Showing 15001 words to 18000 words out of 44953 words
Chapter 6 - Zumuntar kenan Book 1 by Sumayya Abdulkadir Takori.txt
ya yi ficewarsa yana murmushin tura haushi.
****
Ina toilet ina wanka na ji landline din Hajjah na ta faman (ringing) babu wanda ya dauka ta yi ta ruri har ta katse, ta sake kama wani sabon kukan har tana neman ta sake katsewa. Cikin hanzari na ja tawul na daura duk jikina kumfa na fito falon aguje na dauki wayar na amsa da sallama.
Sai ga Ya Fa’iz ya sanyo kai falon, cikin captan na makubar shadda Hilton, ya yi shar kamar ango sabon aure. Shigowar tashi da tunanin yanayin sutturar da nake ciki ya sanya ni rawar kafafu tare da sarkewar harshe wajen amsa sallamar.
Muryar Maman Kaduna ce ta ce, “Fa’izah ga direba nan na turo yanzu ku biyo shi dukkanku tafiya zamu yi Kano gidan Rabi”.
Na yi tsalle na dire na saki ihun murna, na ce, “To Mama”. Na ajiye wayar amma saboda rawar da hannuna ke yi na ajiye shi ba dai-dai ba.
Dagowar nan da zan yi muka yi ido hudu da Fa’iz yana yi min wani irin asirtaccen kallo da shi kadai ya san ma’anarsa, sai dai na nemi kibiyar kiyayyar dake cikin idanun na rasa. Kallo ne na kurulla wanda ya wuce gejin kallon addini. Na tuna a yanayin da nake na saki wani dogon tsaki na juya na shige dakinmu, na shige toilet na rufe na ci gaba da wankana.
Bayan na kammala na fito ina muttsika mai a fatar jikina (Norwegian Formula). Su Ummi suka shigo suna ta hira da kwasar dariya, na ce, “Ku don Allah mu shirya ga direba nan Mama ta turo zai debe mu zuwa Kaduna, daga nan mu tafi Kano wajen Ya Rabin Yaya Muftahu”.
Nan su Ummi har da tsalle aka fada wanka, Zanirah na hada mana kaya cikin (luggage).
Hajjah ta shigo daki ta ce, “Ku kuma shirin me kuke haka kamar za ku tashi sama?”
Na ce, “Hajja Kano zamu”.
Ta ce, “Kano? Wajen autata amma shine baku gaya min da wuri na tanadi tsaraba ba?”
Na ce, “Hajjah muma yanzu-yanzun nan Mama ta yo waya ta gaya min na gaya musu, amma na san ita Maman za ta yi tsaraba ai”.
Muka sha doguwar riga mai rubi biyu ‘yar Oman (tsarabar Baba Sadi ne ta Hajjin Bara), nawa baki da ratsin maroon, na Ummi baki da bula-bula mai hasken sararin samaniya, na Zaneerah ja da baki, muka debi ‘yan kayan da zamu butaka cikin travelling bag.
Kamar jira yake mu kammala, malam Garba direban Maman kaduna sai ga shi ya aiko su Abba ya zo mu fito.
Mun shiga mota Hajjah na daga mana hannu, nice a gaba su Ummi a baya, sai ga Yaya Aliyu ya fito daga gidansu ya ce, “Sai ina kuma ‘yammatan Hajjah?’
Na ce, “Sai Kano”.
Ya ce, “Kano? Gaskiya Fa’iza ban yarda ba, na ji an ce samarin Kano kwarraru ne wajen fashin mata”.
Cikin mamaki na ce, “Matar wa to za su kwace?”
Ya yi hanzarin gyara zancensa da cewa, “Ke dai kada ki kula maza a Kanon, Idan Baban ABU ya ji kin yi saurayi zai gayawa Hajjah ne ayi gaggawar yi miki aure ke da su Ummi, ba zai bari ki yi Sarauniya Amina ba”.
Su Ummi suka kyalkyale da dariya (ban da Zanirah). Na ce, “To na ji ba zan yi ba, amma su Ummi su yi?”
Ya kada kafada ya ce, “Eh, ba komai su suyi, ai kinga su sun girme ki. Baki ga Ummi ta yi biyunki ba”.
Malam Garba ya ja mota muka wuce muna mishi dariya ban da Zanirah da ta yi fuskar shanu tana ta sakin tsaki, to wa take yiwa? Allah masani.
Da muka isa Kaduna already Mama ta shirya ita da Junior, bamu bata lokaci ba sauran yara suka yo mana rakiya bakin mota da kayan Mama Kano ta diba.
Kusan karfe biyar na yamma muka iso Kano, unguwar da su Anti Rabi suke wai ita Gadon Kaya. Unguwa ce da ta tara duka masu karfi, masu karamin karfi, ‘yan kasuwa kawo ‘yan boko babu irin rukunin mutanen da ba za ka taras a unguwar ba.
Duk da babu inda ban sani ba a Kaduna, ban ga kyakkyawan gari mai albarkar al’umma irin Kano ba. Gidan su Aunty Rabi yana ‘Yarda Avanue.’ Mama ke yiwa Malam Garba kwatance har kofar gidan.
Abdul-Rahim dan Aunty Rabi muka fara gani suna wasan kwallo shi da wani yaro dan makotansu, duk da bamu san shi ba, amma tsagin mallancinmu da karan hancin sun tona shi, muka kama shi muka rungume.
Aunty Rabi ta fito da gudu ta makalkale Mama kamar wata karamar yarinya, tana lale Maman Kaduna, lale da ‘yan Giwa, lale da ‘yammatan Hajjah.
Ta yi mana jagora zuwa falonta, Yaya Muftahu ya fito daga nashi dakin shima yana mana marhaban, nan muka ga yadda ake karrama bako, ko da jini ne ba bako ba.
Kwananmu daya washe gari suka kwashe mu don nuna mana Kano ciki da bai dinta, duka kofofin nan, Kansakali, da Kabuga, Gadon Kaya, Kofar Ruwa, Duka Wuya, Dan Agundi, Kofar Famfo da Na’isa babu wadda bamu ratsa ta cikinta ba mun daga kai mun karanta sunan ta ba. Kofar Nassarawa, Kofar Mata.
Manyan wuraren tarihin Kanon Dabo irin su Gidan Makama (Museum), gidan Dan Hausa, Dutsen Dala da Gwauron Dutse, Gidan Zoo, Gidan Sarkin Kano da Fadar Masarautar Kano, har gidan Tsumburbura dake kan Dutsen Goron Dutse.
Haka manyan shopping malls din Kano babu wanda Yaya Muftahu da Aunty Rabi basu kai mu mun ciko ledoji ba, tun daga Sahad, Country Mall, Well Care, Grand Square, Jifatu da Ado Bayero Mall.
Lallai na yarda Kano ta amsa sunanta ta Dabo-ci-gari, yaro ko da me ka zo an fika. Mune har gidan Zoo da gidan Makama Museum. Sannan ranar juma’a mika ya da zango a fadar Sarkin Kano Alh. Ado Bayero muka yi gaisuwa ga Dabon Kano, duk da bai sanmu ba, ranar juma’a ya ware ta yana amsar gaisuwar talakawansa Allah ya yi masa rahma (amin).
Gaskiya mun ji dadin ziyararmu Kano fiye da duk wani gari da muka taba zuwa. Ko da yake mu dama duk yawon namu iyakacinshi Kaduna da Zariya, don haka zuwan mu Kano da kwanaki uku kacal da muka yi tare da Aunty Rabi da iyalinta ba karamin dadinsa muka ji ba.
Bayan mun dawo Yaya Aliyu ne ya tsaya ya sama mana gurbi a Queen Amina, duk da Yaya Hauwa ta so hanawa Hajjah ta ce ta kyale mu. Muka tattara muka koma muka fara karatu babu kama hannun yaro.
A hutun karshen zangon karatu na karshe na aji hudu da muka zo, Fa’iz yana makaranta ya kama daki a cikin makaranta. Don haka na saki jiki nake rayuwata cikin walwala da nishadi.
Ranar wata asabar Baban Kaduna ya zo gidan da maraice, ina uwar dakin Hajjah ina shirya mata kaya cikin (wardrove), ita kuma tana falo tana sallar walha na ji sallamar Baba Muntari.
Hajjah ba ta amsa mishi ba, nima ban amsa ba kamar wadda aka dinkewa baki. Ina jin shi yana waya da Baba Barau, Sadi, Sadisu, Na’ibi, Ibrahim yana fadin duk su hallara falon Hajjah tunda Asabar ce kowa yana gida.
Na ci gaba da abin da nake yi amma daga inda nake ina iya juyo hucin Baban Kaduna da ajiyar zuciyar da yake yi akai-akai. Ba a jima ba suka shiga shigowa daya bayan daya da sallama yana amsawa a wahale.
Zuwa lokacin Hajja ta idar suna ta gaggaishe ta tana amsawa. Sannan ta dubi Baba Muntari da kulawa da kauna ta manyantaka, ta ce, “Wa ya tabo Muntari ne? Wannan sammako da taron gaggawa haka?”
Baban Kaduna bai tanka ba ya ciro takarda cikin breif case dinsa ya mikawa Baba Na’ibi, Baba Na’ibi ya karanta ya mikawa Ibrahim, Ibrahim ya mikawa Barau, Barau ya mikawa Sadi, Sadi ya mikawa Sani, Sani ya mikawa Salisu, dukkansu suka hada baki suka ce da Hajjah.
“Takardar withdrawal ce (kora daga makarantar Fa’iz Abubakar Mukhtar) daga Polytechnic a bisa hujjar rashin zuwa aji kwata-kwata, rashin contineous assessment (CA), sai za ayi jarabawa kawai yake zuwa. Idan kuma ya je yadda aka ba shi answer sheet haka yake ajiye ta baya iya rubuta komi a ciki, sai sunansa da registration number. An dora shi a kan (probation) tun shekarar baya bai gyara komai ba”.
Duk suka yi shiru suna sauraron cewar Hajjah. Ta jima ba ta yi magana ba, sai daga bisani ta ce, “Ba zan ce komai ba sai na yi magana da Hafizin”.
Baba Muntari ya zo iya wuya, ya ce, “Ki gafarceni Hajja, duk lalatar da Fa’iz ke yi don ya samu faragarki ne. Na yi na yi a daina bai wa Fa’iz mota kin ki. Ba shi da aiki sai tukin mota da gyaranta in ta lalace, duk kanikawan garin nan sun san Fa’iz, in ya ce miki yana makaranta to yana tashar mota.
Jiya-jiyan nan (C.I.D) din da nasa ya dinga bibiyar min shi tun lokacin da ya ce miki ya kama daki a makaranta jikina ya bani ba haka kawai ba, don mutumin da karatun boko bai dame shi ba me ya kai shi tarewa a makaranta? To rahoto ya zo min cewa, Fa’iz ba a makaranta ya tare ba yana Kaduna Express (tashar motar Kaduna) ya zama direban peageout da express masu zuwa gari-gari ba ya makaranta.....”
Gaba daya suka dauki salati har ita Hajjah. Ban san sanda dariya ta kubuce min ba, na yi hanzarin shigewa toilet na sheka abata na more. Ban dai ji karshen tattaunawar tasu ba sai fitar su bayan sunyi mata sallama. A raina na ce, hakki ba karya bane. Ina zaace hakkina ba zai lalata Hafizin Hajjah ba.
Washe gari ina wanka Fa’iz ya shigo falon Hajjah, jikina duk kumfa amma haka na kwara ruwan na fito kar labari ya wuce ni, ina ji Hajjah na cewa, “Ubanka gata yake maka, kyakkyawar rayuwa yake so maka ba wani abu ba.....”
Ina jin sanda yake ce mata, “Hajjah ina da matsala ne, hannuna kyarma yake duk lokacin da na rike biro. Hajjah bana iya rubutu”.
Abin da ban taba ji ba a duniya, wato shesshekar kukan Fa’iz. Ya ci gaba da cewa, “Hajjah ko wacce makaranta ce na yarda a kaini, amma kada a rabani dake. Ba zan iya rayuwa bakya kusa dani ba Hajjah. Akwai wata makarantar irin ta ai a nan Zariya a kai ni mana. Wallahi na yarda zan je, amma ni bana son in yi nisa daku ko kadan, don Allah ki taimake ni Hajja, ke kadai ce za ki iya lankwasa shi”.
Hajjah ta dauki carbinta tana kokarin ficewa daga dakin kada ya karasa karya mata zuciya. Hajjah Hadija da Hafizinta Fa’iz (Abubakar) sai Allah.
Cikin dauriya ta ce, “Na gama maganar nan dasu tuntuni Fa’iza za ka Rasha (Russia) kana so ko baka so. In kuma ka isa, je ka ce dasu baka so ba za ka ba. Sun ce kasashen da suka ci gaba ba a yin rubutu da biro ya yin duk wani abu da ya shafi karatu, tafawa ake a computer (typing). Tunda dai ba ni na kawo maganar nan ba Ubanninka ne, to don Allah ka shafa min lafiya”.
Shiru Fa’iz ya yi yana tsane hawayen idonsa da hankici. Abun duniya duk ya bi ya dame shi. Ya san yau an canza masa Hajjansa, ‘ya’yanta sun gama yi mata famfo, kuma ya santa kaifi daya ce, tunda ta ce haka ba za ta taba canzawa ‘ya’yan nata ra’ayi ba.
Shi kam bai son ya tafi ne ba don komi ba sai don yarinyar nan Fa’izah ‘yar Maimuna za ta yi farin ciki ta sakata ta wala a gidan, don ya tabbata shine kadai matsalarta a zaman gidan. Shi kuma a duniya mai adawa ne da farin cikin Fa’izah, in da abin da ya ki jini a duniya to ya ga Fa’iza cikin walwala a gidan nan.
To wai shin meye dalili? Me yasa ya tsane ta kamar ba jininsa ba? Me ta yi masa ya tsane tan? Meye laifin ta? Meye aibunta? Me take yi wanda bai so? BAI SANI BA! Tabbas akwai katuwar (?) alamar tambaya cikin kwakwalwa da zuciyarshi game da yarinya FA’IZAH A.A. GIWA.
Watanni uku da suka biyo baya, Fa’iz ba shi da sukuni duk da yana cikin gidan kullum yana baskwata. Haka kuma a lokacin muna cikin zangon farko aji biyar. Damuwar har ta sabbaba masa ciwo, tun yana yi a tsaitsaye har ya kwantar da shi hajaran-majaran.
[6/3, 4:12 pm] Takori: Wannan ya ta da hankalin Hajjah ba kadan ba, ta yiwa Baban Kaduna maganar a kyale Fa’iz da tafiya karatun nan tunda abin ya kai ga taba lafiya.
Baban Kaduna ya ce, “Don Allah don Annabi Hajjah ki fita daga maganar nan kada kema ya kwantar mana dake, amma sai dai ya mutu na huta ganin dana yana direban tasha in dai ba zai yi yadda nake so ba”. Sai Hajjah ta yi shiru.
Cikin wani hutu da muka zo Fa’iz na shirya kayan shi cikin troller (akwatin tafiye-tafiyen bature) da muke kira (tura ni a tiles). Ummi ta yi sallama ta ba shi kaya cikin leda da Baba Na’ibi ya aiko masa ya yi guzurin tafiya.
Ganin yana loda kaya a jaka ta samu kujera ta zauna a gefensa a darare, ga mamakinta bai mata tsawa ba, bai hantare ta ba balle ya kore ta.
A hankali ta ce, “Yaya Fa’iz tafiyar kenan?”
Ya dago ya dube ta ya yi dan murmushi, “Eh, Ummi ya zan yi? Baban Kaduna ya dage. Daga nan Kaduna na nufa, daga nan mu wuce Kano inda zamu tashi ta filin jirgin Malam Aminu Kano ni da shi”.
Ummi hawaye ya cicciko idonta dai-dai sanda idonta ya kai ga wani karamin album saman kayanshi da yake hadawa. Ta dauka ta bude shafin farko ta shiga dubawa.
Shafin farko hoton Fa’iza ne ta yi tagumi jikin varanda ‘terrace’ na gidan Hajja. Shafi na biyu kyakkyawan hoton Fa’izah ne ta yi tagumi a falon Hajjah. Haka shafi na uku Fa’iza sanye da koriyar suwaita mai kauri da jan siket kanta ba dankwali, wanda hakan ya sakko da jelunan kitson (shuku) dake kanta har bisa dogon wuyanta, tana rungume da (teddy bear) a gidansu dake Zaria. Sai kusan karshe ne ta ga hotunansu da sauran kannensa duka na Giwa da na Kaduna, har da su Walida amma 80% ba album din hotunan Fa’izah ne.
A matukar mamakance Ummi ta daga ido ta dubi Ya Fa’iz hankalinshi baya kanta yana ta shirya kaya haikan. Ta zari mai rungume da Teddyn ta ce, “Hoton nan ya yi kyau Ya Fa’iz in dauka? Fa’izah ba ta san da shi ba ma sam, don Allah ina ka same shi?”
A lokacin ne ya dago ya dube ta, ya zaro ido ya ce, “Ke! Wa ya ce ki taba mani album? Ina ruwanki da kayana?” Ya fauce album din ya danna a jaka ya ja zif. Ya shiga zuba mata bala’i ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba.
Ummi dariya kamar ta kashe ta san (borin kunya ne yake nannade shi da hauka). Ta ce, “Ka yi hakuri Ya Fa’iz ban san baka so a taba ba”. Ta dauki wasu daga cikin hotunansa ta ce, “In dauki wadannan Ya Fa’iz?” Ya dube su daya bayan daya ya ce, “Me kika ce?”
Ta mike da hotunan a hannunta za ta fita, har ta kai bakin kofa ya ce, “Tsohuwa!” A kufule ta juyo don ya kirata da sunan da ta tsana a rayuwarta, amma ga mamakin Ummi sai ta ga ya yi murmushi.
“Don mi kike son hotona bayan duk kun tsane ni don kawai ina gaya muku gasiya?”
Ummi ta girgiza kai tana dariya, ta ce, “Allah Ya Fa’iz bamu tsaneka ba, daman can kai ne ka tsanemu, kuma mu har mun manta ma wallahi. Mun san kuruciya ne ga shi yanzu tunda ka shiga Poly ai baka cika shiga lamarinmu ba balle ka takura mana. Wani abin ma in aka ce ka yi ai ba za ka yi ba”.
Ya ce, “Ko? In ku kun manta ai Hussainar taku ba za ta taba mantawa ba. Domin na zalunceta na wulakanta ta na ci mata mutunci da yawa, wanda nima wallahi ban san dalili ba. Yanzu har nauyinta nake ji saboda halin RAI da muhimmancin ZUMUNCI, kunyarta nake ji wallahi-wallahi Ummi.....”
Ummi ta yi sakatoto! Tana duban sa cike da shakkar ba da Fa’izu (Abubakar) take magana ba, wani ne dai mai matukar kama da shi. Ko kuma mafarki take yi.
Ta ce, “Yaya Fa’iz wai kana nufin Fa’izah?”
Ya girgiza kai ya ce, “It may be itan, it may also be kuma ba itan ba.....”
......”Ban gane ba?” Ummi ta tambaya her voice is trembling (muryarta tana rawa).
Ya ce, “Ba za ki gane ba Ummi, kowa ma ba zai taba ganewar ba, amma Allah ya ga zuciyata na yi nadama da dana sanin abin da na yiwa Fa’izah”.
Ummi ta dan yi zuruu! Tana dubansa, ta ce, “Na tabbata na kuma hakkake cewar Fa’iza ba ta rike ka ba sam a zuci Ya Fa’iz, kullum addu’arta Allah ya shiryi Ya Fa’iz ya ganar da shi illar ‘KARYA, MUGUNTA, ZALUNCI da muhimmancin zumunci”.
Fa’iz ya dafe kai ya dubi Ummi duk idanuwansa sun sauya launi, ya ce, “Yanzu Ummi duk da wadannan sunayen Fa’izah ke kallo na? Kuma haka Ummi?” Tune din muryarshi wannan karon (in subdued) a karye.
Ita ma Ummin ta karaya a wannan gabar, ban da girgiza kai alamar, “A’a”. Ba abin da ta ce. Ya yi mata alamar ta tafi kawai ta kyale shi.
Washe gari kowa ya shirya za a tafi rakiyar Fa’iz, sai na zari mayafi na yi wuf na shige gidan Baba Barau na buya a kitchen. Neman duniya Ummi ta yi ba ta ganni ba, dole suka hakura suka shiga mota.
Daga tagar kitchen din ina hango shigar Ya Fa’iz mota, yana dan waiwaye kowacce kusurwa ta A.B Bamalli Estate kamar mai neman wani abu. Daga bisani ya shiga motar Ya Aliyu ya ja suka fita a get din.
Na yi wata irin doguwar ajiyar zuciya kamar an zare min kaya a kafa, kamar kuma an sauke dutsen Dala da Gwauron Dutse daga kaina. Na yi wata irin kakkarfar ajiyar zuciya.
****
BAYAN SHEKARA DAYA
Shekarar ta zo ne da tarin sauyuka masu yawa cikin A.B Bamalli