Showing 6001 words to 9000 words out of 42941 words

Chapter 3 - BABBAN KUSKURE COMPLETE BOOK BY RASHEEDAH A KARDAM.txt

14 Jan 2025

1589

idonta sun kafe, hakan ya tabbatar masa da suma tayi, wuceta yayi ya nufi cikin gida, da fushinsa.
Falmi ko tana zaune a kan gado, takecin indimiee, wani gululun bak'in ciki ya k'ara tokaraansa, wannan wani irin iskanci ne?. A kan gado take cin abinci. "Mtsss yayi tsaki".
Cikin muryan shagwab'a tace"My Haiydar ka dawo?.
"Bayan tafiyanka yunwa ta dame ni da...
"Keee wa ya kawo min wannan bak'ar mai ido kamar na mage, gida na kuma don iskaci da rainin hankali, zanin dana kwanta da ke take wankewa.
"Mtss shikenan nikam nagama yawo, yarinyanan zata rainani.
"Ta gama sanin sirina.
"Shikenan nikam kin gama dani mtsssss.
Falmi tace"to ya kakeso nayi, ni kasan ko a gida ita, take min wanki. Hatta under wears d'ina ita take wankewa.
"Mtsss sai kiyi tayi ae.
Falo ya fito tare da bata guri, ganin zaman gun bazai masa ba, ya nufi d'akinsa cike da kunan zuciya.
Falmiko tana gama cin abinci a gun ta bar kwanon, ta sake kwanciyarta.
Indo ko ta dad'e a sume a gun, sai da ruwan da ya zuba ya iso jikinta, hakan yata daman farkawa. Hasken ranane ya haska mata ido, da sauri ta mik'e, cike da tsoro, tace"yanzu ta koma gidane ko ta shiga gidan?.
Wata zuciya tace"in kika tafi baki gama aiki ba, wani tashin hankaline. A hankali tashiga gidan d'akin da Falmi take ta nufa, poss d'inta ta d'auka, tafito falo da shirin ko ta kwana.
Haiydar ne ya fito, nan rake ta soma b'ari. Cikin fushi da muryan hargowa yace"ke mai kikeyi a cikin gidan nan da baki tafi ba?.
Kasa bashi amsa tayi masifa ya cigaba dayi, wanda hakan ya tashi Falmi ta fito. Haiydar janyo Indo yayi yace"ki fita min a gida kar na k'ara ganin k'afarki a gidan nan sai na karya ki.
Falmi tace"miye haka wacce zata min aiki zaka kora?.
"Kasan dai ni ban iya aiki ba ko?.
"Ita zata na mana girki da sairan aiki.
Haiydar ya kulu iya kuluwa, yace"kee miye aikin ki da baza kina aiki ba?.
"Ni fa ka ganni ko agida ruwan Lipton sai an dafa min.
Cike da ta kaici yace"baki isa ba to ni bana son girkin yar aiki. Ya wuceta fuuuu yayai d'akinsa qofar ya bako ya kwanta yana mai takaicin abunda ya faru, "daman haka halin Falmi yake?.
Falmi tana zuwa d'aki Mum d'inta takira, sai da ta sanar mata da komai.
Mum tace"yayi kad'an daga zuwanki zai fara fida halinsa to bai isaba wallahi.
"Yar'aiki kuma kamar ta zauna daram, dole Indo ta dawo cikin satin da zamu shiga, tunda baki saba aiki da kanki ba.
"Ki bar min komai a hannuna dole yayi biyayya.
Falmi cike da jin dad'i ta mata sallama, ta kashe wayar.




DEDICATED TO
AISHA MUHAMMAD
(MAMAN ABDUL SHAKUR)


๐Ÿ’•RASH LUVโœ๐Ÿป
[5/28/2016] Rash Karda ๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป
๐Ÿ™†๐ŸปBABBAN KUSKEREN๐Ÿ™†๐Ÿป
๐Ÿ™†๐ŸปDANA TAFKA ๐Ÿ™†๐Ÿป
๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป
๐Ÿ™†๐Ÿป๐Ÿ™†๐Ÿป

NA


ยฉRASHEEDAH .A. KARDAM.


Pg-51~55.


Indo tana fita, kuka take maras sauti, tana rokon Allah ya fitarta ya bayyana mata da danginta. Haka har ta iso gida, tana zuwa bata huta ba ta kama wasu ayyukam, da zatayi ma Hajiya, gashi sun k'aru sabida yan biki.
Falmi kuwa bata sake leko falo ba sai dare, da yunwa ya dameta, wasu matsatsun kaya tasaka. Haiydar na falo yana kalon tashar BBC WORLD ta shigo sai karairaya rakeyi, kalo d'aya ya mata ya kasa d'auke kansa, kasancewan bai da hak'uri. Take ma manta fushin da yakeyi da ita, ganin taki zuwa kusa dashi, tashi yayi a hankali yaje ya rikota, cikin rad'a yace"haba baby na fushin ne har yanzu?.
Sai da ta d'anyi farrr kafin tace"ni yunwa nakeji fa.
Hannu ta ya kamo sukaje dinning, asai yamusu take away. Nan yaringa bata a baki tana ci sai da ta k'oshi, ya sun kuceta sai d'akinsa, nan labarin ya canza.
Hajiya Fiddausi, sai datayi shige da fice, tasamo kan Haiydar, ya yarda Indo ta dawo gidan da zama tana musu aiki. Hajiya tace"ma Falmi ta bari sucika wara sai Indo tazo, a kwai abunda takeyi ne. Falmi badan taso ba ta amsa ma Mum d'inta.
Kwanaki sun tafi yau 3weeks da bikin Falmi, tasoma caza ma Haiydar kai, Haiydar duk lokacin da yazo da buk'atarsa Falmi tayi burus dashi, ko kuma in tabashi had'in kai sau d'aya, to ba zai k'ara ba. Haiydar har ya d'an rame.
Mum takira Falmi tace"to ba zama zakiyi ki zuba masa ido ba.
"Zaki fara tatsansa ne mu had'a jari.
Falmi tace"Mum to taya zan tatse sa da yawa bacin akwai komai a gida?.
"Mtss kee sai kace ba mace ba, bakisan tanda zakiyi ki samu kud'iba.
"Kina tambayansa mana.
"Ko kuma in yazo kwaciyan aure dake, kice sai yazuba kud'i ke bazaki iya ba.
Falmi tace"to Mumcyna hakan zanyi ma kawai.
Mum tace"yauwa yar albarka. (Kira gareku mata masu irin wannan galin, idan mazajenku sun zo muku da buk'ata, kuce sai sun baku kud'i, wannan BABBAN KUSKURE NE, aikata hakan haramci ne dan Allah akiyaye).
Da yamma Falmi tayi wanka tayi kyau sosai, kasancewan bata girki Haiydar ke sayo musu tayi zaman jiransa.
Haiydar ko da sallamansa ya shigo gida, tunda ya kyalo Falmi, ya had'iye wani yawu. Take yaji jikinsa ya mutu, dining ya wuce ya ajiye abinci da ya sayo musu, Falmi ko bata iya cemasa sannu da dawowa ba. Sai shine yace"ya gida fatan kin na lafiya?.
Sai da ta d'au lokaci, kafin tace"lafiya lau nake. 'Dakinsa yaje ya watsa ruwa ya saka 3quater da singlet ya fito, a dining ya ganta. Shima can yaje ya zauna, ya kaleta yace"ki d'auko plate da spoon kiyi serving d'in mu. Sai da ta ya tsina fuska taje ta d'auko ta dawo, har ta zauna yace"ruwa fa ko sai mun gama ci za'a d'auko?.
"Mtssss ta yi tsaki ni na gaji da yawan tashi.
Sai da suka gama ci, Falmi ta zo jikinsa ta zauna, don yau tanason ta fara wankansa, tunda tagane shi mai yawan bukatane, wasani tafara masa, wanda yasaka hankalinsa tashi, gashi kwana biyu Falmi ta hanasa kanta.
Shima biye mata yayi suka dulmuya, sai da taji zai wuce ta mike zubur, cikin dashashiyar murya yace"Falmi karki ki amincewa dani.
"pls ki taimaken una cikin yanayin bukata.
Kafad'a ta ya tsina tace"ni bazan iya ba.
Cikin yanayi tausayi tafara"pls My Falmi ki taimaken dan Allah ina buk'atarki sosai.
"Duk abunda kike buk'ata zan miki matsawan zaki bani had'in kai.
Sai da tayi wani murmushin mugunta tace"kayi alkawari ina fad'i abunda nakeso zaka bani?
Da sauri ya amsa mata"da eh! Zan baki koma miy ne.
Falmi tace"kud'i nakeso masu yawa.
"Haiydar jikinsa na b'ari ya tashi ya duba Aljihun wandinsa ba wani kud'i masu yawa, sai 10k ne kawai don d'azu a gun aiki, yayi sadaka da kud'ade'en da ke jikinsa, ma masu bara, duka dubu goma ta d'ebo yace"ga abinda suka rage min nan.
Falmi tace"nawane wannan don naga da alama basa da yawa?.
Haiydar yace"10k ne kawai bana da kud'i a jikina suna banki.
"Mtss mai dubu goma zasu min, asai baka shirya jin dad'i ba.
Haiydar kamar zaiyi kuka yace"haba Falmi ki taimaka ma halin dana ke. Zugunawa yayi akan gwiwansa, don bayason abunda zai b'ata mata rai.
"Mtsss to mai kake so na maka ne?.
Da rauri yace"ki taimaka min.
Ummmm"zan iya barinka kayi kiss a 10k amma fa da sharad'in bazaka wuce haka ba?.
"Eh na yarda in har zaki bari namiki d'an kiss d'in.
Okay!. Da sauri Haiydar ya taso yazo zai rungumeta, Falmi ta ja da baya, tana masa kalon raini wayo.





DEDICATED TO
AISHA MUHAMMAD
(MAMAN ABDUL SHAKUR)




๐Ÿ’•RASH LUVโœ๐Ÿป
[9/12, 8:17 PM] ๐Ÿฌ๐Ÿ›๐Ÿ’Salma๐Ÿ’๐Ÿ›๐Ÿฌ: ๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป
๐Ÿ™†๐ŸปBABBAN KUSKEREN๐Ÿ™†๐Ÿป
๐Ÿ™†๐ŸปDANA TAFKA ๐Ÿ™†๐Ÿป
๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป
๐Ÿ™†๐Ÿป๐Ÿ™†๐Ÿป

NA


ยฉRASHEEDAH .A. KARDAM.

Pg-81~85.


Cikin hanzari ta soma sauk'owa daga step d'in, don ko makawa babu, wannan muryan Lamid'o ne. Jikinta har b'ari yakeyi, da sauri ta isa falon, sam su Indo basu san, hajiya ta isoba. Sabida karatun da ke tashi a falon, gashi hankalinsu gaba d'aya, yana kan hotuna. Hajiya ta dad'e tana kalon Indo, cikin zuciyarta ko cewa take, "tabbas wannan jinin Lamid'o ne.
"In kuma ba haka ba to kaman yayi kama.
"To tayama za'ayi ace jinin Lamid'o ne, bayan Lamid'o da'akace ya mutu, har anga tokan gawansa.
Jikinta duk ya mutu, da kyar ta iya jan kafarta, zuwa cikin falon tare da yin sallama. Indo a hankali ta d'ago kanta karaf suka had'a ido, take k'irjin Indo ya bada rass! Rass!, kasa d'auke fuskanta daga kan hajiya tayi.
Cikin zuciyarta ko cewa take"wannan kamar matan, dana ke gani a photo da Umma tace na Baba nane.
"Sai dai wannan ta tsufa wancan kum yarinya ne.
"Hmm to nida bayida yan uwa ma.
"Kai inaga kama ne, kawai sukayi da matar.
Ajiyar zuciya ta sauk'e a hankali, ta sunkuyar da kanta, cikin girmamawa tace"sannu Mama anyini lafiya?.
Hajiya da takasa b'oye mamakinta a fili, sai da Hasna tace"Hajiya ana gaidaki ne fa.
Firgit ta dawo daga duniyar tunanin da ta lula, cikin fara'a tace"lafiya Aishatu".
"Ya aikin dai?
Indo kanta a k'asa tace"Alhamdulilah!.
Can sukayi shiru, don Hajiya tana jin wani abu gameda Indo, ta dawo mata da abunda ya wuce, shekara ishirin da d'oriya. Cikin dauriya hajiya tace"Hasna taci abincin kuwa?.
Cike da girmamawa Hasna tace"eh hajiya.
Hajiya ta kali Indo tace"Aishatu nina aika ki zo keda Husna.
Kan Indo a k'asa tana wasa da yan yatsun hannuta, masu kyau gasu dogaye gwanin burgewa.
Hajiya taci gaba da cewa"Aisha ina son ki d'auken a matsayin Mahaifiyarki, kuma wacce zata baki umarni ki bi.
"Aishatu! Ta kira Indo, cikin girmamawa Indo ta d'ago, karaf suka gad'a ido, take taji wani qaunar Hajiya ya shiga jikinta, kuma ta hango tsananin soyayyan uwa da d'a acikin kwayar idon Hajiya.
Indo ta amsa da"Na'am Mama!.
Hajiya tace"Aisha ina rok'on wani alfarma a gunki, kuma ina so kimin alkawari. Zaki amince da duk abunda na fad'a miki.
Indo cikin sanyin murya tace"Mama ae ke uwace.
"Duk umurnin da kika ban zan kasance mai biyayya a gareki, matsawan bai sab'ama addini ba.
Hajiya tace"Alhamdulilah! Nagode Allah ya maki Abarka Aisha.
Indo ta amsa da"Ameen ya Allah.
Hajiya tacigaba da cewa"Aisha inason na had'a ki aure da d'ana Haiydar.
Cikin rud'ewa ta d'ago fiskanta, don ta gaskata mai kunneta ke jiyomata.




DEDICATED TO
AISHA MUHAMMAD
(MAMAN ABDUL SHAKUR)


๐Ÿ’•RASH LUVโœ๐Ÿป
[5/30/2016] Rash Kardam ๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป
๐Ÿ™†๐ŸปBABBAN KUSKEREN๐Ÿ™†๐Ÿป
๐Ÿ™†๐ŸปDANA TAFKA ๐Ÿ™†๐Ÿป
๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป
๐Ÿ™†๐Ÿป๐Ÿ™†๐Ÿป

NA


ยฉRASHEEDAH .A. KARDAM.


Pg-86~90.


Cikin rud'ewa ta d'ago fuskanta, tabbas Hajiya da gaske take maganan, hmm cikin zuciuarta kam cewa take"anya Hajiya tasan mugun tsanar da Haiydar yamin?.
"Taya ma zanyi na auri mijin Aunty Falmi.
"Ina bazan iya ba Hajiya ki canza. Tana wannan tunanine ta ji muryan Hajiya tana cewa"karki damu nasan tunaniki Fatima ce ko?.
"To ita da kanta ta zabi hakan.
"Kuma shi Haiydar d'in ma ya amince.
Indo sam gani take kamar ma farki abunke faruwa.
Hajiya tace" ina fatan bazakiyi min jayayaba.
Indo haka kurum ta tsinci kanta da d'aga ma Hajiya kai ta amince.
Hajiya albarka tayi ta sa mata, tukun ta mik'e tace"barin hau sama zan yi wani abu. Hasna ne ta amsa da"to Hajiya.
Hajiya na tafiya Indo ta fashe da kuka sosai, Hasna ta dawo kusa da ita tace"Aunty Aisha kiyi hak'uri nasan Hajiya bazata tab'a cutarki ba.
"Kuma wataran zakiyi alfahari da aurenku.
Indo cikin kuka tace"Hasna kin san yanda Yayanki ya tsaneni kuwa?.
"Sam baya k'aunar ganina ina numfashi.
"Bazan iya kishi da Auntyn Falmi ba Hasna.
Hasna tace"hak'uri zakiyi komai zai yi dai-dai.
"Kuma batun Ya Haiydar ke zaki ja ra'ayinsa da naki salon.
"Amma sai kin dage kin kuma daure.
"Tashi muje d'akina in miki make-up, don tare zaku koma in yazo.
"Zan kuma baki wasu kaya kina kwaliya sosai.
"Ki bar zama ba gayu pls.
Hannu ta takama suka haura sama, Hasna ta wanke ma Indo kanta ta gyara ta sosai kamar ba ita ba. Wasu sababin kayanta, da bata saba ta bama Indo, tare da had'a mata kayan kwaliya mai yawa.
Falmi ko ita da Haiydar kokuwa suka sha, da k'yar ya rabata da kayan jikinta, sarrafata yasomayi son ransa. Falmi ihu take masa tana cewa"tunda ka amince ma Hajiya sai kaje gun Indo ta baka kanta, banda ni Falmi, tana kuka tana dukansa. Shiko gogan bai masan tanayi ba, sha'aninsa kawai yakeyi. Falmi ta wahala kam, don taki tsayawa, sai da ya d'ibi 2 hours masu kyau, kafin ya koma gefe yana maida numfashi, a hankali ya matso kusa da ita, ya rungumota yace"Falmi ina matuk'ar sinki, amma ke kike jawomana duk abunda suke faruwa.
"Mai yasa kike guje ma shimfid'ata?.
"Ina kiraki bak'ya amsa min why Falmi?.
"Kuma kinsan ni na kasance mai yawan bukata Fatima.






DEDICATED TO
AISHA MUHAMMAD
(MAMAN ABDUL SHAKIR)


๐Ÿ’•RASH LUVโœ๐Ÿป
[5/30/2016] Rash Kardam ๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป
๐Ÿ™†๐ŸปBABBAN KUSKEREN๐Ÿ™†๐Ÿป
๐Ÿ™†๐ŸปDANA TAFKA ๐Ÿ™†๐Ÿป
๐ŸŒป๐ŸŒป๐ŸŒป
๐Ÿ™†๐Ÿป๐Ÿ™†๐Ÿป

NA


ยฉRASHEEDAH .A. KARDAM.


Pg-91~95.


"Mtsss Falmi ta saki wani tsaki tare da mik'ewa tashiga wanka, sai da tayi wanka tana fitowa, kalo d'aya Haiydar ya mata, ya mik'e ya nufi bayi wanka yayi ya fito, yazo gunta yanyota jikinsa yayi, cikin salonsa na rikitarwa yake shafa bayanta, yace"haba my Falmi kinsan ba wata macen da zata tab'a sayen zuciyata.
"Ni nakine ke kad'ai kuma ina qaunarki.
Kalon banza ta masa cike da masifa tace' kai Haiydar kasani nayi danasanim aurenka ni Fatima.
"Gashi yanzu ka jamin kayan raini.
"Wacce nake gani a k'ark'ashina, wai ita zata dawo kishiyata.
"In sam ba zai yiwu ba ina.
Haiyadr cikin muryan lalashi yace"kinsan bazan tab'a had'aki da wata ba.
"Aure ai kamar an fasa tunda baki so.
Hararansa tayi tare da d'iban kayanta ta fita.
Haiydar ko mai ya sha, tare da saka kayansa, ya d'auki key d'in motarsa, don zuwa amsa kiran Hajiya da bata hak'uri ta janye k'udirinta na batun auren Indo.
A gidan su Hajiya kuwa, Hasna ta wanke ma Indo kai, ta gyaramata tare da busar mata shi da dryer, alwala sukayi suka gabayar da Sallah magriba, suka jira sai da akayi Isha'i nan ma sukayi, Hasna tace"Aunty na zo ki zauna gaban madubi kiga wani abu.
Ba musu Indo tazo ta zauna, Hasna ta gyara mata fuska, ta gyara giranta, ta fara mata kwaliya, ni dai Rash ina gefe ina kalon ikon Allah, don naga shafe-shafen da goga wancan yayi yawa. Indo tace"kai Hasna nikam abun ae zai min yawa.
Hasna ta k'yalk'yale da dariya, tace"Aunty na ki tsaya ke dai kiyi kalo kawai.
Murmushi Indo tayi. Hasna tayi kealiya ma Indo, tare da d'auko mata, wani atamfanta riga da skirt, mai kalan ja da bak'i. Indo ta karb'a ta shiga bayi ta saka, tana fitowa Hasna sai murmudhi take, Hasna tace"zauna ki gani.
Indo tace" oh ni kam Hasna har yanzu duk a make-up d'inne haka?.
"Ina zani da kwaliya bacin yanzu bacci zanje nayi.
Hasna tace"Aunty bazaki gane bane.
Hasna ta d'aura mata d'an kwali, ta mik'o mata flat shoe, shima kalan ja da bak'i, sai gyale shima ja da bak'in, yana da stone farare, sai haskawa sukeyi, ne sa kad'an Hasna takoma, tana kalon indo, cikin muryan farin ciki tace"wooow My Aunty na you look so beautiful. Muryan Hasna danaji yasa ni Rash na d'ago da sauri, bansan lokacin da wayata ta sub'uce ta fad'i ba. Ba abinda na furta sai kalman"tsarki ya tabbata ga Ubangiji daya k'agi wannan k'yak'yawan suran.
"Hmm masu karatu kuyi Imagine d'in Indo a cikin wannan shigan, ya kuke gani zata haska?.
Hasna ta fara yabon Indo, tare da d'auko wayarta tashiga d'aukarta photo.
Haiydar yana shigowa gidan su Hajiya, d'akinta ya nufa, da sallama ya shiga, ta amsa masa, bayan ya gaidata, Hajiya ta fara masa nasiha mai ratsa jiki, sanan tace"kar kuma naji kasake cewa kalman da za'a fasa aurenka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login