Showing 9001 words to 12000 words out of 44953 words

Chapter 4 - Zumuntar kenan Book 1 by Sumayya Abdulkadir Takori.txt

yadda duhun dare ya mamaye sararin sama, hawaye suka ci gaba da yi min lugude a fuska.
Hannun mutum na ji ya cira ni tsaye, na bude ido firgigit na mike a razane cikin fadin “Wayyo Allah..... wayyo Hajjah....” Abinki da cikin da ba komai, sai hajijiya ta kwashe ni yuuuu! Gaba daya na fada ga mutumin da ke tsugune a gabana, na daddage na kara sakin ihu....
“Wayyo Hajjah na shiga uku na lalace.... na mutu!”
Ya rungumeni sosai a jikinsa yana fadi cikin tattausar murya irin ta marasa koshin lafiya, “Relax, relax Fa’iza, relax”.
Na dauki lokaci ina tunanin mai muryar, kwakwalwata ta shiga tariyo min inda na san mai murya mai taushi da rashin amo. In ban yi kuskure ba zan iya cewa ta YAYA ALIYU CE.... YA YA ALIYU HAIDAR NA’IBI A.B GIWA.
Na lumshe idona na dan lokaci, bugun zuciyata na saisaita da zazzafan jikin Aliyu, zuciyata da ta yi zafi na yi min sanyi kadan-kadan.
Tsayin minti biyar Yaya Aliyu na rike dani, ya ce cikin kankanuwar murya, “Fa’izah are you ok?”
Na gyada kai, ya sake ni muka mike a tare yana rike da hannuna. Ya dauki jakar litattafaina da daya hannun nasa na hagu muka fita daga dakin karatun, ya bude gidan baya na shiga, ya fiddo cooler din abinci ya bude, kamshin girkin Hajjah ne ya doki hancina, ba girkin cikin gida ba, wannan girki ne da take yi lokaci zuwa lokaci da hannunta, da na dade da sani ya baibaye ni, ya tado min tsohuwar yunwar da na wuni da ita.
Yawun bakina ya wani irin tsinke tun kamin in kai lomar farko sanda Yaya Aliyu ke zuba min a farantin cin abinci (plate), dafadukar shinkafa ce da aka yi rabinta da zallar tsokar kaza da ganyen alayyahu da kabeji.
Ya bude wata foil paper din ya fiddo gasasshen naman nan na kan hanyar Gusau da ya saya mana a hanya a zuwanmu, duk ya ajiye min ya rufe kofar ya shiga mazauninshi ya ta da motar muka soma tafiya.
Bayan ya miko min robar ruwan swan mai sanyi ya ce, “Kina iya kwanciya idan kina jin barci in kin gama”. Da gudu ya fizgi motar bayan ya daga ma masu gadi hannu ya kuma yi signing shaidar cewa an dauke ni.
Amma fa ya sha fada daga malamin da ke kula da shige da ficen dalibai, har ya bawa uku lada. Magana daya yake fadi masu su yi hakuri ba laifinsa bane.
A yayin da wata danja ta tsai damu kusa da wata fitila mai hasken gaske, garin kalle-kallena mai nuna ciki ya dauka na fara dawowa hayyacina, na dubi hannun Yaya Aliyu wanda ke bisa giyar motar, allurar karin ruwa na gani soke jikin jijiyar hannunsa jini na diga amma bai kula ba, tukin shi kawai yake.
Da na kura ido sai na ga hanyar karin jini da wata siririyar allurar ita ma soke duka a hannunsa ya bi fatar jikinsa ya kwanta. Na dube shi a razane domin tun zuwan shi ban ga fuskarshi ba, ya rame sosai ya yi duhu ainun.
Na daga murya da karfi cikin tashin hankali na ce, “Yaya Aliyu ka tsaya”. Ba tare da ya juyo ba, haka nan ban ga annuri a kyakkyawar fuskarshi ba ya ce, “A kan me zan tsaya? Bakya ganin tafiyar dare zamu yi?”
[6/3, 4:12 pm] Takori: Na ce, “Ni dai na ce ka tsaya ko? Baka ganin hannunka yana jini ne?”
Ya ce, “Babu komi wannan, kina so mu yi kwanan hanya ne?”
Na ce, “Eh, mu yi ba komai”.
Maimakon ya tsaya sai ma ya kara ware speed zuwa (200), kada ki ga yadda ‘yan idanuwana suka yo waje, suka yi kwala-kwala. Cikin kuka na ce, “Yaya Aliyu baka da lafiya.... you are bleeding....”
Ya ce, “Don Allah don Annabi Fa’iza ki saurara min, da me zan ji ne? Insha Allahu lafiya zamu je gida babu abin da zai faru sai wanda Ubangiji ya riga ya kaddara”.
“To ka tsaya in cire maka allurar...”
“Na ce ki barshi ko dole ne?”
Yadda ya yi min maganar cikin tsawar da bai taba yi min ba ya sanya hantar cikina kadawa, ban kara tankawa ba don na lura yana cikin wani irin yanayi (tension) mai wuyar fassaruwa. Bai tsaya ba sai a Giwa, harabar adana motocin A.B Bamalli Estate.
Tsakar dare muka iso gida, yadda na ga mazan Estate din duka a tsaye cirko-cirko manyansu da samarinsu a kofar gidan hajjah ya tabbatar min babu lafiya.
Baba Barau ya hau shi da fada, cewa yake, “Baka da hankali ne iye Aliyu? Halaka kanka kake so ka yi? Wannan wace irin wauta ce ka cizge karin jini da na ruwa ka bar gadon asibiti, ce maka aka yi duk cikinmu an rasa mai zuwa dauko Fa’iza daga makaranta?”
Aliyu zai wuce su kwayar idonshi na neman rufewa, ya yi kokarin yin magana amma ya kasa. Ganin yana neman shan kasa Baban Giwa ya kama shi, shi da Baba Salisu suka mai da shi cikin motar da ya fito bai samu ya rufe ta ba. Baba Salisu ya ja motar aguje suka fice da shi asibiti.
Ni dai na shige cikin gida sai kuka nake saboda halin da na ga Yaya Aliyu a ciki a dalilina. Hajjah ta taso ta rungumeni ta ce, “Baki kyauta ba Fa’iza, don me za ki tafi yawo a neme ki a rasa? Ga shi kin ta da hankalin dan’uwanki yana kwance asibiti amma daga jin labarin nan ya tsinke karin ruwan da ake masa ya dauki mota kamin kowa ya farga ya fice ya biki”.
Na dubi Ummi dake zaune da mamakin sabon sharrin Ya Fa’iz, ta sunkuyar da kanta. Na ce, “Ni Fa’izar ce na tafi yawo Hajjah?” Muryata kamar na aro, kamar ba tawa ba.
“Kyale ta kawai Hajjah, babu inda ni da malaminsu bamu duba ba cikin makarantar nan amma yarinyar nan kamar aljana sama ko kasa an rasa ta”.
Hajjah ta ce, “To ai shi kenan zancen ya wuce tunda dai an zo lafiya alhamdulillahi, sai a kiyaye gaba. Ke Fa’iza jeki ki watsa ruwa ki ci abinci kafin asubahi ta karasa”.
Na juyo da idanuna a hankali na dubi Fa’eez dake tsaye jikin bangon falon sai murmushi yake yi mai taushi, da idanuna da suka jawur na ce, “Kwarai, baka ganni ba Yaya Fa’iz, amma rabbil samawati wal’arshi shi yana ganinmu, kuma shi ya san abin da ke boye da wanda yake a sarari. Wata rana na zuwa da zai bayyana shi fili kowa ya gani”.
Na wuce toilet abina yana fadin “Me kike nufi? Karya nake miki kenan?” Ko juyowa ban yi ba na shige toilet na rufo kofar da karfi.
A zuciyata tausaya mashi nake kan halin da ya jefa kanshi a ciki, shin meye amfanin wannan kiyayya da yake nuna mini? Ya san girman ZUMUNCI a cikin addinin Islma kuwa? Me kiyayyar da yake yi min da hakan da yake yi min za su amfane shi da shi? A ce mutum sam-sam baya tsoron Allah a al’amarinsa sai Hajjah mutum ‘yar adam?
Ni kam gani nake in an boye ma Hajjah da sauran mutane abu ko gaskiyar abu ba za a boyewa Allah ba, Allah ka shirye shi, ka ganar da shi illar karya da cin zarafin dan’uwa musulmi ba ma dan’uwa na jini ba.
Na kwanta barci a wannan daren amma sam na kasa, tunanin shin wane halin Yaya Aliyu ke ciki a asibiti shi ya addabe ni? Me ya same shi? Me yasa ya boye min cewar ba shi da lafiya? Me ya tunzura shi ya yi fushi haka irin wanda ban taba gani daga gare shi ba?
Na san dai ba zai wuce abin da Fa’iz ya yi mani a yau ba. A zahirin gaskiya ina tausayawa Fa’iz idan Yaya Aliyu ya fahimci cewa da gangan ya gudo ya barni.
A wasu lokutan Yaya Aliyu na (acting according to) sunansa (mafadaci ne kamar kowanne mai suna Aliyu zakin Manzo). A duk lokacin da ya shiga irin wannan tension din babu mai iya tausasa shi sai Baban ABU wato (mahaifina).
Tsorona Allah tsorona kada na zama silar wargaza zumuncin dake tsakanin Yaya Aliyu da Yaya Fa’iz (Mai sona da mai ki na). Don haka ya zama dole in kare Fa’iz albarkacin ZUMUNCI. In boye abin da ya yin wanda ba Aliyu kadai zai batawa rai ba har Hajjah dake matukar girmama shi da iyayenmu maza.
Dan’uwa kowanne iri dan’uwa ne wanda na sani na kuma tabbata cikin family dinmu babu irin wannan hatsaniyar, ba zan so kuma in zamo silar ta ba.
Na juya ga Zanirah dake gefena tana barci, sai na ga ashe ba barcin take ba sharar hawaye take yi. Na ce, “Ba ki yi barci ba Zanirah?” Ta ce, “Eh”. Na leka fuskarta sosai na ce, “To shin Zanirah me kike wa kuka?”
Cikin dasasshiyar murya ta ce, “Yaya Aliyu? Shin ko a wane hali yake yanzun?”
Na ce, “Wai me ke damun shi ne Zanirah? Wane irin ciwo ne ya cucemu haka ya kwantar mana da Yayanmu Aliyu?”
Ta share hawaye da bayan hannunta ta ce, “Yana da (ulcer) ne ba tun yanzu ba, ba ta tashi kada shi ba sai a ‘yan kwanakin nan muna makaranta, nima da Hajjah ta je mun (visit) take gaya mani. Ya dade a kwance, domin ta ci karfinshi sosai. Ana i gobe zamu dawo Hajjah ta ce numfashi ma sama-sama yake yinsa da taimakon oxygen a asibiti.
Sun samu sun fara shawo kan matsalar aka daura mishi ruwa da jinin da kika gani, lokacin ni Yaya Sani ya dawo dani gida kowa da kowa yana asibitin, wurin azahar Fa’iz da Ummi suka shigo, mu duka muna waje suka shige ciki wurin Hajjah. Babu abin da Yaya Aliyu ya soma tambaya sai ina ka baro Fa’iza? Ya ce, “Wai bai ganki ba....!”
Wallahi sai ya tsinke jinin da ruwan ya dauki flask din abincin da Hajjah ta kawo mishi a lokacin ya fizgi mukullin motarshi hannun Ya Fa’iz, bai hana shi ba, shima sai ya yi ficewarsa. Abinki da taron mata babu wadda ta yi tunanin hana shi (tsai da shi), musamman a cikin yanayin fusatar da yake.
Ya yi waje, Hajjah na kira da su Inna Kaltume amma bai ko waiwaye su ba, kuma babu mai ilimin kiran likita ko nurses a cikinsu balle kiran security na bakin gate. Ya tashi motar suka bude mai ya fita ya tafi dauko ki, shima Ya Fa’iz tafiyar sa ya yi......” Ta ci gaba da kuka, nima haka.
Cikin kuka na ce, “Yanzu Zanirah a ganinki abin da yayanki ke yi a kaina, ko in ce nau’in zumuncinsa gareni yana kyautawa? Zan rantse miki da sarkin sarakuna Fa’iz da niyya ya taho ya barni a Gusau”.
Zanirah ta zaro ido, ta ce, “Shi Yaya Fa’iz din?’
Na yi mata alamar ta yi a hankali kada Hajjah ta ji. Na ce, “Kin san Allah ina tsaye gabansa ya ja motar suka tafi, wannan meye in ba kiyayya ba? Me na yiwa Yaya Fa’iz ya tsane ni a dangi Zanirah? Fa’iz ya nuna bai damu da rayuwata ba, ko da na bi wasu can sun sace ni ba asarar shi ba ce, ko da na fito daga cikin makaranta na bata bai dame shi ba, ko da yunwa za ta kashe ni ba ruwansa bane.
Amma don Allah don Annabi Zanirah kada ki fadawa kowa tunda na kudurta zan rufa masa asiri wurin Hajjah da Yaya Aliyu to zan yi, bana so a samu kuskure daga gare ni kan kiyayyar da Yaya Fa’iz ke mani, na tabbata wata rana Allah zai bayyanawa duk dangi cewa, Ya Fa’iz bai dauke ni ‘ya a cikin gidan nan ba a kan dalilin da ban sani ba”.
Sai na ga Zanirah na hawaye, muka yi ta kukan tare. Daga bisani da muka ga kukan ba zai amfanemu da komai ba, Zanirah ta ce, “Mu tashi mu yi sallar nafila mu rokawa Yaya Aliyu sauki”.
Washe gari su Hajjah za su tafi asibiti da safe na marairaice na ce, “Hajja don Allah?” Ta ce, “Mene ne?”
“Don Allah zan biku”.
“Ki bimu ina?”
“Asibiti wurin Yaya Aliyu”.
“Ki yi me? Kai Fa’iza da rigima kike, to shige mu je”.
Ba abin da na dauka illa hijabi da report-sheet dina muka tafi.
Mun samu Yaya Aliyu yana shan tea da kaninshi mai binshi Mus’ab, ya hada mishi yana mika mishi bired da yankakken dafaffen kwai da (mayonnaise) yana ci.
Hajjah ta washe baki ta ce, “A’a, Aliyu lallai jiki ya yi kyau lafiya ta samu. Mus’abu an iya jinya, sai a dage da cin abinci a kan lokaci kuma yadda ya kamata yanzu ko? Tunda an ji kamshin kofar lahira”.
Shi da Mus’ab suka yi dariya, ya sauko daga gadon da yake an cire mishi karin ruwan, ya gai da Hajjah. Abin da na fahimta duka hankalinshi kaina yake, na tsuguna na ce, “Yaya Aliyu ina wuni?”
Ya ce, “Ko dai ina kwana Fa’izah?”
Hajja ta ce, “Jiya ai Fa’iza da Zanirah basu yi barci ba ina jiyo shesshekar kukansu. Kai, tsakanin Fa’izah da Zanirah ban san wa ya fi son Yaya Aliyun nan ba, ko mi.... Hajja Yaya Aliyu, Hajja Yaya Aliyu ne ya bamu, Hajja Yaya Aliyu ya ce yana gaishe ki.....”
Na rufe fuska da tafukana cikin jin kunya na ce, “Hajjah ai shima yana son mu ne, yana mana kirki, kuma ya damu damu shi yasa muke son shi”.
Hajjah ta ce, “To Allah ya bar zumunci, yasa a daidaita da Hafizina tamkar hakan”.
A zuciyata na ce, “HAR ABADA Hajjah!” Amma a fili murmushi kawai na yi, zuciyata kamar ta fito ta bakin don haushin kalaman Hajjah.
Yaya Aliyu ya ce, “Fa’iza ina alkawarinmu?”
Na zaro (report card) dina cikin hijabina na mika mishi, ya duba ya yi murmushi. Hajjah ta ce, “Ai kamar an san za ka tambaya har an fito aka zura da gudu aka koma aka dauko shi, in ce ko dai an yi abin kirki ba irin na baya ba?”
Ya dago kai yana dariya ya ce, “Anyi da kyau Hajjah, na tara cikin dalibai sittin kinga ko an ka da hamsin da daya”.
Hajjah ta ce, “Lallai Asma’u za ta yi tsalle (Maman su Zanirah) har ta gode Allah, ita ce mai damuwa da sakamakon Fa’izah a kullum baya kai wa rabin na ‘yan’uwanta. To takwara fa (tana nufin Ummi)”.
Na kyalkyale da dariya na ce, “Ta yi na ashirin da daya cikin mutum sittin, ai ta yi kokari domin a primary ana yin magana ko koyarwa da Hausa, a can ko ba a yi kuma an kaita ajin kasuwanci, ni kuma ajin Arabiyya ne tuntuni na iya Larabci tun a gida Zaria, shi yasa nake fahimta sosai cikin ajinmu. Amma ka ga sauran subjects din ai duk ban ci da yawa ba”.
Hajjah ta ce, “Koh? Allah ya taimaka, gata nan ta kara habewa ta suntuma kamar yis, sai fada da karfi kamar diyar zaki amma babu karatun a zo a gani”.
Na ce, “A’a, Hajjah tana kokari”.
Duka suka yi dariya ganin yadda na bata rai, don cikin mu ukun nan babu mai son a soki ‘yar’uwarta ko a gabanta balle a bayan idonta.
Yaya Aliyu ya bar dariya ya ce, “Gaya min Fa’izah ya aka yi suka taho suka barki?”
Na ce, “Wallahi Yaya Aliyu ba yawo na je ba, na shiga teachers area ne gidan su wata ‘yar ajinmu in kai mata littafinta da na ara, shine da basu ganni ba suka taho suka barni”.
Ya ce, “Next time kada ki kara yin irin haka, kin ji na gaya miki, kina wasa da ranki ne da lafiyarki masu muhimmanci ga wadanda ke da bukatar su. Shi kuma da yake babban sakarai ne ba zai iya jiranki ba? Allah Hajjah Fa’iz zai gamu dani da kyar ma in.....”
“Na kashe zancen nan tun jiya Aliyu, kada wanda ya sake tado shi”.
Ya ce, “An barshi Hajjah”.
Har yamma muna wajen Yaya Aliyu, wannan ya shiga wannan ya fita. Sai biyar da rabi Aunty Zainabu Maman su Aliyu da Baba Na’ibi mahaifinsu suka zo, sannan muka bisu muka tafi.
Aunty Zainabu ke tsokana ta, “Fa’izah hutu bai zo da dadi ba, Babban Yaya babu lafiya ina kwanciyar hankali?”
Baba Na’ibi ya ce, “Ai laifin su ne tunda basa matsawa Yayan yana cin abincin cikin gida sai dai ya basu kwai da Indomie su soya masa, kowa ya gaya musu wannan taliyar abinci ce oho!”
Na ce, “Wallahi Baba daga yau ba zamu kuma dafawa Yaya Aliyu Indomie ba, durar tuwo kawai zamu dinga yi masa, ko kuwa Hajjah?”
Hajjah ta ce, “Ni ina ruwana ne?”
Satin Yaya Aliyu guda a asibiti aka sallame shi. Hutunmu ya ci gaba da tafiya cikin dadi tare da Yayanmu mai son mu Aliyu, wanda shiga goma fita goma in zai yi cikin gida sai ya neme ni, ko ya riko min wani abu. Na ci ne ko na amfani, ko wanda zai amfane ni wajen karatu.
Babban farin cikinmu Fa’iz an yi balaguro zuwa Kaduna. Duk gidan ‘yan’uwa mun zaga ba inda bamu je ba sai Kaduna da Zaria.
Hutunmu ya rage saura sati daya mu koma makaranta Baban ABU ya zo suna hira da Hajjah a falonta muka shigo daga Islamiyya ni da su Zanirah, baki daya muka tsugunna muka gaishe shi, muka wuce dakinmu.
Ya daga murya yana fadin “Lallai Fa’iza baki da kirki, kika yi tafiyarki Gusau ba sallama, kika dawo shima kina shirin komawa ba tare da an waiwaye mu ba ko? Ga su Walida kullum basu da zance sai na yaushe za ki dawo, kin kyauta kenan?”
Na ce, “To Baba ai matarka ce ba ta nemana shi ya sa”.
Ya ce, (cikin dariya) “Tana neman ki mana, jiya ma ta ce ka ga Fa’izah yau saura sati daya a koma makaranta amma shiru”.
Na buga tsalle na makalkale shi ina cewa, “Zan bika, zan bika to Baba”.
Zanirah ma ta ce, “Nima zan biku Baba ka sauke ni gidan Maman Ya Fa’iz (mahaifiyarta)”.
Ya ce, “Ke fa tsohuwa (Ummi)?”
Ta ce, “Ni area one za ni”.
Ya dubi Hajjah ya ce, “Wai me yasa uwata ba ta son gidansu ne?”
Haka dai muka debi ‘yan kayanmu muka bi Baba. Sai da aka fara kai Zanirah Kaduna (Jabi Road), ko shiga gidan ban yi ba don sanin cewa Fa’iz na nan. Amma Baba na karya kan mota zai fita a get din gidan sai ga shi ya shigo da litattafai a hannu, Baba ya dan rage gudu suka gaisa.
Wai don

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login