Showing 1 words to 3000 words out of 26020 words
Chapter 1 - TAWA TA SAME NI BOOK 1 COMPLETE DOCUMENT by Halima Abdullahi k. Mashi .txt
Tawa Tasameni 1-01
Posted by ANaM Dorayi on 12:09 PM, 03-Dec-15
________________NA _________________
__________ HALIMA ABDULLAHI K/MASHI_______
Na mike a hankali ina ninke sallaya ban kai ga ajiyewa ba
naji ana sallama,na juya cikin don san in dauki muryar
mai sallamar har kin shigo kenan?nace bayan na amsa
sallamar ta shigo sanye da kayan makarantar islamiya
masu launin farare kar,riga da wando da hijabi. Tace kina
kallona ba zaki yi sauri ba sai munyi latti ko?nace ko
munyi latti ai yau akwai layi na nufi daki dama nayi
wanka sai kawai na dauki kayan makarantana dake goge
kan gado nasa,Amira tace su mama basa nanne?nace eh
basa nan gashi har jamila ta tafi a lokacin islamiya yayi
amma basu dawo ba,na rungume takarduna da Alkurani
na na fito falo muka fita na mika ma amira ta rike min
littattafaina don zan kulle kofar,natura key din inda muke
sawa in mama zata unguwa ni kuma ban dawo daga
makaranta ba sai ta aje min a gun in kuma zan fita tace
in aje mata.Amira ta dube ni ta dubi dakin su mami tace
yau su mami ba zasu bane?nace da kyar ne don yau ko
makarantar boko bataje ba bata jin dadi in mun dawo kin
gaida ita.isarmu islamiya kenan muka tarar da an tare
yan latti ana yi masu bulala,Amira ta soma dariya don ta
sanni da tsoron bulala na dafe kirji ina fadin yau na shiga
ukku zamu sha bulala ni iman,Amira tace don Allah mu
karasa ba kece kika jamanaba?nace Amira ina jin tsoro
ta ja hanuna na bita muna isa gun muka tadda harda
Ahmed yayan Amira don shine Amir dinmu yace don
Allah ku zo inyimuku ku wuce don yan kwanakin nan kun
kware gurin yin latti.Nace don Allah yaya Ahmed kayi
hakuri yace wllh sai nayi maku kun fi sauran ne?da zan
kyaleku ya ci gaba da cewa kuna bata mani lokaci in har
kuka bari kowa ya gama shiga sai na zane ku tas,wani
kusa dashi yace to kai Ahmed ka bar su su wuce
mana,yace Allah Aliyu bazasu shiga ba sai na dakesu
wanda yaya Ahmed ya kira da Aliyu yace to bari ni in
dake su to,yy Ahmed yace sai dae kai na dake ka a
madadinsu,in ko ba haka ba sai dai suzo ni in dakesu da
kaina,Amira na da zuciya don haka sai taje ta mika
hannun shi ko bai bugi hannunba ya zuzzuba mata a
jiki,ganin haka ya sani na kuma rudewa ina faman
magiya don ni kowa ya sanni da shegen tsoro sannan
bani son abinda zai taba mani lfyata don haka ma
dawuya ka ga nayi laifi nakan yi kokari ganin nabi dukkan
dokar da aka shimfida a gida ko a makaranta.Amira
ganin zan bata mana lokaci taje gaban yy Ahmed tace
ka bige ni a madadinta shiko da gayya ya ringa tsala
mata har sai da Aliyun nan suka ce ya isa mana Ahmed
niko hawaye na somayi na kama Amira muka wuce ina
fadin me yasa kika je ya buge ki?ta soma share mani
hawaye muka wuce ajinmu,Shidda na yamma daidai
muka tashi dama mu yan aji biyar Ajinmu a sama
yake,don haka titin kan layinmu naji an kwala mani kira
cikin fada na juyo sai naga anty mariya gabana yayi
faduwa don na san ganin ta ba alkhairi bane hakan ce ta
kasance domin kuwa tana isowa gun mu sai ta hauni da
zagi wai na taho makaranta ban jira su kamal ba don
naga ba kannena bane shiyasa ta cigaba da zagina gami
dayi mani gorin gida wai shegiya agola yar kara nazo zan
fare,Amira tace mani don Allah iman zo muwuce taja
hannuna cikin fushi tayi maganar,anty mariya ta koma
kanta tace ke kar kiyi mani rashin kunya don zanci
ubanki a nan,Amira tace ba dai ubana ba kuma har kika
yarda kika buge ni zakiyi da kin sani,cikin rawar jiki na
rufe ma amira baki muna cikin wannan hali sai ga anty
hadiza da bilkisu da saade dukkansu sai zaginmu suke
yi,Sa'a har da dungurina,nan amira ta kai mata duka nayi
saurin rike amira don kar suyi mana taron dangi su bugi
banza don nasan kadan suke jira anty mariya tace wai
ke amira nan da dukan Sa'a zakiyi?amira tace yo da sai
in barta ta duke mu,don kunga bata ramawa ne,lman din
shi yasa ku ka raina ta, taci gaba da cewa,ai Sa'ar ba
girman lman din tayi ba,bilki tace to ta koma gidan
ubanta mana in kuma bata dashi bane mu sani,naja
hannun Amira muka wuce Amira ta cigaba da lallashina
sannan tace min,don Allah lman in tambayeki mana?na
share hawayen fuskata da gefen hijabina nace ina jinki
tace babanki ya rasu ne ko yana nan? In ya na nan ina
yake?na dan yi shiru sannan nace Amira baba na yana
nan bai rasu ba wasu hawayen suka kuma zubo mani
ban damu da in goge ba na cigaba da cewa yana tudun
wada ta nan kaduna,Amira ta ce to ki koma mana don
zaifi maki kwanciyar hankali komin talaucin ubanka ya fi
zaman agolanci y not ki koma can?nace uhhm Amira
mubar zancen nan wata rana zan sanar dake dalili mai
karfi da ya hanani in bar gidan nan sannan kisan
mahaifina ki kuma daina zargin ko kwadayi ne ya zaunar
dani a nan,Amira tayi sauri ta rike ni gami da tsaidani
wuri guda tace wllh ni ba nufi na kenan ba naga
wulakancin da su Sa'a ke maki yayi yawa ne shi
yasa,nayi mirmushin karfin hali nace no a
Amira karki damu na fahimceki sannan muka wuce gidan
su Amira,kamar minti goma na dauka gidan su Amira
sannan ta rakoni kofar gidansu tace min a cikin satin nan
ba zata shiga gidanmu ba,ina shiga naga su Anty mariya
sun rigani dawowa kuma sun fadi karya da gasky sai
faman fada suke su da iyayensu suna ganina ai dawa
Allah ya hada su ba dani ba suka hauni da masifa,Haj
Kulu mahaifiyar mami harda aibantani gami dayi min gori
sannan tace zata ga Amiran don ubanta sai ta gaya mata
dalilin da yasa ta zagi su anty mariya don ba sa'anin
yinta bane,ni dai sum sum na wuce daki
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Mama na gani a falo ta zuba tagumi da alama taji duk
abinda suke cewa(kishiyoyin nata)ta dubeni fuskanta
cike da tausayina tace Iman menene dalilin da yasa kika
tsokanin mutanan nan bayan kinsan halinsu sarai nace
mama wllh ban san me nayi masu ba na dai ga anty
mariya sun zo da su Sa'a suna ta faman zagina wai ko
na taho makaranta ban jira su Kamal ba ko mene oho
mama tace to naji suna cewa kuna ta zaginsu keda
Amira nace Allah mama ni sam ban ma yi magana ba
Amira dai ce kinsan ta da zuciya shine fa ta tanka masu
amma sam bata zagesu ba,mama tace to don Allah ki dai
na kulasu sam musamman a kan titi in ma sun zo maki
da irin wannan ki dinaga basu hakuri kiyi wucewarki kinji
ko?nace to mama muka mike don yin sallar magariba.
Misalin sha biyu da rabi muka taso daga harda yau ma
yan dakinmu ne kadai ni da jamila da sagir muka je,dama
sauran yan gidan zuwa islamiya bai damesu bane bare
ma hadda,gara ma mami takan je to amma tun fridy bata
jin dadi,muka tadda mama a kicin tana girki na shige
kicin din bayan na ba jamila Alkurani na da hijab ta wuce
daki nayi ma mama sannu gami da amsar albasar da
take yankawa,nace yau me kike dafa mana ne,tace dan
wake nayi in kin gama yanka albasar ga mai can sai ki
soya shi bari in dauko kular baban ku nasa mishi,don
yace zaya aiko a dauka nace dan waken za'a kai mashi
kasuwa mama?tace nima haka na ce mashi sai yace
yasan komi na dafa ba zaiyi shakkar kaishi cikin jamaa
ba,nayi murmushin jin dadin an yabi mamana ai kin iya
girki ne mama,ta fita tana dariya ina jin dadin yanda
mama take sakar mani fuska duk da kasancewa ta yar
fari a gunta sannan mama uwa ce mai wahalar samu
takan ki nata don duniya ta soshi bata fada da zagin
yayanta sai dai nasiha gami da lallashi.bani manta
lokacin da nake karama mama ta kan zaunar dani ta
nuna mani girman Allah gami da cusa mani tsoronshi
tana nuna mani abinda zanyi da tsira daga azabarshi a
wancan zamanin ta kance kar na zagi kowa ko an zage
ni kar na rama sannan kar na yarda sallah ta ringa
wuceni don haka ma tun ina karama nasan sunnoni da
farillai gami da mustahaban sallah da alwala sannan bani
zagi in ma wani yayi naji sai na gudu ince kar na sami
zunubi saboda jin da nayi shiyasa ban iya zagi ba,sannan
mama ta na da hakuri na ban mamaki zata iya zama da
kowa ga ladabi don ban taba ganin tana musu da
maigidanta ba komai yace tana yi sannan ga tsafta komi
namu daban yake duk inda muka shiga ni da kannena
mukan zama abin sha'awa gashi mama ta iya girki sosai
na zamani da na gargajiya shi yasa maigidanta ya kanyi
alfahari da ita baya shayin kawo baki ko shi akai mashi
kasuwa haka nan duk da cewar basu shiri da abokan
zamanta suma suna farin ciki da ranar girkinta don sunci
mai dadi sannan yayansu kanyi rigima a duk lokacin da
suka zo cin abincin kai ko ruwan tea ta dafa daban yake
don zaka iya shanshi ba sai kasa madara ba.nayi zurfi a
tunani bansan har mama ta dawo ba sai dai naji tace
haba iman har yanzu kina kan yankan albasar nan baki
tashi ba?nayi firgigit na juyo tace ai kina tunanin menene
haka?bata saba mana da karya ba don haka na sanar da
ita tunanin da nake na kara da cewa mama ina matukar
jin dadin zama dake kuma ina alfaharin kasancewarki
uwa a gareni tayi murmushi tace sai ki dinga koyi da
hakan kuma kiyi watsi da duk wani kuskure da kika ga
nayi sai da na zuba albasa a cikin man sannan nace wllh
mama ni ba taba ganin wani kuskurenki ba tace kar ki
kuma cewa haka babu mutumin da baya kuskure dan
adam ai ajizi ne nace to,sai da muka gama cin abinci
sannan na nufi dakin su mami don in gaisheta ina son
inje amma ina tsoron haj kulu mahaifiyarta ynxu ma
ganin ta shiga wanka shine dalilin da yasa xan je duk da
dai bayin a dakin yake amma nasan ta shiga wanka ne a
bakin kamal inda na tambayeshi ta na nan yace man ta
shiga wanka na samu mami zaune a falonsu tana cin kifi
nace yan jinya an samu lfy kenan tace kar kice man
komi komi tunda baki zo gaisheni ba nace wlh ina son in
xo gaisheki ina jin tsoro ynxu ma kamal na tambaya yace
mani mominku ta shiga wanka,um kina jin tsoro ne?nace
baki yarda bane tace na yarda nace Amira ta na gaisheki
tace tana amsawa tace ai naji sauki kwarai don naci dan
waken mama sosai kafin inyi magana sai muka ji
maganar haj kulu fuskarta a daure ta nuna ni tace
wannan yarinyar baki da zuciya in banda rashin zuciya
har yaushe zamuce ki bar shigo mana daki amma kin
kasa to yi nan ta nuna min hanyar waje.ta cigaba da
cewa kekasashiya marar zuciya anyi halin uwa mami
tace kai mama don Allah ta kaima mami duka a gadon
baya yi min shiru yar iska duk ba kece kika jawota ba in
na kuma ganinta anan sai naci ubanki ni dai nayi waje
cike da takaicin zagin da nasha.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
washegari monday ga aladar gidanmu duk mai girki itace
zata tashi tunda asuba dafa ruwan tea ko wane daki
suna zuwa su dibi nasu a cikin flask su kai daki suje su
hada,yau haj kulu ce da aiki don haka sai da na bari ta
fita sannan naje diba bansan cewa madara ta kare ta
kicinba sai da nazo hadawa da sauri na nufi daki na iske
mama tana sa ma jamila safa nace mama babu da
madara ko kadan ta dubeni tace kash jiya.... amma ga
dari biyar can kan mirror dauki ki siyo yanda zata isa in
yaso kafin ya wuce sai in sanar dashi nace to na dau
kudin na fita,a tsakar gida na iske mami sanye da
uniform hannunta rike da safa tace har kun gama
karyawa?nace aah ya jiki tace da sauki yau dai zanje
makaranta nace da kyau kam ki leka ta dubeni ynxu ina
zaki?nace shagon sanita aje safar akan window din
dakinsu taje muje in rakaki nace kardai a nemeki tace
kedai muje,dashi ke shagon ba nisa nan da nan muka
dawo shigowar mu kenan haj kulu ta fito daga daki
ganinmu tare da mami ya yi matukar bata mata rai ta
hau mami da zagi gami da daukar alkawarin dukan
mami,haj yaya uwargida sarautar mata itace ta fito daga
dakinta tace ke kulu kina bani mamaki ga yar iskar da
zaki jibga nan ta nunoni sai ki hau yarki da zagi kinsan
fa ita da uwarta in mutum ya sarkafe masu baya ji baya
gani sai Allah da malaman gari indai zakiyi mata addua
to kawai kiyi mata,niko uwar tsoro jin ance zaa bige ni
sai nayi daki da gudu ko mama ban bari taji xancen ba
don bata son tashin hankali kuma Allah ya taimaka ta
kunna rediyo inda tasa kaset na kr2n Alkurani kira ar
sudes,a gurguje muka karya don kar muyi latti muna
cikin sallama da mama kamal ya shigo wai kuyi sauri ko
muwuce inji anty mariya mama ta miko mani naira
hamsin tace gashi sa jikka nace barta mama gafa ta jiya
nan ban kasheba sagir yace meyasa mu ba'a bamu kudin
mama tace ku ai ga kwandonku nan cike da kayan abinci
amma in kun girma zan dinga baku kuma,jamila tace kai
sagir mama tace babu kyau a ba kananan yara kudi yace
wai haka mama? Mama tace e mana nace kai muje kar
ayi ta jiranmu mama sai mun dawo tace to..
haka rayuwa ta cigaba da kasancewa kuma kusan ko
yaushe inada abunyi ban cika zaman banxa ba in bani
makaranta to ina kicin in ranar girkin mama ne don haka
nima babu girkin da ban iyaba na gargajiya ko na zamani
haka nan kuma na kan gyara dakin mama da namu da
falo sannan na kware gun wankin bayi nasa turaren wuta
shiyasa dakinmu kullum yana cikin kamshi da sanyayar
iska mai ddi na kan zauna nida yan kannena in koya
masu kr2 Alkurani da sauran littatafai haka ina taimaka
masu da homework dinsu shiyasa mun fita daban a
gidanmu komi namu tsaf tsaf,a ranar wata sundy lokacin
muna hutun islamiya, hadda ma don muna kusa da fara
azumin watan ramadan da safe misalin karfe goma da
rabi na gama duk wani yan gyare gyare nace da mama
bari na shiga gidansu amira dama nan ne gurin zuwana
tace to ki gaida mmn faruq nace to,na samu Amira tana
faman krtun littafin hausa a falonsu ko sallama ta bata ji
ba sai da na zabga mata uban duka sannan na fizge
littafin na duba sunan shi naga Allura cikin ruwa,nace
kedai kullum kina cikin krtu maman su ta fito na gaisheta
tace mani yasu mama nace tama ce a gaisheki tace ina
amsawa na dube ta nace mama wai baki hana Amira
krtun nan ne?maman su Amira tace nayi nayi taki bari
ynxu ma boyewa take don tasan in na gani yaga shi
nakenace in tana son tayi karance karancenta ta bari sai
ta kai ss sannan ta kijiba sai tayi tayi ba,maman tayi
shiru cikin bacin rai na harari Amira nace kinji ddi mama
ta bata rai saboda ke?mama tace ai ke kina da hankali
ba kamar ita ba ta shige daki Amira ta dubeni tace kinji
ddi kin hada ni da mama nace no Amira in iyayenmu
sunce mu bar abu muyi kokarin bari don gsky zan gaya
maki da ki kijin mgnr iyayenki gara ki bar duniya a guna
kenan tace to naji taja hannuna tace zo muje dakina
nace ke dai Amira baki son fadin gsky muna shiga na
zauna bakin gadon nace mata don Allah Amira kiyi kokari
ki barin krtn nan tun da mama ta baki damar yin krtn in
kinje ss.Amira tace nayi kokarin na bari na kasa ne,nace
ni ko kingani nan ko me mama tace na bari ko da zan
rasa raina ne ba zan bari don bani da tamkarta nai shiru
ina tunani hawaye ya zubo min na dubi Amira nace don
dai iyayenku duka biyun suna nan raye ko ince a tare shi
yasa baki san zaman agolanci ba cikin hawaye ban san
sanda nace.........
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
sunana na gsky shine Amina kuma naci sunan kakata ce
mahaifiyar babana ,babana da mamana yan asalin wudil
ne a wani kauye da ake kira indabo a jihar kano,babana
gidansu sun gaji sarauta don babanshi ne dagacin
kauyen,yanxu haka itako mama yar malamai ce don
babanta shine limamin garin sunan mahaifina idris kuma
shine da na hudu a gurin mahaifinsu yana da yayye yaya
samaila sai yaya musa sai babana idi kamar yadda suke
kiranshi sannan sai kannanshi biyu bala da sani su
shidda ne a dakinsu matan dagaci biyu ne uwargida
Amina mahaifiyarsu babana kenan wadda naci sunanta
sai abokiyar zamanta basira wacce aka bashi sadaqarta
ita kuma yayanta ukku Auwal,salisu sai hindu,suna
matukar zaman lafy ba wani bambanci wannan shiyasa
yayansu hadin kai da son junansu gashi suna ma
mahaifinsu dagaci umar biyayya kuma dukkansu gidan
liman suke daukar krt mama ko a lokacin tana kaduna
gidan yayanta mai suna mal bashir ya dauko ta ne tunda
mahaifiyarsu ta rasu shi babban malami ne a tudun wada
daga yawan almajiranci Allah ya zaunar dashi a inda yayi
auren shi da baba uwa itama dai yar can din ce da yaje
ya auro ta,yana almajiranci a wani zuwa da yayi gida
shine ya tafi da wasu almajirai a cikinsu harda idi
babana kenan domin yayi sauka tuni,zai dora ne su ko
su mama su hudu ne a wurin liman kawu bashiru shine
babba sai kawu Aminu sai kawu kabiru sai mama ita
kadai ce mace tana da shekara tara mahaifiyarsu Allah
yayi mata rasuwa kasancewar ita kadai liman ke aure sai
kawu bashir ya dauko mama dama baba uwa bata taba
haihuwa ba ko ince har ynxu Allah bai bata haihuwa ba
sai ko ta rike mama,shi ko liman isuhu aka bashi sadaqar
mata guda biyu da taimakon baba uwa mama mai suna
habiba ta samu shiga firamare shi ko baba yana nan
yana hadda gidan sai Allah ya hada shi da makocinsu
Alh adamu a dalilin dan gwanjo ne a kasuwar bacci yasa
baba yana rubutu yana kai masa daga nan yace yana
yayi sanaa irin ta gwanjo alh adamu shima dai dan kn ne
ana ce mashi adamu garko duk girinsu daya sai dai shi a
garko yake bayan nemi izinin malaminsa wato kawu
bashir kawu yace tunda kayi sauka hadda kakeyi ba bu
komai ko da rana za ka iya haddar ka Allah ya bada saa
wannan sanaar itace hanyar arzikin mahaifina tun yana
kasawa a bakin titin kasuwar bacci in an kwance dila a
bashi ya kasa har ya koma kwance dilar shima kafin
shekara ukku har ya sayi rumfa kuma yana sayan diloli a
wannan lokacin ne Allah ya ba baba uwa ciki ta haifu da
namiji kuma mama a lokacin ta kammala primary shiko
babana duk da ba a gidan yake ba yanzu yana zuwa da
daddare haddar shi ya sanar da malam kamar yadda
suke kiranshi