Showing 12001 words to 15000 words out of 26020 words

Chapter 5 - TAWA TA SAME NI BOOK 1 COMPLETE DOCUMENT by Halima Abdullahi k. Mashi .txt

sameki?na
cigaba da kuka yana ta magana nayi shiru,yace nasan
su hajiyarmu ne ko?nan nayi magana nace basu bane
ni da mamanmu ne,yace duk yanda akayi kece kika
tabo ta nace wani ne ya saya mani waya shine take
ganin kamar na rokeshi ne,yace to ta kwace wayar ne?
nace nifa ba kwace wayar ne ya bani haushi ba,yace
na fahimceki kafin ya kara wata maganar sai ga
yayanmu sun nufo cikin gidan shi da Anty Mimi shima
ya ja birki yana ce ma yaya Kabir brother me ya
sameta?kabir ya soma yi mashi bayanin cewa bafa
wani abu bane wai yayanta ya bata waya shine maman
Sagir tace wai ta rokeshi ne,ya dan dubeni sannan ya
dubi yaya Kabir yace to yanzun ta kawo karanta ne?
yaya Kabir yace no na dai tambayeta ne shine take min
bayani,ya dubeni yace wannan marar kunya da ya
zauna mani a kujera shine yayanki?daka mani tsawa
yayi nace shine yace good gara da ta kwace wannaki
bashi da kunya bai iya gaida mutane ba sai aikin kallon
mutane don haka in ya kuma zuwa kice mishi ya tsaya
daga bakin gate sannan ki san kin maida mishi wayar
nan,a fusace ya yi cikin gida daga ni har yaya Kabir da
kallo muka bishi Kabir yace ki tafi inda aka aikeki,na
tafi ina mamakin wannan karfin hali wai (barawo da
sallam)
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Ashe yana shiga gida dakinmu ya shiga dama shima
duk safiya yakan shiga falonmu ya gaida mama tamkar
yanda yake gaida mama tamkar yanda yake gaida
sauran matan babansa,bayan sun gaisa ne sai yake ce
mata maman Sagir mai ya sami yarinyar dakin nan na
ganta tana kuka? Sai mama tayi mishi bayani ta kara
da cewa nasan ba zata rokeshi ba na dai mata haka ne
don kar ta kuma karbar wani abu gunsa,yace hakan na
da kyau ta maida mashi zan sai mata waya bansan
bata da waya ba kuma sanda na dawo ban san tana
nan ba,mama tace ka barshi kawai yayansu nima zan
sai mata nafi son sai sun kammala krt don yan
satittuka ne suka rage masu su soma jarabawa yace
haka ne in ta gama ko ba na nan zan aiko mata da
waya,mama tayi godiya sannan ta kara da cewa ga
kuma dawainiyar kayan da ka sai mata jiya an gode,na
dawo na samu zai fita daga dakinmu na dan dube shi
harara ya watsa mani nayi sauri na dukar da kai,na
shige daki.
Sam ya manta da cewa tare da Mimi suke sai da ya
shiga dakin Haj yaya sannan ya ganta zaune tana cika
tana batsewa ya zauna a kan kafet din dakin
kasancewar mahaifiyarshi tana kan kujera ya gaisheta
ta amsa a ciki ciki sannan tace kai wai ba zakaji
magana ba ko?ya dubeta yace haj me ya faru?tace ai
kafi kowa sanin abinda ya faru don tsabar iskanci ku
taho da mimi amma ku taho amma sai ka bar ta anan
tana ta faman jiranka kuma kasan makaranta zata je
tace tun tara take da lectures yanxu goma da rabi a
ina kasa gaba?kafin yayi magana mimi tayi saurin cewa
wurin fa bakar yarinyar nan ya tsaya wai sun ganta
tana kuka suka firgice shida Kabir sai tambayarta
sukeyi ban.......tsawa ya daka mata ke shiga hankalinki
ni sa'anki ne?uban wa yace da zaki makaranta ki biyo
ta nan?me zan miki?karki sa ma bakinki kwado zaki
sha mamaki duk sanda ana min magana kika tsoma
baki ya nuna kofa da hannunsa yace see your way,fita
a nan ta mike jiki na rawa mama ki daina min fada a
gabanta kin manta ita ce matar da kika zaba mani na
aura?zata raina ni ne hajiya in kina min haka a gabanta
har tana sa baki dan raini,wllh taci albarkacinki ne da
sai na mata dukan tsiya,ya cigaba da cewa bata san
cewa ni saboda ke ni zan aure ta ba ba wai don tayi
mani ba?haj yaya tace tsaya tsaya ba na son cin fuska
ka manta ni da uwarta nono daya muka sha?bayan
haka ma mimi bata da makusa ubanta balarabe ne ka
kuma sani inma ilimi ne akan nema take gashi tana
sonka sosai amma kai sai faman goce goce kake yi shi
yasa na canza shawara kafin ka tafi sai an sa ranar
aurenku,ya dubi haj yace ki dai yi hakiri na dawo don
kar aje ana dagawa tace sam ban yarda ba yace to shi
kenan ta juya zancen dake cewa wacece take kuka ku
ka tsaya kai da Kabiru?yace waccan yarinyar da nake
aike ce,nan ta hau bala'i da masifa tace dama in banyi
da gaske ba sai Habiba ta shanye min yara yanda ta
shanye babanku kallonka kawai nake yi wannan
mummunar yarinyar yanzun itace abincinka gyaran
dakinka,aike yanzu itace tunda haka kafi so ai sai kayi
sauran ka ka soma kai shawara gun Habiba haka tayi
ta sababi yana bata hakuri har dai ta sauka,Niko tuni
nakai dinkinmu gun yaya Sulaiman nan da nan kuwa sai
ga kaya ya kawo,na rakoshi zai hau mashin nan mukayi
kicibis da yaya Kabir suka gaisa da yaya Sulaiman ga
mamakina sai naga yaya Kabir ya daure fuska ya
dubeni yace na lura baki jin magana ko Iman?me yaya
Abdulrahim yace maki?na dibe yaya kabir nace ai to
wannan ba yayan da ya bani waya bane wannan wani
ne bai saurareni ba yayi cikin gida muka fita ina ta
mamakin wannan abu da yaya Kabir yayi na dubi yaya
sulaiman da nufin nayi magana sai kawai shima naga
yayi fuskar shanu(wato ya hada rai)yace wannan kuma
wanene?nace yayanmu ne yace ni ba wani yayanku na
kula ke sam baki ma san halin da nike ciki ba ko?
gabana ya fadi nace me kake nufi?yace ina cikin
mayen sonki,na dade da yin nutso cikin kogin sonki don
Allh ki taimaka min da ganin wannan da ya wuce sonki
shima yake yi,nan take hankalina ya tashi na gudu nayi
cikin gida dakinmu na fada na kwanta a kan gado
rigingine nayi fuskata na kallon silin na soma tunani,
yaya Abubakar sona yake,yaya Ibrahim sona yake,yau
ga yaya sulaiman da wannan zancan har kuma yana
tunanin wai shima yaya Kabir sona yake, ban ganeba?
na mike zumbur tamkar an tsunguleni nace da na shiga
uku ni Iman muddin Haj Yaya taji wannan lbr na ciji
yatsana na soma sintiri a tsakar dakin tabbas da zan so
yaya kabir ko ba komai yana dan yanayi da yayanmu
wata zuciyar tace min in yana yanayi da yayanmu shi
kenan sai ki soshi a matsayin da yayan naku ya taka a
zuciyarki?shin kina neman ma kanki rigima da
mahaifiyarki?menene laifin Abubakar da ba zaki soshi
ba?ya jima yana maki dawainiya dake in ba ki son shi
ga Ibrahim nan shima dan uwanki ne sannan in dama
za kuyu adalci to da Sulaiman kika zaba ki tuna shine
yake maki hidima ta fannin dinki tun kina karama har
yau dinnan shi ke maki dinki,
****hhh! Lallai yariya taki tasameki,duk cikin wayit
blood ne*****
ban san shigowar mama ba sai dai naji an girgiza ni
sannan nayi sauri na jiyo cikin tsoro naga tana kallona
tace iman me kike tunani haka?na shiga uku ni Habiba
na soma in ina,ina cewa ba komai ta girgiza kafaduna
da karfi cikin daga murya murya tace kinsan tsawon
lokacin dana dauka ina maki magana nan kuwa baki
sani ba,na jima a nan ina kallonki kina safa da marwa
tamkar wadda abin duniya ya dama,ta ja hannuna muka
zauna a bakin gado ta sanyaya murya tace Iman sanar
dani matsalarki don baki da wanda ya fini kuma na jaki
a jikina don irin wannan ranar wato don neman
shawara kar kiji komai sanar dani ta fada tana kallona
nayi shiru ina tunanin mama gaskiya dole ne ma na
sanar da ita sai dai ba zan gaya mata maganar kabir
ba, na dubi mama nace yayyena duka uku sune suka
sani shiga wannan tunani,tace kamar yaya?na dukar da
kaina kasa sannan nace yaya Abubakar da yaya
Ibrahim da kuma yaya Sulaiman kowanne yazo wai
yace yana sona,Mama tayi shiru kamar ruwa ya cita
tace ke me kika gani?ta cigaba da cewa Abubakar da
ne ga yayar mahaifinki cikinsu daya,Ibrahim kuma dan
kanin mahaifinki ne da suke uba daya shi ko Sulaiman
dan wana ne nima cikinmu daya sai ki fadi min wanda
kika zaba?nayi shiru tunani ya dawo sabo mama tace
ba tunani zakiyi ba sanar dani abinda kikace masu ke
kin amsa musu dukansu ne?nace aa duk hakuri na
basu,nace ni karatu zanyi amma tamkar sun hada baki
kowa sai yace zai jirani yaya Sulaiman ne ma ban
tsaya yi mishi magana ba,mama ta dafa ni sannan tace
yanzu gaya mani a cikinsu wa kikafi so?sai na baki
shawara nace gsky mama ni cikinsu bana son kowa,ta
mike tana fadin alhamdll gara hakan don dama ko da
dole sai na zabi daya ne,to nace gara Sulaiman yaron
na da mutunci,kuma naji ma ina fuskantarshi game da
ke ma na dade da gane cewa sonki yake nayi kwadayin
dama shi kadai ne yace yana sonki taci gaba da cewa
yanzu in naceki amince dashi sai ace don yaron
danuwana ne shi yasa don haka ki kwantar da
hankalinki kinga jarabawa na matsowa kar ki yarda na
kuma samunki kina wannan tunani ba yarda za ai ki
auri wanda bakiso ba mai matsa maki don karatu ma
zakiyi,haka mama tayi ta lallashina har dai na saki jiki
sai dai a raina maganar yaya Kabir itace a raina.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Tun ana saura kwana uku bikinsu anty mariya dangi
suka cika gidan,fannin Haj Shuwa da yanuwa Haj
Yaya,sai yan uwan Alh Mukhtar wato yan maska Aunty
Mimi ma a ranar tazo don ranar ne za'ayi
dayis,yayanmu ranar bai wuni gida ba sai yamma dama
ni banje masu wurin da suke yin lalle ba nida Amira
mukaje mukayi kitso sannan mukayo namu lallen a can
don dama mu ba ma saka mai a kanmu. Misalin karfe
biyar na yamma yayanmu ya aiko Kamal ya kira ni nazo
yace na kawo masa wani abu tabawa in akwai dan
yinwa yakeji na koma ba wani abin kirki sai na rana
kuma ya huce nasan ba zai ci ba,don haka sai na dafa
mashi indomie da kwai na kawo mishi natarar da Aunty
Mimi a dakin sai naji raina ya baci na ajiye zan juya
yace ke kizo ki zuba mani mana na dawo sai tace ka
barta sai na zuba maka ,bai dubeta ba yace min samin
mana kina kallona baki sanni bane?nayi kasa da kaina
sannan na zuba mishi na dauko mishi coke da ruwa
sannan na juya zan fita sai naji yace shiga bedroom ki
dauko wayarki tana nan a kan katifa,na dauko sannan
nayi mashi godiya,washe gari a command quest za'ayi
kowa ya shirya cikin anko nima na sanya nawa ankon
nayi kyau sosai na fito harabar gidanmu a nan ne ake
daukan yan matan tuni kowa ya tafi sai Amarya da
kawayenta wadannan kuma bana tunkare su ba itako
mami tuni dama tana can don sune masu shirya gurin
dasu bilkisu da sauran kawaye,ina tsaye na jingina da
bangon dakin yayanmu ina kallon kawayen amarya suna
ta kai da kawowa kowacce na rike da waya tamkar
masu gasarta nan na tuno da tawa mama tace na aje
sai mun gama zana jarabawa ina wannan tunanin naga
anty mimi sun fito itada yayanmu itama anko ne a
jikinta irin nawa tayi matukar kyau dama anty mimi ba
dai kyau ba gata fara yanda mami ke gaya mani
mahaifinta balarabe ne zamanin da Haj Laure
mahaifiyarta suke zuwa kano to jidda a can Allah ya
hadata da wani balarabe ta aura shekarunsu ko goma
ne da aure ya rasu lokacin Anty Mimi na shekara
shidda shine ta gudo da ita ba tare da sanin dangin
babanta ba,sannan ta sake aure shine ta haifi yaya uku
sanda naji wannan lbr a raina nace ashe jirgi daya ya
debomu ni da ita.....Ku ziyarci blog dinmu domin
karanta Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347




DOCUMENT CREATED BY
ZAHARADDEEN SHOMAR
WHATSAPP 08168575100










Tawa Tasameni 1-03
Posted by ANaM Dorayi on 02:31 AM, 29-Dec-15
Under: TAWA TASAMENI
__________NA HALIMA ABDULLAHI K/MASHI
Garama ni ubana yana nan, haka danginshi, nayi nisa
cikin tunani na ji horn ba karewa na juya can wajen da
ake horn din bakin gate sai naga ashe su yayanmu ne
zasu tafi ban fahimci wai ni suke ma horn ba sai da anty
Mimi ta bude gaban mota tace ke na dubeta na dafa
kirjina nace ni?eh da Allah zo nan ana maki horn kinyi
banza da mutane, na nufi gunsu ina zuwa naga yayanmu
ya sako hannu ya bude baya yace shiga,gabana na
faduwa na shiga motar don nasan ba wanda ya taba
shigarta a yan gidanmu sai yaya Kabir na zauna sannan
na rufe sanyi da kamshi sune suka ziyarceni tamkar wata
munafuka haka na zauna a motar kaina a kasa, suko
suna ta labari bana jin dai muryar yayanmu sai ta anty
.Mun yi nisa sannan na dago idona sai kawai muka hada
ido da yayanmu ta madubi nayi sauri na sunkuyar da
kaina kasa har mukaje ban tanka ba,ban kuma daga
idona ba,sai da naji an tsaya sannan na dubi gurin yan
mata ne cike na buda zan fita sai naji yayanmu yace
karba,na juyo sai naga yana bani kudi ne sababbi yan
naira hamsin na amsa nace Allah ya saka da
alkhairi,anty Mimi ta shaka sosai da na kalli fuskarta ni
dai nayi ciki ko zan ga Mami, ana cikin hidima shalele
suka kira don haka gun ya cika da karan kidan police
band Sa'a tazo tace kije ana kira gabana yana faduwa
nace inji wa?ta harareni dole sai kinji? ki zo mana na
bita can baya mukaje ganin Anty Mimi da Amare da
kuma kawayensu yasa wata faduwar gaba ta sameni na
dai daure na isa wurin,Anty Mimi ta kai mani rankwashi
akai tace ina jakarki?nace tana gun Mami tace nawa
yayanmu ya baki?nace ban kirga ba nan ta shiga
zayyane masu wai wannan wace irin yarinyace,Anty
Hadiza tace ai wannan daga ita har uwarta annoba
ce,Anty Mimi ta cigaba da cewa kunga jiya a gabana ya
bata waya irin tawa ce sak koda ganin kwalin sannan yau
zamu taho nan ta zo ta rabe ya dauko mu tare kunji
biyu,cikon na uku kuma sai gashi ya raba mana kudi
kilan ma daidai ya raba tamkar wasu kishiyoy,nan suka
taru a kaina wannan ya kai mani bugu kowa dai na fadin
albarkacin bakinshi, Mami ta iso daidai lokacin da wasu
kawayen Anty Mimi suke cewa asiri tayi mishi daga
gani,in ba haka ba me zaiyi da wannan mummunar
yarinyar gara ma ki dauki mataki tun da wuri akan abin,
Mami tazo tana cewa Anty Mariya kuzo anguna sunzo fa
ana ta nemanku,kan suyi magana Anty Mimi tace Mami
muga jakar wannan jakar,sai sannan Mami ta ganni ina
kuka tace Iman menene?Bilki tace ba'a sani ba ke dai ki
bada jaka a kace Mami tace bazan bayar ba nace Mami
bata ta mika mata sai da suka kirga kudi daidai da nata
dubu ashirin da biyu ne dama ban kirga ba,saura sukace
kar ki bata ko sisi Mami tace wllh sai naga ya wa
yayanmu in har kika dauki kudin nan,Anty Mimi ta watso
kudin da jakar a jikina sannan tace ki jira abinda zai biyo
baya ta wuce sauran suka bi bayanta aka bar daga ni sai
Mami inata kuka,Mami ta kwashe tana tambayata abinda
ke faruwa na zayyane mata komai itama na kula ta dan
yi mamakin kudin da ya bani tace Iman yayanmu yana ji
dake fa nace Nami ku kula da wani abu daya yayanmu
nice nake mashi aiki,shiyasa yake mani alheri amma wai
suna zargin wai yana sona ne ni nasan ko mata sun kare
yayanmu ba zai taba cewa yan sona ba ke kinsani balle
yana da kamar Anty Mimi,Mami tace ai itama anty Mimin
ba wani kyau ne da ita ba uban gashi ne kamar jirgi ya
daso tasha kuma a tsaye take ba wani diri kirji kamar na
bera ba wasu nonuwan kirki nace to shi dai tayi mashi
Mami tace ke zo muje ba wani yi mashin da tayi kawai
saboda mamansu zai aure ta.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
TAWA TA SAMENI,haka na fada ranar daurin auren anty
mariya ba wani abu yasa na fada ba sai ganin munsa
less iri daya da Anty Mimi wato wanda yayanmu ya bani
nasa daya daga ciki me ruwan lemun tsami takalmi da
jaka iri daya itama ni take kallo ta zauna kofar dakin
yayanmu a fararen kujerunshi ranta yayi matuka gun baci
naga ta yi cikin gida ni kuma sai na nufi gidan su
Amira,dama dazun ta aiko Faruq wai ta dawo dama jiya
ne ta tafi unguwar dosa gun kanwar mamansu da suka
dawo kwanan nan shine taje kwana,ta fito wanka na
sameta nan nake zayyane mata abin dake faruwa ta
dinga mamakin karfin halin irin na nasu Aunty Mimi dan
yayanmu ya min kyauta ta kara da cewa komai ya sai
maki ba zai biyaki ba irin dawainiyar da kike mishi ba
nace suna zargin fa wai sona yake yi,Amira tace haba
dai nasan ma ba zai fara ba domin kin......na katse
Amira nace ni ba ajinshi bane nasan da haka kuma ko
mata sun kare ba zai so ni ba Amira tace ba nufi na
kenan ba ina nufin matsalar dake tsakanin mahaifiyarki
da tasa ai yasan da wannan matsalar ba zaima ce yana
sonki ba.Nace ato su sai hauka suke yanzun nan na
hadu da anty Mimin shine ta ganni da kayan nan har
jakar to tayi cikin gida ban san me zai faru ba,dama
bikin nan sai yan tsegungumi sukeyi dangin Haj Yaya
naci gaba da cewa kinsan abin da ya faru ne da babansu
Mami ya tambayi Haj Yaya game da kayan da za'a siya
don yayanmu ya riga ya sai masu sai yace to suyi mashi
list din kudin sukayi mashi hauka to hauka mana wai fa
miliyan daya da rabi suka rubuta shiko ya kira mama tayi
mashi lissafin kayan dakin mata mata har da na jere da
na kicin duk ta sanar dashi naji ya bata kudi sukaje ita
da Anty Yagana suka sawo mashi komi don Mama cewa
tayi sai da tayi ciko suka kawo ya dinga sa mata albarka
itama ta bashi nata gudummuwar na zannuwan gado to
wannan abin shi yayi matukar tada hankalinsu Haj Yaya
da har sunce sam kayan nan bai masu ba shine baban
yace yayi in baiyi masu ba to su sai nasu da kudinsu
kafin Amira tayi magana sai ga Jamila kanwata da
kukanta wai ana fada da Mama nace mama da wa tace
Mama da mutane yan biki nace yau mun shiga uku ko
takalma bansa ba na nufi gida Amira ta biyoni,tun a
harabar gidan nake jin hayaniya yaya Kabir na gani ya
fito daga cikin gidan ranshi a bace da ganina ya nufoni
yace kar ki shiga zo nan,na soma kuka ina cewa ni dai
na shiga uku ya ja min hannu zo muje karki shiga,nace
ina kuka yaya Kabir barni naje naga Mama yace
Mamanki tana dakin Alhajinmu zo muje ya jani dakinshi
ya zaunar dani kan kujera sannan ya tsugunna gabana
yace kiyi shiru zan tambayeki ne,nayi shiru ina share
hawayena yace yaya Abdulrahim yace yana sonki? nace
aah yayi ajiyar zuciya sannan yace alhmdll yayi shiru
zuwa can yace a gaskiya Iman na dade ina sonki shiyasa
ma har yau na kasa kula duk wata ya mace da sunan so
na mike tsaye na ce Kabir tun ina ganinka da gashi kar
ka yarda na kuma jin wannan zancen kana ganin balain
da muke shiga kullum a gidan nan sannan zakace wai
kan sona ni dai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login