Showing 39001 words to 42000 words out of 44953 words
Chapter 14 - Zumuntar kenan Book 1 by Sumayya Abdulkadir Takori.txt
cikin A.B Family dake cikin rabinta.
Na girgiza kai tare da sallama, da gudu na karasa jikin Mama a (sofa-bed) muka rungume juna domin mun jima bamu hadu ba, tun bikin Zanirah, ga kuma soyayya mai karfi tun fil’azal wadda ta zarta ta jini kawai, har ma da haduwar jini da Allah ya hada a tsakaninmu.
Mama ta ce, “Oh! Su Fa’izah an gudu Kano don ba Zanirah ko duriyarku ba a ji, ko waya babu, kun kyauta kenan?”
Na ce, “Kin san Baban ABU ya hanamu rike waya Mama, kuma na je ne don na huta na samu nutsuwa. Amma wallahi Mama kullum kina raina”.
Ta ce, “Na sani, na kuma yarda Fa’izah”. Ta dubi Ummi ta ce, “Sai tsohuwa!”
Ummi ta shagwargwabe fuska ta ce, “Allah Mama ki bari....”
Muka sa mata dariya ganin yadda ta yi da fuska kamar za ta barke da kuka. Mama ta ce, “Mutuminki kullum ya yo waya korafinsa daya, yaushe za ki baro Kano? Yau dai ga Ummi a gidan nan, anjima zai yo waya bakina ya huta cewa, ban sani ba”.
Cikin matsananciyar murna Ummi ta makalkale Mama tana dariya kamar ba surukar ba, ta ce, “Allah da gaske Mama Ya Fa’iz na tambaya ta? Don Allah Mama ya muryarshi ta koma? Ban taba magana da shi a waya ba tunda ya tafi”.
Mama ta ce, “Muryar Fa’izu ta karye (kwata-kwata) da Ukrainian language da Belarusian. Da kyar nake fahimtar Hausar shi. Su Shu’aibu ba ma sa ganewa gara ma in yana Larabci ko Turanci”.
Ummi ta yi zugum (her passion for him heightened). Tana duban Mama hannuwa tallabe da fuska ta ce, “Kin san Allah Mama, na yi dana sani tunda fari da na san haka ne da na shiga Arabic Club da Fa’iza tayi-tayi dani in shiga a makaranta na ki, don a ganina yawa ne in tsaya koyon Larabci tunda ba a fiya amfani da shi a nan Nigeria ba”.
Mama ta ce, “Ayya! Kin yi babban kuskure, domin Larabci shine harshe mafi soyuwa a wurin Ubangiji da ya zabe shi a cikin harsunan duniya ya saukar da Alkur’ani da shi. Har yake cewa, “An saukar da shi Alkur’ani BALARABE....” Kuma Annabi (S.A.W) ya ce, “Ku so harshen Larabci saboda uku. Na daya ni Balarabe ne, na biyu Alkur’ani Balarabe ne. Na uku harshen ‘yan Aljanna shine LARABCI!”
Ummi kamar ta fashe da kuka, na yi dariyar mugunta na ce, “Rabu da ita Mama, ba zan taba manta sanda su Ummi suke min dariya don ina Alifun Ba’un ba. Wahid-Ithna-thalatha ban iya 123 da ABCD ba, ga shi na muku wayo.
An ce ana jifan tsuntsu biyu da dutse daya, don a ci amfaninsa. Yau Ummi Turancin me za ku nuna min? Sai dai in nuna muku LARABCI”. Na yi mata gwalo.
Ummi ta yi zugum, da alama kalma ta kare a bakinta. Na yi dariya mai isata har cikina ya kulle. Ummi ta zo iya wuya ta tashi ta fice daga dakin, muka ci gaba da yi mata dariya.
Mama ta ce, “Sai yaushe za ku je wa Hassanar ku ne?” Tana nufin Zanirah.
Na ce, “Kai-kai! Mama so soon haka? Ai ba a zuwa gidan amare sabon aure sai sun haihu”.
Mama ta lakace min hanci ta ce, “Ai su da yake sun damu daku zuwan su uku duk kuna Kano. Ba kuma don kowa suka zo ba sai don su ganku”.
Na ce, “A’a Mama, da da gaske sun damu damu da sun bimu inda muke. In babu jirgi akwai mota, tsakanin Kaduna da Kano awa biyu ne kacal. Ke dai basu gama amarci bane ma je suna in da rabo”.
Mama ta ce, “Kamar mai gani har hanji an zo ana ta laulayin ciki kamar wadanda suka yi tuntube da shi a dokin kofa. Ku yaran yanzu ko kadan cannot excercise patience. Mu zamanin mu sai amarya ta shekara biyar dakin miji ba ta samu ciki ba”.
Duk da zuciyata ta dan sosu ban bari Mama ta gane ba. In Aliyu bai son Zanirah, ai ita Zanirah tana mutuwar son shi. Za ta san duk hanyar da ta bi ta janyo hankalin abinta gare ta. Sai na samu kaina a yau ina mai dan KISHIN Zanirah Mukhtar Abubakar Bamalli Giwa!
Karfe tara na dare duka al’ummar gidan na bisa tebir suna cin abincin dare, har mu da muka bakunci gidan. Da tuwon laushi miyar alayyahu da aka wadata da naman Turkey (talo-talo) aka kuma shirbine ta da man shanu dan asalin GIWA.
Na lura Abdul zubi kawai yake ba kakkautawa, ban san sanda na yi dariya ba. Yahya mai bin Fa’iz ya ce, “Kalau kike dariya ke kadai?”
Na ce, “Baka ganin yadda yaro ya samu abincin zage-zagi ya rude baya so ya bari ya fara hadiye na bakinsa kafin ya kara loma?”
Abdul ya yi murmushi, ya san da shi nake. Can kuma ya ce, “Yanzu ba zan ce miki komi ba sai mun koma Kano kina cin bandashe (gurasa da kuli-kuli) tukunna”. Kowa yasa dariya.
Daga daki Mama ta fito tana fadin “Ku yi sauri Fa’izah, cin abincin ne kuma ya koma hira da shewa? Aiken ku zan yi unguwar Sarki ku amso min ankon ‘yar Hajiya Saratu da kun gama, dare yana yi”.
Karar wayar landline dake gefe ya sanya kowannensu yin wurgi da cokalinsa ya nufi inda wayar take, kokawa fa ta kaure domin Ummi, Yahya, Shu’aib da Junior kowanne ya ci alwashin shi zai fara daukar wayar ko ta halin kaka.
Mama ta ce, “Yau ina ganin sakarci, to bari in raba gardamar nan. Duk cikinku babu mai tabbacin kiran nasa ne ko ba nasa bane, tsammani kuke Fa’izu ne, kuma ba lallai ya tabbata shi din bane haka ne?”
Duk suka tsaya suna tsuma, ta ‘kauna’ da ‘doki. “Don haka ke babbar Yaya (ta nuno ni) dauki wayar ki jiye mana waye kamin wani ya dauka don a raba gardamar”.
Na yi dariya cikin ginshira na tsiyaya ruwan FARO mai sanyi a tambulan na soma kwankwada. Sanyin ruwan na sanyaya makogarona, yana taimakawa wajen digesting (narkewar) daddadan tuwon da na ci. Na yagi tishu na goge baki da hannu.
Ummi ta kufula ta ce, “Kina gani fa Mama sai ta gama yi mana yanga”.
Mama ta ce, “Kai, dadina dake gajen hakuri Ummi”.
Na yi murmushin tura haushi sannan na mike na nufi wayar landline da har lokacin ba’a bar kira tana tsinkewa ba, wayar na daga na amsa da “Assalamu Alaykum!”
Shiru kake ji, ga shi da alama ba a ajiye ba. “Hello!” Shima shiru. Na sake sallama aka yi shiru, ina shirin mikawa Mama wayar cikin kufula da mamakin wannan ikon Allah, ka kira waya kuma ka yi shiru kudinka na tafiya a banza. Muryar mai cike da ginshira ke tambayar “Impertinence Fa’izah ko?” (Fa’izah mai tsiwa?).
Tuni jijiyoyi masu ba da jini shi kuma ya yi circulating dinshi ga sassan jiki sun tsaya cak! Da ba da aiki. Jijiyoyin cikin kai masu ba da doka da oda su ma sun yi yajin aiki na (temporary). Muryar da ba zan taba mantawa da ita ba, muryar dan uwa amma MAKIYI. Muryar FA’EEZ, HAFIZIN HAJJAH, FA’IZU MUKHTAR ABUBAKAR BAMALLI GIWA.
Ban amsa ba. “Kaif halikum Fa’izah? How are you Fa’izah?” Maimakon na amsa sai na yi azamar cire wayar daga kunnena na mikawa Ummi jin wani mugun fushi ya taso min wanda duk kokarin zuciya ba za ta iya boye shi a gaban kowa ba, including UWA-MAHAIFIYA dake gabana tana karanta duk wani motion dina a kan wayar danta da kyawawan idanunta, masu cike da matsananciyar kauna gare ni. Irin kaunar nan da baki baya iya bayyana ta, domin Allah ne ke assasa ta.
Sai na zare wayar sannu a hankali daga kunnena na mikawa Ummi, tare da zare jikina daga cikinsu na yi dakin Mama don bakin ciki kamar in rushe da kuka.
In da abin da na tsana a duniya to abin da zai tuna mani da shekarun da na kasance cikin fargaba da ukubar Yaya Fa’iz ne. Balle ya tuna min da shi kansa. To gaba daya yau muryarsa na ji a cikin kunnuwana, muryarshi ta dawo min da ranakun can baya marasa dadi da na rufe babin su ta dawo da tsanarsa danya a zuciyata.
Haka na yi sallar isha ina ta sake-sake. Da na idar na bishi da muguwar addu’ar Allah ya gama shi da masifar duniya da ta lahira a can inda yake. Yasa a fatattako shi daga karatun ko garin tukin jirgin, jirgin ya fado ya ragargaje da shi. Amin summa amin. Don kam hakika ni mai bakin ciki ce da duk wani ci gaban FA’IZ GIWA kamar yadda yake a gare shi shima.
A daren Ummi hanani barci ta yi da labarin hirarta da Fa’iz. Da hanzari na taka mata birki.... “Excuse me please. Shin Ummi ina ruwa na ne? Me ya shalle ni cikin wannan al’amarin naki? A duk lokacin da za ki yi hira, ki yi wadda ta shafe ni ban da ta Fa’iz! Na tsani Fa’iz!! Na tsani duk wani abu da ya shafe shi ban da iyayen da suka haife shi da ‘yan uwansa wannan (Individualistic matter) ne (sha’anin mutum daya). A duniya bani da abin ki, abin tsana, abin neman tsari da kariya daga sharrin sa bayan shaidan, sai Fa’ezz Bamalli”.
****
Washe gari karfe goma na safe Queen Amina College ta yi mana, inda muka hadu da malamanmu da muka jima bamu gani ba. ALHAMDULILLAH, takarduna sunyi kyau har fiye da na Ummi, na tashi da Credentials a gaba dayan ( 9 Subjects) dina. Ummi tana da seven credits, sai dai tana da A a Fine-Art.
A shekarar duka muka samu gurbi a jami’a, inda Yaya Aliyu ya samarwa Zanirah gurbi a jami’ar Lagos (UNILAG), inda za ta karanci likitanci (Medicine). Daga Baba na har mahaifin Ummi babu wanda bai yi mamaki da umarnin Hajjah ba na ta amince a nema mana gurbi a jami’ar Bayero ni da Ummi mu koma Kano da zama wajan Aunty Rabi, sai hutun karshen kowanne zango ta amince mu je Giwa da sauran garuruwan Zaria ko Kaduna.
Yaya Muftahu shi ya shiga ya fita ya samar mana gurbi a fannin da kowacce take so, inda aka bani B.A Arabic, Ummi kuwa B.A Hausa. Duka a Faculty daya wato (FAIS) sai dai tsangaya (Department) da suka bambanta.
BAYERO UNIVERSITY KANO
Rayuwar mu cikin jami’ar Bayero, sabuwar rayuwa ce a garemu da ta zo da sabon salo irin na kowanne JJC (Joiny Just Come) a jami’a. Abubuwa da yawa (which are normal) ga sauran daliban jami’ar (is abnormal to us), irin su shan hannu da maza da wasu matan marasa kamun kai ke yi da sunan jami’anci, shan taba sigari da samari da matasa ke yi wanda ba a yi sam a A.B Estate. Shan lemo a shago a tsaye ga matan aure da ‘yammata, ko saka wando ga wasu matan Hausawa duka abin kallo da waiwaye ne a gare mu kafin mu saba.
Mu kam bamu saba gani ba a inda muka taso, don haka muka shiga dari-dari. Sannu a hankali idonmu ya zo ya bude tangarau muka fahimci (reality) na rayuwar jami’a ba (peer group infuluence) bane (koyo abokan karatu ko tsararraki) kawai (imitation) ne wato (kwaikwayo) ‘to fit together’ (a zama iri daya).
Akwai wadanda karatu ne ya kawo su ba (imbibing) wato kwaikwayon abubuwan da canjin zamani ya kawo ba. Akwai kuma ‘yan ‘imitation’ din ko da a ce ransu bai so don kar a ce musu kauyawa. Irin wadannan su nake gani a matsayin kauyawa ba wadanda suka kalla a kauyawan ba. Su kuma ina kallon su ‘yan ra’ayin rikau. Irin wadannan mutanen a duk inda suka tsinci kansu basa canza ‘doctrines and principles’ dinsu kuma da wuya a rinjaye su daga kan abin da suka riga suka yarda da shi.
Yau bamu fito lacca da wuri ba sai wurin karfe biyu na rana, in ban da kururuwa ba abin da cikina ke yi, don ko karin kumallo ban dauka ba. Babu yadda Yaya Rabi ba ta yi dani ba don in zauna in karya amma na ki, saboda sanin halayyar Dr. Ramadhan Alkali, muddin ya riga ka shiga aji to ka rasa laccar sa kenan. Ni kuma ba zan so in rasa laccar ba, don a cikinta ne zai fadi (exam concentration area) din kwas dinsa.
Tafe nake a hanzarce don kokarin isa ga ‘coke village’ in samu abin da zai warware min hanji. Idanuwana sun rufe saboda yunwa ban kula da budurwar dake tsugune tana goge takalminta da ya yi kura da tishu don ganina ya dushe tsabar yunwar dake addabata, muka yi karon ba zato da budurwar saura kadan ta kifa.
Ta mike a hanzarce za ta yi bala’i. Wa zan gani? Haulatu Shehu, kawarmu (Head-Girl) a Queen Ameena, Haulatu S. Shehu. Na ce, “Haulatu Sani?”
Ta ce, “Fa’izah Ahmad?’
Na ce, “Ya Jamilal Munzar! (wato ya mafi kyawun masu gani)” A guje muka sheka muka rungume juna tare da juyi rikija-rikija muka rankaya coke village tare. Hirarraki da tambayoyi tamkar su kashe mu. Kamin wannan ta kai aya wannan ta antayo tata tambayar.
Ta ce, “Fa’izah kuna cikin garin Kano amma ko ki neme ni?”
Na ce, “Ayya Haulatu, ban san gidanku ba, kin ganni nan bayan unguwar su Aunty Rabi Gadon Kaya (Yarda Avenue) ban san ko ina ba, ban da kantuna da muke zuwa sayayya”.
Ta ce, “Ina address din da na baku tun muna makaranta da phone no?”
Na ce, “Mun baro su cikin littafinmu a Giwa”.
Daga nan hira ta barke. Ta ce, “Lallai ne Ubangijinmu ke nufin mu da zumunci tunda har ya sake hadamu a nan. Allah abin godiya. Ina Ummi?”
Na ce, “Ummi tana makarantar nan ita ma a Hausa Department”.
Ta ce, “Ni ina Mass-Communication, kai ni Haulatu na zo jami’a a sa’a tunda na kara haduwa daku. Tun rabuwarmu babu ranar Allah da za ta fito ta fadi ban tuna ku ba”.
Na ce, “Duk kin canza Haulatu, kin yi kiba kin kara kyau da haske, ko kin yi aure ne?”
Ta ce, “Har da albarkarsa na like jikina. Matar Abdullahi Yakasai ce. An daura min aure bayan candynmu. Bikin ne dai ba ayi ba har yanzu Abdullahi ya tafi (Law School) sai ya kare nan da wata shida”.
Na ce, “Sunan kanina, Allah ya sanya alkhairi Haulatu. Sunan kanina mai bina kenan”.
Ta ce, “Kwarai, kin taba gaya min kina da kani Abdallah, yanzu ajinshi nawa?”
Na ce, “Abdallah ai an zama samari, yana SS I, Walida na JSS 2”.
Ta ce, “Me kike karanta?”
Na gaya mata harshen Larabci. Ta ce, “Kin burge ni Fa’izah, Allah ya kara fahimta, ya kara mana kaunar Manzo (S.A.W)”.
Kai hirar da muka kwarara ni da Haulatu a ranar tana da yawa. Duk tarihin mijinta Abdullahi wanda ya kasance dan’uwanta ne ta bangaren mahaifiyarta sai da ta gaya mini. Sai da muka yi (missing) lacca guda saboda dadin hira, dama Haulatu uwar surutu ce barin in sun hadu da Ummi. Haduwar Ummi da Haulatu sun kusa shidewa don murna.
Daga ranar amintarmu ta ci gaba da Haulatu daga inda muka tsaya a sakandire school. Naja’atu na ABU Zaria in ji ta. Duk inda ka ga Zarah ka ga wata wato ni, Ummi da Haulatu. Mun je gidansu a ‘Yankaba ba sau daya ba, ba sau biyu ba, ita ma ta zo mana, har kwana take in lokacin jarabawa ne mu yi karatu tare, musamman da gidan Aunty Rabi ya fi kusa da makaranta. Ta saba da Aunty Rabi sosai.
Albarkacin Haulatu babu inda ba ma takawa a cikin Kano, daman an ce sai da dan gari a kan ci gari. Ummi ta yi manema har ba adadi, ni kuwa rashin sakin fuska da kora da hali wanda ya fi kora da sanda shi ya sanya duk wanda ya zo wajena da sunan so baya marmarin sake dawowa.
Ummi kan ce lokaci ne, lokacin abu ayi shi. Ni ba auren su zan yi ba kawai suna rage min lokaci. Sai in kama baki in yiwa Ummi kallon mamakin yadda jami’a ta sauya ta lokaci guda.
A haka muka kare 100 level bayan jarrabawar da ta kusa tsaga mini kwanya muka fara 200 level. Idon mu ya kara budewa sosai a sanadiyyar ratsawar ilimi da cudanya da masu shi. Hausar bakinmu ta dai-daita da ta ‘yan Kano, kai ka ce nan ce mahaifar mu.
Mu muna using N a muhallin R, wannan shi ke sa Haulatu da sauran abokanan karatunmu ke cewa muna Hausar Giwa. In Haulatu ta tashi tsokanata sai ta ce, “Kin tuna Ummi ranan nan a anguwan sarki? Ba za ku bar wannan maganan ba? Yaya Rabi kin ga Ummi na tsokanana ko????”
****
[6/3, 4:13 pm] Takori: ****
Karfe goma na safe su Ummi suka yi shirin tafiya taren su Bashir a filin jirgi. Tun asuba da na yi sallah fuskata babu walwala, kallon kowa kawai nake zuciyata a cunkushe da bakin ciki da bacin rai maras dalili.
Hajjah yau ko gaishe ta ban yi ba, babu wanda na yiwa magana. Na zubawa allon talabijin ido kuri kai ka ce program din nake saurara, amma ina! Zuciyata ba ta tare da gangar jikina, abubuwa masu ban al’ajabi da ban tsoro kawai take wassafa min masu shirin faruwa dani.
Kafin karfe goma na safe gidanmu ya cika ya batse da dan Adam, sai busa algaita ake ‘yan daurin aure suka fara layin shigowa gai da Hajjah suna fita, ‘yan’uwa ne da abokan arziki. Kafin Babanninmu su shigo sun sha ankon farar shadda (getzner) sai sheki suke.
Suka zube a falon Hajjah suka kwashi gaisuwa suka fita. Ina daga uwar daki ina hango ficewarsu ta taga daya bayan daya. Mintina talatin bayan fitarsu na ji gabana YA FADI! A dai-dai lokacin da dakikar agogo ya nuna karfe goma sha daya na rana, a lokacin ne aka daura aurarrakin masu ban mamaki, da suka ajiye kundin tarihi da wani aure bai aje ba cikin zuri’ar Abubakar Bamalli Giwa.
Wani maroki mai zakin muryar tsiya yake fadi da murya mai karsashi da kwarzantawa cikin babatun magana “ALHAMDULILLAHI! ALHAMDULILLAHI!!” Sai da ya fada har sau uku. “An daura auren FA’IZAH AHMAD ABUBAKAR GIWA da FA’IZU MUKHTAR ABUBAKAR GIWA. HADIZA da MUHAMMADU BASHIR, a kan sadaki lakadan ba ajalan ba. Allah yasa anyi a sa’a, yasa anyi sai bakin rai, Allah ya sanya alkhairi ameen.....”da sauran babatu irin na maroka.
Maimakon in kira yi sunan Allah sai na kwarara ihu da iyakacin muryata