Showing 3001 words to 6000 words out of 26020 words
Chapter 2 - TAWA TA SAME NI BOOK 1 COMPLETE DOCUMENT by Halima Abdullahi k. Mashi .txt
kawu shi dai habiba yake so mutumcin da
baba yake dashi a idon malam shi yasa har ya amince
koda kauye suka ji wannan zance sunyi murna don akwai
zumunci mai karfi tsakanin gidan dagaci da gidan
liman,kauye aka koma akayi biki sannan su mama da
baba suka dawo shekara biu da aurensu baba yayi kudi
sosai da gwanjo tuni ya gina gidanshi a unguwar sanusi
ga motocin hawa da na haya da ya sai ma mama sannan
ya tallafi yan uwa na kauye hakika yana da halin kanawa
na asali don akwai taimakon na kusa dashi haka ya debo
yayan yan uwa sa daga kauye ya sasu a makaranta dan
yana da haushin rashin bokon da baiyi ba danma
cudanya da mutane yasa ya fara jin dan turancin sa na
yan kasuwa matsalar baba da mama daya shine rashin
haihuwa har wannan lokacin mama ta fishi damuwa shi
ko ko a jikinshi yace Allah baya barci a gefen mama ita
ma tana taimakawa yan uwanta dama tuni daga dagaci
har liman sun keta hazo sannan angyra gidansu tsohuwa
Amina(kakata) sun kaita ita da abokiyar zamanta harda
yayyan babana,su mama dai kowa a kauyen ya gama
zuwa a cikin iyaye da yayye sannan suma suka je ita da
babana.kowa yaje sai ya roka masu Allah ya basu
haihuwa har cikin dangi sun fara korafi gami da nuna
masa ya kara aure ita ko tsohuwa Amina macece mai
nagarta da ibada da yarda da kaddara don haka itace
mai tsawatarwa sauran yan uwanta da kannen alh idi
(wato babana)takan mika lamarinta ga Allah don haka
kullum ma tana yi masu adduar Allah ya basu yaya na
gari masu albarka,shekaru goma da aurensu Mama na da
babana sun dawo ummara ta dawo da jinya mai tsanani
bayan jin jiki da jinyar asibiti sakamako ya fito cewa tana
da ciki fadar farin ciki ma bata baki ne,anan da kanshi
baba yake mata rubutu take sha..... Ku ziyarci blog
dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Wata tara da 'yan kwanaki ta haifo ni sankaceciyar kowa
ya zo barka sai ya yaba girma da gashina sai dai ni baka
ce tamkar mahaifina tun ina yar jaririyata har yau ban
canzaba, dangin babana na dauko domin gaba dayan yan
uwanmi dangin baba kamar mu daya muna da dan kyau
daidai namu sai anan na dubi Amina nace kin dai ganni
har yau ban canza ba na cigaba da cewa dangi sun
kwararo daga kauye da birni anan naci sunan tsohuwa
Amina, kawar mama kuma makociyarta itace ta ba da
shawarar a kirani da iman,na taso cikin gata da tsantsar
so gun iyayena da yan aikinmu da yayyena wadanda
babanmu yake riko,shekara takwas na halarci makaranta
nursery mai suna salmat intl dake kasuwar santara
market makarantar yayan masu kudi ce don haka krt ba
wasa duk lokacin hutu babana ya kansa a kaini kauye
don yace asali mafari wannan yasa na saba da kakata
Amina da yan uwana 'ya'yan baba lami mata sa'anina
Hassana da Ussaina muna wasa dasu kuma sune suke
kaini ganin dangi a sauran kauyukan,ina matukar son
kauye musamman yanayin damina tayi min a garin
domin muna zuwa gona kakata tana ji dani don haka
nima ina sonta suma dangi kowa na sona kawunnaina da
liman suma ina zuwa in yi masu kwana biyu yau ina nan
gobe ina can gata dai gani nan cikin sai in hutu ya kare
zamu dawo wani sain da kuka nake dawowa a hado mani
tsarabar kauye mai yawa dangin uwa da na uba sannan
mu dawo tare da su yaya Ibrahim da yaya Abubakar,yaya
Abubakar dan baba lami ne shiko yaya Ibrahim dan Baba
Auwal ne(wato dan kishiyar kakata)tun kan a haifeni
suke gidanmu kuma suna makarantar gumi college SS2
don haka tare muke zuwa hutu kauye dasu,kuma muna
kama dasu don duk wanda ya ganmu yasan yan uwa ne
saboda kokarina a kai ta turanni gaba a makaranta
sannan kusan kowanne malami ya sanni don haka ina da
shekaru goma sha daya na kammala primary din tare
kyaututuka masu yawa muna zaman jiran fitowar
sunayenmu ne,na fuskanci matsala ta soma kunnowa
gidanmu in da mama ta tada hankalinta ni ban san dalili
ba amma nasan nasha ganinta tana kuka in nace mama
menene?sai tace idonta ke ciwo kuma koda yaushe
zanga anty yagana kawar mama tana zuwa gidan su
shiga daki da mama suna yan shawarwari,ni bansani ba
wai ashe baba ne zaiyi aure da wata banufiya mai suna
fati kuma ance ma mama bata da mutunci shine hankalin
mama ya tashi tace da baba gsky ya canza mata sai
baba yace karyar mutane ce kawai ya dinga lallashi gami
da ban baki sannan ya kara mata jari har na naira dubu
dari takwas dama tuni ya sai mata motocin bus guda
biyu da babura ana mata haya dasu,anty yagana
makociyarmu ce yar asalin maiduguri ce amma zama ya
kawo yayarta da mijin yar in da suke zaune kurmin mashi
yayarta ce ta aurar da ita ga wanda take so Alh shu'aibu
ma'aikaci ne a water board, tana da yara ukku kusan
tare aka haifemu da yarta ta fari mai suna saudatu,suna
amintaka da mama sosai haka ni da sa'adatu
makarantarmu daya,bayan haifuwarmu ne anty yagana ta
kara haifuwar yara biyu Nurfa da abida,Mama ko shiru
tun daga kaina,anty yagana itace ta ba mama shawarar
su hada jari su soma harkar yan kunnen gwal da jallabiya
da zannuwan gado suna bada sako ta hannun wani
abokin Alh Shuabu ne mai suna Alh Mukhtar Maska
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Dan zinare ne a kasuwar sheikh Abubakar gumi yana da
shagunan jallabiya da gwala gwalai,shine yake kawo
masu kaya in ya fita dubai harka ta amsu don da an
kawo xaka ga matan manya suna zuwa suna dubawa
suna saya don haka mama ta cire hankalinta daga batun
auren baba,bayan auren amarya Fatima ta tare a dakinta
da farko ta kwantar da kai amma ganin yadda mama ke
facaka da kudi yanda baba ke ji dani sai hankalinta ya
tashi ta shiga tsiro fitintunu iri iri yau tace kaza gobe
tace kaza tasa su yaya Ibrahim da yaya Abubaar a
gaba,a nan mama ta taka mata birki tace kar ta sake ta
takura masu suma gidan ubansu ne in tana jin masifar
tata ta yi da wanda ya ajiye ta bada yara ba,wannan
rigima har gun baba jin bata sami gsky ba shi ne tayi yaji
sai da tayi wata sannan ta dawo,dawowarta shine ya
zama sanadin juya mana baya duk yanda baba yayi sam
baya sauraron mama da farko ban gane ba saida
sunanmu ya fito munci makarantar mu salmat da mama
ta sanar da baba sai yace kar mu dameshi ya gaji da
biyan kudin makaranta,ni ba wani kokari ba shi maimuna
gwarzo zai maida ni na ringa kuka ina rokonshi sai ce
min yayi inyi hakuri shi ya gaji,haka na cigaba da zuwa
islamiya da hadda boko kam ina ganin saudat tuni har ta
shiga SS1 niko ina gida ,anty yagana tace da mama ta
biya mani da ita tana da kudi tace ai ta mashi magana
yace bai yarda ba,wata rana na dawo daga hadda da
rana jugum na samu mama tayi a dole na zauna kusa da
ita na dafa ta nace wai mama baki da lafy ne?tace kaina
ke min ciwo iman,na tashi na nufi gun da muke aje
magunguna na dakko mata panadol na dibo ruwa a kofi
na kawo mata ta amsa tasha sannan tace kije dakin
yayan ki duk wanda kika gani cikinsu kice yazo zan
aikeshi wajen kawunku malam nace nima zanje mama
tace to amma sai kinci abinci ko?nace e nayi sashen su
yaya da gudu,a kofar dakinsu na tsaya nayi sallama yaya
Abubakar shine ya amsa nace in shigo?yace in dai
tsohuwa ce kar na ganta anan(haka su kan tsokane ni
wai tsohuwa)na shiga nace kaine dai tsoho bani ba yace
me yasa zaki sa mana tsufa daki don Allah kije waje
nace naki din aje wajen baka girmeni ba ma zaka ce min
tsohuwa,ya kwashe da dariya yace waneni da girmanki
kece fa kika haifi su kawu da mama da baba anan gidan
haushi ya kamani na hau tsaki irin na shagwaba ina son
inyi kuka nace sai na gaya ma mama na juya zan fita ya
jawo ni zo mana yar kanwata tawan zo mana kiji mama
ta aiko ki guna ne?nace eh tace kazo zata aikemu gidan
kawu malam ya mike ya dungureni shine baki fadi mani
tun dazu ba?ya rike min hannu muka tafi dakin mama
ban san me tace mashi ba na dai ga ta bashi kudi sanna
tace in tafi falo inci abinci kafin ta gama bashi sakon,na
kunna tv na kamo cartoon ntwk ina kallo ina cin abinci
sai naga anty Faty ta fito ni ban ma ganta ba sai gani
nayi an kashe tv din na dube ta nace aunty ina kallon
tom and jerry ne,tace na kashe ko zaki kunna ne?niko
ban san gatse ba sai nace eh cikin masifa tace to zo ki
kunna har ga Allah ni ban san gatse tai min ba sai kawai
na tashi na kunna tv din remote din na hannunta kafin na
juyo sai saukar mari naji dau na yanke da ihu sai ga
mama da gudu ita da yaya Abubakar dama shi akwai shi
da zuciya yace faty me tayi maki,anty faty tace in dole
sai kasan abin da tayi min to ka nemi sani daga gareta
dube ka dan kauye don kazo ka waye shine zaka kawo
mana raini ko?yace naji ni dan kauye ne ke baa ma san
asalin naku kauyan ba,don ba muga yanuwanki ba waya
sani ma ko daga sama kika fado banza yar iska haka
zaki kare a neman asiri,sai tayi kanshi da zagi harda
duka nan da nan ya sharara mata mari gami da ture ta
mama da tuntuni take tsaye tace kai Abubakar wuce
kasai kabar aiken sai anjima,ta nuna ni ke kyma yi daki
na mike sannan na jiyo mama tana cewa kin gani ko faty
wannan shine abinda na jima ina sanar dake ki daina
shige ma yarannan kinki ji to kinga irin.......kan mama ta
karasa sai ta katse mata hanzari da masifa ke munafuka
bake kika sasu ba?to albishirinki yau dinnan zaki san
matsayi na bakinsa Abubakar ya mareni ba?zaku gane
baku da wayo yau,nayi shiru a daki ina kuka mama tace
to ina jiranki da alkhairi anty Faty tace ni kuma da sharri
nake jiranki yau da nai nasarar rava alkhairi da tunanin
wata ya mace haka zan rabaku da gidan nan mama ta
ce to ai Allah ya fiki kuma ba ya barci kuma yana tare
da masu hakuri ta cigaba da cewa ke ko nasan baki san
haka ba tunda kin yi nisa ba zaki taba jin kira ba to sai
muce Allah ya shiga tsakaninmu da ke in kuma mai
shiryuwa ce Allah ya shiryaki,Ku ziyarci blog dinmu
domin karanta Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
ta shigo ta sameni inata faman kuka ta zauna kusa dani
ta jawo ni jikinta tace iman wace adduar kike min,nace
ina rokon Allah yasa ki daina samun matsala da
baba,mama tace ki hada da babanki shima ki dinga yi
mishi ki roki Allah ya kareshi sannan ya raba shi da
dukkan sharri da ake mashi,nace mama wanene yake ma
baba sharri?tace aa mugun abu ai ba sai kasan me maka
zaka roki Allah ba,nace to insha Allahu zan dinga yi
mishi,da dare sai ga dan aiken baba,yaya Ibrahim ne
baba ya aiko wai muzo ni da mama babban falo babu
neman ba'asi ya dauki hannu a gaban mutane ya mari
mama ga yan aiki ga yayyena ga ni ga anty faty bayan
marin ya cigaba da fada wai kar ya kuma jin an taba
mishi mata inko ta kuma marinta ta mari aurenta mama
tana rike da kumatu sai nan tace cewa tayi maka na
mareta?yace to yau kuke me yasa tun da kuke tare bata
ce kin mare ta ba sai yau kuma tace tana son in rama
mata shi yasa mama tace shi kenan ni Allah ya rama
mani ta shige daki,duk da karancin shekaru na sai da
nayi mamakin baba wai ya rama wa anty mari?na juya
na dubi anty sai naga tana wani ciccika tana batsewa
wai an rama mata, na bi mama daki na iske tana kuka na
dafa ta nima na soma kuka ina cewa mama kiyi hakuri
Allah ya saka maki. Anyi haka da kwana biyu na dawo
daga kitso in da yaya Abubakar ya kaini tudun wada na
mari yaya Abubakr din da wasa don ya dameni da
tsokana tun a mota wai tsohuwa mai dan koko Allah
kashe ki musha gumba,nayi banza dashi sai da ya tsaida
mota sannan na dan kai mashi marin wasa kadan na
bude motar nayi cikin gida da gudu,yace ni kika mara?sai
na rama shima ya fito yana dariya ya biyoni yana kirana
nayi falo da gudu ina cewa so kake in tsaya ka rama ban
kula ba na bude labulen falon na fada sai kawai naji na
bige mutum lokaci guda kuma naji anyi jifa dani ashe
nayi karo da anty faty ne shine ta jefar dani kuma ta
biyoni da duka takeyi yaya da har ya juya da yaga na
shige falo sai kuma yaji kukana nan da nan ya dawo ya
iske anty nata faman dukana cikin zafin rai yake ma anty
magana yace don Allah me yarinyar nan ta yi maki kike
dukanta haka?yanzun nan fa muka shigo?ta juyo kanshi
da zagi da gori,jin hayaniga shi yasa mama ta fito ta
dubeni ta dubi yaya sannan tace Abubakr ba zaku daina
daukar min magana ba ko?yaya yace wllh mama bamuyi
mata komi ba niko sai faman kuka nake ita ko anty faty
sai zage zagenta takeyi jin mama bata kula ta ba sai
kawai ta shaki kwalar rigar mama tana cewa yau din nan
na tsara zaki bar gidan nan duk na cinki miji ya
wulakanta ki amma don bakin naci kin dage kin ki tafiya
ko,ta cigaba da cewa to yau din nan za'a kama kai a
koma wurin mai dattin hula,yaya ya fincike hannunta a
wuyan mama sannan ya daura mata mari yace marar
mutunci yar dangin jaraba rigima dai ta ki karewa har
yamma sai da tayi ma babana aike har kasuwa wai yazo
nan da nan sai gashi lokacin ma kowa ya kama gabanshi
yaya Abubkr bai ma nan ni kuma ina daki mama tana
koya mani karatu sai ganin baba mukayi ya shigo ko
sallama babu ya jawo ni a gaban mama ya hau duka da
wayar wuta ina ta ihu gami da neman taimaki amma ina
mama ko kallo ban isheta ba sai da ya gaji sannan ya
barni don kanshi,sannan ya dubi mam yace ke kuma in
tambayrki?mama ta dubeshi ba tare da tayi magana ba
yace dake muka hada muka sayi gidan nan?mama tayi
shiru yace ba dake nake magana ba mama tace ai ina
jinka yace to ina son daga yau na sakeki saki daya
sannan na barki minti goma ki barmin gidana.....Ku
ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Duk da nike karama ina jin ya ambaci saki sai na kara
yanka ihu itako mama duk da dauriya da tayi don kar tayi
kuka ace gabana sai da kuka na ya sata hawaye koda
mama ta gama kimtsa kayan ta ta fito falo zata tafi na
biyo ta da gudu ina kuka babana yana zaune yana cin
abinci da bai tanka ba sai da anty tayi mashi wata
magana sai yace da mama ki tafi da yarki in kinji
shawarata don ni ynxu nafi son yaya maza daga tsatson
faty ga mamakina sai naji mama tace to Allah ya baku
sannan na gode da shawara amma ko mun tafi da iman
ai kanan nan a matsayin ubanta ko?maimakon yayi
magana sai kawai ya kalli anty faty komi tace mashi oho
sai ya juyo ya kalli mama yace kuje dai sai yanda hali
yayi idan nine ubanta to na aiko maki amma fa gunki
zata ci gaba da zama ba ba tare da mam tayi magana ba
ta jani ko takalmi babu mukayi waje,wannan fita da
mukayi itace fita ta karshe daga gidan babana mahaifi
kuma har yau ban kuma zuwa ba ban kuma ganin
babana ba ko anty fati ba. Muka koma gidan kawuna
marikin mamana daki guda kato bayan sati biyu babana
ya aiko ma mama da dukkan kayanta haka mama ta
cigaba da zaman iddarta har ta gama, itace tayi mani
komi na shiga SS1 a makarantarmu wato salma,ina jin
dadin zama da baba uwa wato matar kawuna suna da
yay biyar yaya suleiman shine babba sai yaya nura,anty
rukayya ke binshi sannan sai nana itace sa'ata sai
karamin su mai sunan kakanmu liman ake kiranshi don
sunan liman din yaci wato isuhu,nana maimuna gwarO
take itama js1,yaya suleiman tela ne kuma yana zuwa
poly ko da yake san da muke a maigidansu saura yan
kwanaki ya gama shi ko yaya ustaz ne don yanzu haka
ya na koyarwa a wata islamiya nan kusa da
gidansu,sannan shima zuwa tashi wato sanawiyya a
unguwar ma'azu,anty rukayya kuma tana aure ne a
badarawa yaya suleiman yana debe mani kewar su yaya
Abubakar don shima yana tsokanata kasancewar mu
abokan wasa ne ya kance mani matar ni kuma ince
mashi ya mani tsufa bana sonshi yaya nura baida faraa
shiya sa nima ban cika kulashi ba,Ku ziyarci blog dinmu
domin karanta Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
wata rana ina zaune daki sai mama ta shigo lokacin
kuma gab da babbar sallah ne mama tace iman shirya
muje kasuwa nace to dama na riga nayi wanka sai kawai
na dauki hijabina mai less a kasanshi nasa takalmina
nace mama na shirya muka nufi kasuwa,bayan mama ta
gama mana yan saye sayenmu nida nana sai tace muje
wajen yan zinari zata sai wani nace to muka je shagon
shi makare da gwala gwalai kala kala da fara'arshi ya
tari mama,naji yana cewa haj Habiba sai yau kikazo
kasuwa?mama tace wllh ko Alh mukhtar maska inafa son
nazo amma ban samu lokaci bane sai yau ya turo mana
kujera yace mu zauna ya nunani yace wannan yarki ce
ko?mama tace aa yace ke yarta ce ko yan mata?nayi
murmushi yace ga murmushin nan irin naki ke ya
sunanki?nace sunana iman yace suna mai dadi,sannan
ya juya gun mama yace kin sami sakona a gun yagana?
don tazo shekaranjiya ta kawo wasu karyayyun yan
kunne,mama tace bamu hadu ba gsky mun dai rabu akan
zata zo nan din yace sakona bai isa ba kenan?mama
tace eh sai ya dubeta ya ce zaki samu ganina zuwa
yaushe?sai nazo gidan naku,mama tace lafy dai ko?yace
sai alheri mama tace to ko yaushe kaxo zaka sameni sai
dai da safe ina zuwa islamiya yace ba matsala zan shigo
tudun wadan yanzu me kike so?mama tace ina son in
saima Iman dubai ne kasan da na daukar mata a cikin
kayan da ka kawo mana wancan sati ukkun da suka
wuce to sai na ga kuma sun mata girma sai naba yagana
tace kace mata sai bayan sallah shine nace bari nazo
gunka ko zan samu wani,yace ba zaa rasa ba in kuma
kinga ba wanda yayi miki to ki sai mata saudiyya mama
ta zabar kirar dubai na wajen dubu tamanin har da abin
hannu guda biyu yace gasky kina ji da wannan yar taki
mama tace kai maska don na sai mata yan kunne?yana
dariya yace sai nazo zan amshi kudin mam tace a'ah ga
dubu hamsin nan bansan zan sami masu tsada haka ba
mukayi sallama ya bani dubu daya yan hamsin hamsin a
cikin kudin nayi godiya muka tafi,bani manta ana jajibir
sallah