Showing 3001 words to 6000 words out of 49794 words
Chapter 2 - GOJE SADAUKI UMAR RETURN NA BINTA UMAR ABBALE .txt
kadan, amma bai nuna a fuska ba.
Ya bude gwangwanin Milo din dake hannunsa, wani abune mai duhu a ciki, da alama magani ne aka kwaba da mai, ya kalleta da fadin." Zaki iya nuna min gurin da kunamar ta cijeki."?
Wani irin kallo ta tsawa masa, ta dauke kanta, ranshi ya baci ya daka mata tsawa da fadin" Taimakonki fa zanyi kike min kallon banza kin san wanene a gabanki kuwa."?
Hannu tasa ta goge fuskarta ta daure zugin dake damunta, cikin rashin tsoro tace." Sanin wanene kai bai dameni ba, na dai san ka amsa suna biyu wato *barawo* kuma dan *ta'addah."!*
Ya tsira mata idanuwansa masu kaifi! yana mamakin maganarta, *'barawo kuma d'an ta'addah!* tunda yake a duniya babu wanda ya ta'ba kiransa da sunan *barawo* sai ita, kalmar *d'an ta'addah* kuwa yana ji tana yawo a gari a kansa.
Ya girgiza kansa cikin yanayin maganarsa yace." Wannan shine karon farko da aka ta'ba kirana da wannan kalmomin a gaban idona, kiyi kokarin kiyaye harshenki kafin ki bar hannuna, *GOJE!* nake ba'a kawo min wargi duk tsagerancinki ni zan daidaitaki.
Ta kalleshi a wulakance kafin tace."A hakan? babu tarbiyar! ka fara daidai ta kan............'Barin makauniya yayi ya fuskarta, a take hancinta ya tsinke da jini, tasa hannu ta dafe, jiki na kyarma! take kallonsa, fuskarsa ta rikide da zallan bacin rai!
"Zaki janyo nai miki mugun rauni a gurin nan, babu ruwana da kowace masarauta kika fito, ki sani ba'a nuna ni da yatsa ban karya ba! sannan ba'a jayayya dani, kuma bana magana biyu, *Billahil-lazi hurramanu!* duk sanda kika kara fadin wata mummunar magana akaina sai na illataki."!
Shuru tayi jikinta yayi bala'in mutuwa ganin yanda hancinta ke zubar da uban jini shine abinda yafi zaburar da ita.
Ta kalleshi, yana safa da marwa a gurin, tace." A kan me ba zan kira ka da wannan suna ba? ka sato ni a gaban iyayena domin su baka kudi. akan me ba zan kiraka da *'Barawo* ba me kake bukata? da ka kawoni daji ka ajiye kana azbtar dani, kamar ni *Zinatu* wacce ta gaji sarauta gabada da baya ina rayuwa a wannan kazantaccen gurin, tare da kai makaskanci to saurara kaji da kyau! wannan jinin da ya zuba, be zuba a banza ba, wallahi sai kayi daka sanin zubar dashi."!
Hannu d'aya yasa cikin aljihun jins din dake jikinsa, ya dan sunkuya tare da dogare gwiwarsa, fuskarta ya dago da hannunsa, yana kallonta tana kallonsa, yace."Daga wace masarauta kika fito naga kina girmama kanki kina mutunta kanki, duk wanda ya gaji saurata baya kambaba kanshi kamar yanda ke kike, ina so ki sani zargin da kike a kaina kar ki gazgata, Allah ya kawoni ne tareda jama'ata domin na taimakeki, kuma zan taimakaki bakin kokarina, amma ni zan koya miki tarbiya.
Magana za tayi ya sanya yatsunsa biyu ya murje fatar bakin...........tsam! ya rike lebunan yana ligwigiwitawa, kukan zucci kawai take, jikinta yayi mugun sanyi, yana sakin bakin ta silale a gurin, yaja tsaki da furta "kalankasa kawai."!
Zanin dake nannad'e a jikinta ya janye duk tana jin abinda yake amma tsabar yanda jikinta yayi tubus, ta kasa hanashi sarrafata.
Bai damu da kallon wasu sassan na jikinta ba, domin gabad'aya babu wani feelings a tare dashi, tunda yake sai yace babu ranar da wata mace ta ta'ba tayar masa da hankali duk zubi da kirar dake gareta, Asalima yakan jima bai shiga yanayi na bukata ba, shiyasa auran baya gabanshi, wanda uwar rikonshi wato kakarsa Uwale keyi masa surutu akan hakan.
Da kanshi ya lalubi inda kunamar! ta harbeta ya shefe gurin da magani, ganin duk yaran nashi sun bar gurin yasa ya bude mata jikin domin qunar tasha iska.
Har ya gama abinda yake a gurin bata daina zubar da hawayen takaici ba, tayi turr! da wannan rayuwar da take ciki, a tunaninta hanya ba zata iya had'awa dashi ba, sai gashi w *Kazami- Bagidaje!* irin sa yana ganin sirrin jikinta. tana ganin wannan ko hadimanta (masu yi mata bauta) sun fishi kyawun gani sai gashi a banza yana yin yanda yake so a kanta ya tatta'ba jikinta babu tsoro ko shakka a tare dashi hawaye masu zafi ta goge tana jimanta al'amarin.
Taji dadin maganin sosai domin tana tsaka da tunanin hanyar da zata bi domin kubutar da rayuwarta bacci mai nauyi ya dauketa.
*****
Kana ganinta kaga bafulatana, doguwa ce sambal kyakykyawa a fuska, gata fara tas! ta tara duk wasu abubuwa da da namiji ke bukata amma hausawa sukace wai Dan Adam tara yake be cika goma ba, Hamra'u bata da cikkar kirji hakanan kuma babu baya a tsaye take kamar muciya da zani, sai dai akwai tarbiya da kunya irin ta fulani.
A nutse tayi sallama a gidan, Uwale dake uwar daki ta amsa, da fadin.'' 'Yar halak yanzu nake maganarki a zuciyata.
Murmushi tayi ta cire takalminta, ta shiga dakin, Uwale na kurbar kunu ta mika mata kofin da fadin " Bisimillah."
Girgiza kai tayi tana murmushi tace." Ai daga gida nake kuma sai dana karya kafin na fito.
Dariya tayi irin ta tsoffi tace." Hamra'u kenan wai me yasa duk sanda zan baki abu sai kice daga gida kike ko dai kankyamina kike ne."?
Da sauri tace."Aa Wallahi ba haka bane Uwale na koshi."
Tace."To ai shikkenan duk ya mutan gidan."? Tace."Suna nan lafiya lou alhamdullhi babanmu yace a gaisheki da kyau.''
Tace."Ina amsawa ai a cikin satin nan nake so nazo gidanku mu gaisa sai kuma *UMARU* Yayi tafiya gashi zai dauki sati guda bai dawo ba.
A sanyaye tace."Yanzu fa nake shirin tambayarki ina yake shine zakice yayi tafiya kuma sai yayi sati zai dawo."
Tace."Eh haka yace min da zai tafi kin san dai yanayin al'amuranshi, wani sa'in ma har wata guda ya kanyi yana gwagwarmaya a daji"
A raunane tace." Ni wallahi ba naso yana irin wannan yawace-yawacen tsoro nake kada 'yan fashi su kasheshi ko kuma namun daji su cinyeshi."
'Yar dariya tayi tana sud'e kofin kunun data gama sha tace."Sai dai kiyi hakuri Hamra'u wannan mijin naki yayi nisa addua kawai zaki dinga yi masa.
Tace."Kullum inayi masa addua tare da sauran jama'a." Tace."yawwa hakan yana da kyau, sannan ki cigaba da hakuri insha Allahu, hankalinsa zai karkato kanki."
Idonta ya cika da ruwan hawaye, tace."Uwale sai nake ganin kamar baya sona tausayina kawai nake gani a kwayoyin idonshi.
Tace." To in banda abinki Hamara'u ai sai da so ake tausayi, da baya sonki ba zai tausaya miki ba."
Shuru tayi tana nazarin maganar, itafa tunda take dashi babu wata kalmar so daya taba furta mata, asalima yana kiranta da kanwata, amma bai taba cewa Hamra'u ina sonki ba, sai dai yana tsananin bata kulawa komai take bukata idan tayi masa magana kai tsaye yake mata, wannan dalilin yasa iyayenta da ita Uwalen suke ganin kamar sonta yake, ajiyar zuciya ta sauke ta kudire a ranta cewa idan ya dawo zata cire kunya ta tambayeshi matsayinta a zuciyarsa.
Hamra'u 'yar kanin Uwale ce, tun tana yarinya Allah yasa mata so dakaunar Goje tun be fahinta ba har Allah ya fahintar dashi, be ajiyeta a wani matsayi na daban ba face wanda take dashi a zuciyarsa, gabadaya tunda ya taso baya da ra'ayin soyayya, shiyasa baya fahimtar tarin 'yan matan dake k'aunarsa, Samari da yawa a karkarar tasu suna kishi dashi, a cewarsu sai kace shi kadai ne namiji ko wacce budurwa bata da magana sai tasa, ransu yana baci mutuka, suna kuma bala'in kishi a kan haka, ita kanta Hamra'un akwai wanda yake mutuwar sonta amma fafur taki amince masa ita dai Umaru takeso wanda bata da tabbas a kansa..............
Uwale, kayan dillacinta ta dauko ta nada gammo ta dora aka, tana gyara yafan mayafi take fadin."Hamra'u ni zan fita dama a irin wannan lokacin nake samu na nemi halalina idan kin gama gyara min gidan ga kwado ( dan mukulli) akan taga ki kulle gidan ki bawa Tasallah ta ajiye min."
Tace."Uwale inace Yayana ya hanaki yawon dillaci nan kuma kin san Babana ma baya so me kike bukata ne a duniyar nan."
Tsaki taja da fadin." Sai kiyi kuma kinga tafiya ni babu wanda zai hanani neman kudi." tana gama maganarta tasa kai ta fita daga gidan.
Hamra'u girgiza kanta kawai tayi idan da sabo ta saba da hakan , a nutse ta mike ta fara ayyukan dake gabanta....
***********
*WAIWAYE*
K'allo d'aya nayi masa na fahimci wanene a gabana, ko da yake koda zanyi shekara d'ari ba tare da na sanyashi a idona ba to ba zan mance kammaninsa ba, *Sadauki Omar* kenan Sarkin dake kan karagar mulki a jahar *Kano* Adalin sarki wanda al'ummarsa ke jin dadin mulkinsa.
Yana nan a yanda kuka san shi tsayayye! kuma jarumin namiji! kamanninsa suna nan sai dai alamun girma da ya baibayeshi amma a tsaye yake da jarumta babu abunda ya samu nakasu a cikin halayensa da d'abi'unsa.
Yana tsaye a tsakiyar babban falonshi hannuwansa goye a banyanshi yana kai kawo a gurin, kallo daya kayi masa zaka fahimci yana cikin damuwa.
Cikin nutsuwa da kamala tayi sallama be juyo ba ballantana ya amsa sallamarta,
kai tsaye inda yake ta nufa, sai na bita da kallo, ina hasashen a inda na san fuskarta, Gimbiya *Aysha ce fa* zuciya tayi saurin tuna min ita
Cike da dumbun mamaki nake kallonta tana sanye cikin laffaya milk color da adon zaiba kafarta sanye da takalmi rufaffe irin na sarauta, ban hango wata tawaya a tare da ita ba domin kuwa jikinta ya nuna alamun hutu da jin dadi sai dai alamun shekaru sun tura hakan ma sai ka 'kura ido a kanta sannan zaka fahimci cewa ta kwana biyu a duniya.
Hannunta ta d'ora kan kafadarsa, a nutse ta kira sunanshi *"Jarumi."* be juyo ba ballantana ya kalleta, sai ta dora kanta kan kafad'arsa, hawayen da take boyewa suka kufce, wai shin ya za suyi da wannan ibtila'in da yake kokarin ruguza musu farin cikin da suke ciki na tsayin shekaru masu yawa................
*Ga wanda bai samu damar karanta Sadauki Omar ba, zai tura 1k domin samun damar karanta littafi biyu tare da Goje! Sadauki Omar return*
*#500 via 0543282124...Binta umar gtbank, idan kati zaki tura ki min magana ta WhatsApp da wannan number... 07084653262........Mutanan Nijar ku tuntunbi wannan number....*
*22796074090* Mutanan Nijar zaku turo min katin Mov ko airtal na Dala dari.
*GOJE!*🏹
🐕🦺🐕🦺🐕🦺
_(SADAUKI OMAR RETURN👑💫_)
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
*_MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION🖊️📚_*
_____________________
FREE PEGE
*7&8*
_*Banyi tsammanin rubuta wannan littafin a kusa ba, asali ma nayi wa kaina alkawari cewa na daina sakin littafi sai na kammala, amma cikin ikon Allah ya nufe ni da fara rubuta wannan littafin ba tare da nayi tunanin hakan ba, ina rokon Allah ya bani hakuri da juriyar rubuta abinda za'a amfana dashi, sannan ina mika godiya ga dubbanin masoyana wanda na sani da wanda ban sani, hakika duk wanda Allah yayiwa baiwa ta jama'a dole ya gode masa, babu abunda zance da masoya sai godiya da fatan alkairi, sannan a cigaba da hakuri da yanayi na rayuwa, koda zanyi wa wani laifi a bisa rashin sani to ina neman afuwa🙏🏻 d'an adam ajizi ne, ina fatan zaku bibiye ni a wannan littafin nawa mai suna a sama, ku bani hadin kai sannan ku bini a sannu a hankali domin isar da sakon dana dauko, #500 kacal zaku biya domin karanta cikakken labarin.*_
*WANNAN NAKI NE*
_(AUTAR MANYA)_
*A cikin marubuta ke ta dabban ce a gurina🤝🏻🥰*
Jin kukanta yake har tsakiyar kansa, koda can baya son ganin tana zubar da hawaye ballanatana yanzu da ta riga ta zama garkuwa a tare dashi.
Ajiyar zuciya ya sauke ya juyo tare da rike kafad'unta, hannu yasa ya share mata hawayen dake zuba a saman fuskarta, ta rike hannunsa da fadin.'' Ka bari nayi kukan domin shi kadai zanyi na samu sassaucin abinda nake ji a cikin zuciyata."
Ya girgiza kansa da fadin." Ke kin san bana son zubar hawayenki Aysha me zai sanya ki kara tayar min da hankali bayan wanda nake ciki."
Ta tsira masa idanuwanta wanda suke cike da ruwan hawaye " Me yasa ka kasa fahimta ta? me yasa ka dauki laifi kacokan ka dora a kaina bayan idan adalci a za'ayi kaine babban mai laifi dangane da faruwar wannan al'amarin."
Girgiza kansa yayi zuciyarsa nayi masa wani irin zafi da k'yar ya iya magana." Bani da laifi Aysha ba zan haifi d'a a cikina na lalata shi ba, ba zan gaji da fadi miki cewa tarihi ne yake maimaita kansa."
Ranta ya 'baci da jin furucinsa, a duk sanda zai fadi wannan kalmar akan wannan al'amarin sai taga kamar akwai rashin adalci a cikin maganarsa.
Tana kokarin magana, Safa ta shigo da sallama a bakinta, suka amsa tare da bin ta da kallo har ta karasa inda suke tsaye. fuskarta kadai zai nuna maka cewa akwai rashin kwanciyar hankali a tare da ita, ba ita ta haifi Yarinyar ba amma tafi kowa shiga tashin hankali da rashinta.
A raunane ta kalleshi da fadin.'' Ranka shi dade har yanzu babu wani labari ko."?
Kanshi ya daga da fadin." Babu wani labari Safa watakila ma yarinyar nan bata raye domin duk iya binkice anyi amma ba'a samu wani labari mai dadi ba."
Kuka ta fashe dashi, ta nemi guri ta zauna tare da rufe fuskarta da tafikan hannayenta.
Ganin tana kuka yasa Aysha da sauri ta kama hanya domun fita bata so duk su lalace a gurin koke-koke domin mutukar tana kallon kukan Safa to itama zata iya taya ta.
Karo sukayi da juna, Aysha kanta a kasa yake shiyasa bata ga shigowarta ba, Maijidda ce matar mijinsu, da ya aureta bayan shekara masu yawa da suka wuce.
Kasancewar basa shiri da juna yasa tayi saurin kauda kanta ta wuce, ita kuma hamshakiyar ta bita da wani irin kallo kafin ta ta'be bakinta cikin wata irin tafiya ta isa da ta'kama tayi sallama a falon.
Shi kad'ai ne ya amsa sallamar Safa har yanzu kuka take yana tsaye ya gaza rarrashinta shima da zai samu yayi kukan da yaji sassauci a zuciyarsa.
Wawan kallo takewa Safa kafin tace."Ke a ganinki hakan kauna ce? kullum baki da aiki sai kuka uwar data haifi yarinyar ma har ta fiki dauriya Safara'u kuka bashi ne mafita ba."
Safa ta dago kanta tana kallonta da mamakin furucinta, za tayi magana kenan, Yace." Abinda nake ta so su fahinta kenan yanzu ita kanta Ayshan ta gama nata ta fita, na fada masu cewa addua itace abinda ya cancanta.
A tausashe tace."Hakane ranka ya dade shiyasa ko kadan ban zubar da hawaye na akan wannan al'amari ba, abinda nayi shi ya cancanta, ya kuma kamata, tun ranar da al'amarin ya faru na sanya almajiran mahaifina suyi saukar al'kur'ani na tsayin sati guda, da izinin Allah yarinyar nan tana hannu nagari za kuma ta dawo gida cikin aminci."
Safa ta watsa mata wani irin kallo na zargi kafin ta tashi tare da kama hanyar fita.
Sunanta ya kira ta juyo tana kallonsa babu walwala ko ta kwabo a fuskarta.
Yace."Kada ki cigaba da wannan kukan bashi da fa'ida ko kadan addu'a zakiyi kinji ko."
Ba tace masa komai ba ta fita ta basu guri, kai tsaye sashen Aysha ta nufa, ta sameta tare da babban yaron su wanda suke kiransa da magajin Sarki.
Tana shiga ya mike tsaye yana mata barka da zuwa, ta zauna kusa da 'yar uwata kafin ta bashi umarin zama.
Ya zauna kasan kafafunsu, a nutse yace." Mommah don Allah ku kwantar da hankalinku bana so naga daya daga cikinku na zubar da hawaye ni nayi imani da Allah da manzon Allah yarinyar nan tana hannu nagari da yardar Allah zata dawo gida cikin koshin lafiya.
Aysha bata iya magana ba, Safa tace."Babana ina mamaki idan naji kai da mahaifinka kana maganar mu kwantar da hankalinmu, ta ina hankalinmu zai kwanta? a cikin wannan yanayin yarinyar nan sace ta akayi kuma akwai sanya hannun makusanta bana shakka a cikin maganata."
Yace."Hakan tana iya kasancewa amma Mommah kada ki manta fa yarinyar *Zinatu* bata jin maganar kowa kuma a daran da al'amarin nan zai faru gabadaya sai da kuka hanata fita amma saboda rashin tarbiya ta tsallake maganarku to me zai sanya hakkinku be bibiyeta ba."
Shuru sukayi domin kuwa babu mai bakin magana a cikinsu, abinda ya fada gaskiya ne, yarinyar ta fita zakkah a cikin zuriarsu, sai kuma Allah ya jarabcesu da tsananin sonta, shi kansa maimartaba wato mahaifinta baya son laifinta, ko kad'an duk da ya san abubuwan da take na rashin kyautawa a masarautar duk zafinsa baya iya tsawatar mata, sai 'yan uwanta mata dake gidajen auransu suke tsaye a kanta, wani sa'in su din ma bata saurara musu rashin kunya take musu kuma ta kwana lafiya, babu wanda take shakka sai shi Magajin sarkin, shima a bayan idonsa zaginsa take tana fadin be isa ya hana rayuwar jin dadi tun bayan dawowarta daga kasar waje bayan ta kammala karatunta ta dawo da mugayen dabi'u irin na turawa, duk wanda ya nuna mata kuskure akan abinda take cewa zai shafi masarauta da martabar mahaifinta sai ta d'aura gaba dashi, halin da ake ciki shi kansa Magajin sarkin ba tayi masa magana saboda yana tsawatar mata akan abubuwan da take na rashin tarbiya, jin kade - kade sanya matsatsun kaya bayan baiwar da Allah yayi mata na qira, yawace-yawacen pary cloub club babu inda bata shiga tayi b'arna da kudi da famkama da manya motoci ta fito babu abunda ya dameta.
Da yawa mutane ba sayi mata kallon cikakkiyar mace saboda mummunan dabi'unta. Don akwai lokacin da wani babban malami ya nemi