Showing 30001 words to 33000 words out of 49794 words
Chapter 11 - GOJE SADAUKI UMAR RETURN NA BINTA UMAR ABBALE .txt
alkairi, Nagode sosai da kulawa da shawarwari Allah ya raya zuria, ya jikan MAMA yai mata rahama🙏🏻
FREE PEGE
*27&28*
Ya jima kansa a 'kasa tun bayan 'kare maganar Asp din yake cikin nazari da tunani, kafin ya d'ago kanshi ya fara magana kamar haka............Sunana *UMARUL-FARUKU* Ni d'an asalin wannan jaha ne wato jahar katsina.".........Asp din ya kalleshi na 'yan sakkwani kafin ya mayar da hankalinsa kan takarda da biron dake hannuna, yace."Ina sauraranka." numfashi ya fesar kafin ya cigaba da cewa." Kamar yanda na fada maka hakane an haifeni a karamar hukumar malumfashi cikin wani k'auye mai suna *'Kafur* ban taso na iske mahaifiyata a raye ba amma na taso da mahaifina da kakata wacce ta zama garkuwa a gare ni, mahaifina asalin sunansa Tanimu, amma da yawa jama'ar gari sunfi kiransa da *mai jakai!* dalilin sana'arsa ta jidon 'kasa akan jaki domin siyarwa da masu aikin gini da sauraransu. mahaifina ya bani dukkanin wata kulawar da ta cancanta ya ilimatar dani ilimin addini daidai gargwado yanzu haka ina da izifi sittin na al'kur'ani maigirma, duk da acikin k'auye muke sai da yayi k'okarin ganin na samu ilimin zamani (boko) hankalinsa bai kwanta ba sai da na kammala 'karamar makaranta wato secondary school............bayan hakan sai ya fara koya min sana'a domin dogoro da kai, a lokacin dana kai shekaru ashirin da biyar a duniya sai tunani na ya sauya wani guri, a zahiri dai kowa ya sanar sana'ar mahaifina wato *Jaki da mangala* ban gaji farauta ba, amma sa'i guda na tsinci kaina dumu-dumu a cikin harkar, mahaifina baya so ko kad'an saboda yayi wa harkar mummunan fahimta, dalili duk wata nutsuwa da nagarta ina da ita, amma daga ranar dana fara harkar farauta sai wasu daga cikin dabi'una suka sauya, ni zanyi shedar kaina cewa tunda na fara wannan harkar ban ta'ba haura gidan wani nayi sata ba, ban kuma ta'ba tarewa wani hanya nayi masa k'wace ba sannan kuma ba'a ta'ba kamani da laifin fyad'e ga yaran mutane ba, wannan sune munanan laifukan da zan aikata a kira ni da wani mummunan suna! busa hakin sigari ko Shakar Shisha wannan sanya kai ne ga wanda yayi ra'ayin hakan. wannan dabi'ar da nakeyi sai ta janyo cecekuce da surutai a gari cewa na zama d'an iska takai ta kawo babu irin sunan da mutane basa kirana dashi, mahaifina ya d'au damuwar hakan yasa a cikin ranshi har ciwo ya kama shi wanda shine ya zama ajali a gareshi, lokacin da ya fadi ya mutu jama'ar gari suka dauki mutuwarsa suka ala'kanta ta dani cewar b'acin raina ne ya kashe shi, a duk lokacin naji wannan maganar hankalina yana tashi mutu'ka! ni dai na san babu wanda ya isa ya kashe kuma babu wanda ya isa ya raya sai Allah! amma jama'a sun juya maganar domin wani sa'in ma ita kanta kakata Uwale takan jefeni da maganar a duk sanda ranta ya b'aci dani.........Da yawa yawan mutane suna ganin rasuwar mahaifina zata karyar min da gwiwa na janye kudirina sai abun ya basu mamaki! domin ana adduar bakwai na cigaba da harkoki na! idan na fita farauta na kanyi kwanaki ko satittika a daji! kuma da ikon Allah na kan farauci duk abinda nakeso kuma nayi guzurin magunguna iri-iri! ba zance maka ga iya adadin mutanan da suka samu lafiya ta dalilina ba, ina kar'bar 'karamar sadaka na bada magani daga cikin irin ilhamar da Allah yayi min, wannan hanyar itace ta zama hanyar abincina, domin ko bana gari kakata takan bada magani tayi d'awainiya da kanta bayan 'yan sana'o'in da take........Tafiya tana 'kara tafiya ta kowanne fanni ana samun cigaba da tarin masoya da kuma tarin ma'kiya domin duk abinda zaiyi ba zai rasa d'aya daga cikin abinda na fada a yanzu ba, shekara biyar da ta wuce ina fita farauta ni kad'ai! cikin ikon Allah sai na fara samun magoya baya a hankali a hankali na tara jama'a da yawa wanda muke tafiya tare dasu wannan harkar! jama'ar gari suka dauke mu mutanan banza saboda muna yawo da karnuka bayan haka kuma shaye-shayen magungunan tauri da sauransu, yanda jama'a suke kallonmu muma haka muke kallonsu a hangunce! domin mu mun san bama aikata wani mugun aikin da zai janyo mana zubewar mutumci wannan harkar ba *Daba!* bace, ba kuma *Ta'addanci* muke ba, muna neman halak dinmu ne domin mu tsira da mutuncin mu." Cike da karsashi da kwarin gwiwa ya 'kare maganar!
Shuru ta ratsa gurin tun bayan 'kare maganarsa Asp din yake rubuce-rubuce yayi 'yan mintina a haka kafin ya d'ago kansa suka had'a ido! ya d'anyi murmushi da fadin." *UMARU-FARUK!* Maja ya'ki! ni Asp Musa Baharu! nayi imani da cewa babu *RAGO!* ga duk wanda ya amsa wannan suna domin Asali al'amarin ya dau'ko."
Murmushi yayi wanda ya tsaya kan fatar bakinsa......Asp din ya cigaba da cewa." Yanda kayi min cikakken bayanin tarihin rayuwarka cikin nutsuwa babu inda-inda yasa naji bana shakka a kanka amma ina so yanzu ma kayi min cikakken bayanin yanda akayi har ka samu nasarar shiga sansanin mutumin da jami'an tsaro suke shakkar tunkarar inda yake, hukumar tsaro tayi mutukar mamakin! yanda akayi kai da yaran ka kuka samu hanyar shiga wannan gurin, bayan baku da manyan makaman kare kanku."
Murmushi yayi wanda yake fito da zahirin kyawunsa ya tsira masa ido kafin yace." Me yasa kai ka yarda dani da sauri haka? me yasa har yanzu baka gazgata cewa Ni ne *UBAN DABA BA."?* Asp din yayi murmushi da fadin." Saboda sanin makamar aiki shiyasa kallo guda nayi maka na tabbatar da cewa ba kai ne wanda muke da bukata ba."
Girgiza kansa yayi still da murmushi a fuskarsa, Asp ya cigaba da cewa." Kayi min cikakken bayanin yanda akayi kuka samu nasarar shiga wannan guri da kai da jama'arka ina sauraranka."
Huci! mai zafi ya fesar! kafin yace." Na jima ina jin labarinsa na yawo a gari a duk sanda muka fita farauta sai mun ci karo da irin ta'addanci da yake, muna cin karo da gawarwarkin mutane bila adadin! mata da maza harda kananun yara! idan mun nausa mu ci karo da motoci irin na haya dana gida a k'one! wasu da rai wasu babu rai! mukan tsaya mu basu taimako daidai gwargwado kafin mu wuce! to wannan dalilin yasa ni d'aukar alkawarin ganin 'karshen ta'addancinsa duk da na san bani da alhakin hakan amma zuciyata bata karye ba, na zauna da yarana muka tattauna, da yawa daga cikinsu ba suyi na'am ba, sai dai kuma suka bi umarnina domin bana ajiye kara su tsallake! sannan kuma ba kai tsaye muka tunkari sansanin ba sai da muka bi matakan kariya kamar yanda yake da dabaru! da suddabaru iri-iri to muma muna dashi, domin sai da mukayi kwana biyar a dajin bai san da zaman mu ba! sai lokacin da naso ya san hakan, sosai yayi mamaki da faruwar al'amarin nayi masa bazata! kuma na fara karya alkadarinsa kenan tunda har na samu nasarar fitar masa da wani sassa na jikinsa to da ikon Ubangiji sai na gurfanar dashi a gaban hukuma."!! ya kare maganar cike da cin alwashi da cikawa kansa al'kawari!
Asp yayi murmshi mai ma'ana kafin ya latsa wayarsa serving yayi na recoding din da dauka. yasa wayar gaban aljihun rigarsa, mai da hankalinsa yayi kan rubutun da yake, bayan ya kammala ya sauke ajiyar zuciya da fadin." *JAN GWARZO! MAJA YAKI!* Yanzu zamu d'an huta zuwa anjima zamu d'ora insha Allah, bari nasa nasa a kawo maka abinci da ruwa idan kuma akwai bukatar yin wani uzuri kana iya magana."
Key yasa ya kwance masa hannu amma be kwance kafafun ba.
Ya fito da waya ya kira wani jami'i minti uku ya shigo, ya bashi umarnin kawo abinci mai kyau da ruwa da lemo." Ya 'kame tare da sarawa kafin da sauri ya juya ya fita daga ofis din cikin bin umarni.
Idonsa ya sauke kan agogon dake kafe a ofis din, daya da rabi na rana lokacin sallah yayi, sai ya mike tsaye Asp din ya kalleshi tare da tambayarsa, Uzurinsa ya fada masa, da kansa yaje ya bude masa kofar toilet din ya bashi hanya har ya k'araso bakin toilet wanda da kyar yake cire kafa sakamakon sasarin dake d'aure da kafafun!
Alwala ya d'auro ya fito, shima Asp din ya shiga ya d'aura alwalar ya fito suka tada sallar a tare............... Tare sukaci abinci har suka kare babu wanda yayi magana a tsakaninsu sai dai nazartar junansu da suke.
Asp wani jami'i ya k'ira ya umarceshi da ya shigo masa da yarinyar da suke maganarta.
Tare suka shigo ofis din ya kame tare da sarawa kafin ya fita, Asp ya kalleta tare da nuna mata gurin zama, ta zauna kujerar dake kusa dashi sai ya kasance gabad'ayansu suna fecing Asp din.
Tunda ta shigo kanshi yake k'asa sam baya so ya daga kai ya kalli fuskarta saboda tsabar yanda yake jin tsanarta a cikin zuciyarsa.
Wani irin kallon k'askanci take masa! ranta ya 'baci sosai da ganinshi lafiya lau babu duka! ko mugun rauni! a jikinsa, ita a tunanin yanzu yana nan a galabaice! kammaninsa sun sauya saboda duka! sai taga akasin haka lafiyarsa lau da nutsuwa a tare dashi fuskarsa sai fitar da annuri take irin na musulunci bayan haka kuma an kwance masa sasarin dake hannunsa.........Sai duk jikinta yayi sanyi a fakaice take aika masa da mummunan kallo! wanda take a bayan duhu domin be san abinda take ba, sai shi Asp din dake hankalce da duk abinda yake faruwa.
murmushi kawai yayi kafin yayi gyaran muryar da ta sanya shi dago kansa suka had'a ido, still da murmushin a fuskarsa Yace." *Jan wuya!! Goje kake mugun makangari sai kuree."!* Dariya yayi irin wacce bai ta'ba yin irinta ba, gabadaya suka shagala gurin kallonsa tabbas da ya san yanda dariya ke masa kyau to daya yawai ta ta, shima Asp din dariya yake yace."Na fahimci wannan kirarin yana maka dadi ganin yanda kake kyalkya dariya irin haka."
Hannu yasa cikin suman kanshi ya d'an sosa kafin ya girgiza kai da fadin." Gaskiya ne ina mutukar jin dadin hakan! da yawa jama'ata na kambaba! daraja ta ina farin cikin hakan amma ban ta'ba dariya irin na yau ba, naji dadin hakan ranka ya dade nagode sosai."
Yace." Ka cancanta da duk sunayen dana kira ka a halin yanzu, tun bayan shud'ewar zamanin maya'ki namijin duniya *ALI K'WARA* ban sake jin labari ko yin gaba da gaba da gwarzo irinka ba, *UMARU* muna sanya ran zaka maye mana gurbin wannan bawan Allah da mukayi rashi."
Ya girgiza kansa da fadin." Insha Allahu a shirye nake dana bada gudumawata bakin rai bakin fama zan kare 'kasata cikin ko wane irin yanayi."
Asp yace."Lallai kuwa idan hakan ta kasance 'kasa zata gyaru za kuma a samu sau'kin faruwar munanan ayyukan da sukayi wa kasa dabaibayi.''
Ofis din ya sake daukar shuru na 'yan mintina kafin ya kalleta tana zaune tsuru abin duniya yai mata zafi ganin yanda ma'kiyinta ya samu sake har yana kyalkaya dariya anya kuwa bukatarta zata biya a kansa........Asp ya katse mata tunani da fadin."Meye sunanki."?
Banza tayi masa ta dauke kai domin shi din ma mugun haushinsa takeji...........Ya sake maimaita maganarsa, still bata tanka ba.
Sai ya fusata! ya buga tevur din dake gabansa da karfi! yace." Ko da kurma nake magana."!?
Kawai sai ta fashe da kuka! hawaye share-share! ta d'aga masa hannu da fadin." Kaga saurara Asp ka daina buga min tsawa haka ko ubane ne kai."!?
Ya zuba mata idanuwansa da 'bacin rai a fuskarsa da maganarsa yace." Kina 'karkashin tsaro a halin yanzu duk abinda kike ta'kama dashi dole ki sauke kibi doka idan ba haka ba yanzu zaki fuskanci hukunci mai tsauri."!
Shuru tayi ba tace uffan ba, ya koma ya zauna yana mayar da numfashi! ya kalleta tare da sake maimaita maganarsa.
Cikin izzah! tace." ZINATU nake 'ya ga Saraki sarkin sarakuna arewa wato *SADAUKI OMAR!.*
Asp yayi gaggawar kallonta, ta tsira masa ido cike da tsiwa tace." Ko kana mamaki ne."? duk da akwai hakan a tare dashi amma sai yayi sauri ya basar yasha kunu! da nuna mata shi da hannunsa....."Kin san wannan."? ta kalleshi a sheke kafin tace." Eh na sanshi." yace" meye alakarki dashi kuma wane dalili ne ya kai ki wannan gurun."?
Tsaki! taja za tayi magana ya daga mata hannusa, ta kalleshi babu walwala ko ta kwabo a tare dashi, yace." Wannan shine last warning na k'arshe kada na sake miki magana kiyi tsaki ko abu makamanci haka kina k'ar'kashin hukuma! hukunci zai bi ta kanki duk matsayin ubanki dake kanki." ( Hausawa sukace dan kuka shike janyowa iyayensa zagi) ganin babu wargi yasa ta shiga taitayinta, ya sake maimaita maganarsa.
Kai tsaye tace." *'Barawo* ne shine ya sato ni daga masarautarmu domin samun makudan kudi daga gurin mahaifina."
Kallon mara hankali yayi mata kafin yace." Ya akayi kika gazgata hakan bayan kawai bude ido ki kayi ki ka tsince ki a gabansa a lokacin da wuta take kokarin cinye ki, ina tunaninki yake a lokacin?
Shuru tayi tana tunani, zata iya tuna lokacin da ta fito da daddare domin zuwa partyn 'kawarta dake murnar karin shekara daga cikin shekarunta, tana kokarin bude motarta domin shiga al'amarin ya faru, daga lokacin bata sake sanin komai ba sai bude idonta tayi tai arba dashi a gabanta bayan ya bata taimakon daya dace, amma zuciyarta taki aminta dashi har yanzu tana zarginsa.
Asp ya nuna mata shi da fadin." Wannan da ke zaune a gabanki bai cancanta da wannan sunan ba, domin kuwa ya taka muhimmiyar rawa a rayuwarki! kada ki sake kiransa da wannan sunan."
Hannu ta d'aga da niyyar magana ya katseta da fadin." Duk abinda kike tsammanin faruwarsa ba zai faru ba da izinin Ubangiji muna da hankali kuma muna gudanar da aiki bisa hankali da nutsuwa saboda haka baki da hurumin magana a yanzu, binkice ya bar kanki a halin yanzu, insha Allah kuma zamu sadaki da iyayenki yau ko gobe."
Bakinta ya mutu murus! ta rasa abin cewa tsabar yanda al'amarin yayi mata bazata! ta dinga zabga musu harara tana murguda baki babu wanda ya sake bi ta kanta maganarsu suke cikin fahimtar juna kafin ya kira wayar ma'aikaci guda, yana shigowa ya bashi umarnin kaita gidansa. Ya kalleta da fadin." Zaki zauna da iyalina na 'yan kwanaki kafin mu gama gudanar da binkice. "
Kamar za tayi magana sai dai taja bakinta tayi shuru, mi'kewa tayi ta kama hanyar fita, direban yabi bayanta cike da bin umarni...........
*#500 via 0542382124...Binta umar gtbank, idan kati zaki tura ki min magana ta WhatsApp da wannan number... 07084653262........Mutanan Nijar ku tuntunbi wannan number....*
*22796074090* dala dari katin airtal ko mov
*GOJE!*🏹
🐕🦺🐕🦺🐕🦺
_(SADAUKI OMAR RETURN👑💫_)
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
*_MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION🖊️📚_*
_____________________
FREE PEGE
*29&30*
Kusan a tare suka d'auke idonsu daga barin kallonta, Asp din yayi magana amma shi uffan bece ba har ta gama harare-harare! ta fita daga ofis din. Ya d'an ja k'aramin tsaki da fadin." Yarinya nan babu tarbiya a tattare da ita duk kuwa da cewa ta fito daga tsatso mai kyau, ba ta gaji dattako da karamci irin na mahaifinta ba, duk da ba a garin kano muke zaune ba muna da labarin dattakon mahaifinta mutum ne mai karamci da mutunci yana aiki da hankali da ilimi yana kuma gudanar da mulki a bisa tsari na isalama."
Beso ya tanka a cikin al'amarin yarinyar ba amma ganin yanda Asp din yake jaddada maganar yasa yace." Akwai irinsu da yawa wa'inda suka dauki mulki wata tsiya idan akace mahaifinsu nada sarauta ko wani muk'ami sai su dauki girman kai su dora a kansu suna ganin babu wanda ya isa dasu, hakane maganarka mutumin kwarai yana iya haifar baragurbi acikin al'umma jarabtace kawai daga Allah.'' Yace." Kwarai kuwa wannan haka yake sai dai kawai mu roki Allah ya shirya mana zuria baki d'aya." Ya amsa da ameeen ya Allah.
Shuru na minti biyu ya ratsa gurin, cikin 'yar tsokana Asp din yace." Akwai abinda na manta ban tambayi *MAI DAWA!* ba."?
Murmushi yayi da fadin." Akwai sauran tambayoyi kenan."? Girgiza kai yayi da fadin." Tambaya daya ce shin kana da iyali kuwa.''?
Girgiza kai yayi gami da dan ta'be bakinsa.........Asp ya dan zare ido da fadin." Kana nufin babu iyali kenan."
Kai ya daga masa still da murmushi a fuskarsa.
Sai kawai ya shiga girgiza kansa da fadin." Gaskiyar magana yanda kake jarumin namiji mata hudu suka cancanta da kai amma ace ma ko daya babu." cike da alhini ya kare maganar.
Sai abun ya bashi dariya ya dan dara kafin yace." Asp matsalar mata nada yawa shiyasa nayi zamana a haka ba wai don bani da bukata ba, kawai nafi bukatar kwanciyar hankalina nayi duk abinda nake so ba tare da wani ya caza min kai ba.''
Yace." To ai hakan nan ake hakuri dasu da matsalarsu Umaru kowane maigida yana da matsalar iyali mussaman idan mace fiye da d'aya yake da ita, dole ba zaka rasa shi da matsala ba, nima matana biyu sai dai kowacce da gidanta kuma yanzu haka ina shirin yin ta uku da yardar Allah sai na cike domin ina da ra'ayin hakan."
Ya girgiza kai da fadin." Kayi kokari sosai kuma ka aikata sunnah Allah ya baka ikon yim adalci a tsakaninsu."
Ya amsa da "Ameen ya Allah ina fatan kai ma kayi koyi dani."
Girgiza kai kawai yai baya tsammanin hakan domin baya san damuwa ba lallai sai ka tara mata a gidanka za'a tabbatar da jarumtarka ba, shi