Showing 6001 words to 9000 words out of 26020 words
Chapter 3 - TAWA TA SAME NI BOOK 1 COMPLETE DOCUMENT by Halima Abdullahi k. Mashi .txt
Alh mukhtar maska yazo gun mama ni dai na
dawo daga kitson sallah nida Nana na iske bako a dakin
yaya suleiman da zai tafi mama ta shigo tace naje na
gaida shi don yana ta faman magana in na shigo nazo
mu gaisa,na zauna a kasa dashi na gaishe ahi yace kin
dawo muga kitson na nuna mishi yace iyye yayi kyau
sosai yasa hannu a cikin aljihun shi ya dauko kudi
sababbi yan naira ashirin bandir daya yace ga goron
sallah don kilan ba zaki ganni ba naki karba nace ka
barshi muna musu mama ta shigo jin musun da mu ke
ne tace sunyi yawa ne alhaji ka rage yaki dole na amsa
nayi godiya.Amira wacce tayi shiru tun da na soma
magana kamar ruwa ya cita sai da nayi shiru sannan
tace gsky iman ke yar gata ce to amma sai nan gaba
zaki sani in Allah ya kawo karshen muguwar matar
babanki,nace Allah yasa,Amira ta gyara zama sannan
tace anty faty matar babanki ta haihu?nace kai har
yanzu Allah bai basu ba tace to ina yayyenki Abubakar
da Ibrahim kuma?yanzu basa zuwa nan?nayi murmushi
nace kin cika tambaya Amira zaki yi kyau da yar aikin da
nake ra'ayi wato yar jarida Amira ta basar da abunda
nace tace baki amsa mani ba nace basu san nan gidan
ba don kwanaki baba uwa tace masu mama tayi aure,sai
kuma ta kuma cewa to ina yayansu mami abdul wa ma
kika ce mani?nace abdulrahim sunanshi mami tace yana
england shi dan wasan kwallo ne nima ban sanshi ba
amma ya sha masu aike nima na gani,shi kuma kabir
aikinsa shi dai amira tace haba nasan shi mana ba shi
ne yake karatu a kano ba,tace ai shi naga ba ruwanshi
don naga yana maki wasa nace gsky shi kam ba ruwan
shi ko zai zo hutune ya kanzo da yar tsaraba su sweet
biskit da yan kayan lashe lashe ya ba kannenshi tonima
yanda ya basu haka yake bani don haka nima nake
sonshi a raina ganin shi nake kamar yaya abubakar duk
da bai tsokanata irin na yaya abubakar din amma kinga
yayan nasu da ke waje ina tsoron ranar da zai dawo,ta
dube ni don mi kika ce haka?nace don ina jin yanda suke
lbr shi wai ya cika masifa ga duka sannan nasha jin
yanda suke bada lbr irin son da yake ma hajiya
yaya,sunce yana son mamarsa kamar ransa don bai hada
ta da kowa ba yanda mami take bada lbr sai kinyi
mamaki sosai abin kamar ba gaske ba to kuwa ai kinsan
dole ne ya kuma ki duk abunda taki gami da tsanar shi
tunda sunce komi tace mashi yayi,don haka ina jin ance
yau zai dawo zan hada ya nawa yanawa na kama gabana
na koma can gidan kawu na malam,Amira ta dinga man
dariya wai na cika shegen tsoro nace ai ke dariya ma
nabaki?lallai Amira, tana dariya tace dole ne nai maki
dariya ma naga dai komai son uwar shi sai kin mata abu
sannan zata sanar dashi sannan in baki sani ba su maza
ba yawancinsu basu da daukar zance na tsegumi haka
wannan sai mata sai ko sakaran namiji ina jin wannan ba
zai maki haka ba don shi dan boko ne nayi shiru ina
nazarin maganarta can nace wannan gasky ne to Allah
yasa dai kar ya kulani,Amira tace amin,mun kaure
munata zuba lbr sai kawai ganin yaya Ahmed mukayi
nace a'a yayanmu ustazi ba sallama ne?yace ku dai
bakujin sallamar to mama tace a tashi ayi sallah dama
masallaci zani,yasa kai ya yi waje na mike nace bari na
wuce gida kawai,Amira tace ai baki isa ba sai kinyi
sallah kinci abinci sannan zaki bar gidan nan,na kwace
daga riko da tai min nayi waje ina dariya nace yaushe
rabon da ki shigo gidanmu,ta biyo tana kira na gudu
gashi nayi sa'a mamansu tana daki tana sallah a
gidanmu ma mamanmu sallah na sameta tanayinima sai
na shige dakinmu naga jamila tana barci na tashe ta
muka yi alwala muna idar da sallah nima na kishingide.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
DOCUMENT CREATED BY
ZAHARADDEEN SHOMAR
WHATSAPP ,08168575100
Tawa Tasameni1-02
Posted by ANaM Dorayi on 01:20 AM, 20-Dec-15
Under: TAWA TASAMENI
TAWA TA SAMENI
NA
HALIMA ABDULLAHI K/MASHI
Ranar lahdi da daddare sai gasu yaya abubakr sunzo
nan muka sha fira, ynxu anty faty ta gama mallake
babana sai abinda tace gashi har ynxu Allah bai basu
haifuwa ba sai karyar bari,na tausaya ma mahaifina
kuma na yi alkawarin sa shi a addua insha Allahu zan
kuma roki mama ta barni inje na gaida kakata in munyi
hutu mun jima dasu sannan sukayi sallama damu suka
tafii,muna shirye shiryen soma jarabawa zango na ukku
don shiga SS2 aka yaye mu a islamiya inda mukayi
walima a gidansu Amira duk gidanmu ni kadai nayi
sauka mami kuma sai shekara mai zuwa don tayi wasa
da karatun mama da maman su Amira harda Anty
yagana duk sun mana bige bigen abubuwa irin su
kalanda da robobi,hankici da sauransu,da zamuyi rabon
katin walimar har su yaya Abubkr sai dana bawa Amira
nayi mata kwatancen taje takai masu kuma sunxo mani
da kyautututukan su inda suka bani waya a kwalinta
wai inji babana na amsa cikin fargaba na kai dakin
kwananmu na boye shima yaya Sulaiman yazo kuma
shine ya dinko mana kayan da muka sa ranar walima
nashi gudummuwar kenan wata shadda ce galila mai
kyau da hijabai. Sai da komai ya natsa sannan na
dauko wayar dasu yaya suka bani na kai ma mama na
mika mata leda ta amsa ta gami da tambayar menene
a ciki?nace su yaya Abubkr ne suka kawo wai inji
babana na fada mata cikin tsoro,ta saki ledar daga
tsaye tace ke kuma ki ka amsa to ko menene ma a ciki
zan maida musu ni,haka kuwa akayi ta kira yaya
Abubkr a waya ta bashi gami da yi mishi gargadin karta
kuma ganin wani sako daga babana da sunan wai nawa
ne tun daga nan suma su yaya Abubkr din ta daina
sakar masu fuska.mun shiga SS2 cikin sa'a da nasara
ranar wata jumaa mun tashi daga makaranata na tsaya
ina amsar sakon wani littafi da zan amsar ma Amira
gun wata yar ajinmu Hauwa aminu don yanxu in tana
karantawa nakan zauna ta bani lbr ko ta karanta mani
na amsa na isa gurin da Musa yake tsayawa wato
direbanmu ban sameshi ba na tsaya nayi sororo can na
hango wata yar ajinsu mami don yanxu ba aji daya
muke dasu ba ni ina A su suna C na isa gunta sai na
tambayeta ko taga su Sa'a?don mami bata zo ba tace
mani sun tafi abinsu nayi shiru na kuma ce mata motar
tazo?tace ba bus din gidanku ba?na daga kai tace to
sun dade da tfy,sai da nayi nisa a tfy kasa sannan wani
tunani yaxo mani na tsaida mashin na hau sai da muka
zo har kofar gate din mu sannan nace bari na shiga na
amso maka kudinka ina shiga harabar gidanmu naga
matasan layinmu sun cika a kofar dakin yaya Kabir har
da wadanda ban taba ganinsu a layinmu ba,nace a
raina ko yaya Kabir ya dawo ne?don ynxu yana bautar
kasa ce a Bayelsa na shiga gida na sanar da mama
abinda ya faru tace to a nawa ya kawoki?nace 40,ta
bani 50na kai mashi a hanyar dawowa cikin gida ne
nayi karo da Anty Hadiza dasu Anty Mariya suna dauke
da manyan tururuka da kuloli a kai,Bilkisu kuma tana
dauke da dauke da plates da cokula ga wani kwando
mai dauke da kayan shaye shaye na dube au na kauce
a hanya,amma duk da haka sai da anty Mariya ta daka
min tsawa ke akuya ban hanya,na matsa musu suka
wuce,na shiga ina mamakin wane bako ne yaxo ake
mashi hidima haka?bayan naci abinci nayi wanka nayi
sallah na shirya cikin riga da siket yan kanti ina zaune
a tsakar daki ina yin note sai ga mami da gudu ta shigo
tana kwala min kira iman! iman!!na tashi da sauri ina
fadin gani nan nace menene?don duk na tsorata sai
tace min ki tayamu murna yayanmu ne ya dawo ya
bamu waya nayi ajiyar zucya na dungure mata kai nace
har kinsa duk na tsorata na amshi wayar kirar nokia yar
karama mai murfi gsky ta burgeni sosai nayi mata
murna tace su dasu Sa'a iri daya ya sai masu don
dama ya sai ma su anty Mariya tun tuni,nace kunji
dadin wllh tace muje ku gaisa mana ko zai baki kema
na dube ta cikin sauri nace ki rufa mani asiri ai ni ynxu
ba zan taba yarda ya ganni ba bare da hankalin kaina
naje inda yake ta soma dariya gami da fadin kin fiye
tsoro me zaiyi maki?daga ganinki sai ya hau dukanki
sai kace mahaukaci?tacigaba da dariya na ture littafin
gabana na dube ta nace don Allah ki sanar dani wani
abu game da yayanmu mana, Tace Abdulrahim
sunanshi na gasky wato Abdulrahim mukhtar maska a
yanda naji ana cewa tun yana dan karamin shi sam
baida yawan fara'a ga miskilanci don zai iya kwana bai
damu da yayi ma wani magana ba in ana son aga
fara'arshi to a bashi kwallo sannan kwallonshi ta samo
asali ne tun yana makarantar primary inda yayi ta cin
gasar da aka sha hada su da wasu makarantun,haka
yacigaba har secondary,bayan kammala yaso a barshi
yaci gaba da kwallonshi amma sai babanmu ya kiya
sam dole yaje ABU zaria inda ya karanci politics har ya
samu degree bayan ya gama sai ya shawo kan
babanmu da kyar yayi wasanni da dama a nan gida
nigeria kafin ya fita england inda wani coach yayi mishi
hanya,
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Na dakatar da ita nace ke ni ban tambayeki lbr kwallo
ba,kunce yana dukanku ko?mami tace Allah yana duka
sosai ma,amma sai ka mashi ba daidaiba,na dubeta
nace kamar yaya ba daidaiba?tace baya son ya saka
abu kaki ko kai shirme,bai son kazanta kuma in ka
ganshi yana son ka gaisheshi amma baison yawan
gaisuwa ,kana ce mashi ina kwana is ok,yana da cin
abinci kinsan yan kwallo gashi da tsafta yana son
kamshi ke gadai abubuwa nan,in har kin kiyaye komai
babu abinda zai faru tsakaninku ko ynxu ki tashi muje
ki gaishe shi mana,nace a'a mami gaisa wata rana
nace to ynxu ya dawo kenan?tace aah bai dawo ba
kenan,zai koma wannan zuwan ma in gaya maki haj
yaya ce ta matsa yazo don su gana da yar gidan haj
laure,anty mimi nace ita zai aura kenan?mami tace
kuma abinda baki sani ba yana matukar bin maganar
iyayenshi don ko wuta suka ce ya shiga zai iya shiga
musamman haj yaya bai hada ta da kowa ba yana
matukar jin maganarta,na dube ta cikin tsoro nace kinji
ko?tana ce mishi ya koreni zai koreni ko dai ma in tafi
ne?mami sai dariya take yi min,Kamal ne ya shigo ya
sanar da mami mamansu na kiranta.Bayan kwana biyu
ya raba tsaraba har su jamila da sagir ya basu,mama
ma ta samu less da shadda da takalmi sagir din ma
harda Jc shi da kamal,su mami english wax ya kawo
masu ni dai banje ba kuma bai sani dani ba don ban
yarda ya gani ba,ran da ya yi kwana ukku da dawowa
mama ta amshi girki da rana ina tayata aikin burabisko
mami ta same mu a kicin tace yaya yace a kai mishi
abinci,nace yana cin birabisko ne?tace oho nace to
inbazaki laifi ba kije ki ce mishi burabosko ne don kar a
yi mishi laifi,tayi musrmushi sannan ta fita,anty yagana
tayi sallama ta shigo na fito daga kicin na amsa,sannan
na gaisheta gami da tambsyarta saudat tace tana gida
sannan ta wuce ciki tana ce min maman naki na ciki?
nace eh,mami ta dawo tace yace akai ma abokanshi
shi kuma a dafa mashi indomie amma ke zaki dafa ko?
tace eh nace to don kar inyi kuskure mami tayi dariya
tace kai ke kam kin cika tsoro,sababin kuloli mama ta
bani na zuba masu birabisko da miyar kaji yaji curry sai
kamshi yake,na dauka na tafi nayi sallama a kofar
dakinshi aka amsa mani cikin faduwar gaba na shiga
nace sannunku mutum uku suka amsa kaina a kasa ban
kalli kowa ba nace a ina zan ajiye?cikin dauriya nake
magana gabana sai faduwa yake wani daga cikinsu
yace maska tana magana,da sauri na dan dubi wanda
aka kira maska yana ta faman danne danne waya
tamkar ba dashi ake magana ba,dayan yace ke ajiye
kan wancan table din,na dubi table din sai naga akai
yayanmu ya dora kafarshi ,na dubi mai maganar nace ai
yasa kafa a kai yayi murmuahi sannan yace ajiye ko
ina kinsan halin yayan naku sai hakuri na ajiye a
gabansa don mami tace dama su ne zasu ci na juya
zan tafi sai naji murya mai sanyi amma cikin fada
akace ke haka ake bada abinci a gidanku ko?na juyo da
sauri ga mamakina yana danne danne wayarshi kamar
yanda na sameshi,sai a lokacin ne ma na dan kalli
fuskarshi, kykkyawa ne na ban mamaki don duk gidan
yafisu kyau sak kamarshi daya da hajiya yaya,tsawa
naji in ba zaki zuba musu ba dauki ki tafi,da sauri na
duka jikina na kyarma na zuba musu nan dakin ya bude
da kamshin miyar kajin na mika wa kowa sannan na
mike dayan yace dan bamu ruwa nace to zan fita
dayan kuma yace ga fridge nan na nufi gun fridge ina
tunanin yanda zan bude dan ban taba ganin irinshi ba
cikin sa'a ina dafa shi sa i naji na latsa wani abu sai ko
ya bude kayan shaye shaye ne kala kala na rasa
wanda zan dauko musu sai na dauko musu ruwa a
babban gora na dauko five alive na aje masu da na
duba saman fridge din sai naga kofuna irin na wajen na
dauko tiran kofunan gaba daya na aje a gabansu,ina
kokarin mikewa ne mami tayi sallama suka amsa har
da yayanmu ta shigo dauke da kula da plate da cokali
na fita na dan tsaya a kofar dakin ina jiran mami
labarin abinda yayanmu yayi mani sai na jiyo itama
tana shan nata fadan,muryar yayanmu ne yana ce mata
yar iska haka ake dafa abinci?indomie ne din ba za ki
iya dafawa ba?ina cewa ganin kin danfi su mariya abin
kirki ashe kema useless ce,sam ban ga wani amfani ba
gun mace matsawar bata iya abinci ba,ko aure kukayi
irin abinda da zakuyi kenan ko?sai naji muryar wani
acikin abokan yaya yana cewa to kayi hakuri mana
maska,ai yara ne sai naji muryar yayanmu din yana
cewa no.......
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Nasir kar ka goyi bayan wadannan yaran sam basu iya
komai na mata basu iya girki ba basu iya gyaran daki
ba,sam basu iya komai na mata ba yan iska sai dare
yayi ka gasu suna surutu da samari sannan ace masu
yara?yaci gaba da cewa bari kiji ba za'a yi asarar
wannan abincin ba maza ki dauka kije ki cinye shi ina
nan shigowa har dakinku inci ubanki in baki cinye shi
ba ina nan yanda kuka sanni ban canza ba fita useless
kawai,nan mami ta same ni a kofar daki duk na kara
firgicewa na dubi mami wadda ke zubda hawaye nace
mami yanzu ya zakiyi da wannan uwar taliyar don
Allah?tace zo muje sai da muka isa gun lungun shiga
cikin gida sannan ta dubeni tace don Allah iman ci
wannanabincin kiji nasa hannu na dandana daidai kam
yayi sai dai da ta dam kara wasu abu zai danfi wannan
dadi,nace yayi mana tace to kinji shiyasa ni sam bana
son ya sani wani aiki ga tozartani a gaban abokanshi
nace to ki kai ma masu wanke wanke su tafi dashi gida
mana tace wai in kaiwa su lami masu aiki?nace eh
tace baki san yayanmu bba kenan kar kiyi fata irin haka
ta hada ku kuma duk matar da ta aureshi ta shiga
uku,nace anty mimi zatayi fama muka wuce cikin gida
bansan yanda mami ta kare ba,sai washegari a school
take ce min zubar da rabi tayi ya sameta tana cin
rabin.Washe gari gab da magriba na dawo daga
islamiya da shike ina zuwa sanawiyya na shigo
gida,zaune a kofar dakin yayanmu samari ne su hudu
sai shi yayanmu yana tsaye yana daddana waya,nadan
yi mamakin yanda baya gajiya da danne danne waya
ban taba ganinshi ba waya ba kuma ko da yaushe cikin
danna ta yake tun daga nesa nake kallonshi sanye
yake da dogon wando da riga daga nesa nake kallonshi
sanye yake da dogon wando da riga mai gajeran hannu
masu ruwan bula da ratsin fari an rubuta adidas a
jikinsu,gsky yafi yan gidanmu kyau,maza da mata dogo
ne yana da dan fadin ga kwarjini gashin kanshi a
nannade ina tsammanin yana sanya mai ne akan ko
kuma haka gashin nashi yake?oho ban san dalili ba duk
sanda na ganshi sai gabana yayi wani mugun faduwa
bana raba daya biyu don ina jin tsoronshi ne,na iso daf
dasu kanshi a duke yana danna waya amma sai naji
yace ke in kin shiga kice Sa'a ko Bilki su kawo mana
butoci,to ba ma magana dasu Sa'a ko ince basa min
magana kuma ban ga mami ba sai naje dakinmu na
dauko butoci guda biyu na kai masu shi baya gun ina
zaton bayinshi na daki zaiyi sagir na tura sagir ya
kwaso mana butocin,wata rana asabar zan tafi
islamoya don yanzu bana jiran kowa a yan gidanmu dan
ba lokaci daya muke karatu dasu ba sai dai na biya wa
Amira mu tafi,sanye nake da hijab har kasa nasa safa
da nikab yayanmu na gani yana kulle dakinshi sanye
yake da gajeren wando da yar rigar nike kafarshi da
safa da takalmi but na kwallo da alama zai motsa jiki
ne,nazo zan wuce ya dan dubeni ina jin yana son ya
gane kowacece kamar na gaishe ahi sai kuma na fasa
ina zaton bai gane ni ba,na gota shi kadan sai ya juyo
yace ke gabana ya fadi dama cikin faduwar gaba
nike,na dawo kaina a kasa nace gani baiyi magana ba
ya gama rufe dakin ya matso gab da ni sannan yasa
hannu ya dage nikab din idona ya firfito don tsoro yace
ooh na dauka mami ce,ya cigaba da magana fuskarshi
a daure ke na lura sam baki gaida mutane ko?na dan
saci kallonshi fuskata yake kallo na kali kasa sannan
nace ina kwana?yace wuce bani so sai da na roka
kenan dubeta ,a raina nace masifaffe kar ka amsa din
na tafi abina.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Zama da Amira yasa yau da gobe nima na soma
karanta littafi kuma sai da na tambayi mama tace
amma na dinga karanta masu kyau kuma masu amfani
sannan in har zan karanta to ya zama bani da aiki ko
na makaranta ko na gida shi yasa ma nafi yin karatun
da daddare kasancewar bana fita ko ina ko samari
sunzo kirana mama bata matsa mani ba don tace in kr2
nake son nayi to na tsayar da hankalina gun
karatun.Yau monday muna hutun easter bani da wani
aiki duk na gama kwance nake bisa gadona ina karanta
wani littafi mai suna auren kisan wuta ina jin dadin lbr
banji sallamar mami ba sai dai naji an fisgw littafin
daga hannuna cikin sauri na tashi tana dariya tace kai
iman,ke dai kina krt nan baki jin komi,nace lbr ya
hadu,tace hala na soyayya ne?nace eh tace ai na sani
nace kin san me?ai ku ne kuke soyayya ni kin ganni da
saurayi ne?naci gaba da cewa wallahi ni banma yarda
akwai wata soyayya da kuke cewa ba,mami ta soma
dariya tace lallai yarinya da sauranki ke da kike karanta
littatafai ai ke