Showing 24001 words to 26020 words out of 26020 words

Chapter 9 - TAWA TA SAME NI BOOK 1 COMPLETE DOCUMENT by Halima Abdullahi k. Mashi .txt

da uwata ba ya
mike ya zo kusa da ita wllh wllh in kika kuma hada ni da
ita sai na fasa auran nan ke ko an daura sai na sakeki
akan Iman,
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Yayi waje ya barta cikin mamaki da tsoro koda haj yaya
ta dawo bata sanar da ita yanda suka yi ba ta dai ce ya
bata hakuri ya tafi haj yaya tace ai nasan zai rabu da
yarinyar nan sai ma kin shiga gidanshi Mimi tace haj ce
min yayi fa in anyi bikinmu da sati biyu zai tafi england
ya barni dama yaje dani don akwai masu mata a can,haj
yaya tace gsky haka za'ayi sai dai za'a yi fama kafin ya
yarda na ma huta hankalina ma ya kwanta baya kusa
bare in ta fargaba kar yace yana son yar iskar 'yar can
shima Kabiru zuwa zanyi na matsa mishi yayi auran
tunda yana aikinshi dama jira nake yayanshi yayi tukunna
cikin farin ciki Mimi ta fita ta san da haj yaya ta mishi
magana shi kenan zai yarda su tafi tare.
Da yamma na dawo daga gidansu Amira in da ta nuna
min gwaggwaro ba tace don Allah kisa yammata kowa
zai sa mu uku iri daya ?ami ta sai mana kalar namu
daban ne ma nace to in ya shiga da kayana zansa danni
ba anko zan sa ba tace me zaki sa?nace kayan gun
yayanmu,a falonmu su hajiyar maska ce da sauran
dangin alhj wadanda suka zo biki na rusuna na gaishe su
sannan na shiga dakinmu sai da naci abinci sama sama
sannan nayi wanka ina gaban madubi ina shafe shafe
waya tayi kara na dauka ga mamakina sai naga lambar
yayanmu ina da lambar amma bai taba kirana ba nima ko
da wasa ban kirashi ba nasa kunnena ban ce komai ba
inaji yace hello?sannan yace kina jina?a kasalance nace
umm da wani abu nake ji yana fita daga wayar zuwa
cikin kunnena yana raba ma jikina qani sako ne mai
wuyar fassara yace me kike yi yanzun?na samu kaina da
rike murya nace mashi ina shafa mai ne yace to kiyi
kwaliya da kyau amma kar ki kula ko wanne saurayi
kinjini?nace eh dukkanmu muka yi shiru bai kashe wayar
ba nima haka can yace to sai mun hadu a can ya kashe
na rungume wayar a kirjina ina jin tamkar shi na
rungume,soyayya kenan ban taba tunanin akwai ranar da
zata zo na shiga irin wannan halin ba sai gashi yanzu ina
ta nutso cikin kogin son wanda bai ma san inayi ba,Allah
kenan shi ne mai iya sanya fari ya koma baki.Kwaliya
sosai nayi tamkar ni ce amarya nasa lesa din da ya
umarceni nasa ya shiga da gwagwaron sai takalmi da
jaka su ma kalan gwagwaron ne ni kaina dana dubi
madubi sai da naji tsoro don kyan da nayi wayar Mami
na kira tace min tana can hotel din na kira Amira tace
min tana mota ne taga an gama kwashe mutane shine
taga kabir ta tambayeshi ni shine yace kamar ya ganni a
can ace mata ina gida ko fitowa banyi ba na mike na cire
gwagwaron na rike na fito falo dankwalin na rufa kaina
nayiwa mama sallama tace kai kin ko yi kyau,iman yau
dai ba zancan hijabi kenan?nayi murmushi na fita ina isa
harabar ajiye motoci duk an gama kwashe mutane sai
kawayen amarya na nufi waje da nufin in hau mashin sai
ga yaynmu shi da Nasir da wani abokinshi ya dubeni
yana daga cikin yayi min alamar in tsaya da ido na ko
tsaya ya fito ya kirani gefe yace kin ganki kuwa?kinyi
kyau fa nace nagode yace to ya baki tafi ba?nace ai
yanzun na fito shine naga an watse sai kawayen Amarya
yace kina da kudin liki ne?nace ina dasu amma ba
sababbi bane yace ok bari mu shiga ki amsa na bishi
abokanshi na zaune a falonshi ya shige uwar dakinshi jim
kadan yace Iman na ce na'am yace zo na shiga da
sallam ya amsa sannan yace shigo mana kin tsaya nan
kudi na gani a kan katifarshi ga yan ashirin ga yan
hamsin har zuwa dari biyar,ya dubeni dauka wanda
kikeso na sa hannu zan dauki ashirin ya dafe hannuna
sannan yace ki dau wannan yan dari biyu ne,ya samin a
tafin hannuna na gode na fada ina kallon idonshi,Man din
akwai sirrin kyau mai birgewa muka fito falo ismail ya
dubeni yace kai maska wannnan yarinyar ko dai kai kake
ma kanka farauta ne? Sai naga yayi kicin kicin da fuska
ya harari Ismail yace ku kun cika yarda girma ban da
yarda girma menene na cewa inayi ma kaina farauta?
bani son haka,jikina yayi sanyi zan fita yayanmu ki jirani
zan sa akaiki
Ina tsaye a bakin gate yazo ya dubeni menene kike bata
ranki?na dubeshi ba komai ya juya ya kira musa musa
direba yazo yace ina zaka na ganka da key a hannu?yace
haj ce ta aikeni gidan haj laure,yace to ka kai Iman gurin
party nan hotel yace to can na sami su Mami da kowa
yana ta hidimominsa inata neman Amira sai can ita ce
ma taganni muka zauna kujerun gaba na ce uwar sauri
shine kika wani taho Amira tace kar kiga laifina yayanku
Kabir shi yace min kina nan,nace don ni ce zan shirya
gun ba?dole na riga kowa zuwa yana sani don dai ya
dauke ki ne ta ce anji ki min shiru mu bar zancan.Biyar
saura ango da amarya suka zo less dina na gida irinshi
amarya tasa nace gara da na sa wannan din na dubi
ango sanye yake da wata dakakiyar shadda ruwan
sararin samaniya tamkar less din jikina ina cikin mamaki
Amira tace kunyi anko ke da ango sanya gwagwaron ki
nasa na gyara cikin raina nace kila ma don muyi anko ne
yasa yace nasa,mai gabatarwa ya fito yana kiran
kawayen Amarya bayan bude taro da addua suma
abokan ango an kirasu yawanci duk turawa ne,sai
kadan,Nasir da Mami aka hadashi tako sha harara gurin
ango can aka kira sunana Iman idris zata ba amarya
shawara ba don na iya turanci ba da nasha kunya
Amarya ta cika don haushi niko duk na tsargu Amira
tace don Allah tashi kije mana nace Amira bansan me
zance ba dadai tun a gida ne aka sanar dani da na
rubuta ana ta kiran suna na na dubi yayanmu yamin kar
da ido fuskarshi ba walwala na mike daidai lokacinda mai
gabatarwa yace ko bata nan ne?Iman Idris a hankali
nake tafiya har naje kan abinda aka tanada don hawan
mai magana da sallama na soma sannan nayi wa Annabi
salati kafin na soma bata shawara akan zaman aure na
kawo ayoyi da hadisai wadanda sukayi magana akan
zaman auren da hakkokin auran kansu.
Dana gama na sha tafi gun mutane na koma na zauna
haka akayi ta gabatar da komai har zuwa sanda zasu
ciyar da juna don kar in gani na dauko wayata ina ta
danne danne zuciyata kuwa sai zugi takeyi,can na mike
zan fita Amira tace ina zaki je gashi shalele na ta waka
yanxun za a soma rawa dole na tsaya suna shiga
yayanmu a tsaye yake baya rawa amma Amarya har da
juyi nace wawiya ba kunya ba jan aji nice na fara liki ina
ta zuba musu kudi cikin dauriya yayanmu ya juyo ya fara
zuba min na juya zan fita ya rike min riga amma ba
wanda zai kula don ta gefe ya rike ya dan matso kusa da
kunnena kar ki fita yanzun ki min rawa din dan ban iya
rawa ba nima ai ban iyaba Amarya ranta ya baci ta
dubeni ashe ita ta kula da abin da mukeyi guri ya kaure
liki wasu sun sha nice amaryar ne?ko ra'ayi ne?oho sai
ni suke ma liki gudun rikici yasa na fita abina na koma
na zauna,Amira tace yar gori a ina kika sami kudi kike
bari dasu?nace shi ya bani dubu ashirin kuma na like
musu abinsu Amira tace duka?nace a'a Mami ta iso
gunmu taja hannuna zo muje ki dan taka nace bana
rawa fa ta dubi Amira tace duk yanda suke da yayanmu
wai bazata yi rawa a bakinshi ba Amira tace ai ta basu
shawara yanda zasu zauna da juna,Mami tace yauwa na
tuna dazun me yace miki da naga ya wani karkato dai da
kunnank?nace ba zan fada ba Amira tace ashe kin lura
kema?sunyi kyau tamkar itace amaryar nace kun cika
sharri Mami tace to zamuje kiga hitunanku da masu hoto
sukayi suna ta saidawa a waje mu uku muka fita wajen
hall din gsky mami ga hotunanmu nan nida yayanmu
wani tare mukayi wani ni kadai wani shi kadai an barbaza
wanda yafi birgeni wanda mukayi da yayanmu ya dan
karkato yana min magana fuskarshi a sake ni kuma ina
murmushi fuskata tayi fayau idanuwana sunyi haske
kitsona ya zuba a kafaduna Duk masu daukar hoton nan
sai da na bisu na saye hotunanmu sannan muka koma
ciki nace kije kunnan gidado tace a ina zaki ganshi ta
fita kiran,ni kadai na zauna can ji an min sallama cikin
hausa da bata goge ba yace na zauna?nace zauna mana
ya zauna nadan dube ahi kamar na so na gane fuskarshi
yace baki ganeni ba?nace ban ganeka ba yace abokin
Maska da muka zo daga England nace ok na ganeka,yaci
gaba da cewa ina sonki amma Maska yace krt zakiyi?
nace haka ne yace toh zan jiraki mana nace kayi hakuri
dan zan dade ban gama ba,koyaushe zan jiraki,muna
cikin hirar ne can idona ya kai Ango da Amarya harara
ya sakar min na dauke kaina daga duban gunshi a raina
nace kai gara kai ka kama taka naci gaba da hirata jim
kadan wayata tayi kara na duba sai naga lambar
yayanmu da sauri na dubi gurin da yake bashi nan sai na
dauka nace hello ya katseni ki sameni a wajen hall din
nan gurin wayoyin nan ta kofar baya na fita da sauri can
bayan wasu furanni na ganshi na isa cikin fargaba ya
dubeni fuskarahi ba annuri yace me gayen nan yace
miki?nayi shiru ba zaki gaya min ba?ya daka min tsawa
jikina yana rawa nace yace ne yana sona,da sauri ya
dubeni sonki?.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Na gyada kai alamar eh yace oh my God bana sanar
dashi krt zakiyi ba?to naji me ke kikace mishi?nace nima
haka nace mishi ya dunkule hannunshi ya naushi dayan
hannun sannan ya dinga kai kawo a filin gun mamakin
shiga damuwar dayayi na tsaya yi a raina nace ya bar
amaryarshi yana yin abin da bai dameahi ba,kamar ya
san tunanin da nakeyi sai naji ya dawo gabana daf dani
yasa hannuwanshi ya rike kafaduna yace kar kiga na
shiga wannan halin kiyi tunanin inayin shishigi ne a cikin
abinda bai shafeni ba,no yin karatunki shine kwanciyar
hankalina kuma muddin na yarda wannan dan iskan ya
soma cusa maki ra'ayin sonshi to zai min illa domin
nasan Adam ba sanin yau ba yana da sa'a a rayuwarshi
zai yi wuya ya nemi abu bai samu ba tamkar ni yake,so
bazan yarda da huldarku ba,nayi shiru ina tunanin
wannan iko na yayanmu tunda yace tamkar shi yake sai
ma naji ya burgeni na dubi yayanmu nace to in dai zai
bari na gama karatuna why not na aureshi in kasan yana
da hali mai.....kafin na karasa sai saukar mari naji cikin
firgici na dube shi shima ni yake kallo ranshi a
bace,hawaye ya zubo min a kan fuskata yace kina hauka
ne?kike kiran wani ya aureki?sai kuma naga yayi shiru ya
juya min baya,Aminatu yaja sunan kafin na amsa sai ya
juyo da sauri ya zo guna ba zato sai gani nayi ya
rungume ni tsam tsam a jikinshi gabana yana faduwa
jikina na kyarma amma na kasa kwacewa ,nama kasa
kokarin kwacewar gwaggwarona kaina ya fadi gashina ya
bayyana a waje kitsona ya sauka a kan kafaduna ni kam
tamkar an jona ni a lantarki haka nake jina,cikin sanyin
murya yake magana,Amina bana son ki saurari Adams
zaiyi ma rayuwata illah nafi son sai kin gama karatu ne
kafin ayi maganar auranki,ki fahimceni ba ina nufin
hanaki aure bane a'a ina son kiyi krt ne,wani haushi naji
ya kamani domin a lokacin nayi zaton zai ce min yana
sona ne,yanda naga yayi mugun shiga damuwa sannan
ya kamani ya wani rungume yana faman ajiyar zuciya
tamkar jinjirin daya kwana uku ba tare da ya sha nonon
uwarshi ba ina fama da sonshi tamkar na mutu shi kuma
ya nan yayi aurenshi sannan ya zo ya wani rungumeni
yana min maganar banza nasoma kici kicin kwacewa ya
girgiza ni yace come on my sister ki.....kafin ya karasa
maganar da zaiyi sai jin salati mukayi akanmu,cikin
tsananin tsoro na juya su dayawa daga cikinsu akwai
kannanshi da Amarya da Haj Laure uwar Amarya da
wasu daga cikin danginsu,duk tsoro ya kamani,Amarya
tasa kuka na dubeshi shi kuma ko ajikinshi duban su ma
yake yi na tattare zani zan gudu sai naji ya sa hannu ya
riko ni.......Masha Allahu Alhamdulillah, mun Kammala
littafi na daya Mu hadu a littafi na biyu
jinjina agareki HALIMA ABDULLAHI K/MASHI
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Share








DOCUMENT CREATED BY
ZAHARADEEN SHOMAR
WHATSAPP ,,08168575100

7
8
9

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login