lokacin na gaba
Haka suka taho suna addu a da neman mafiita sai dai duk yadda suka dauki lamarin ya wuce Nan don kusan tsayin wata biyu Amma Babu bayanin komai Wai bincike ake duk yadda yan uwa da dangi ke shiga da fita Kan lamarin Dole aka saurara aka barwa Allah ikon shi


Agefe guda Kuma Kabir mashi kashe arna fakuwar eng AK ya dawo da martabar shi dominko yanzu Dole tasa ake bashi aikin kwangila ya Kuma yi yadda yake so don da gaske son Rai yafi yawa cikin aikin shi Wanda yake zaftare kaso arba in cikin dari sittin shine za ayi aiki dashi ko Babu nagarta inda Kuma izzatu da fulani suke warwasawa yadda suke so don yanzu duniyar dasu take damawa kudi suna ta shigowa asusun izzatu ya cika ya tumbatsa yayin da fulani Bata da sauran damuwa komai ta nema tana samu don haka suke Jin Basu da sauran matsala




Tsayin watanni shida Wai ana bincike inda daga karshe aka Mika batun gaban kotu don Alkali ya yanke hukunci


Zuwa kotun ma Bai zo da sauki ba domin ko wasu Bakin fuskoki ne suka zo suka bada shidar zur akan eng AK Wai dama Yan unguwa suna jitajita akan shi game da lamarin shi inda wasu ke ganin Yana da hannu a kungiyar matsafa don an Sha gano yaran da suka Bata agidan shi don haka kotu ta yanke mishi humunci irin Wanda yake yankewa yaran jama a
Sharri dai kala kala inda daga karshe Ubangiji ya kawo mishi dauki ta hanyar binciken da akayo gidanshi ba a samu wata shaida da zata nuna shi amatsayin me hannu a kungiyar matsafa ba haka Kuma duk tsayin lokacin ba akama shi da abinda zai alamta tabbatar zargin ba
Abinda dai akayi mishi an karbe duk abinda ya mallaka don biyan diyyar ran da ya kashe na Wanda aka samo kafa da hannu har da kokkon Kai


Haka aka sallamo shi ya dawo gida Inda murnar iyalai da Yan uwa ta kasa boyuwa acewar hajiya mama ita dukiya dama bakuwa ce Kuma raba bawa da arziki sai mutuwa inda take mishi nasiha da kar ya damu da abinda aka karbe mishi yanzu ne ma yake da damar sake samun wani arzikin fiye da Wanda yayi don ita hassada takin arzikice (Allah kajikan haj Saliha Zaria ita ke fada min hassada takin arzikice me hassada kuwa Yana cewa Allah Bai iya ba to Wanda yace Allah Bai iya ba ya kake zaton zai Kare?)


Bai damu ba ya Kuma amsawa hajiyar da cewa komai ya samu bawa da sanin Allah Kuma bawa Bai Isa kaucewa kaddarorin shi ba ko da kuwa zai shige akasa ne don haka ya riki hajiya da tayi mishi ADDU A Allah yasa ya cinye jarrabawar shi


Haka Yan uwa da abokan arziki ke ta zuwa yi mishi jaje kasancewar shi mutum me ALHERI kowa nashi ne inda Kuma yake matukar Jin kunyar mutane akan sharrin da aka kala mishi amma Allah shi zai wanke shi


Rayuwa tayi wata irin sauyawa agidan shi Babu abinda ya tsira dashi sai gida hatta da motoci an karbe sai Yan kudin da sukayi saura abanki


Kallon lamarin yake tamkar mafarki Wai yau shine a wannan bigiren Amma babu komai ya godewa Allah da ba imanin shi ya rasa ba sai ya karbi kowace irin Rayuwa da ta Zo inda ajalin shi ya riska Dole ya mutu Kuma Dole ayi hakuri


Sauyin da Rayuwa tazo dashi har ta Kai an cire su Mubarak daga makarantar kudi zuwa ta gwamnati don ba za a iya biya musu kudin ba inda takai abincin da za akai baka ma na neman gagara sai dai dayake lubabatu macece me kokari itake Kara karfafa mishi gwiwa akan yayi hakuri dai kar yayiwa Allah butulci da sannu bawa ke cimma Rabo da arziki
Haka Kuma da sannu kunkuru zaije inda jirgin sama yaje




Hajiya da Yan uwa da abokan arziki wadan da Basu zamo kaza me ci ta goge Baki ba suke ta hidimta mishi don Suma ya hidimta musu lokacin tasu bukatar Amma fa da yawan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login