Showing 18001 words to 21000 words out of 44953 words
Chapter 7 - Zumuntar kenan Book 1 by Sumayya Abdulkadir Takori.txt
Family. Tafiyar Fa’iz da tafiyar Yaya Aliyu bada jimawa ba jami’ar Lagos yin digiri na biyu.
Don haka a hutu na gaba da muka zo mun yi kewar Yaya Ali ba kadan ba. Na yi kiba na yi bul-bul na dan yi haske dai-dai misali, sai sheki da kyalli nake yi, ke kuwa babu fargabar Fa’iz ko kadan wanda shine kadai matsalata a rayuwa.
A wannan hutun da muka zo ranar wata asabar ina dakin Hajjah ina sallah na jiyo sassanyar muryar Yaya Aliyu a tsakar gida yana gayas da Hajjah. Bai tambayi kowa ba, bai tambayi komai ba daga gaisuwa sai “Hajjah ina Fa’izah ne? Ban ji motsinta cikin gidan nan ba”.
Hajjah ta ce, “Tana ciki, nake jin sallah take. Ka san in aka soma doka nafilfilin nan sai Allah. Ai ma hushi ake da kai tunda ka tafi Lagso ba sako ba aike balle waya”.
Ya kama kai abin ban dariya, ya ce, “Oh! Ni Aliyu Bamalli na shiga uku!!” Ya yo cikin dakin da gudu-gudunsa. Hajjah ta yi dariya ta ci gaba da abin da take yi.
Zaneerah ta ya da tawul din da take tsane jikakken gashin kanta, ta zaro ido ta wara hannuwa tare da daka tsalle ta dire gabana ta ce, “Yaya Aliyuuu! Muryarshi a tsakar gida Fa’izah!!” Ta yi wuf ta yi bakin kofa zata fita.
Na ce, “Ke Zanirah baki da hankali ne? Haka za ki fita daure da tawul?” Zanirah ta dubi kanta ta ce, “Oh! Na gode Fa’izah, kin san Allah duk na rude sabida murna”.
Na bita da kallo a lokacin da take zurma doguwar riga a jikinta, jikinta har rawa yake yi. Ni yadda take rawar jiki a kan Yaya Aliyu da al’amarin sa, ko ni da ya fi nuna kulawarsa a kaina bana yin hakan balle irin wannan zumudin, ni haushinsa ma nake ji wallahi tunda ya tafi bai neme mu ba, ba waya ba sako.
Tana kokarin fita yana kokarin shigowa, sai suka yi karo garam! Ya yi hanzarin ja da baya tare da ware ido.
“Zanirah kin makance ne?”
Da gudu ta nufe shi ya yi hanzarin kaucewa a hankali ya ce, “Zanirah kin girma, shekaru goma sha biyar, kada ki sake ki kara yi min irin wannan oyoyon kin ji ko?”
Ko ni kaina ba don na nutsu ba da ba zan ji shi ba, domin cikin kwantaccen sauti ya fada.
“Wannan sai su Hanifa sune yara (diyar Baba Sadi)”.
A raina na ce, “Ai ko Hanifa ba za ta yi haka ba, ita ma Zanirar ban san yau ina ta samo wannan bakuwar al’adar ba wadda sam bamu tashi da ita ba. Amma da na yi la’akari da dadewar da muka yi bamu ga Yaya Aliyu ba, sai ban ga laifinta ba, at the same time, na yi mata uzuri da ajizanci wanda dan Adam baya rabo da shi.
Zanirah na dariya ta ce, “Yaya Aliyu ka rage min fa, da watanni biyar cur!” Ya ce, “Yar gari, ashe kina sane?”
Bai koma ta kanta ba ya shigo ya russuna har inda nake, kamshin daddadan turarenshi ya doki masunsunata.
“A roka damu Alasabbinaki”.
Na zumbura baki na gyara zaman carbina cikin hannuna na kau da kai. Cikin dariya ya sassauta murya ya ce, “Na yi laifi ne Princess? I’m so sorry. Wallahi ban yi da niyya ba....”
Na kara turo baki na kau da kai. Yaya Aliyu ya yi dariya ya sa hannu cikin bakar leda ya bude, kamshin wani irin lafiyayyen balangu ya doki hancina.
Na hadiye wani tsinkakken miyau ji kake mukut! Dariya ta kashe Yaya Aliyu. Ya sa hannu ya zare carbin ya tura min kunshin balangun gabana. Ai ban bata lokaci ba tuni na ja kunshin leda cinyata na juya mai baya, na manta da fushin na soma dauka ina dannawa wani na bin wani.
Zanirah ta zo ta zauna za ta ci na doke hannun ta, ta ce, “Yaya Aliyu Fa’izah kadai ka sayo wa?” Muryarta abin tausayi.
Ya ce, “Eh, domin shine favourite dinta, kowa ma na sayo mai abin da ya fi so a rayuwarshi”. Ya sa hannu a aljihu ya fiddo alawar cakulet mai kwakwa (Bounty) ya mika mata. Zanirah ta yi tsalle ta cafke ta yi waje, na tattara ledar namana na mike zan bita amma Yaya Aliyu ya rike gefen hijabina, gaba daya na juyo.
“Wai me na yi ne don Allah Fa’iza? Na taho gari ya gari tun daga Lagos domin ki amma kike zumbura min baki?”
Na bude baki cikin mamaki na ce, “DOMIN NI?”
Ya yi saurin girgiza kai, ya ce, “A’a, DOMIN KU”.
Na ce, “To sakar min hijabin na gaya maka kada Hajjah ta shigo”.
Ya yi saurin saki. Na koma na zauna na ce, “To don me tunda ka tafi makaranta ba sako ba waya Yaya Aliyu? Don me za ka koma makaranta Yaya Aliyu?”
Ya yi murmushi ya ce, “Fa’iza ke yanzu ba makaranta kike ba?”
Na ce, “To in anyi degree ba shi kenan karatun ya kare ba? Da dadewa na taba jin an ce ka yi digiri”.
Ya girgiza kai “Is just the beginning Fa’izah digiri na farko shine tushen duk wani ilimi. Ilimi ba shi da iyaka, ba shi da karshe sai dai ka yi iya wanda za ka iya ka bari. Ina so na yi ilimi mai yawa ba digiri kadai ba, ko baki son wata rana in zamo Farfesa kamar Baban A.B.U? In yi gida nawa na kaina a duk inda nake so a outside ba a A.B Bamalli Estate ba cikin kauyen Giwa? In yi family mai tsari irin na Baban A.B.U? In yi rayuwa mai tsari irin ta Baban A.B.U? Ba irin ta su Baba Barau ba Fa’izah”.
Ban san sanda na tuntsire da dariya ba. Na ce, “Ai ni na yi zaton don ka gaji da kai mu makaranta da dauko mu ne da zuwa mana visiting shi ya sa ka koma karatun don ka gaji da saya min nama, Zanirah (Bounty) Ummi (Kit-kat), ka gaji da kai mu shopping da koya mana karatu, shine ka tafi”.
Dariya mai suna dariya kam Yaya Aliyu ya yi ta har ya gaji, ya ce, “Fa’iza yaushe za ki daina wauta ne don Allah? Shin in tambaye ki, da can waye ya sani yi muku hidimar makaranta? Waye ya sani sai muku balangun da alawa? Waye yake sani in kula daku in ba don ina son ku ba?
Na rantse da sarkin sarakuna ba zan taba gajiyawa da hidimta miki ba muddin rayuwata! Ko da bani da shi, zan yi aikin karfi da lafiyata in nemo in yi miki in har za ki yi farin ciki. Balle kuma alhamdulillahi Allah ya hore mana arziki na duniya dai-dai gwargwado, ta yadda har nake raina ‘yar hidimar da nake muku wanda har ke kike kallon ta kike kiranta hidima.
Ko da duk abin da na mallaka zai kare wurin sai miki nama ba zan damu ba, saboda dalilin da har yanzu kika kasa ganewa. Kada ki kara saka wannan a ranki (wai ina yi muku hidima), kada ki kara tunanin hakan, sa a ranki wannan Dutyn Aliyu ne”.
Ina wani irin murmushi mai fitowa tun daga karkashin zuciyar dan adam na ce, “Ba zan kara ba Yaya Aliyu”.
*****
Washe gari muna gidan Baba Na’ibi (gidan su Yaya Aliyu) muna kallon wani wasan kwaikwayo na ANTAR-BN-SHADDAD da ABLAH, domin mu zuri’armu kaf daga shekara kasa da sha takwas, ba a kallon finafinan Turawa, na Hausa ko na India, ko na ‘yan kudu (Nigerian Film), sai hikayoyi na Larabci da Risalah, ko tarihin Sahabbai da ake yi a matsayin film kamar na Khulafa’ur-Rashidun.
Domin wannan finafinai da na zayyano a sama a ganin Hajjah duk nau’i ne na illata tarbiyyar yara da hana su mai da hankali ga karatu. Daga na yake-yaken Larabci (Adventure) sai zaluncin da Isra’el ke yiwa ‘yan’uwa musulmi na yankin Gaza, sai Islamic Channel wadanda suke nuna halin da kasashe marasa karfi ke ciki, irin su Somalia da irin tallafin da NGO’s suke yi musu, irin su ‘Human Appeal Organization’ masu daukar nauyin irin wadannan kasashe ta hanyar abinci, ilimi, asibiti da tufafi.
Wadannan al’umma masu ban tausayi abubuwa ne dake karawa yara imani da wadatar zuci. Sai ko labaran Larabci na Al-jazeera, CNN, BBC. Saboda yawan kallon al’amuran Larabawa da nake, da sauran labaran Larabci da kallon rayuwarsu a talabijin, dadin-dadawa ana yin Larabci as (Subject) a ajinmu, sai ya kasance na iya Larabci sosai, kuma shine harshe mafi soyuwa a gare ni tun ina (Area One). Tun ina karama Allah ya dora min kaunar Alifun-Ba’un, Alifun-Arnabun, Ba’un-Baqaratun.
Maryam ta dube ni muna cikin kallon ta ce, “Wai me Antaru ya ce kenan Fa’izah?’ Na fassara mata, ban ida rufe bakina ba Yaya Aliyu ya shigo.
Ya samu gefen mahaifiyarshi ya zauna, ta ce, “Ya ya dai Yayansu? Na ganka rather moody? In ce ko ka dauki abincinka ka ci?”
Ya dan yi tsaki ya ce, “Mama na sha kunun alkama fa a wurin Hajjah yanzun nan”.
Ta dube shi tsaf, cikin babbar murya ta ce, “Aliyu!” Da hanzari ya dago ya dube ta.
“Na gaji kullum magana daya ta ki ci ta ki cinyewa. Yanzu kamar kai Aliyu sai an rarrasheka ka ci abinci za ka ci, sai ka ce wani karamin yaro, da gangan kake wasa da lafiyarka, to na daina, sai dai ka kashe kanka kai kadai, wallahi ka kwanta ciwo ko hanyar asibiti ba za ka ganni ba. Ko da yake in ka kashe kanka ai kai ka jiyo, wa ka yiwa asara?”
Na juyo daga kallon T.V na ce, “Mama mu mana? Mu aka yiwa asara”.
Zanirah ma ta ce, “Tabbas mu ya yiwa asara, we cannot, never found a caring brother like him, Yaya Aliyo don Allah daure ka dinga cin abinci in ka mutu mun shiga uku”.
Na ce, “Mun shiga uku ko mun shiga tara?”
Ummi ta ce, “Har mun lalace”.
Zanirah ce ta mike ta yi kitchen da zafin namanta, ta shako plate da dankali soyayye da murtukekn kwai, ta zo ta zauna tsakanin Mama da Yaya Aliyu kasancewar suna zaune kujera daya ne mai cin mutum uku.
Cike da kulawa ta mika mishi, kana cikin muryar lallashi da kulawa ga karamin yaro in ya ki cin abinci ta ce, “Yaya Aliyu don Allah ka ci”.
Gaba daya aka kwashe da dariya har Maman dake bambamin fada, babu shakka yadda muke kula da Yaya Aliyu da hidimarsa, da yadda shima yake kula damu da al’amuranmu, yana yi mata dadi, don ko Maryam da suke ciki daya ba ta kulawa da al’amarinsa kamar yadda muke masa, haka shima.
Ga shi tana masifar son Yaya Aliyu kamar ba dan fari ba. Ita cikakkiyar lauya ce mai zaman kanta, sam ba ta irin kawaicin Momina, mu’amalarta da Yaya Aliyu kamar ta Yaya da kaninta mai binta da suka fito ciki daya. Hakan ba karamin bani sha’awa yake ba, in yi ta dakacen ina-ma a ce nice.
Na taso tsam daga inda nake zaune zuwa garesu na ce, “Mama tashi ki bamu fili in bai ci ba dura zamu yi masa”.
Ita da Yaya Aliyu suka sa dariya, ta ce, “Lallai kam ‘yammatan Hajjah kadan daga aikin ku, kuma aikinku yana kyau, Allah ka bani tsawon ran da zan ga da wacce za ayi tsakanin ke, Ummi da Zanirah.....”
A hargitse Yaya Aliyu ya yi ma Mama gyaran murya ga alama bai ji dadin abin da ta fada a gabanmu ba. Ta mike ta bar mana falon tana dariya tana fadin “Sannu-sannu ba ta hana zuwa sai dai a dade ba a je ba”. Sai da muka tilastawa Yaya Aliyu ya cinye abincin nan tas, sannan muka kyale shi.
Ya ce, “Ummi ban ji yadda aka riski Queen Amina ba?” Ta ce, “Tambayi gimbiyar taka mana ni ai baka yi dani Yaya Aliyu, ka kawo mata nama, Zanirah pack din Bounty, amma ni ko sannu don ni lukuta ce tun ranar da ka fada Zanirah ke tsokanata ba a yayin lokutayen mata”.
Ya murmusa a hankali, ya fiddo pack din kit-kat a aljihunsa ya cillawa Ummi. Ta dauke tana dariya tana godiya, ya ce, “Saboda Allah Zanira ina ruwan ki cikin wannan maganar har da kike tada ta bana nan?”
[6/3, 4:12 pm] Takori: Ta ce, “Rabu da ita Yaya Aliyu, ita ta fara ce min mai wuya uwa marikin lema, an fada din, ba a yayin lukataye sai ‘slim’ din ki yi duk abin da za ki yi”.
Ya fiddo mata ido ya ce, “Kada na kara jin irin wannan maganar, babu kyau gorin halitta Zanirah, kada na kara ji”.
Ummi ta ce, “Rabu da ita Yaya Aliyi, so take jikinta ya gaya mata ta ga ranar lukutin jiki, sai shegen cika bakin tsiya babu kwanji, don ta ji Hajjah na cewa ta girmemu to ba shekaru biyu ba ko goma kika bani in kika kara ce min lukuta lallasaki zan yi”.
Yaya Aliyu ya rasa inda zai sa kansa don dariya, ya ce, “Ana girma ana cin kasa Ummi da Zanirah! Inda Fa’izah ke burgeni kenan, tunda kuka shiga aji hudu ta watsar da shirme ta bar muku”.
Ummi ta ce, “Eh, ai daman a wajenka Yaya Aliyu Fa’iza ba ta laifi, ita ce ta iya komai, bayan ita din a bayan idonka tantiriyar kanta ce”.
Yana dariya ya ce, “Bakya son a fadi gaskiya, amma Fa’izah ta fiku hankali, nutsuwa da kamewa. Ko zaman wuni guda mutum ya yi daku zai fuskanci haka”.
Ummi ta sake kuluwa, ta tashi faram-faram ta fice. Yana kiranta yana ba ta hakuri amma ba ta juyo ba. Zanirah ko a jikinta, daman ita yarinya ce mai matukar sanyi cikin al’amuranta ba ta da fushi, ba ta da daukar zafi ko kadan a kan duk abin da za ka yi mata, da wuya ka ga bacin ranta. Kullum fuskarta cikin annuri take, ita dai barta a cika baki da kokarin karatu kamar Alhuda-Huda.
Ya maido duban shi gare ni ya ce, “Fa’izah ba a bani labarin Sarauniya Amina ba”. Na ce, “To Yaya Aliyu me zan ce maka ga yara duk sun zubo min ido?”
Maryam ta ce, “Lallai ma, su waye yaran naki?” Na ce, “Gaku nan mana juniors ‘yan JSS”. Ta ce, “Mts! Ke har yaushe kika fara SS din da za ki raina mutane?”
Yaya Aliyu ya ce, “Ke rufe mana baki ko na hambareki, wa ya sako ki cikin zancen nan? Ko sa’arki ce?” Na faki idonsa na yi mata gwalo, ta dalla min harara.
“Maza dauko biro da takarda ta rubuta min labarin Queen Amina”.
Zanirah ta ce, “Ba za ta iya ba Yaya Aliyu, ba ta iya Turanci sosai ba”.
Ya ce, “Da kowacce luggah Fa’izah rubuta min labarin Queen Amina, be it Hausa, Arabic, English, Fulfulde, Kanuri, Yoruba or Igbo, in har kika rubuta am sure zan iya karantawa in fahimta”.
Da karsashi na karbi takardar da biro, na matsa nesa dasu na soma yarfawa Yaya Aliyu kyawawan rubutu da harshen Larabci tsaftatacce. Na mika masa ya shiga karanta musu a fili, ga fassarar abin da na rubuta.
“Yaya Aliyu mun je Queen Amina lafiya, makarantar Sarauniya Amina babbar makaranta ce mai kyawun tsari, tsohuwa mai tsohon tarihi. Malamansu da dalibai duka masu kwazo ne. Bamu da kawaye, amma muna gaisuwar musulunci da duk wanda wata mu’amala ta hadamu da shi. An kai ni ajin Arabic, an kai Ummi ajin zane-zane (Art) saboda shi ta fi iyawa.
Akwai club-club a Queen Amina, irin su Maths Club, English Club, Jet Club, Arabic Club, Hausa Club, Science da sauran su. Na raba kafa na shiga Clubs har guda biyu, wato Arabiyya da English Clubs, Ummi ta shiga Jet don Allah bai halicce ta da kwakwalwar rike karatu ba, Jet kuma ana koyar da sana’o’in gida ga dalibai ne.
Aunty Hauwa ba ta kulamu ba ta neman mu, ta ce don ita muka dawo Queen Amina, don haka ba ruwanta damu mu manta mun santa, ba abin da take kawo mana daga gidanta ta ce mu karata”.
Nice Kanwarka.
Fa’izah A.A Giwa.
Yaya Aliyu ya ajiye takardar ya ce, “Good, very good, a tafawa Fa’iza, na ce a tafa mata!” Raf! Raf!! Raf!!! Suka hau tafi. Ya yin da Yaya Aliyu ya shiga manna min sababbin wa-zo-bia a goshina har guda shida.
****
To haka rayuwarmu ta ci gaba da mikawa, tafiya ta yi tafiya. Shigarmu ajin karshe a sakandire na dauke da wasu muhimman al’amura da ba zan taba mantawa dasu ba cikin tarihin rayuwata. Don haka ya zama dole in farka shekarar baki dayanta.
Alal hakika a lokacin na fara wadatuwa da abin da ake kira “Hankali” wanda yawan shekaru ke samar da shi. A lokacin ne kuma na fahimci mu’amalata da Yayana Aliyu ba komi ba ce illa SOYAYYAH! Soyayya ce muraran yake nuna min cikin ‘yan’uwana baki daya ba tare da shi kansa ya sani ba, a gaban kowa baya iya boye kulawarsa gare ni. Duk dangi babu wanda bai kwana da sanin matsanancin son da Yaya Aliyu yake min ba ko ba a furta ba.
Sai dai da bakinsa bai taba ko da kuskuren gaya min da fatar bakinsa ba, sai dai actions and emotions dinsa su nuna. Ko da cikin hira ya yi subul da baka sai ya yi kokarin gyarawa ya mai da zancen ko subutar bakin sa (otherwise).
Shekaru na goma sha takwas kenan, duk wani budurci ya tabbata gare ni. Hankali da nutsuwa sun wadace ni. A zahiri, tunda na soma hankalin nima nake so da kaunar Yaya Aliyu, so ba na wasa ba. Cikin kannena da tsararrakina da danginmu duka zancena daya ne (Yaya Aliyu). Shin don mene ne ba zan so Aliyu ba.
Mutumin da ya kwashe shekaru goma sha daya yana kula dani, kulawar da iyayen da suka tsuguna suka haifeni basu yi min ita ba. Yana bauta mini, yana dadada mini, yana faranta mini. In har ban so Aliyu Na’ibi ba, wallahi ni butulu ce cikin butullun ababen halitta wanda zuciya ba ta aiki a jikinsu.
Tun daga aji biyar na sakandire na dauki wasa na aje gefe, na bude file na sanya shi na adana a cikin akwatun karfe. Na yi “facing” karatuna yadda duk wani dalibi na kwarai ke yi da taimako da shawarwari da kulawa tattare da kwarin gwiwa irin na Yaya Aliyu.
Allah ya hore min baiwar kirkira (fiction) na labarai masu