Showing 9001 words to 12000 words out of 49794 words

Chapter 4 - GOJE SADAUKI UMAR RETURN NA BINTA UMAR ABBALE .txt

har yanzu matarka bata kaunata, meye laifina ? me kuma nayi mata? haihuwa dai Allah ke bayarwa ba wani ba, nima ban cire rai ba."


Tausayinta ya rufeshi, sassauta murya yayi yace." Maijidda kada ki sanya damuwa a ranki nida na aureki nafi kowa sanin halinki babu wanda zai kawo min jita-jita a kanki na dauki maganarsa, maganar haihuwa kuma kada ki cire tsammani, zaki haihuwa da izinin Allah, bayan haka kuma baki da shamaki da zuriata zaki iya yanke hukunci akansu ba tare da na daga kai na kalleki ba."




Gabad'aya suka kalleshi a lokacin da yake wannan maganar, Aysha gaza hakuri tayi tace." Ba zai yuwu ba ranka ya dade ana duba nagarta da cancanta kafin a yanke hukunci babu wani d'a da zan haifa na amince ya dauki wannan matarka taka a matsayin me kaunarsa duk mutumin da ya fito da kiyayyarsa a sarari a kanka be kamata kayi rayuwa dashi ba.


Gabadaya sai suka rasa inda maganarta ta dosa, ta mike tsaye tana gyara lifayar dake nade a jikinta, sunkuyawa tayi da fadin." A tashi lafiya." Bakinsa ne ya mutu kawai ya bisu da kallo a lokacin da suka kama hanyar fita, Ya girgiza kai yana jimanta al'amarin wato dai har yanzu Safa taki zama cikkakiyar mai 'yanci a gidan auranta, tana biyewa Aysha suna zuwa har gabanshi suna masa rashin kunya, to babu shakka zai sa kafar wando guda dasu.




***********
Washe garin ranar da ciwon ciki ya tashi, yaransa suka kewayeshi suna masa sannu, yana kwance idanuwansa a lumshe yake amsawa, daya daga cikin rayan nashi, yace." Allah ya taimaki *Mai dawa!* ga magani na had'a maka." A hankali ya bude idonshi ya dora kan 'kwaryar maganin dake hannunsa, ya mutse fuska yayi ya mayar da idonsa ya rufe da fadin." Alba ka ajiye wannan maganin ka matsa min lemon tsami guda shida."
Da sauri yace." An gama ranka ya dade.


Ya dan sauke numfashi tare da sake rintse idonsa shi kadai yasan irin ciwon da marar shi ke masa.


Alba ya k'araso gurin cike da bin umarni yace." Allah yaja zamaninka ga abinda ka bukata.


Ba tare da ya bude ido ba yace." Nagode Alba kuna iya tafiya Allah ya bada sa'a." Suka amsa da ameen kafin su bar gurin sai da sukayi yi masa kirari kamar yanda suka saba.




Kimanin minti biyar da tafiyarsu ya tashi da kyar, ya jima yana yamutse-yamutse kafin ya dauki matsatstsan lemon tsamin ya shanye tas, ya ajiye ya koma ya kwanta, yana danne saman cikinsa.




Tayi mamaki da gari ya waye be zo ya dubata kamar koda yaushe ba, kawai tashi tayi a bacci ta samu ruwa cikin kwarya da asuwaki sai manya manya ayaba da mangwaro a gabanta.


Ta wanke bakinta da fuskarta, dama can ibadah bata dameta ba domin data dameta da duk yanda za tayi sai tayi ta gabatar da sallolin da suke kanta.



Yunwar da takeji bata tsammanin Ayaba da mangwaro zasu kawar da ita, taja tsaki tana harare-harare a gurin da babu motsin kowa sai ikon Allah.


Jikinta ta duba tayi fututu! fatar jikinta duk ta bushe tayi datti! ta dubi qunar da duk ta bushe tana mata kaikayi, ruwan hawaye ta goge tana tunanin jin dadi da irin rayuwar da take ciki amma lokaci kankanki rayuwa ta juya mata baya.


Kullum idan za ta kirashi da *'Barawo* zai kalubanceta kan cewa shi ba *'Barawo!* bane to idan ba haka ba waye silar zuwanta wannan kasurgumin dajin."?


Ta girgiza kai cikin qunar zuciya ta kudiri aniyar irin rashin mutuncin da za tayi mata huce takaicinta.




Ayaban kadai ta iya ci ta dauki kwaryar ruwan ta shiga tsakanin bishiyu kayanta jikinta ta cire tas ta wanke jikinta, gurin wankan ta jike rigar data zame mata garkuwa, bata damu ba kawai tasa breziyya ta mayar da wandonta ta fito a haka, taja ta tsaya tana dube-dube a gurin.


Babu motsin mutum sai kukan tsintsaye da alama yau ma sun fita sun barta a dajin ita kad'ai.


Ajiyar zuciya mai zafi ta sauke taja tsumman zanin ta dan daure tsakain cinyoyinta kafin ta nemi saman wani kuttuturun icce ta zauna tana tunanin halin da iyayenta ke ciki na rashinta, ta san mahaifinta sai yafi kowa shiga tashin hankali rashinta a kusa dashi.




Ya kai minti arba'in cikin halin ni 'yasu kafin Allah ya sassauta masa, ya mike zaune da kyar! duk da halin da yake ciki hankalinsa na kanta burinshi ya tashi yaje ya duba halin da take ciki.


Ya mike babu kuzari a jikinsa, kai tsaye gurin da take ya nufa...................Rintse idonsa yayi da karfi yana Auziya a fili sakamakon ganin da yayi mata ita ba tsirara ba ita mai tufafi domin breziyar dake jikinta bata hanashi ganin kamai ba........"Subahanallah !
Ya jima a tsaye a gurun yana kiran sunan Allah! kafin yayi namijin kokarin bude idonsa yayi ya'ki da shaid'an da kuma zuciyarsa ya durfafeta babu alamun wasa a tare dashi............










*Don Allah idan ba sayan littafin nan zaki ba kada ki dauki number ta kiyi min magana abubuwan da yawa Nagode🙏🏻🤝🏻*






*Ga masu bukatar sadauki Omar 1k za'a tura domin samun damar karantawa littafin tare da Goje! sadauki Omar return*
*#500 via 0543282124...Binta umar gtbank, idan kati zaki tura ki min magana ta WhatsApp da wannan number... 07084653262........Mutanan Nijar ku tuntunbi wannan number....*
*22796074090* katin mov ko airtal.








*GOJE!*🏹
🐕‍🦺🐕‍🦺🐕‍🦺
_(SADAUKI OMAR RETURN👑💫_)


*BINTA UMAR ABBALE🍒*


*_MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION🖊️📚_*
_____________________




FREE PEGE








_Ina mika sa'kon ta'aziyya ta ga al'ummar musulman duniya baki daya, Na babban rashin da mukayi, hakika ba zuri'ar Malam kadai ne sukayi rashi ba duk duniya ne, muna rokon Allah ya jikin Malam Ahamad B.u.k (Bamba) Ya sanyashi cikin Aljanna madawwamiya Allah ya kyauta namu zuwan bayan tasu🙏_




*9&10*
Ya jima yana kokarin kawar da yanayin daya yake ciki amma abun ya gagara! yakan zama sakarai mara dubara a duk sanda irin wannan yanayin zai shiga jikinsa, gabadaya wayo da dubararsa nemarsu yake ya rasa, jikinsa ya takure guri daya, yana jin wani irin sanyi tare da tashin tsigar jiki. Ba da son rasa ba ya juya kanta, yaga tana wanke fuskarta da ruwan daya ajiye,
Asuwaki ya mika mata tabi asuwakin da kallon banza kafin tasa hannu a wulakance ta karba, duk da asuwakin sabo ne sai da ta wankeshi sannan tasa a bakinta, dauke kansa yayi yana girgiza kai ya lura da yarinyar kyankyaminsa take, a tunaninta ko yasa asuwakin a bakinsa.


Wani buhu ya janyo ya dauko wasu mangwaro masu nuna manya guda uku, ya wanke tas karamar wuka ya zaro daga jikinsa ya mika mata mangwaron da hade da wukar.
Hannu na rawa ta kar'ba yawunta na tsinkewa, bala'in yunwa takeji dama.


Kafin tayi amfani da wukar sai data tasa ruwa ta wanke duk da tana ganin acikin gidanta ya fito da ita amma bata yarda da tsabtar duk wani abu da zai fito daga jikinsa ba.


Inda Allah ya taimkashi, kayan dake jikinsa masu kauri ne wannan dalilin ya hana girmanshi fitowa amma a zahiri gabanshi yana tsaye kyam! sama da awa daya da rabi yaki kwanciya duk da 'yan dabarun da yayi abun yaci tura, sa'i da lokaci yana shiga irin halin amma na yau yafi muni.


Itacuwa ya had'a ya kunna wuta ya zauna yana gasa jikinsa duk a kokarinsa na ganin ya kawar da abunda ke damunsa.


Ita da take zaune ba tsirara ba ba kuma mai suttura ba, ta yun'kura ta mike da kyar take tafiya har ta cimma inda yake jin zaune.


Zata zauna ya daga mata hannu, ba tare da ya kalleta ba yace."Ki koma ki zauna a inda kike ko kina bukatar wani abu ne."?
Hararsa tayi tana murguda baki kafin tace."Naga kana shan dumi kai kadai shiyasa nazo nima ina bukata.
Tana maganar tana kokarin zama kusa dashi.


Tun daga sama har kasa yake bin ta da kallo, har ta samu guri ta zauna tana kara hannuwanta a jikin wutar, yanayin zaman da tayi yayi masifar jefashi cikin tashin hankali, inda ita kuma a wautar ta bata kawo komai ba tana ganin ai da tun farko yayi niyyar lalata da ita to da yayi amma ta lura sam ba wannan ne a gabanshi ba.


Ya dinga kokarin dauke kansa da kanta amma Shaidan yana kara 'kawata masa suffarta, gaza dauke idanuwansa yayi daga kanta, ya cigaba da satar kallon wasu guraran da suka bashi sha'awa a jikinta, amma be yarda ta fahimci halin da yake ciki ba.


Sun jima a haka babu wanda yayi magana a cikinsu, kafin suji bushe-bushe na kusanto inda suke da alama yaranshi ne suka dawo daga farauta.


Ta kalleshi a lokacin da ya tsirawa shara'ban kafarta ido. Tayi saurin gyara kafafunta tana watsa masa harara.


Ya sauke ajiyar zuciya tare da sake tamke fuskarsa cike da bada umarni yace."Ki tashi ki bar gurin nan."
Yanda yayi maganar babu wasa yasa ta tashi tsaye, yayi saurin dauke kansa, kawai sai taja masa tsaki ta wuce!
Abin ya bashi mamaki mutuka! ya girgiza kai tare da nazari da tunanin matakin da zai dauka a kanta


Gurin gabad'aya ya rikice da gangi da bushe-bushe duk a sakamakon dawowarsu, hannu tasa ta toshe kunnuwanta takaici kamar ya kasheta, da yake da akwai hasken wutar daya kunna tana kallo suka dinga firfito da matattun macizai da mesa tare da sauran dabbobin da suka farauto,
Abun ya dinga bata mamaki ganin sun daga wani lafcecan maciji sun sanya wuka mai kaifi sun rabashi gida biyu, suka tsire shi a jikin wani itace kafin su barbada masa gishiri da wani abu ja da alamar manja ne sannan suka sanyashi a wuta suna gasawa.


Hankalinta yayi bala'in tashi, karni da wari duk ya cika gurin zuciyarta ta dinga hantsilawa saboda tsabar kyankyamin abunda suke.


Tana nan zaune tana kallon ikon Allah suka gama gasa maciji nan wanda bai sani ba sai yace bushashshan kifi ne suka fara yankarsa da wuka suna ci hankalinsu a kwance.


A gurin ta dinga kyalaya amai duk sai da ta amayo mangwaron data sha, taja gefe guda tare da toshe hancinta.




Sai da dare ya tsala sosai sannan kowa ya nemi makwanci, yana sanya kafarsa yaji ya taka abu cabal! yayi saurin kunna fitilar hannunsa yana dubawa, aman da tayi ne duk ya bata kan shimfidar, tana rakube a gefe guda bacci ya dauketa.


Yaji takaicin bata mai shinfida da tayi yaja tsaki tare da samun ruwa ya wanke kafarsa ya dawo yana tunanin inda zai sanya hakarkarinsa ya kwanta ba don bacci ba.


Kusa da ita ne kadai babu kazanta kuma baya so ya kusanceta gudun abinda ka iya zuwa ya dawo, domin har yanzu yanayin be bar jikinsa ba.


Kawai sai ya yanke shawarar zuwa gurin yaranshi domin samun matsuguni, tsakaninsu babu wata tazara mai tsayi kuma yana da tabbacin babu abunda zai sameta, rigar jikinsa ya cire ya rufa mata a jikinta sannan ya bar gurin.




Da yake baccin ya dauketa a cikin tsoro da fargaba yasa ta dinga munanan mafarkai da namun daji sun biyo ta zasu cinyeta sai ta farka a gigice! tana kwalla ihu! da fadin." Kura ce! kana inaaaa! *GOJE!!* zata cinyeni."!
Gabadaya suka tashi tsaye da shirin ko ta kwana, amma ba subi bayansa ba, shine ya cimma inda take tsaye sai rawar dari take a tsaye.


Yana zuwa ta rungumeshi, tsam! tsam! tana wani irin kuka da fadin." Kura ce ta biyo ni."!!!


Ya dinga nanata mata addua a kunnuwanta har ta samu nutsuwa, ya zaunar da ita, amma fafur taki zama wai dole sai sun zauna tare. ta rike masa hannu katamau!


Shi kam taushin hannunta da dumin da yake shine yayi masifar sanyayyar masa da jiki,


Babu zato babu tsammani ta janyoshi duk karfinsa, sai ya tsinci kansa a zaune a kusa da ita, yayi mamakin hakan mutuka


A maimakon ta saki hannunsa, tunda yana kusa da ita, sai ma ta sake shigewa jikinsa, tana boye fuskarta a kirjinsa dake waje babu riga sai singlet.


Tsigar jikinsa ta tashi gabadaya ya rasa nutsuwarsa, so yake yafi karfin zuciyarsa amma ta kanainaiyeshi, ta hana shi tsira da mutuncinsa.


Haka suka wanzu har asubah! tana makale a jikinsa, ta hanashi sakat daga yayi motsi zata zabura! ta matseshi, tana goga masa sassan jikinta.


Da kyar ya iya furta magana." Sai ki sakeni haka asubah tayi babu wata dabba da zata zo ta cutar dake."


Kanta ta cire daga kafardarsa tana kallonsa da jajayen idanuwanta tace."Kayi wa Allah da Annabi ka hada tawagarka mu bar dajin nan! duk abunda kuke bukata mahaifina zai baku kada ka cutar dani ko kuma wata dabbar tayi sanadiyar rayuwata.


Ya jima yana mamakin furucinta ashe tana da hankali irin haka.


Sai shi ma yayi mata magana irin ta samu hankali yace."Bana bukatar komai a gurin mahaifinki, kuma ki daina dora zarginki akaina ni ba 'barawo bane Allah ya nufeni ne da na taimaka miki."
Yana kare maganarsa ya nufi bakin kogi da asuwaki a hannunsa, kallo ta bishi dashi har kurewa ganinta kafin ta girgiza kai tana tunanin wani abu akansa.




Sai da gari yayi haske sosai sannan ya dawo gurin dunga nesa yake hangota a kwance rigingine, ta dogare kafafunta a kasa cinyoyinta a waje amma ta suturta gabanta, saurin dauke kansa yayi har ya karasa gurin be sake kuskuran kallonta


Ya dauki rigarshi data cillar masa ya rufa mata a jiki, baya so yana ganin abinda zai tayar masa da hankali.


Ai da sauri ta cire rigar ta cillar da ita can tana ya mutse fuska, zaune ta tashi tace."Idan zaka kwana kana rantsuwa cewa kai ba dan ta addah bane ba zan yarda ba wallahi."




"Ke baki isa nayi rantsuwa a kanki ba, kuma idan kika sake kirana da wannan sunan zan nuna miki ta'addanci na."!
Yanda yayi maganar shi ya tsorata sai tayi shuru amma bata fasa yi masa kallon banza.


Ya dauki rigarsa data jefar yana girgiza kansa ya rasa wace irin yarinya ce me manta alkairi ina laifin wanda ya suturta ka.


Rigar ya sanya a jikinsa, can kasan makoshi tace." Kazami kawai." Yaji abinda tace amma be tanka mata ba, ya juyo, tayi saurin dauke kanta, janyeta yayi kan daddumar ta fadi kasan gurin, ba tare da ya saurareta ba ya bar gurin da daddumar a hannunsa.


Ta ciji yatsa tana bin bayansa da mummunan kallo.


Daya daga cikin yaransa ne ya karbi daddumar ya wanke tas ya shanya kan wata bishiya.




Ya umarcesu da suyi shirin fita shima tare zasuje don baya tsammanin zai zauna da yarinyar tana 'bata masa rai bayan masifar data jefashi a ciki.


Be saurareta ba ya hada kan tawagarsa suka fice ba tare data sani ba, hankalinta ya kai kololowa gurin tashi, lokacin data fahimci ita kadaice a cikin dajin sai ta raina kanta da wayonta, tana kuka ta kama hanya ta cire tsoro da fargaba kokarinta ya za'ayi ta fitar daga kanta daga cikin masifa.




Aikuwa kanta ne ya juye! a maimakon tayi baya sai ta dinga gaba, tana kutsawa cikin dogwayen bishiyu na kuka da tsamiya nan ta dinga arba da manya manyan birai iyaye da 'ya'yansu, hankalinta ya tashi, abinda ta tsana kenan a rayuwarta, gwagwgwan biri! ido sukayi da wani kato ya tsufa sosai! yana zaune duguzun-duzugun jikin wata narkekiyar bishiyar kuka!


Da baya da baya ta farayi kafin ta juya a sukwane tana falfala gudu hade da kiran sunansa *GOJE!!* shi kuwa Gwaggon birin nan dariya yayi da ya fahimci tsoronsa take sai ya kudiri aniyar tsokanarta, ya fara bin jikin bishiyu yana tsalle yana mata dariya har ya dura a gabanta.


Zubewa tayi tana daga masa hannu yawun bakinta ya bushe "Don Allah kayi hakuri! wayyo Allah na wayyo na shiga uku kuka ta dinga yi hawaye da majina sunyi kaca kaca da fuskarta.


Daya bayan daya suka kewayeta iyaye da kakanni! da alama sassaninsu ta shigo bata sani ba.


Kanta ne ya dinga juyawa a gurin kafin ta fadi, suma tayi, ba tare da bata lokaci ba wannan dattijon birin ya dauketa yasa a kafada, kataf-kataf ya fara tafiya da ita iyalinsa suka rufa masa baya.




Dabaru irin nasu sukayi mata ta dawo hayyacinta koda ta bude ido ta ganta a tsakiyarsu, sai ta mayar da idonta ta rufe jikinta sai karkarwa yake, su kuwa suna zazzaune sai cin manya manya ayaba sukeyi suna gurnani da alama zantuka suke a tsakaninsu.




Sai gefin magariba suka dawo, hankalinsa ya tashi lokacin daya duba sama da kasa be ganta ba,


Dajin ya shiga yana yana sasssare mattatun itatuwan da suka cika gurin, ya fito da sarewa yana busawa tare da cigaba da ratsa cikin dajin.


Zumbur! ta tashi zaune jin busar sarewar na kusanto gurin da suke, daga can nesa ya tsaya yana hango tawagarsu tana tsakiyarsu sai kace 'yar tsana saboda kankanta.


Kai tsaye gurin ya nufa yana cigaba da busa sarewar dake bakinsa, tsakiyarsu ya shiga yayi wani irin tsugo gaban dattijon birin nan yana me cigaba da busa abinda ke bakinsa,


Murmushi yayi ya dora hannunsa me cike da gashi da farata zako-zako a hannunsa a saman kansa, kafin ya cire ya nuna masa ita, yana gurnani!


Kansa kawai ya girgiza ya nufi inda take, hannu ya mika mata ta mike tsaye kafafunta sai kyarma! suke a haka suka bar gurin.


Saboda fargaba da mutuwar jiki yasa gabadaya kafafunta sukayi sanyi da kyar take iya jansu, bakinta ya mutu murus! tsabar tashin hankali binsa kawai take duk inda yaja ta, b'angaransa kuwa yana sane yaki goya ta saboda tayi bala'in bashi haushi, ya tabbata idan wata dabbar ce sai yasha mutukar wahala kafin ya samu damar fito da ita daga cikinsu idan sun barta da rai kenan.
Wannan Gwaggon birin sun saba dashi sosai duk sanda zasu shigo farauta dajin basu da matsala dashi da iyalinsa, wani sa'in ma har kyautar ayaba mai yawa suke basu.


Cikin mawuyacin hali suka karasa gurin da suka yada zangon ya jefar da ita ta fadi kasan gurin, zaune ta mike tana kallonsa ya juya mata baya gabadaya jikinta yayi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login