Showing 30001 words to 33000 words out of 44953 words

Chapter 11 - Zumuntar kenan Book 1 by Sumayya Abdulkadir Takori.txt

kafin ya bar gidan ba.
****
Ban tashi sanin fitinar so ba sai a wannan ranar. Ban yarda it is injurious ba sai a wannan ranar. Ban san cewa its unbearable pain ba sai a wannan ranar da na tabbatar zuciyata ba za ta samu abin da ta dade tana SON ba, wato Ali Na’ibi.
A gaskiya so abu ne mai dadi in ya zo da matsala marar dadi. Kamar yadda Ya IM ya ce na (GIRMA YA FADI) “It’s so sweet, yet so painful”.
Wai sai na kama jin haushin ‘yar’uwata Zanirah (kishi), a ganina duk ita ta yi saurin girman da ya gundiri Hajjah har ta yi tunanin aurar da ita, kuma ta rasa wanda za ta likawa duk gidan sai Aliyuna, Yaya Aliyu, Aliyu Haydar Na’ibi A.B Giwa.
Daga ni har Zanirah, kowacce ta kasa barci sai juyi a kan gado. Da abin ya isheni kawai sai nasa kuka wiwi. Tunanin in na rasa Yaya Aliyu, idan ba Aliyu ne ya zamo mijina abokin rayuwata ba shin ya ya rayuwata za ta ci gaba da kasancewa? Ya Allah kada ka baiwa Hajjah ikon karfafa zumuncin akan wannan, ya Allah ka fidda Aliyu zuciyar Zanirah. Don na laluba na duba na hanga ko ina ban ga ta hanyar da zan iya cin kankanta in bar mata ba in ita ba ta ci girma ta bar min ba, sai dai duk mu rasa, ko duk mu samu.
Zanirah ta mike ba zato ta kunna fitila dakin ya gauraye da haske. Ta shiga kallona tsaf, ba ta ce komai ba sai ta shiga toilet ta dauro alwala ta zo ta burma hijab ta hau doka nafilfili.
Hankalina ya kara dugunzuma ya tashi, don a ganina Zanirah na rokon Allah ne a kan ya mallaka mata Yaya Aliyu ni ya hanani. Sai na kara rikicewa da kukan tun karfin gunjin da zan iya a hankali yadda sauran jama’ar gidan ba mai ji na.
Ba shiri Zanirah ta sallame sallarta ta ce, “Fa’izah wai lafiya ne?”
Na dan saurara da kukan na ce, “Na fara kukan rabuwar mu ne Zanirah....”
Da alama ba ta yarda ba har zuci, sai ta yi murmushi ta ce, “Allah yasa hakan ne har zuciyarki. Da sai in ce rabuwa ta zama dole ai, tunda babu yadda za ayi mu dauwama tare a matsayin mu na ‘ya’ya mata. In babu aure akwai mutuwa, akwai kuma kaddarorin Ubangiji iri-iri”.
Mu karasa a littafi na 2
Tare suke,Takori
[6/3, 4:12 pm] Takori: Hawayen da suka shimfido min su suka sanya na mike na yi daki aguje ina kuka wiwi. Yaya Hauwa ta taso za ta biyo ni ta rarrashe ni amma Hajjah ta ce ta kyale ni kawai in yi kukan zuciyata za ta yi min sanyi, kukan sabo ne da fitar SO.
Na ci kuka na a gado na share hawaye, na jiyo zubar ruwa a (toilet) wanda ya tabbatar min Zanirah wanka take yi. Idona ya kai ga abin da na jima ina fakon Zanirah don in dauka sai yau na hange shi cikin kwabar kayanta wato ‘DIARY’ dinta. Na yi hamzarin daukowa ban yi nawa ba wajen bude shafin farko. Kwanan watan ya nuna Zanirah ta yi rubutun nan ne tun muna JSS (karamar sakandire).

“Ban san abin da ke damuna ba, amma kamar son Yaya Aliyu nake in na yi la’akari da yawan tunaninsa da nake da mafarkinsa cikin barcina, da kwadaituwa da son ganinsa akai-akai. Me kenen hakan ke nufi?

Sai na shiga bude sauran shafukan a gurguje. Duk yawanci abin da ya shafi kuruciyarmu ne. Sai wani da ya dauki hankalina wanda kwanan watan ya tabbatar min Zanirah ta yi rubutun ne ranar 10/10 wato ranar da muka je Area One ni da ita (Zaria).

“Dole ne in yi jihadin fitar da Yaya Aliyu a raina, domin ina son shi ne a yayin da na fahimci zuciyarsa, rayuwarsa, ruhinsa da gangar jikinsa sunyi nisa a soyayyar ‘yar’uwata (Fa’izah.) Fa’izah da zumunci basu cancanci in yi tarayya dasu a son komai a duniya ba. Yadda nake son Fa’izah bana son abin da zai sosa ranta. Na tabbatar da Fa’izah ta san ina begen Yaya Aliyu, babu abin da zai hana ta bar mini.... zan ci gaba da lallamin zuciyata har sai ta mance da Yaya Aliyu.... in har Fa’izah za ta iya yi min wannan halacci ni me zai hana na kasa? In anyi duniya don Rasulillahi daga yau na cire son Aliyu a raina domin Fa’izah.......”

Da na kawo nan sai na rushe da kuka sosai, hawaye na zuba a kan littafin. Dai-dai lokacin da Zanirah ta bude kofar toilet ta fito, kukan da ta tarar dani ina yi ya kara tsuma raunanniyar zuciyarta.
Ta tsuguna nan a bakin kofar ta shiga rera kuka ita ma, muka taru muka yi ta yi kamar akuyoyi. Cikin gunjin kuka Zanirah ta ce, “Fa’izah ki yafe ni...... wallahi ban ci amanarki ba.... Ban taba sanin Yaya Aliyu ne mijin da za a daura mana aure ba..... da na san shine wallahi da na bar garin da in zauna in ga wannan rana.... wallahi ban san cewa Yaya Aliyu bane ban sani ba Fa’izah.... ban san za a daura ba.....”
Na mike da azama da sassarfa na isa ga Zaniraha muka rungume juna muka ci gaba da rusa kuka tare ba mai jin na wani.
Na ce, “Zanirah kada ki ce haka, (waman qaddarralahu haqqan qadrihi.) Kada ki kara fadin haka Zanira, ban taba zargin ki da wannan ba, mune muka yi kuskure, kuskurenmu ne ni da Yaya Aliyu da muka yarjewa zuciyoyinmu muka basu fili a kan abin da suke so, alhalin muna da masaniyar ko in ce mun kwana da sanin cewa babu auren soyayya a zuri’ar A.B muka bi ta kai muka take. So we are to be liable for the outcome, ban zarge ki ba ko kadan Zanirah. Baki da wani laifi, babu wata amanata da kika ci. Addu’ata da fatana Allah ya karkato da son da Yaya Aliyu ke mini da wanda nake masa kanki, ya baku zuri’a dayyaba... Ya bani miji kamar naki Zaneerah...!”

****
Yaya Aliyu bai tashi zuwa Giwa ba sai karshen wata kamar yadda ya saba, wanda ya yi dai-dai da sati biyu kenan daurin auren shi.
Tun daga gidan mahaifinsa, mahaifinshi Baba Na’ibi ya kira shi ya yi masa gamsasshen bayani. Ya kara zancensa da cewa, “Aliyu ka bi Hajjah da duk yadda take so in har kana so ka taimakemu mu rabu da ita lafiya. Hajjah mahaifiyarmu ce da ta tsuguna ta haife mu daya bayan daya. Bamu da ikon bijirewa tsarinta da mahaifinmu Allah ya ji kan rai ya dorata a kai, ka sanyawa zuciyarka hakuri da dangana tamkar kowane Da cikin gidan nan da ka budi ido ka gani.
Domin a yadda Hajjah ta dage a kan auren nan naka da Zanirah, ta kuma kawo hujjojinta masu ma’ana mu kanmu mun ga gaskiyarta mun mika mata goyon bayanmu wanda a baya bamu bayar ba.
Ta sanya tariya sati biyu masu zuwa, na biya sadaki dubu sittin, ga lefe kuma da Babanka Ibrahim ya yi maka, su Hauwa ya tura Kano suka hado komai, gobe in Allah ya kaimu za su Zaria (gidanmu kenan). Don Babana ne alwalin Zaneerah.”
Aliyu Na’ibi a zaune yake bisa kilishi dai-dai kafafun mahaifinsa, amma sai ga shi tsaye gaban Baba Na’ibi ba tare da ya san lokacin da ya yunkura ya mike tsayen ba.
Wani kakkauran gumi ya wanke shi daga kwanyar kansa har zuwa yatsar kafarsa. Ya bude baki zai yi magana yawu ya kafe kat, a bakinshi. Bakin ya bushe fayau! Iyaka kokari Ali ya yi wurin tattaro kalma daga can kasan makoshinsa......
“Don me kuka yi min haka Baba?”
Da karsashi da tausayin da ake son boyewa karfi da yaji ya ce, “Don mun isa daku dukkanku”.
Aliyu ya ce, “Bana son Zanirah da irin soyayyar da kuke nufinmu da ita, ban taba sonta da aure ba Baba”.
Baba Na’ibi ya mike tsaye idanunshi tinjim da kwallah ya ce, “Aliyu babu bambanci tsakanin Zanirah da Fa’izah, abin da ya yi Fa’izah shi ya yi Zanirah. Uwar da ta haifi uban Fa’izah ita ta haifi uban Zanirah. Tare suka taso tun suna kanana, komai nasu iri daya ne sai a halayya da suka bambanta. Ka yi hakuri ka jure sauyin da Allah ya yi maka ka yi koyi da mai sunanka”.
Ya ce, “Matsalata Baba ba zan iya daina son Fa’izah ba.....”
Sai a wannan lokacin hawaye suka sakko bisa kundukukinsa.
Baba Na’ibi cikin dimuwar wai yau Aliyu ke kuka a gabansa, kukan ma a kan mace. Sai ya ce a harkuze,
“To Aliyu ka yi yadda kake so, ka yi duk abin da kake ganin shine dai-dai, tunda mu bamu san dai-dai ba. Sai dai ina tabbatar maka da abu uku, na daya muddin ka wulakanta Zanirah sai Allah ya saka mata, domin ita ma yadda ka tsinci al’amarin haka ta tsince shi bakin iyayenta.
Na biyu muddin ka tsinka igiyoyin nan guda uku da muka damka maka sai dai ka nemi wasu iyayen amma ba cikin zuri’ar A.B ba. Na uku muddin ka dagawa gyatumar mu hankali tsakanina da kai sai Allah ya bi min kadina na haifar ka da na yi na raine ka har ka yi girman da za ka soka wa uwata tsinke cikin idanu”.
Hawayen Aliyu na zuba ya ce, “Ta ya ya Baba za a daki mutum sannan a hana shi kuka?”
Baba Na’ibi ya ce, “Har karya shi za ayi a ce in ya yi nishi Allah ya isa! Na dai gaya maka daga yau babu sauran wata hulda tsakaninka da Fa’izah sai ta ‘yan’uwantaka. Zanirah kuma idan ka wulakanta ta don kanka, sai dai a kullum kake tunawa ita ma ba ta taba cewa tana sonka ba dole a kai mata. Amma da yake ita mai biyayya ce ba ta dagawa ubanta hakarkari kamar yadda ka daga min ba”.
Haka ya fice daga dakin Baban cikin mummunan yanayi da ba zai misaltu ba. A take ya zari mota ya bar garin kwata-kwata ya koma inda ya fito (Ikko), fadi yake kamar zararre, “Ku rike amaryarku can bana so...... Ta ya ma za ayi na auri Zanirah?”
Gidan babban amininshi Isa Kaita ya aje motarshi. Isa ya kai shi filin jirgi ya bi jirgi zuwa Lagos.
Mu muna can dakinmu na ‘yammatan gidan muna jiran ango ya shigo ya bamu kudin alibidi da lancin din da zamu yi a Zaria da Walima a gidan Baban A.B.U. Labari ya iske mu ai Yaya Aliyun ya zo ya kuma koma Lagos ba tare da ya kwana ba ma.
Ban da salati ba abin da Hajjah ke yi tana fadin “Zai zo ya same ta”. Amarya Zanirah ta yi kamar ba ta san ma me ake cewa ba, ta yi bakam. Ta dauki remote ta karo sautin wakokin yaran Larabawa na (Ad-difl - wal-bahr).
A take na gano matsalar Yayan namu, wato ya ji labarin wannan rikitaccen al’amari na Hajjah. Ni kam da na mai da al’amurana ga Allah da addu’a, nafilfili dare da rana da addu’o’i na musamman cewa, in soyayyar Aliyu ba alkairi ba ce a gareni Allah ya sanya min hakuri da dangana, ya yi min zabin alkhairi mafi kyau, domin zabinsa shine zabi. Abin da nake maimaitawa kenan cikin sujjada ta a ko da yaushe.
Tuni nake da tabbacin Ubangijin nan maji rokon bayinsa ya amsa mini, zuciyata sarai, duk wani duhu da kunci sun gushe. Babu abin da zuciyata ke kwadayi kamar ganin daidaituwar auren Zanirah da Aliyu. Na kudurtawa zuciyata zan yi amfani da mahaukacin son da yake min in ciyo galabarshi a kan Zanirah.
Na dauki wayar Hajjah na yi kofar gida can inda babu kowa tsakanin motoci, na danna lambobin Yaya Aliyu wadanda tuni na haddace su. A washegari kenan da tafiyar shi.
Ta yi ringing har bakwai bai daga ba. Kafin ya daga a fusace a na takwas, “Wai wane ne? Mene ne?”
Wani sanyi da ya ratsa zuciyata ya tabbatar min har yanzu ina son Aliyuna, na kasa magana. So shu’umi ya rugurguza duk wata kalma ta bakina.
Aliyu ya sake cewa, “Hello! In ba wani abu ba kuma sako bane zan ajiye ina sauri zan tafi Ibadan ne”.
Cikin jarumta na ce, “Yaya Aliyu, kana da ikon zuwa Ilorin, Abeakuta, Benue da Akwa-Ibom ma amma bayan ka zo ka dauki Zanirah kun tafi tare. Ni wannan wane irin so ne da kake neman lika min kashin kaji cikin ‘yan’uwa? Yanzu kowa ya bude baki cewa yake, “Aliyu ya ki Zanirah ne domin Fa’izah”.
To muddin son da kake ikirarin kana yi min na gaskiya ne ba kuma ka kaunar tashin hankali na da kasancewata cikin zargin jama’a, to ka dawo ka tafi da matarka yau ko gobe. Ko da baka son Zanirah ba haka ne hanyar da za ka nuna ba Yaya Aliyu. Wannan hanyar da ka bi ka nuna cewa ka ki bin abin da iyayenmu ke son ka da shi ne. Ka yi butulci ga alkhairin da suke hango mana ta hakan.
In kuma don ka batawa Zanirah rai ne ka yi hakan, wallahi Zanirah baka gabanta, harkokin gabanta take. Dakacen auren take yi, sai don ba yadda za ta yi ne. Ni din dai nice cikin damuwa..... tunda ni dangi za su tsana, ni zan shiga bakin duniya...!”
Da fadin hakan na kashe wayar baki daya ba tare da na tsaya sauraron amsar da zai bani ba, wadda na tabbatar ba shi da ita din.

****
To Ali kam ya nuna ya haifu cikin uwarshi Zainabu, da ubanshi Na’ibi, kuma mai son farin cikin Fa’izah. A washegari ya dawo Giwa, inda ya saki kudi aka yi shagulgulan al’adarmu namu na Mallawa. Ya nuna tamkar komi bai faru ba, kamar Zanirah zabin shi ce ba zabin iyaye ba.
Amma zuciyar ta fi duhun dare duhu. Babu yadda ya iya fadan da ya fi karfin ka aka ce sai ka mai da shi wasa. Iyayen nan bashi da saman su, Hajjar nan ta fi karfin komi a garemu in har muna da iko, in har bamu da shi, zamu yi iya kokarinmu mu nemo masu shi suyi mata.
Sai dai abu ne da har illa masha Allahu ba zai taba kankaruwa daga zuciyarsa ba wato SON FA’IZAH! In ka ga ramar da Yaya Aliyu ya yi kamar wanda ya taso daga gadon asibiti bayan doguwar jinya. Jirgin karfe taran dare aka ajiye za su bi zuwa Lagos.
Aliyu ya dubi Hajjah ya ce, “Tunda har anyi mai wuyar Hajjah, ba a bari in koma ni kadai in shirya in dawo in dauke ta? In gyara muhallina daga na saurayi zuwa na mai iyali. Saurin da gaggawar na mene ne? Cikin abokan aikina duka babu wanda na sanar mawa na yi aure kawai sai a ganni da mata kamar na sato ta? Yanzu haka a tsakiyar aiki nake zuwa Ibadan a bani lokaci ko da sati daya ne in je in dawo don Allah.....”
Hajjah goyon Mahillah diyar Baba Barau take a bayanta ba ta ko dube shi ba. Ta sunkuci fidarta dake shake da cereal ta yi daki tana bambamin fada har da kumfar baki. Ta ce, “Karewar gyaran gida mai da gidan fadar shugaban kasa. Karewar rashin so Aliyu sayar da kan Zanirah garin Yarabawa. Amma kafarka-kafar Zannura”.
Aliyu ya yi tsit! Na fashe da dariya, Zanirah ko tsabar takaicin yadda Hajja ke mai da ta matar cushe kamar jakar da ta rasa miji na san shi yasa ta zub da kwalla.
Kamar za ta fashe da kuka ta ce, “Ni dai gaskiya Hajjah ki daina ce mun Zannura.....”
Hajjah ta ce, “Zannuraini an fada, ainahin sunanki kenan (ma’abociyar haske biyu)”.
Zanirah ta zumburi baki ta ce, “Hajjah Zunnuraini sunan namiji ne (Usman kenan)”.
Hajjah ta ce, “Allah ya bamu albarkacinsa. Abin da yasa na saka miki suna Zannura saboda an haife ki Ranar Arfah, kuma kwanan watan ya yi daidai da ranar da Najeriya ta karbi ‘yancin kanta daga hannun Turawa, ga ki fara kal kamar auduga, ga kyau ga kyan hali. In baka so Zanirah ba ina jin babu zuciya da mazantaka a tare da kai”.
Kalaman Hajjah sun girmi kunnuwan dukkanninmu daya bayan daya muka zame kowa ya bi hanya daban mai billar da shi wani sashe na gidan. Yaya Aliyu kuwa tunda ta dauko bayanin asalin sunan Zanirah ya bar dakin don haushi.
Ta fannina nima na nuna ni ‘yar halas ce, nayi ma Zanirah gudunmmuwar (kayan amfanin kitchen) masu karko da tsada ‘yan Japan. Turare mai tsada ‘versace’ da ‘hugo boss’ na ango Yaya Aliyu, na ce, “A sha kamshin amarci lafiya Aliyu da Zanirah”.
Sai a wannan lokacin ne Yaya Aliyu ya dago ido ya dube ni da wata muguwar harara da ban tsammana ba. Zanirah dake gefen shi cikin farin (swiss lace) mara nauyi mai yarfin (silver) dinkin buba da zani, kunshi baki sidik ya kama tafukan hannaye da kafafunta. Gashin nan ya sha relaxing ya kara baki ya kwanta a dogon wuyanta, amarya dai sak!
Ta dago kanta a hankali daga kan yatsun kafarta ‘yan sirara itama ta harare ni. Ga mamakinmu duka sai cewa ta yi, “Wanea irin amarci kike fade Fa’izah? A ya yin da zuciyoyi biyu basu dai-daita da juna ba? Auren da ake lallashi da takurawa mijin ya so ka, shi kike ambatawa amarci Fa’izah? Kaico da auren da ake roko da lallashin mijin ya dauki amaryar yana gudu.
ZAMANI YA CHANZA, ya kamata iyaye da kakanni irin Hajjah su gane hakan, su ajiye traditionality su bi modernity in dai ba fadar Allah da manzo bane. Domin maimakon a gyara zumuncin sai a bata, ko a zalinci daya a kasa kwatar masa hakkinsa don a dorar da zumunci”.
Ta mike ta yi waje tana mai fidda zafafan hawaye. Na kasa cewa komi sabanin Yaya Aliyu da ya kyabe baki ya gyara kwanciyar sa cikin kujera. Tsam! Nima na mike na bar wurin. Ummi ta bimu da kallon tausayi baki dayanmu.
Karfe shida saura minti talatin, iyakar rakiyar mu dasu Zanirah filin jirgin saman Kaduna, inda suka hau jirgi mai zuwa Legas.
Sai a wannan lokacin ne zuciyata ta soma turiri, tana kurma ihun yarda da zancen Zanirah ZAMANI YA CHANZA.... ya kamata Hajjah da ire-irenta su ajiye traditional false beliefs su yarda love is a natural nature that cannot be totally eradicated. Yanzu ne na tabbatar na rasa Aliyu har abada! A lokacin da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login