Showing 21001 words to 24000 words out of 26020 words

Chapter 8 - TAWA TA SAME NI BOOK 1 COMPLETE DOCUMENT by Halima Abdullahi k. Mashi .txt

na juyo na
koma gida ikon Allah nema ya kaini kofar dakinmu a nan
na zube ban kuma sanin in da kaina yake ba na dai
farfado na gani a gadon asibiti Mama tana zaune a kan
kujera tana rike da hannu na wanda aka sa min karin
ruwa ta min sannu na amsa da kyar a hankali na soma
tuno abubuwan da suka faru shi kenan yayanmu ya zama
na Anty Mimi ko shakka babu yana mutuwar sonta,na
tuno wata rana ina shara a dakin yaynmu har na gama
zan fita yace nazo nan na juya na koma nace gani yace
baki sa turaren daki ba nace na mance ne,na shiga
bedroom din shi idona ya sauka akan wani kyakyawan
frame kamar kaida in dai zan shiga uwardakin yayanmu
to ba abinda nake fara kallo sai wannan frame din yana
da kyau ga dauakar hankali gashi saitin kofa da ka shigo
shi zaka fara gani,na manta batun turaren daki na tsaya
duban frame rubutun jiki yan kanana shi yasa ban taba
karantawa ba amma lokacin sai na hangi rubutun saman
kamar hausa akayi nayi mamaki frame mai kyau da
shegiyar tsada irin wannan amma da hausa na ce kai yau
sai na dauko shi na karanta duk da wane yare ne na
duba dakin ko naga abinda zan taka don yayi sama sosai
ba wani abu mai tsawo sai tebur karami kuma na glass
ne na jawo shi a hankali na taka daya ke nima ina da
tsawo na dauko,tabbas da hausa akayi rubutun a saman
an rubuta:
Zinariyata Zuciyata ta jima tana begenta daga lokacin da
idanuna suka fara ganinta,na tsunduma a sonta duk
karancin shekarunta duk sanda na dubi idanunta sanyi
kasala sha'awa suna gajiyar dani bare in naji kamshinta,a
lokacin da nayi nisa da ganinta sai barci ya kaurace ma
idanuna sai tunaninta bana jin dadin wani girki sai nata
Allah ka azurtani da aurenta domin na samu ni'imarta
har ka azurtani da 'ya'ya masu albarka daga gareta
(A)amin.
jikina yayi sanyi sai dai abin daya bani mamaki shine
yanda (A)a cikin (A)tamkar irin na zoben da yayanmu ya
bani a cikin kayan tsaraba nace kai kilan ma ba (A)guda
biyu ba ne wani tambarin ne na wani camfanin a can
England din,na dubi fulawoyin dake jikin frame din da
tsuntsaye masu ban sha'awa ina cikin juya shi ina cewa
nasan Mimi yake nufi,shine Mami tace min baya sonta
ashe ma ya jima yana sonta gashi yace tun tana
karama,ina cikin tunani naji yayanmu daga falo yace baki
ga turaran bane?nan jikina ya soma rawa ina kokarin
maida wa ne tsautsayi yasa na goce,frame din ya fado
sai kan tebur din glass ji kake tats,jikina ya hau bari na
soma tsuma tamkar mazari,na dauki frame din baiyi
komai ba teburin ne ya fashe naga an daga labule da
sauri na dubi kofar yayanmu ne tsaye nayi duba zuwa ga
fuskarshi ya wani daure fuska me ya kai ki gurin frame
kina ganin sirrina ko?hawaye ya soma zarya a kan
kumatuna nace a'a zan goge ne yayi kura ya daka mani
tsawa yi min shiru kuma sai kin biya dukkan abinda kika
fasa min,na durkusa kan gwiwoyina na soma cewa don
Allah kayi hakuri yace ai zaneki zanyi yanzun nan
muryata tana rawa nace please yayanmu ya dubeni cikin
wani yanayi mai wuyar fahimta sannan yace gyara min
wirin ki wuce,ban san kan kwalba nasa gwiwata ba sai da
na gama gyra dakin sannan naji zafi na duba.kamshin
turaren da naji shi ya dawo dani cikin hayyacina ko ba'a
fada ba nasan yayanmu ne ya shigo Asibitin nan ban
gama tunani ba ya kwankwasa kofa ya shigo dama fuska
ta kofa take kallo don haka yana shigo dani muka soma
hada ido sai naga tamkar an kara mashi wani kyau....
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Na lumshe ido sai naji wasu hawaye sun zubo min ina
jinshi suna gaisawa da mama ya tambayeta jikina tace
da sauki ban ma san har na kwana ba sai da naji yace
tun jiya bata tashi ba?mama tace dazun nan ta farka ina
mata magana banji ta amsa ba nayi mata sannu ta amsa
bata kuma magana ba sai hawaye da ke zuba daga
idonta shiru yayi na dan lokaci sannan yace bari inga
likitan mama tace yanzun nan babanku ya tafi gurinshi
tun jiya ma yace ciwon zuciya ne yake son kamata ni na
rasa mai yarinyar nan ta nema ta rasa da har ta sa
kanta cikin tunani,muryar yayanmu naji cikin sanyin shin
nan yace ai maman Sagir cututtuka sunyi yawa ba sai
mutum yana wani tunani ba Allah dai ya sauwake ya
juya zai fita sai ga a
Alhj ya turo kofa yayanmu ya matsa Alhj ya shigo yana
ma mama bayani sun tabbatar da zuciyata na son ta
harbu sannan yace su tuhumeni ko akwai wanda takeso
ne ko abinda ya shafi haka yayanmu yace Alhj bari nima
na ganshi likitan sukace to lokacin Alhj yasa an tashe ni
zaune ni kaina nasan na rame sosai cikin kwana daya
yayanmu ya dubeni yace sorry Iman na dubeshi yaune na
fara jin ya kirani da Iman na daga kai alamar
amsawa,yace maman Sagir me taci?mama tace bata ci
komi ba yanzu ne dai zan hada mata to amma tace sai
tayi sallah tukunna,ya dubeni zaki iya yin sallar ne?nace
eh tare da taimakon mama nayi alwala muna fitowa daga
bayi yayanmu yayi mana sallama yace da daddare zai
dawo haka na cigaba da jinya har tsawon kwana uku
kullum yan dubiya suna zuwa,Amira da Mami nan suke
yini haka yayanmu da yaya Kabir nan sau uku suke zuwa
sai dai duk lokacin da yayanmu yaga yaya Kabir
haushinshi yake ji, gudun fadan alhj yasa kishiyoyin
mama suka zo sau daya kuma basu kawo mana abinci
sai dai anty Yagana da maman su Amira kayan ciye ciye
kam yayanmu ya kashe kudi har Anty Mimi ya kawo ta
gaisheni nasan dai dole tazo ba don son ranta ba,niko
ban ma ji wani dadin zuwanta ba don ma kadan ya rage
ciwona ya dawo musamman ma da naga sun sa anko
yellow kampala sun man kyau sai dai kishi da ya sani
gaba,ban san yanda akayi su yaya Abubkr sukaji ba sai
dai ganinsu nayi yaya Ibrahim ne yake ce min babana
yana nan zuwa,yace a gaisheni naji dadi har ina
tambayarshi yaushe zaizo?yace kilan yau ko gobe nace
kilan a sallame ni yau ai a ranar aka sallameni kafin sati
na dan girgije,yan skull dinmu na comp ma sun zo duba
ni randa na cika kwana goma ranar na koma zuwa
makaranta lokacin saura kwana hudu bikin yayanmu su
Mimi duk sun damu da bikin sai rawar kai suke yi har
Mami na cewa da ban warke ba bikin ba zai mata dadi
ba sannan suna son kudi gun yayanmu nice ma zan
amsar musu nace ke Mami ki rabu dani ba wani kudin da
zan tambaya a raina nace in baku san dan dole zan
zauna a garin nan ayi biki ina nan ba da ba dan mama ba
zata yarda ba da naje tudun wada gidan kawuna sai
angama sai na dawoa dare yayanmu ya aiko nazo lokacin
ina zaune a falo ni da mama tana nuna min memo data
buga da sunansu au Jamila da Sagir sai agogon bango
suma guda dari wai in bashi ince ni na buga na dauki
guda daya ina dubawa hotunansu ne sunyi kyau sosai na
hadiye wani abu da yazo min wuya na dubi mama nace
sunyi kyau amma kin sha kudi tace yaya za'ayi ai yana
da mutunci sosai Abdulrahim na ce umm waya baki
hoton su?tace gun Kabir na amsa na rike hawayen idona
lokacin da naga sunana a matsayin wacce ta buga kafin
nace wani abu ne jamila ta shigo anty Iman kizo inji
yayanmu na danyi tsaki nace kice kaina na min ciwo ba
zan iya zuwa ba a raina nace ba zanzo ba tunda ka
kama matarka a hannu kasata aikin,Mama ta dubeni kije
mana Iman kije mishi da agogunan nace banjin dadi ne
mama tace daure na mike na ciccibe kwalin agogunan na
ce bari na kai wannan sai na kuma zuwa na dauki dayan
da kyar nakai dakin nayi sallama na shiga yana zaune da
kaya a gabanshi fuskarshi babu walwala ya dago kai ya
dube ni yaya kai din na dan lumshe ido sannna nace da
sauki na kula tun da nayi rashin lfy sam baya son yimin
tsawa ko fada ya dubi kwalin dake gabana yace menene
wannan?mYaya gudummuwata kenan a ba jama'a. Ina
zuwa na koma na dauko dayan kwalin na samehi yana
duba wa ya dubeni yace amma sunyi kyau mun gode,na
danyi yake nace um ya turo min kayan gabanshi yace ga
naki kayan bikin harda ankon,nace ai Baba yayi mana
ankon,yace duk da haka ki dauka ina son ki kaima telanki
da yake maki dinki don ya iya sosai nace yaya Sulaiman
ne ya ma samu aiki yanzu bai cika zaman shagon ba sai
dai yaranshi,yace to kikai inda za'ayi maki mai
kyau,takalman ki jakunkuna sai yau za'a kawo anjima
kadan gidan Nasir na manta su nace na gode ya kuma
duban hannuna ke bakiyi lallen bane?nace eh yace kiyi
gobe zanzo na kaiki saloon mamaki ya kamani nace ko
dai yana zaton da Amaryar yake magana ne?ni da ban
taba shiga motar shi ba,na boye mamakina nace ai bana
sa relaxer kitso nakeyi yace to kiyi kitson kinji ni?nace
to.kaya ne kala shida less biyu super biyu sai material
daya sai shadda,shaddar din kakkiya ce ta sha aiki riga
da zani sitayal din ya hadu ga shaddar mai tsada,turare
kala uku masu kyau da mayukan shafawa sai sarka da
'yan kunne,Mama ta dubeni tace oh ni Habiba wannan
hidima tayi yawa, shida ke cikin biki kayan nan Iman
ba'a karbe su duka ba bani wayata gata can a chargy,na
dauko mata shi ta kira tana mishi korafin yawan kayan
bansan me ya ce mata ba naga tayi murmushi tace ai
kanwarka ce kowane ai ta maka kabiyata kenan?can
kuma tace to shi kenan an gode Allah yasa ayi wannan
biki lfy ya kuma bada zaman lfy.Washe gari na shirya sai
tudun wada na kai dinkunan a can nayo kitsona da lallen
filawa mai ratsin ja,gidansu Amira na biya tace min
zakije Arabian day din ne yau?nace Mami tay min
magana amma da kyar in zani kinsan bana shiri da
Amaryar,
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Amira tace indai ba zakije ba nima ba zani ba dama
domin ke zani nace to bari in zani zan maki waya ba
karfe hudu bane?na duba lokaci a wayata karfe biyu da
minti arbain nace bari na shiga gida dama dinki nakai
tudun wada,Amira ta dubeni tace name kuma ba kinyi
anko ba?nace jiya yayanmu yace ga nawa ankon dana
duba sai naga ba anko bane ya dai minne ne kala shida
harda takalma yau da safe ya bani takalman kala
uku,Amira tace gsky jininku ya hadu,sanda baki da
lafiyannan kar ki ga yanda ya damu ba dan munsan
yanayin rayuwar shi kenan yin alkhairi ba damin zargi ko
sonki yake na kai mata duka nace me zukekiyar mace
kamar Mimi me zaiyi dani?Amira tace Iman kina da kyau
amma sihirtacce ne sai na kusa dake komai sonki ko
kuma yasan kyau zai gane kiga Mimi mai mata kallon
gane muni zai ga muninta don tana da goshi da
kuma....na katse ta mu bar zancan nima ai in an kura
min ido za'a ga muni nawa,Amira tace Allah baza'a gani
ba sannan ne ma za'a ga kyaun ki nace um bari na shiga
gida. A gurin Arabian day kowa yayi kyau Amarya cikin
jallabiya baka da dan hijabi tana zaune a gun da aka
tanadar mata muka shigo nima sanye nake cikin
Jallabiya mai hawa biyu baka da ja hijabina da takalmina
jajaye ne, Hijabin dan karami iya wuya su mami da Anty
Mariya da kawayenau sai kai kawo suke ni kam guri
guda na kame mai kyamarar sai daukata yake tamkar
nice Amarya,ga masu Hotuna,Amira tace kai Iman kin
tafi da imanin masu hoton nan sai ke suke dauka kafi n
inyi magana Bilkisu tazo tace kai bafa wannan bace
Amaryar ba kun ganta tayi maku kama da Amare?nan
suka juya suna daukar ko ina haka taro ya tashi lfy ba
tashin hankali,washe gari sister day da safe yayanmu ya
aiko nazo dakinshi na same shi ya dubeni me kike
yanzu?nace ba komai yace to abokaina ne na england
yau zasu iso ina sonki shirya masu abinci kaloli masu
dadi don gidan Nasir zan saukesu kamar nawa ake
bukata?ko muje kasuwar tare in yaso sai ki duba
abubuwan da zakiyi amfani dasu gaba daya a wajen
girkin?nace to bari na sanar da mama yace shima bari
yayi wanka,cikin riga da wando na material ruwan
madara da filawoyi jajaye dan hijabina dan karami sai
takalmi sai abinda ya kamata na siya da kulolin girkin da
zan masu har da na sha ina tsaye jikin motarshi ya fito
daki sai da ya shiga su Sa'a da Bikisu da Maryam
kanwar anty Mimi dukkansu ni suka tsura ma ido na
shige mukayi gaba,ba wani hira muka yi ba ya dai sa
wakar tashi dakusan duk kullum sai naji ta a dakinshi tun
ina jin haushin wakar har yanzu nima ina sonta kuma
nama sai album din wakokin mata celine dion ina
wakokin don sanyin muryarta,wayata ta soma kidan kuch
kuch hota hai na kai hannu zan dauka sai naga yayanmu
ya dafa wayar ya dauka ya duba sunan Amira ya gani sai
ya mika min nayi ajiyar zuciya sannan na amsa
hello,Amira yaya dai?tace kina ina ne?nace muna hanyar
kasuwa ne menene?tace na sha kina gida ne na
shigo,nace bana gida in na dawo zan shigo gidan muyi
aikin abincin baki tace to sai kin dawo.
Sayayya mai yawa mukayi komai nace biyu sai yace na
dau uku,gidansu Amira ya saukeni ta fito muka kwashe
kayan,mun shirya abinci kala kala dana sha a sabbabin
kulolin da muka siya muka shirya muna gamawa muka yi
wanka na shiga kenan don nasa kaya yayanmu ya kira ni
nazo yace kun gama?nace eh yace to ga musa dryva nan
ya kaiki gidan Nasir ni kuma zamuje mu dibo su sauran
minti biyar su shigo KD daga Lagos nace to,banyi wani
shafe shafe ba nasa atamfa charas babba riga da siket
ne dinkin shot play sai karamin gyale muka jera abincin
nace Amira tazo muje tace aah ba ruwana da wannan
yayan naku zai iya kado ni,nayi dariya nace shi
kenan,nayi kusan minti talatin da zuwa sannan suka iso
cikin harshen turanci suke magana nima na gaishesu
cikin yaren nasara,Nasir yace ko inyiwa Mami waya ne
tazo ta taya yarinyar ne?ya harareshi yace ban ce ba
nikuma bayan sun zauna na gabatar masu da kayan ciye
ciye da shaye shaye na gida dana company,wani shima
bakin fata ne duk sanda na dubeshi sai mun hada ido
dashi haushinsa ya kamani can kuma wani daga cikinsu
yace Maska wannan itace Amaryar?yace a'a ita kanwata
ce sai yace to zaka bani kanwarka?don tana da kalar
asalin yan Nigeria yayanmu ya daure yace baya son
wannan maganar bakin fatar dake kallona yace Maska ni
zaka ba wannan mai kyaun din,don bana neman wata
kasani,y hiayanmu bai kuma magana ba ya dubi Nasir
yace bari na kaita gida na dawo,ya dubeni tashi muje na
dube su nayi musu sallama, a mota yace in zaki fita ki
daina shafe shafen nan na dubeahi nace ban shafa komi
ba sai hoda,yace duk inda kikaje sai ance mun ana sonki
ni kuma krt nake son kiyi ni dai nayi shiru yace kin tuna
alkawarin da kikayi min ko?nace eh yace to kar ki yarda
ki yi wasa da cika alkawari kin jini?nace e.A kurarren
lokaci muka isa gun Sisters day Angoma bai zoba na
tambayi Mami tace min yayi ma Amarya waya yana tare
da baki muka zauna,nanma ba laifi bikin yayi kyau ranar
ne akayi sa lalle banje ba, washe gari lunching a
hamdala hotel za'ayi sanye nake cikin dogayen riga na
shiga dakin yaynmu dan amsa kkranshi yace zauna na
zauna a kasan carpet ya dubeni yace yau wane kayan
zakisa,nace anko zamu sa yace to kar kisashi kisa sky
blue din less din nan,na gama kanki ba tare da wani
tunani ba na zame dan kwalin kaina kananan kitso ne
2step mai zigzag,yace to rufe ki shirya sosai ya dubi
dakinshi yace ga kayana nan dukkan abinda kike so ki
dauka na baki ki dauka nayi shiru na sunkuyar da kaina
ya taso ya tsugunna gabana Aminatu ya kira ni a hankali
cikin sanyin nan nashi na dube shi nidai da zance frame
din nan nake so amma sai nayi shiru ya kuma kiran
sunana na dube shi yace kina son Fridge?nace a'a TV
fa?nace a'a,Radio fa?nace a'a yace to me kike so?na
dubi hotonshi yana sanye da farin JC mai ratsin ja yayi
tsalle zai kama kwallo ina balain son hoton ya dube ni
shi kike so?na kada kai alamar eh bayan shi fa?nace ba
komai ya mike ya ciro min hoton ya hado da wani shima
mai kyau cikin jan JC kan kujera ya zauna sannan ya
kama hannuna gabana ya fadi naji wani yarr a jikina ya
rike yatsuna da zoben nan yake jiki wanda ya kawo min
tsaraba kar ki rabu da wannan zoben komin wuya kinji?
kasa magana nayi,yace wannan lallan ya min kyau waya
miki?kafin na bashi amsa sai akayi sallama gami da
shigowa gaba daya tsoro ya kamani da na juya naga
Anty Mimi itama tsoron ne da mamaki a kan fuskarta na
dubi yayanmu shi ko namijin duniya ko a jikinshi ya saki
hannuna yace Mimi lfy na ganki yanzu?ta juya da gudu
tana kuka yace me aka mata oho,yayi tambaya ya ba
kansa amsa na mike da hotuna sai nayi gidan su Amira
ban koma cikin gida ba ita ko Anty Mimi dakin Haj Yaya
ta nufa da kukanta da komai,ta sanar da hajiyan komai
haj yaya ta cika tamkar zata fashe ta dubi mimi tace
kince yana rike da hannunta?Mimi tace sai kallon juna
suke yi,haj yay tace lallai ma yaron nan jiya fa haka su
Bilkisu suka ce min sun ga ya shiga mota da ita banyi
maganin abun ba bari in kirashi,ta soma daddana waya
tana fadin kannanshi bai taba sa su a motarshi ba sai
wannan bakar mummunar yarinyar,ta soma magana kazo
yanzun nan ta kashe wayar taci gaba da fadin sun
asirceshi shima kamar babanshi na shiga uku ni Murja
tsakanina da Habiba Allah ya isa ban yafe mata
ba,yayanmu yayi sallama ya shiga dakin tana zaune kan
kujera sai cika takeyi ya ballama Mimi harara sannan ya
shiga ya zauna,duban wulakanci ta mishi sannnan tace
yanzu kai saboda Allah me ke tsakaninka da yarinyar nan
Iman yar karama da ita shine ta ke juyaka ta shanye ka
nan gaba ma kila kace aurenta ma zakayi ko?ya
sunkuyar da kai kasa bai amsa mata ba tace jiya ina
kukaje?yace Haj waya kawo maki wadannan kananan
surutan ne?nifa mutunci ne tsakanina da yarinyar nan
tana hidima dani sosai don Allah haj ki daina jin zancan
mutane yarinyar nan ita da uwarta suna da kirki kum....ta
katse shi an baka kaci a cikin abinci ba dole kace haka
ba na gaya ma ka koyaya ni zan mummunan saba maka
ta nuna Mimi wannan ita menene laifinta?da zaka sasu a
kasuwa sai kowa ya riga zabar Mimi kuma zanyi
maganin agola a gidan nan wayarta tayi kara ta dauka ta
duba ka dai ji na gaya maka ga babanku nan ma ya
dawo shi ne yake kira bari naje,ta dube shi sai ka bata
hakuri ai,tana fita ya galla ma Mimi harara sannan yace
ke ma zan yi maganinki bakina hada ni

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login