Showing 15001 words to 18000 words out of 26020 words
Chapter 6 - TAWA TA SAME NI BOOK 1 COMPLETE DOCUMENT by Halima Abdullahi k. Mashi .txt
ba ruwana,ya zaro mani ido gami da
tasowa kamar zai bugeni yace sai kin soni kuma ni da
ruwana ba abinda ya dameni da fadan iyayenmu,na mike
zan fita yace kar ki yarda ki fita su Haj Laure zasu dake
ki muddin kika shiga,jin maganar duka ni uwar yan tsoro
na dawo na zauna na sanyaya muryata nace sun doki
Mama ne?yace suna hauka ne?ita ko kulasu ma batayi
ba shine yar Alhajinmu da tazo daga maska tace ta
shuga dakin Alhajin tasa na mashi waya yanzun nan yana
zuwa shiyasa nace kar kije,na cigaba da kukana yaya
Kabir yana lallashina har nayi shiru ya dinga shigar
dakan shi a guna yana ce min in na yarda yasan
Akhajinsu zai tsaya man kuma zai nemi canjin gun aiki
mu bar kaduna haka ya yi ta cusa min raayi har na soma
yarda,sai dai ina tunanin mama ba zata amince ba na dai
yanke shawarar zan ci gaba da addua. wayar yaya kabir
tayi kara yace in dauka don nafi kusa da wayar,na dauka
sai naga sunan yayanmu sai na mika masa yace ya baki
dauka ba?nace yayanmu ne ban san mai yake ce mazhi
ba na dai ji yace gata nan sai na kuma jin yace dakina
sai gabana ya fadi,sai naji yace to gata nan zuwa,ya
dubeni yace alhaji yazo yana dakinshi an ce kije,nace
yayanmu na gurin ne?yace shi ne yayi min waya wai
Jamila tace nine na tare ki ina kike yanxu sai shine nace
gaki nan ki tafi ko na raka kine?nayi saurin cewa a'a don
kar agan mu tare,cikin dar dar na shiga gidan yan biki
sai ni suke kallo gashi ko takalmi babu a kafata na shiga
ciki nayi sallama a kofar falon Alhaji na shiga Alhaji na
kan wata kujera irin ta karfen nan ne dama nan ne gun
zamanshi sai Mama akan kujerar gefen damanshi dayan
gefen Haj Yayace sai Haj Shuwa kusa da ita Haj Kulu na
dakin sai yaya ta maska(wato yayar Alhj)yayanmu na
kan kafet kusa da kafar Alhaji nima na shiga na samu
guri kusa da Mamana na zauna a kan kafet.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Alhj na gaisar sannan yayi gyaran murya yace to gara ke
Murja(haj yaya)menene sanadin wannan fadan?na
tambayeki dazu kince sai an kira Iman gata tazo sai ki
fda muji ynxu,ta soma magana cikin sababi ni dai Alhj
kawai kayi mani tsakani da Habiba da kuma 'ya'yana in
kai ta gama da kai to ni da 'ya'yana li'ilafi,,tashanye min
yara basa cin girkin kowa sai na 'yarta sannan yanzu shi
wannan miskilin dana gani kamar zai zama namiji amma
ba haka bane ya tashi sai kashe mata kudi yakeyi harda
yi mata anko da matar da zai aura me hakan yake nufi?
na dai san rokonshi sukayi don haka ayi mana iyaka dasu
ba 'ya'yanta ba nawa,tun da ta soma bata tsaya ba kuma
ba a katse ta ba,jin tayi shiru sai na dago kai na dubi
kowa kowa dai ita yake kallo sannan na dubi yayanmu
wanda kanshi yake kasa Alhj yace to naji naki ke kuma
Habiba ya abin yake?Mama ta soma magana cikin sanyin
murya lafuzza masu kyau tace ni dai Alhaji a gefena ba
wani matsala yarinyar nan dai itace matsalar, da zaka
amince min da sai na dauketa na maidata wajen
kawunta don inda bata nan gidan da baza ta ga ma
'ya'yan Haj Yaya ba bare su sata aiki sannan muddin
tana nan gidan ba zan hanata aiki ma kowa ba har Hajiya
Yaya inda zata sata,amma kiyi hakuri Yaya zan maido
maki da dukkan abinda Abdulrahim ya sai ma Iman
sannan kuma sai kiyi mashi magana ya daina sata aiki a
zauna lfy,na dubi Mama hankalinta a kwance tayi
maganar sabanin Haj Yaya wadda ke cika tana batsewa.
Dakin yayi shiru sai can a
Alhj ya soma magana yace Murja! Haj Yaya tace na'am
da karfi tana karkada kafa yace ina son kisan cewa
'ya'yan nan nawa ne kuma wancan ma tawa ce don ni da
kaina na daukota ko uwarta bata san zan kawo ta sai dai
ta ganmu Allah yasan wannan don haka ba zaki raba min
kan 'ya'ya ba kinyi kadan,Habiba yarinya ce a kanki
amma tafiki hankali da tunani saboda haka kar ki yarda
ki amshi duk wani abu da yayi mata kuma aiki duk wanda
yayi niyyar sata kar ya fasa don haka na gama wannan
maganar sannan ki gargadi laure ta kiyayeni da wasa naji
ta taba Habiba ko Iman sai nasa an daureta gara ma ta
tabaki zaifi mata sauki,Haj Maska tace yayi daidai
hakan,Murja in ka girma to kasan ka girma don haka sai
ta soma kuka tana cewa dama namiji ba dan goyo bane
nan na dauki kudina na baka ko basu ne silar arzikin naka
ba?daban haka ai da har yanxu kana a fakirin ka dole ka
min sakamako da mun wulakanci ta nuna ni tace ke
kuma zakiga hukuncin da zan yanke a kanki muddin kika
kuma ko kallon min 'ya'yane na durkusa da sauri(don har
ta mike)nace don son Annabi(SAW) kiyi hakuri bankade
ni tayi waje sauran kishiyoyinta suka take mata baya,Alhj
ya bisu kallo sannan yace Allah sarki to Allah ya sa ku
gane,ya dubi yayanmu yace kaima kayi hakurin dai zan
baka cikin sanyin murya yace Alhj kaimin izinin na koma
england jibi,yace na maka amma yaushe zaka dawo?kar
kaje ka kuma zama yace nan da wata shida ne yace to
Allah ya kaimu ya fita na bishi da kallo.
Karya ne gane halin da fuskarshi take ciki wato laifinmu
yake gani ko na uwarshi,ban taba ganinshi cikin dogayen
kaya ba tunda yazo sai yau boyel ne baki amma kanshi
ba hula Alhaji ya dubeni yace Allah yayi maki albarka
Iman kiyi koyi da halin mahaifiyarki kinji?na daga kai ya
cigaba da cewa muddin kikayi halin uwarki to kin
dace,sannan mijin da zaki aura ma yadace,su Abdulrahim
da Kabir duk yayyanki ne duk abinda suka saki
kiyi,sannan in sun maki kyauta ki amsa kice kin gode
nace to Alhj na gode,na mike na fita dakinmu na wuce
kai tsaye kan gado na fada raina a cunkushe na rasa me
ke daga min hankali son da Kabir yace yana min ko
matakin da Haj Yay tace zata dauka a kaina ne?wata
zuciyar tace duk ba wannan bane tafy yayanku ce
wannan amsar da zuciya ta bani itace sanadiyar tashina
zaune saboda tashin hankali da naji ni a ciki na mike ina
safa da marwa nace a fili ban so akayi wannan rikicin ba
ba zanji dadi ba muddin yayanmu ya tafi kai zanje na
bashi hakuri in ya tafi na mutu,da sauri na dauki hijabina
na fita falo nan nayi turus ganin mama a falon tace ina
kuma zaki?karon farko da na soma yi mata karya nace
gidansu Amira tace me xakiyi?nace takalmina da gyalena
dauko tace ko bari zata aiko maki ko ki aika Jamila kar
ki fita ko ina ynxu zo nan kiji,na isa gunta na zauna tace
kin dai ga abinda ya faru ko?nace eh tace to ina son kiyi
taka tsan tsan da kowa a gidan nan banda yawan
shigewa duk wanda ya saki aiki to kiyi masa kamar
yadda kikaji Alhaji yace maki,nace to ta kuma duba na
tace yanaga kinyi wani sukuku dake?nace bani son
tashin hankali ne mama shiyasa tace kar ki damu aikin
shedan ne kuma ki cigaba da addua sannan daga ynxu
zan na tashin ki duk dare in tashi yin nafila sannan zaki
dinga yin azumin litinin da alhamis,sai mu dinga tare in
kuma an gama bikin nan zanje wurin kawunki na samo
mana addu'o'i na tsari mu dukufa,Allah ya ja mana
gaba,sauran maganganun da mama takeyi duk banji su
ba ina ta tunanin yanda zan ga yayanmu don nasan nice
na jawo wannan tashin hankalin gaisuwar da naji mama
ta na amsawa shine yasa na juyo Mami ce ta dubeni
tace ya dai?na mike muka shiga dakinmu kan gado muka
zube na dube ta nace ya dai tace ina gidan walima muna
shirya guri sai ga Sa'a wai ana fada da mamanku da su
Haj Laure har sunce sai sun zane ku?nayi tsaki nace kan
fa kaya ne kin gansu nan jikina yayanmu ya bani ashe
irin na Anty mimi ne shi kenan sai tashin hankali gashi
yanzu ma yace zai koma jibi,Mami tace ai dama bayan
biki da kwana biyu yace zai koma nace to ai gashi ba'a
gama bikin ba ni gani nake ma duk laifina ne hawaye
suka zubo mani akan kumatu Mami ta tsaya kallona baki
bude shi ne harda kuka?kuma ma ina wani laifinki anan?
nace nasa kayan tace to baya baki don kisa bane?shi
yayanmu in zai ma mutum kyauta ba ruwanshi da wani
nuna bambanci nace rakani na bashi hakuri,Mami tace
tab ai sai dai kije ke kadai yayanmu ba ya son ai ta
faman bashi hakuri musamman in yana cikin tashin
hankali gara makin zauna,ke menene naki na damuwa?
kina ganin zaki iya hana shi ya tafi ne?nace bani na ja
komai ba,tace sannunki da kai ta mike zo muje gidan
walima nace ni kaina ma ciwo yake bazan sami zuwa ba
ta tafi na koma na kwanta na cigaba da kuka rurus,saidai
za'a a tsira ni ko da bindigane ba zan ce ga abinda nake
ma kuka ba sai da nayi ya ishe ni sannan ciwon kai ya
yomin sallama kafin wayewar gari nayi rigif ko sallar
asuba kasa yi nayi sai wurin bakwai na safe yinin ranar
nan haka nayi shi, misalin karfe uku Alhj ya shirya da
Yaya Abdulrahim yace Habiba danku zai wuce fa,kan
Mama tayi magana shima Yayan namu ya shigo ban san
lokacin da na mike ba ya zauna a kan kujera yana gaida
mama bayan ta amsa sannan ta ce ikon Allah tafiyar ta
tashi ne Abdulrahim?na dauka gobe ne?yace eh gobe ne
zanje lagos ne na kwana shida na safe jirginmu zai tashi
yanzu ma jirgin karfe biyar zanbi zuwa lagos din yana
magana niko bakinshi nake kallo da sauraron muryarshi
mai dadi tamkar ba namiji ba ne yake magana ba Mama
da Alhj suka shiga dakinta ya bisu da kallo sannan ya
juyo ya dubeni na dukar da kai gabana sai faduwa yake
yi,ga mamakina naji yace Amina nayi sauri na dago kai
baki bude ina dubanahi shima ya kafa min idanu na
sunkuyar da kai don ba zan iya cigaba da kallon kwayar
idonshi ba sai ina ganin wani abu yana fitowa daga idon
shi,yana shigowa nawa,murya kasa kasa yace zan tafi
kiyi mani addua kaina a kasa nace adawo lfy Allah ya
bada sa'a,a lebanshi naga ya amsa,Alhj ne ya fara fitowa
yana cewa Abdul walarka nace Mam zata baka?yace no
Maman Sagir kar ki damu ba sai kin bani komai ba Mama
ta fito da dambun nama dayawa tace to ka tafi da
dambun naman nan Iman tayishi shekaran jiya ya dubeni
sannan yace to zan amshi wannan sai naji wani sanyi a
raina suka fita nima na daga labulen dakinmu ina kallo
ga yan biki nan sai a dawo lfy suke mashi harda su Haj
Yaya dasu mama aka fita harabar gidan wajen ajiye
motoci nima na fito ina daga can baya ina kallonsa har
aka shigar mashi da jakunkunan shi cikin boot din
motarshi yaya Kabir ne zai jashi,ga wasu abokanshi
suma zasu shiga wata motar ya fito daga dakinshi har
ya sauya kayansa da jc jajaye masu ratsin fari dogon
wando da riga mai dogon hannu sai takalmin kwallo Anty
Mimi ma ta fito sai kuka takeyi haushinta ya kamani a
ganina nice yafi dacewa inyi kuka ba ita ba ko mai yasa
oho zai shiga mota kenan ya hango ni sai naga ya tsaya
yana kallona har Anty Mimi ma ta juyo taga wa yake
kallo?sai taga ni yake kallo sai naga ta kawar da kai niko
sai na kwantar da kaina a jikin bango sannan na daga
mashi hannu alamr bye bye sai ya shige mota suka tafi
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Tun daga wannan rana ban kuma wani sukuni ko
walwala ba har mamakin kaina nakeyi kullum cikin
damuwa bana wani cin abincin kirki gashi kowa ya gane
halin da nake ciki a gida da makaranta sai dai kowa ya
tambayeni sai nace bani da lfy ne.Azumi da nafilflii
kullum cikinsu nake
,ranar da yayanmu yayi kwana biyar da tafy Mama taga
abin ya isheta bani magana sosai koda yaushe a kwance
ga jarabawa ta matso amma bana wani krt sati da lahdi
suka zo suka wuce amma banje islamiya ba wato
(sanawiyya),Ranar monday mama tace kar naje
makaranta na shirya muje Asibiti nace lfy ta kalau tace
na dai shirya muje kawai rimi clinic mukaje mama tayi
ma likita bayanin yanda nakeyi,likita ta barshi dani bayan
fitar mama sai likita ya dubeni yace sanar dani yadda
kikeji sai nace kasala nikeji sai kirjina da ke min nauyi
kuma bani son yawan surutu yadan gwaggwadani sannan
yace kina yawan tunani ko?nace eh yace to tunanin me
kikeyi?nace ba komai yace karya ne da na rasa ta cewa
sai na ce jarabawa ce nake tunani ba dan ya yarda ba
yace to shi kenan ki daina yawan tunani kisa Allah a
gaba ya rubuta mana magunguna muka tafi,haka nayi ta
shan magunguna amma tamkar ana zugani Mama ta
koma na gargajiya ni dai nawa shane a haka jarabawa ta
same ni mukayi ta nidai ban sa rai da zanci ba ranar da
muka gama ne a nata murna masu hoto nayi,niko sai
kallon mutane nake,Mami ta dafa ni tace ga wata yar
ajinku can tana nemanki nace ina take?ta nuna min ita
ashe Hauwa'u Aminu ce nan tamin korafin rashin sanin
gidanmu ita kuma ta bani no wayarta ni kuma nace mata
in na fara anfani da tawa sai taga tawa lambar,sai da
zamu bar harabar makarantar ne sannan naji duk kewar
makarantar ta ka mani.Abdulrahim zaune a kan kujera a
cikin falon Hotel din da yayi masauki, ko nace nan ne
dama club dinsu suka kama mashi tun farko,kanshi yana
jingine a bayan kujera, tebur ne dan karami cike da
kayan ciye ciye da shaye shaye amma sam ya kasa cin
komai tunanin yakeyi wayarshi tayi kara ya juyo ya dube
ta kamar kar ya dauka sai kuma ya dauka Mimi ce ta
kirashi bai san dalili ba sai yaji wani kunci a ranshi amma
sai ya daure ya dauka,tace yayanmu kana lfy?yace lfy
kalau,yake dinfa?tace ina nan lfy dama naga tunda ka
tafi baka kira ba ne,yau kwana shida kenan?yace ban
sami dama bane,tace to ina jiran kiranka,yace to kawai
ya kashe wayar juyawa yayi ya dubi abincinshi kusan
minti arbain kenan da kawo abincin amma ya kasa ci ya
kai hannu ya bude plate din abincin da yafi so yayi order
amma sam sai yaji kamshin abincin ma baya mishi dadi
kokadan a fili yayi magana yace yarinyar nan ta bata ni
da kalolin abincinta masu dadi,yayi shiru yana tunani tun
zuwan shi kasar nan bai wani ci abinci ba daga ruwan
lipton sai dambun naman nan,kwankwasa kofar akayi ya
bada izinin a shigo ne abokinshi ne shima dan kwallo ne
amma shi bature ne ya dubi Abdulrahim sannan yace
cikin turanci Maska naga baka shirya ba ne,wannan
karon baka so dawowa ba ne tunda ka dawo sam baka
da kuzari,me yasa?Abdulrahim ya mike yana fadin
tunanin gida nakeyi ya shige dakin barcinsa shima ya
shiryo cikin JC na training suka fita.A daran daya cika
kwana bakwai da zuwa yana zaune a harabar Hotel din
haske ne ya kewaye gurin kamar rana gabanshi
gwangwanin coke ne da dan karamin plate cike da
dambun nama sannan ya kai hannu ya dauki wayarshi ya
soma sana'ar wato danne danne wayarshi can yayi tsaki
ya kashe wayar ya mike,da ya kamata ya nufi gurin
abokanshi ne tunda ba dare ne yayi sosai ba kuma yasan
zasu sa ran zuwansa, amma sam sai yaji ba zai iya ba
saboda wani abu da ya taba zuciyasa sama ya nufa
dakinshi ya zauna a bakin gado sannan ya aje tarkaccen
hannunsa a kasa wayarshi ya rike sannan ya soma
sarrafata cikin kwarewa, Babanshi ya kira bayan ya
dauka sai yace Alhj ina yini?bayan sun gaisa sai yake
cema Alhj dama ya kira ne dan ya amshi lambar wayan
Maman sagir domin yana da lambar kowa a gidan itace
bai da ita,Alhj yace gata nan ma Habibar ku gaisa,bayan
sun gaisa ne sannan ya bukaci lambarta ba tare da wani
tunani ba ta bashi,ya jima yana tunanin dalilin karbar no
kafin daga karshe ya gane sai dai wani tunaninshi abin
zai zamar mashi abin kunya da nunawa cikin
abokai,muddin suka san halin da yake ciki,nan a dalilin
wata kankanuwar yarinya wacce da yayi auren wuri
tabbas zai haifi kamarta.Kwance yake akan gadonshi
amma sai sautin daddadar muryar yarinyar yake dawo
mashi ya tuno ranar da bashi da lfy duk gidan ba wanda
ya kula dashi tamkar ita muryarta ya tuna sannu
yayanmu za ai maka wani abu ne?ya sake tuno yanda ya
kara tsorata ta ranar da ta daukan mashi kujera tabbas
in tana cikin tsoro tana matukar burgeshi yayi magana a
fili inda yace nayi missing din ganin tsoranki.
(Lallai Iman kinga takanki, mudai daganan sai muce!
Allah yakyauta)
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Ya cigaba da juyi a kan gado ba komai ke dawainiya
dashi ba sai begen yarinyar da yake gani abin kunya ne
ace ya sota ya tuna da mimi yarinya mai kyau jinin
larabawa sai dai shi baya jinta a ranshi yanda yake jin
wannan yar mitsilar yarinyar zai auri Mimi ne kawai don
bin umarnin mahaifiyarshi kuma ya san duk inda suka
shiga ba zai ji kunyar nunata ba a matsayin matarshi
shekarunta ashirin da biyar shi kanshi shekara biyar ya
bata bugu da kari gashi ta soma zurfi a karatunta,amma
in yace wannan yarinyar zai aurà shima yasan rigima zai
jawo,yanda mahaifiyarshi ta tsane su wata zuciyar ta ce
mashi ga yaran nan da rashin kunya tana jin kace kana
sonta to raini ya shiga tsakaninku gara ma Mimi hadaku
akayi kuma kasan ta mutu kanka don haka baza ta maka
wani rawar kai ba,"A dawo lfy Allah ya bada sa'a" ya
kuma tuno muryata da yaji na karshe sannan lokacin da
ta rakube a jikin bango tana mashi bye bye ya dawo
mishi tausayinta yaji lokacin kuma jikinshi na bashi kamar
itama tana jin yanda yake ji a ranta,zaune ya mike yana
magana shi kadai tamkar wanda ya tabu yana fadin
Amina kiyi hakuri bani da shà'awar auran mata biyu ki
bari in runtsa ya kuma fadawa kan gado.Niko yanzu na
zama kurma bana magana sosai ban kuma cika son
magana ba sai dai maganar su Amira ce ke damuna da
suka ce wai ina ciki mayen soyayya na dai ki sanar dasu
wanda nake so,inko har zancensu gsky ne to na debo da
zafi don ko in har yanda zuciyata ke mani game da
yayanmu so ne to ko shakka babu gara na rufa ma kaina
asiri nayi shiru da bakina don nasan ko yaji ubana zaici
don nasan ni ba ajinshi bace,me kamar Anty Mimi?
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
kammala karatuna shi ya ba samari damar damuna
tamakar anbi su an gaya musu musamman ma yaya
Kabir shine yasani wannan ya sani wancan,su yaya ma
suna zuwa,ban manta wata rana yaya Kabir ya aiko Sagir
dinmu ya kirani na fito na sameshi a daki kan kujera na
zauna fuskata na kallon wani katon hoton yayanmu
sanye yake da JC kore da fari irin na yan wasan Nigeria
hannunshi a kan kirjinshi daga gani lokacin suna taken
Nigeria ne aka dauke shi,muka gaisa da yaya Kabir ya
soma yi min