Showing 27001 words to 30000 words out of 30354 words
Chapter 10 - MASARAUTAR GOBIR Book Complete Writing by Mrs Sadauki .txt
sauke labule daidai kuma lokacin ɗaya daga cikinsu ya ɗan tada kai tsabar tsoro har sai da na dafe zuciyata.Ido uku ne da shi,biyu irin na mutane ɗayan kuma can tsakiyar goshi ban ida shiga firgici ba sai da na ga wani abu na fitowa ta idon ya na cin abinci nan na fahimci shine ke fitar da gurnanin.
Da sauri na saki labulen ina mai tambayar kaina ,“ina kuma Bilal ya kwaso matsafan nan?” shiru na yi sai yanzu na gane wato shi yasa anty tace suka ƙi cin abincin sai ita da mijinta suka ci saboda su idonsu uku ne biyu na nan duniyar ɗayan kuma na ɓoyayyar duniya.
Tunani na soma yi mine ne dalinlinsu na abota da Bilal tabbas akwai wata a ƙasa,tunanin nawa ne ya tsaya cak jin ɗaya daga ciki ya na tambayar anty Sailuba “ni kam ku nawa ne cikin gidan nan? Ko kun samu ɗan hutu ne ?”
Ba ta kai ga basa amsa ba shi ma wani ya ce “ƙamshin Gombowa ”
“Tun shigowar mu na ji ƙazinin ɗan ƙabilar Gombo”
A karo na biyu kenan da na ji kalmar sunan Gombo ɗin nan,a hankali na ƙara buɗe labule ina leƙo cikin rashin sa'a hasken idona ya sauka a rigar ɗaya daga cikinsu,raɗam ya fito kamar fitilar nan da aka yi yayi mai hasko hoton Obama.Ɗayan ne mai face da wanda hasken idona ya sauka kan rigarsa ya juyo baya,muka haɗa ido da shi .........
Nan na kawo ƙarshen free page duk mai son ci gaba zai biya 500 via 2670215530
ZULFAU YAHAYA Ecobank sai ki turo shaidar biya ta WhatsApp +22795045822 ko kuma katin MTN ,ƴan Nijar kuma carte moov ko airtel ta 500f.
NB:Daga lokacin da book ɗin nan ya zama complete 800 ne.
29 jully 2024
MRS SADAUKI ce 🌚
[09/09 à 10:39] MRS SADAUKI 👑M~SHURAIM🤍: ```MRS SADAUKI💫✍️```
My book is only 500 via
2670215530
ZULFAU YAHAYA Ecobank,ko kuma katin MTN na 500₦ ƴan Nijar kuma carte airtel ko Moov ta 500f sai a turo da shaidar biya ta WhatsApp +22795045822,in kin san ba ki biya kuɗin karatu ba kar ki karanta min littafi domin mallakina ne .
*FCWA ☀️*
11-12
https://chat.whatsapp.com/FMimfpwTVDDBjZmDZw2Uhs
*Inda muke turo available products din mu don ki gani, ki zaɓi wanda kike so sannan ki siya ko ki tallata kema kisami naki*🥰
*Kayan mu order muke daga ƙasashen waje, foreign ne masu kyau da quality*
*Duk abinda mukayi posting available ne, daga kin siya za'a turo miki abinki ba ɓata lokacin jira*.
08032350261
😍😍😍DAMARKUCE LOKACINKUNE MUN RAGE FARASHI SOSAI DAN KUMA KUSAMU KOMAI DA KUKA SANI ZAKU SAMESU KWASHA KWASHA ARHA GARABASA 🤝🤝🤝KUMA DUK INDA KIKE KAYANMU ZASU SAMEKU CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH
Da sauri na saki labulen ina jin zuciyata na dukan uku-uku,ina nan daga tsaye dafe da saitin zuciya na ƙara jiyo amon muryar su “ zarginmu ya zama gaskiya fa mine ne abun yi?”
“ Ta fito kawai mu gane wa junanmu tun da duk bisa hanya ɗaya muke”
“Hhhh ai kuwa dai ƙila ita ma da nata plan ɗin a kansu”
Shine abin da na ji su na faɗa ,amma na yi mamakin haka a gaban sun anty Sailubar suke faɗar haka ko dai sun tashi ne? Don gusar da zargina sai na ƙara kama labule don na sake leƙawa,ina buɗe wa na yi tozali da ƙaton ido manne a jin ƙofar ɗakin nawa ban san lokacin da na fasa wani matsanancin ihu ba da ya karaɗe duk illahin gidan.Ruwa ne suka soma ɓulɓulowa su na cika gidan ga baki ɗaya hatta cikin ɗakuna.
Tuni siffata ta canza zuwa kala biyu bindin kifi ya fito min,ruwan su suka ja ni izuwa falo.
“Waooo!” suka haɗa baki su na kallona sai nitso nake ina kaɗa bindi cikin ruwan,sai wannan lokacin kuma na ankare anty Sailuba da mijinta Bilal sai bacci suke yi kamar waɗanda ba su da rai.
“ Azo ka na gani abin da nake gani?”
“Yes Musty ina gani”
“Naser kai fa?”
“Ina gani ni ma ” duk suka tsoma bakinsu a nan ne na san sunan kowa daga cikinsu.
Musty ɗin alamun ya fi su ƙarfi da surutu ya dube ni da kyau ya ce “ muna so mu san plan ɗin ki akan wannan ahalin?”
Idona na buɗe ina kallonsa waɗanda har yanzu ba su bar mugun hasken nan ba,“ku fara sanar da ni naku plan ɗin tukuna” na faɗa tare da dukan ruwa da bindina suka bada wani bacaaal.
Suka ƙara kallon juna kafin shi Musty ɗin ya ce “ ki yi mana alƙawari za ki taimake mu”
Na juya baya ina mai cewa “ tun da ba za ku faɗa ba kun ga tafiyata”
“Tsaya mana ,Musty kawai mu sanar da ita zai fi.Muna zuwa nan ne don jawo hankalin Bilal ya shigo a tsagenmu amma mun gagara yin galaba kansa,ruhinsa na da mugun ƙarfi shi da matarsa”
Na juyo ina duban Naser ya faɗa wanda na fahimci kuma duk cikinsu ya fi sauƙi don ya na da tsoro.“ Ta ya aka yi duk ƙarfin ikon ku amma suka fi ƙarfin ku?” na jefo tambayar ina kallon Naser ,sai da ya ɗan yi shiru kafin ya ce “ kin san su na da yawan addini su na salloli kan lokaci ”
Na lumshe idona ko da ya zo nan da zancensa,ina jinjina wa anty Sailuba wacce ta yi riƙo da Addini duk matsatsin aikin shago bai hana ta yin sallah muddin lokacinta yayi na fahimci hakan tun lokacin baya da nake wuni wurinta kafin na soma yi wa anty Hinda aiki.
“Na san ke ma shine dalilin da ya hana ki cin galaba kansu duk da ba mu san ke mi yasa kike bibiyar rayuwarsu ba” Azo ya faɗa ya na matso wa kusa da ni.
Wani irin zafi ne na ji gangar jikinsa na fesar wa duk da kuwa ina cikin ruwa,na ce “ ta ya aka yi ka san ina bibiyarsu?”
Yayi murmushin gefen baki ya ce “ in ba haka ba mine ne zai fito da ke daga can cikin asalinki ki zo nan? Tun daga Gombo kike sannan a yadda kike Siren kika juri zama a wajen ruwa kawai don ƙudirin ki.Faɗa mana mine ne shi?”
Ban da lokacin tunani ,na kuma fahimci ko masu ganin abin da normal mutane ba su gane ba komai ne suke da sanaya a kai ba.Ba don haka ba tabbas da za su fahimci ban zo nan da niyyar cutar da su anty Sailuba ba,amma don kar su raina mini fiƙirata sai kawai na ce musu “ yanzu dai kawai mu zama ƙawaye daga baya duk za mu tattauna akan abin da ya shafi duniyarmu,tun ɗazu kun saka bayin Allahn nan bacci ya kamata ku tashe su haka”
Azo yayi wata dariya ya na mai cewa “ da alamu fa Siren tausayin su kike”
Na girgiza kai na ce “ ko ɗaya,kawai ban so su zargi wani abu ne”
“Kuma kin yi gaskiya komawar ki ɗakin ki”
“Kafin nan ta janye ruwan nan da ta cika mana ɗaki da su”
Murmushi na yi ina mai kai hannu ina taɓa Munduwar wuyana haɗi da kallon ruwan da ido ina basu umarnin su koma,a haka na shige ɗakina ni ma tuni ruwan kuma sun ƙwafe tsab .Na kwanta kan shimfiɗata ina kallon rufin ɗakin ina cewa “ karo na biyu kenan da na ji sunan Gombo,shin ina ne ? Wace ƙabila ce?” ban ida rufe bakina ba kafin wani girgije ya danno kai tamkar shine rufin ɗakin.Munduwar wuna ta soma zuƙo girgijen nan a hankali ya soma tarwatsewa na zamar haske mai kamar mai sai kuma ya shiga radadowa ina fasa ƙirjina ya na shiga “ Mamaaa!” na furta da ƙarfi saboda amon muryarta da ya cika mini kunnuwa ,yayin da kuma hoton siffarta wacce take flou ta bayyana gare ni ga wani Baby a hannunta kafin ta aje shi tsakiyar daji ta ce “ sunan ki Sarah !”
Hawaye suka zubo mini kan kumatuna,na samu abu na farko daga cikin tarihina wato jefar da ni mahaifiyata ta yi sai dai ban san dalilinta na yin haka ba.
Daga can falo ina jin su Musty na yi wa su anty Sailuba sallama,babu jimawa kuwa ta shigo ɗakin ta na mai kiran sunana “ Sarah taso ki yi kallo baƙin sun tafi” na girgiza mata kai saboda ba na cikin yanayi,“ fushi kika yi don na hana ki fitowa?”
Kai na girgiza tare da tashi na zo na rungume ta da ƙarfin tsiya ina mai cewa “ anty Sailuba ina son ganin Mahaifiyata,ina jin kewarta.Ina son jin soyayyar nan da ke tsakanin uwa da ƴa amma ni wurin Kaka Anaba na taso wacce babu alaƙar jini ko ɗaya a tsakanin mu”
Anty Sailuba ta riƙe ni ta na cewa “ haba Sarah kar ki sa na yi kuka mana,kin ga dama yanzu haka ina cikin wani yanayi.Sannan wa ya faɗa miki Kaka ba jininki ba ce,ƙila ta faɗi haka ne don ta hora ki ”
Na sake ta na ɗan ja baya ina mai girgiza kai na ce “ a'a gaskiya ta faɗa don yau ɗin nan aka nuna min lokacin da Mamana ta jefar da ni a cikin jeji”
Anty Sailuba ta jefo min wani kallo “ don Allah kar ki sa na fara jin tsoron ki,wa ya sanar da ke to?”
Shiru na yi don ni kaina ban san ya ko wane ne ba.
“ Kin ga sai da safe bari na je na yi karatu ” har ta kai bakin ƙofa na tsayar da ita ta hanyar kiran sunanta,ta juyo na ce mata “ ki ƙara dagewa da addu'a haka ma mijinki” ba ta ce komai ba ta fice.
Sailuba
Ita tun farkon zuwan su Naser gidanta sam ba ta so haka ba,sai dai babu yadda ta iya saboda su ne manyan abokan mijinta duk da ba ta san su ba kafin aurensu da Bilal amma a yanzu bai da wasu bayan su.
A duk lokacin da za su kawo musu ziyara haka za ta kwana cikin kasala da mugayen mafarkai,sai dai ba ta taɓa alaƙanta hakan da su ba abu guda kawai ta riƙe shi ne addu'a sannan ta na yin sallolinta kan lokaci wannan kuma na ɗaya daga cikin turbar da Bilal ya ɗora ta don shi Ustaz ne ya na da karatu sosai saɓanin Sailuba da ko izo ɗaya ba ta da.
Yanzu bayan fitar su Musty haka kawai ta ji ta na son yin tilawar karatun da ta iya,Bilal ya sanar da ita zai wuce makarantar da yake bada karatu wannan yasa ta shiga ɗakin Sarah don ta zo ta yi kallo.Sai da ta yi alwala sannan ta soma karatun fatiha,falaqi da nasi zuwa suratul Masad.Sam ba ta raina karatun da take da haka bayan ta gama ta shiga yin addu'o'i na neman tsari da kuma neman buɗi.
A can gidan Hinda kuwa hatta salloli ba su sa sun zubar ruwa a jikinsu ba, ƙememe suka bari ta wuce su.Sai faman saƙa da warwara suke,Sharifa da ta gaji da abun ta ce “ Mama ina ga kawai mu je gidan Kaka ta bamu magani tun da dama aikinta ne bayar da magani”
Hinda ta ce “ wa ya sani ma ko ita ce ta yi mana ture? Kin ga babu inda zan je in zuwa za ki yi ban hana ki ba sai kin dawo”
Sharifa ta saka kuka ta na yi “ shikenan in na mutu sai ki huta”
“ Tashi mu tafi tun da kin fara jawo mana mutuwa” cewar Hinda ta na mai zarar mayafi, Sharifa ma haka .
Gidan Kaka suka nufa sai suka tarar da shi a rufe suka shiga bubuga shi , Sharifa ta ce “ dubi langa-langar ƙyauren nan wai shi ne ya rufu ruf ko rawa bai yi”
Hinda ta ce “ banza wa ya faɗa miki normal ƙyaure ne? To aljanu ke rufe shi ” sai kuma suka ci gaba da bugawa.
Kaka wacce ke can ɗaki ta na shagali ita da ƙawayenta bokaye da suka kawo mata ziyara ta ce “ ku na ga zan je na ga ko waye ke bugun ƙyaurena”
Ɗaya daga cikin tsoffin ta ce “ kika sani ƴar tsintuwar ki ce ta dawo” sai duk suka kwashe da dariya,Kaka ta ce “ ai na bar zama da ita,ina dalili ta min kisan gilla tsakar dare” sai kuma ta je ta buɗe gidan.
Hinda ta ce “ gafara dai Kaka,ki daɗe ki yi ƙarko akwai wata bayan ke ne mai bayar da magani ? Kai babu guda ɗaya ce rak Hajiya Kaka mai abun ban mamaki,mun zo ne a bamu magani sakamakon wata cuta da ta shafe mu”
Kaka ta basu wuri suka wuce sannan ta ƙara jan ƙyauren ta rufe,ta yi musu iso suka zauna kan tabarma.Kayan aikinta ta fidddo ta ɗora fitila aci balbal sannan ta soma wasa da ƴaƴan wuri,tsawon lokaci ta na yi kafin ta ɗago ta dube su ta ce “ duk wanda ya ce muku zai iya karye asirin nan da aka yi muku kawai yaudarar ku ce zai yi ya ci kuɗin ku,sihiri ne wanda ba a cika samunsa ba a wannan duniyar amma ku jira na kira ƙawayena mu ji mi za su ce” Kaka ta kira su kuwa,tsofi ne biyu har sun fita tsufa abin da Kakar tace su ma shi suka faɗa kafin ɗaya ta ce “ Anaba wannan ai sihirin ruwa ne ,doli ya na da alaƙa da wanda yake aiki da Mamy Water ko kuma sam wanda ba nan duniyar yake ba ” ɗayar ta cabke zancen da “ ko kuma duk duniyoyin biyu mabanbanta ya na rayuwa cikinsu ba”
Furicin nan ya haskawa Kaka fitila har ta fahimci tabbas aikin Sarah ne,ta gyara zama ta ce “ Hinda mu ga kuɗin da ke gare ki zan yi miki aikin nan don yanzu na fahimci tushensa ”
Ba tare da wani tunani ba Hinda ta kwance kuɗin da ke ɗaure da ga haɓar zanenta ta bai wa Kaka,ƙawayenta suka shiga tambayarta “ wai mi za ki yi? Anaba kar ki jefa kan ki cikin masifa aljanun ruwa ƙarfi ne da su sun fi waɗanda muke aiki ƙarfin iko”
Kaka ta ce “ babu wani nan ku dai ku jira ni yanzu na dawo” ta faɗa tare da ɗaukar wata ƙwarya ta fice,ba ta zarce ko ina ba sai gaɓar ruwa.Ƙwarya ta aje gabanta sannan ta soma wasu suratai daga ƙarshe ta jefa kuɗi cikin ruwan,canɓallll sautin faɗawar kuɗin ta fito kamar ƙyaftawar ido kuwa ruwan suka fara tashi sama su na hargowa kafin wata murya ta soma yi wa Kaka magana “ faɗa mana mi kike da buƙata?”
“ Magani domin warkar da wasu”
“Ai kin san da cewa komai ya na da farashi ko?”
“Na sani a bani maganin” Kaka ta faɗa ba tare da ta tsaya tambayar mine ne farashin ba,ƴar ƙwaryar da ta ajiye ce ta soma cika da ruwa tsulululu har sai da ta cika tab kafin Kogin ya bar motsi.Cike da murna Anaba ta ɗauki ƙwaryar ta koma gida,da kanta ta yi wa su Hinda wanka abun mamaki kuwa sam ba su ji ƙaiƙayi ba.
“Mun gode sosai Kaka Anaba haƙiƙa ke shararriya ce kuma gwana wurin warkar da cuta” Hinda ta faɗa kafin ta ja hannun Sharifa su koma gida.Sai a lokacin suka samu suka yi sallah,da suka zo kwanciya bacci suka kasa saboda uban zafin da suka ji sai zufa suke .Wanka suka yi,Sharifa ta kunna masu fanka a haka suka samu suka yi bacci,sai dai abu kamar wasa sai gumi ya jiƙa shimfiɗar tasu.Da farko Hinda ce ta soma tashi ta sake yin wani wankan kafin sharifa ita ma ta yi,sam ba su kawo komai a kansu ba kawai sun ɗauka yanayin garin ne ya ɗau zafi.
SARAH
Da tunanin Mamana na samu bacci ya ɗauke ni,ko minti biyu ban yi ba tsinci kaina can ƙarƙashin ruwa ina wasa da su cike da nishaɗi.A inda nake ƴan mata ne kewaye da ni su na min taɓi kowacce da bindinta na kifi ga dogon gashi sannan fuskokinsu masu kyau ne farare tas saɓanin ni da ke baƙa ƙirin.Na tsaya da wasa da ruwan na ce “ ya aka yi dukkan ku farare ne amma ni kuma baƙa ?”
Wata murya ta namiji ce ta bani amsa “ saboda ke Mamarki kika ɗauko” da gudu na ga ƴan matan na tserewa su na cewa “ ga sarki nan ! Ga sarki nan!”
Na juyo muna kallon juna da wani kyakkyawan namiji zai kai a ƙalla shekara arba'in da biyar,kansa ɗauke da kambun sarauta na zinari haka ma daidai damatsansa an yi masu ado da wani ƙaton awarwaron zinari.Wuyansa kuwa sarƙar Munduwa ce irin tawa sai dai tasa ta fi tawa girma ,ya zo kusa da ni ya jawo ni ya na shafar gashina idonsa ne suka ɗau wani haske ya dinga juya su ya na umarta gashina ya ƙara tsayi sai gashi kuwa gashin nawa ya zama dogo har bisa gadon baya .Sosai na ji daɗi,cikin murna na ce “ wane ne kai?”
“Ni ne Babanki Sarah ” ya bani amsa tare da ɗora min wata gyanɗama a baki ya ce “ sha! Ruwan ƙarfin iko!” ban musa ba na soma sha,shi kuma ya na shafar gashina ya na mai ci gaba da cewa “ barkar da ranar zagayowar haihuwar ki” sai ya cire kambun sarautar kansa ya ɗora min .
“Sarah? Sarah keeee!” muryar anty Sailuba ta tashe ni daga bacci,a hankali na ware idona sai na ga ɗakin da duhu.
“Ƙwan lantarkin ɗakin ki ya ƙone sai an saka sabo ,tashi dai ki yi sallah lokaci yayi” sai kuma ta fice.
Zaune na yi kan shimfiɗa mafarkin da na yi ya na dawo min,ina nan zaune sai na ga ɗakin ya cika da wani mugun haske kuma .Ban yi wani dogon tunani ba na fahimci daga inda hasken ke fitowa,na kai hannu na laluba kaina .Wani irin taushi da santsi ne suka ziyarce ni,wato gashina ya zama dogo irin na turawa hatta Kambu sarautar da na gani a mafarki ga shi a hannuna.Juyasa na soma yi kafin na soma shafarsa,ƙaton jan dutsen da ke tsakiya ya fitar da wani farin haske hakan ya bayyana mini kyakkyawar baƙar fuskata.A karon farko da na fara ƙarewa kaina kallo,ina da doguwar fuska mai siririn hanci idona sun so su yi shige da na mage,gashin girata da na idona su na da yawa sosai yanzu kuma ga wani ƙarin