Showing 33001 words to 36000 words out of 44953 words

Chapter 12 - Zumuntar kenan Book 1 by Sumayya Abdulkadir Takori.txt

tayoyin jirginsu suka rabu da kasa. Sai na fashe da kuka a lokacin da wani bakon tunani ya bakunce ni, wato yanayin idanun Zanirah (oily eyes).
Sau da dama Yaya Aliyu kan ce “Fa’izah ina ma kema irin kwayar idon Zanirah gare ki? Wallahi da na ji dadi na.....”
Hawayena suka sake ninka na da.... Ga Zanirah nan complete din ta ka samu Aliyu. Hawaye na ya sake ninka na da, na kifa kaina a kafadar Ummi muka ci gaba da kukan tare. Inda wanda ya san sirrin son da nake wa Yaya Aliyu, to Ummi ce, don tare muka rayuwa a makaranta fiye da Zanirah dake Giwa a lokacin da muka mallaki hankalin kanmu.
Babu irin tsarin da ban yiwa rayuwar aure na da Yaya Aliyu ba. Yadda za ta kasance, yadda zamu yi ta, yadda zamu gudanar da ita da yadda zamu tafiyar da ita, amma a yau Hajjah and her false beliefs (a ganina) sun rushe komai.
Lokaci guda wata irin sabuwar zuciya ta shige ni mai dauke da sabon perception. Na san dadin ‘So”, haka na san dacin rasa shi. In Allah ya yarda ba zan yarda in auri wanda bana so ba! Ba zan yi auren zumuncin ba, ba zan yi auren A.B Family ba. Zan zamo mutum ta farko da za ta canza A.B Family, zan zamo mutum ta farko da za ta yi auren soyayya a cikin zuri’ar Abubakar Bamalli Giwa.
Bare zan aura wanda zuciya da ruhina ke so da kauna, wanda zai jiyar dani dadin soyayya da zakin dake cikinta. Ko duk duniyar nan za ta taru a kaina ba zan yi auren A.B House ba sai wanda zuciyata ta aminta da shi. Nake so, yake sona da irin soyayyar da muka yiwa juna ni da Yaya Aliyu.

****
Yau wata guda kenan da tafiyar su Zanirah in har na lissafa dai-dai, amma babu ko duriyarsu. Aliyu dai ya yi waya wa Hajjah cewa yana bakin aiki a Ibadan, don haka ba zai samu zuwa gida karshen watan nan ba sai na sama, suna tare da amaryar a Ibadan. Uhm! Namiji kenan. In ji Umma Sulaiman Shu’aibu ‘Yan Awaki. Kudan zuma, indararon roba ta ko ina zuba kake. Allah ya gyara.
Takurawar da Mansur Modibbo ke min a gida Giwa da Zaria yasa duk garuruwan suka fice min a rai. Domin dai ni tunda na rasa Yaya Aliyu bana jin zan iya wata aba wai ita soyayya nan kusa. So dai guda daya ne, na sha shi na warke, bana fatan Allah ya kara maimaita mini. Ko ina fatan hakan ba cikin garuruwan nan uku ba, Zaria, Giwa da Kaduna. He must be a stranger! Very far away!!!
Ban gama jinyar wancan ciwon ba yake nema na da in dasa wani, “Shin shi wannan bai ma da tausayi ne Ummi?” Na tambayi Ummi a yammacin wata asabar. “Wai da me zan ji ne? Yeah! I would love to marry a stranger, but he must be from far..... and he’s a stranger but not from far....”
Don haka na rika yin baya-baya da shi da kora da hali wanda ya fi kora da sanda, duk da mahaukacin son da yake min kuwa. Ba wai don yana da wata makusa ba, dukkan halayen shi ababen yabo ne.
Ni da Ummi mun kasance cikin kewar Zanirah, kullum kamar wadanda aka yiwa mutuwa. Hajjah kanta daurewa take tana sabgoginta, amma rashin Zanirah a gidan ita ma yana dukan ta. Daga mu yi tagumi, sai mu kwanta. Mun daina barin yara su kunna T.V a gidan balle radio. Sai mu ce sun dame mu. Mun dai mai da gidan kamar gidan mutuwa, farin cikinmu ya takaita, ba Zanirah ba Aliyu. Muna cikin kewar da ba za ta misaltu ba, ko yaushe muna kwance a daki kamar tsumma.
Don haka na ji dadi da Hajjah ta kawo shawarar wai mu tafi Kano gidan Yaya Rabi mu huta gajiyar baki kafin fitowar takardun karatunmu mu ci gaba da karatu. Dukkanmu ba karamin mamakin wannan magana ta ci gaba da karatu muka yi ba.
Na yi tunanin ko Hajjah ta yi hakan ne don ta samu na manta da Yaya Aliyu gaba daya. Abin da ba ta sani ba shine, tuni na bude kundi na sanya Aliyu a ciki (as a past tense). Wallahi ko da zan mutu babu aure, babu huldar da za ta shiga tsakanina da mijin Zanirah (other than) ta ‘yan uwantakar da ta hada.
Muka shirya tsaf sai Kano. Yaya Rabi mutum guda har da rabi don zumunci da son dan uwa. Zan iya cewa duk ‘ya’yan Hajjah babu wanda ya kaita kirki. Zama da ita da raha irin ta mijinta Yaya Muftahu ya wanke mana damuwa kakaf. Don sai ya zamanto Yaya Rabi ta cike mana gurbin Zanirah, Yaya Muftahu ya cike mana gurbin Yaya Aliyu. Sai muka kwantar da hankalinmu muka bude sabuwar rayuwa mai dadi.
A irin hirarrakin da muke yi da Yaya Rabi ta kan so a sako hirar su Zanirah, ko da wasa Yaya Rabi ba ta taba sanin mun so juna ni da Yaya Aliyu ba. Irin maganganun da take sakin baki tana fadi a kansu a gabana ya kan kona min rai ya tado wani kwantaccen ciwo da na riga na samu ya warke.
Akwai sanda za ta ce, “Allah kadai ya san irin soyayyar da suke barzaa yana muzurai yana cewa baya so din” Ko ta ce, “Uhm! Su Zanirah ana can Ikko ana romansewa”. Ko ta ce, “A gaskiya Zanirah ta caba miji. Ga kyau ga kuma kyawun hali. Aliyu Mutum ne wanda zai shagwaba matarsa, ya bita da duk yadda yadda ta yi da shi, ba irin Bashir, Fa’iz da Mus’abu bane”. Na kan kau da kai ne kamar ban ji ta ba. Ummi ta yi dariya kawai. Haka nan ban taba tankawa ba sai Ummin.
Tsakanina da Ummi yanzu mun koma mun dinke kamar da. Domin ta lura in har tana son hulda dani to fa sai ta ajiye zancen makiyina Fa’iz a gefe. Ba ta zancen Fa’iz a gabana kamar yadda duk hotunan shi da ire-iren kayan da yake aiko mata ta tattara su ta aje a wata katuwar jakar Hajjah a Giwa. Amma dai ai na ji TAKORI ta ce, “ZUCIYAR MUTUM, BIRNIN SA!”
[6/3, 4:13 pm] Takori: ZUMUNTAR KENAN 2
Washe gari muka raka Momi bikin walimar ‘yar aminiyarta Dacta Ladi, cikin Tudun-Wada. Lancin din da aka yi na ‘yammata a (Congo Conference) ya taimaka ainun wurin rage mana damuwa dukkanmu, kowaccenmu ba ta dawo haka ba sai da saurayi. Suka biyo mu har gida, Momi ce ta lallabasu ta ce su dawo gobe lokacin magariba ta yi ido na ganin ido ya fi. Washe gari kuwa da safe muka tattara muka koma Kaduna.
Har muka kare satin ni da Zanirah kowanne ya kasa sakin jiki da dan’uwansa. Abin da bamu taba tunani ko a mafarki zai taba faruwa a rayuwarmu ba. Kai SO din nan bala’i ne, masifa ne ba karama ba tunda har ya iya farraka (shiga tsakanin) ni, Ummi da Zanirah.
Ranar da zamu koma makaranta mun shirya tsaf cikin uniform. A bakin gate zan shiga motar Baban Kaduna ya ajiye ni makaranta, ita kuma za ta shiga school bus direban Baban ya maida ta Giwa (GGSS Giwa) sai ta riko hannuna. Ta matse gam cikin nata, hawaye ya fito daga idanunta ta yi azamar dauke su da yatsunta.
Ta ce, “Fa’izah ki fidda damuwar dake damun ranki ki yi (facing final exams) dinki yadda ya kamata, wannan ce damarmu ta karshe ta gina (future) dinmu, kada mu bari abin da bai kaita muhimmanci ba ya rushe”.
Na murmusa ina kokarin mai da nawa hawayen na ce, “And you too Zanirah!”
Amma a zuciyata cewa nake, “Kin manta ne Zanirah, an ce “LOVE IS OVERALL!”
To haka rayuwar ta kasance mana ba dadi a makaranta ma, kullum zullumina kammaluwar jarrabawarmu, isowar karshen karatun nan.
Gab da zamu zana JAMB na shiga samun katunan fatan alkhairi daga Yaya Aliyu masu dauke da kalamai masu karfafa zuciya tare da kwantar da hankali.
A kalamanshi ya fi ambata ‘nasararki na nufin nasarata, kwanciyar hankalinki shine tushen samun nasarar, nasara ba ta zuwa da sauki, nasara sai an sha gwagwarmaya ake samun ta. Soyayyar da ba a samu tangarda ko bambance-bambancen ra’ayi ba, ba ta kai wa gaci.
Fa’izah ki sa a ranki ba zamu yi aure bane kawai in dama tun fil azal Allah ya rubuta ba zamu yin ba”
Wannan kwarai ya taimaka min wajen samun nutsuwa na zana jarrabawar JAMB lafiya cikin kyakkyawan zaton samun kyakkyawan sakamako, wanda zai fitar dani kunyar iyaye da masoyana.
Tsakanina da Ummi sai kallo da ido in an haxu a hanya, haka nan kunnuwana basa huta jiye min irin sakonnin da take samu daga Fa’iz akai-akai ba. Daga bakin Naja’atu da Haulatu. Tare da tabbatar min Ummi ta yi nisa a son Fa’iz ta yadda za ta iya batawa da kowa ma a duniya bani ba, don haka in daina tunanin zan iya hanata ko zan rinjayeta ta bi ra’ayina.
Yaya Aliyu ya kawo mana ziyara muna wata biyu da dawowa, bai fi saura sati uku mu kammala makaranta ba kenan. Hankalina ya yi mugun tashi da ganin yadda Aliyuna ya koma kashi da rai, ido a lungu, dama jikinsa fyalan-fyalan babu kwari haka yake, dogon Bamalle mai suffa irin ta Baba Na’ibi.
Baki a bude nake tambaya “Shin Ya Aliyu ulcer din ta kwantar da kai ne bamu nan?”
Ya girgiza kai ya ce, “Ko daya Fa’izah. Illah Hajjah da Baban ABU dake neman zauta ni. Hajjah ta rantse ta kuma ta rantse ba ta san zancena dake ba, ba kuma za ta yi miki aure yanzu ba.....”
A tsaye nake amma sai ji na na yi ragwaf, na yi zaman rakuma a gaban Yaya Aliyu. Idanuna ke fitar da wasu irin hawaye amsu zafi da yaji da ban taba fitar da irinsu a rayuwata ba, a yayin da nake cewa, “Ni kam Yaya Aliyu na hakura, ba zan iya jayayya da Hajjah ba, na hakura har ga Allah.
Dama an ce duk soyayyar da ta yi tsayi irin haka da kyar ne take kai labari.... Na hakura..... ko ba komai ba zan yi bakin ciki ba don ka auri ‘yar’uwata jinin jikina Zanirah ba..... ina da yaqinin ban barka a hannun da zan yi tararrabi ba, you are in safe hands, domin Zanirah nice, ni Zanirah ce, babu bambanci daga kamanni da halayya, sai ma wanda ta fini. Zan so ka yi farin cikin jin cewa Zanirah na matukar son ka, irin son da tunaninka bai taba baka ba......”
Ya katse ni cikin tsawa..... “Fa’izah baki da hankali? Kina hauka ne, kina so ki kashe ni ne? Shekaru goma sha biyu da na kwashe ina dakon soyayyarki, dai-dai da rana daya zuciyata ba ta taba hutawa ba da azabar soyayyarki da abin da za ki saka mini kenan wai kin barwa wata ni?”
Na sunkuyar da kai kasa yayin da hawayen suka sunce a kundukukina suna rige-rigen tadda kasa, aguje suke bulbula wani na bin wani suna masu tuna mini kaunar da Yaya Aliyu ya shekara nuna mini.
Wahala wadda uwa da uban da suka haife ni basu yi min kwatankwacinta ba in an dauke hakkin haihuwa. Duk da bai ambaci wahalar da ya sha a kaina ba sai ‘kauna’ da ‘soyayya’ ya zama dole ni din in tuna da wannan.
To amma babu abin da zan iya a ciki. Tsana ga Zanirah ko kuwa kin biyayya ga Hajjarmu? Gyatumar da iyayenmu ma basa tsallake umarninta?
Ina mai girgiza kai a gaggauce na rarrafa ga Yaya Aliyu yayin da na kama tafin kafarshi ina kuka, na ma manta a cikin ofishin vice muke, ina fadin “Ka yi hakuri Yaya Aliyu, ya ya kake so in yi toh? Kana nufin in baka hadin kai mu yi butulci ga Hajjah da Baban Kaduna da Mama Asma’un da ta tsuguna ta haifi Zanirah amma ta fifitani a kanta? Ko ko Hajjar da ta sha wahalarmu, wahalar da iyayenmu basu sha ta ba? Ba zan iya ba! Ka yafe ni Yaya Aliyu!!
Na san ka so ni, ka bautu a son da kaunata tsayin shekaru, to haka Zanirah ma ta kwashe shekaru tana begen zama a muhalli na. Na tabbata za ta yi maka biyayya fiye dani tunda son ta ya rinjayi naka. Sanin kanka ne Zanirah mutum ce mai sanyi da saukin hali, nutsuwa da hankali tamkar kai, it must surely be a perfect match as usual within A.B family. Nima Allahu ya bani gwarzon miji tamkar kai mai hali da aqida da kamannin Yaya Aliyu. Kundin shafukan rayuwata will be incomplete without the scenes of Yaya Aliyu.....”
Na juya ina tafiya da baya-baya ina masa murmushi ga hawaye na bulbula. Aliyu bai iya ya ce mani komi ba illa buga hannuwanshi duka a jikin garu (bango) ya kifa kai a jikinsu yana rusar kuka, kukan da bai taba yi a rayuwarshi ba, kukan da wani namiji kwatankwacin Aliyu dai bai taba yi a kan mace ba......
“Hajja kin cuce mu..... kin yanke mana buri a dab da wa’adin cikarsa..... kin guntile ingantacciyar soyayyar da aka dasa ake mata ban ruwa ta yi yado ta ba da yabanya ana gab da cin amfaninta..... Anya zamu iya yafewa Hajjah? Meye amfanin soyayyar da take nuna mana tunda a karshe cuta take zama? Babu!!
(Rabuwar mu da Yaya Aliyu kenan).

****
Na yi matukar kokarin ganin na manta da Yaya Aliyu, na fidda son Aliyu a raina, na yi kukan, na yi addu’ar, amma a kullum son Yaya Aliyu ke dawo min danye jagab, sabo fil a zuciya.
Meye sauran farin-cikin ne a yanzu a zama a A.B House a yanzu ni Fa’izah! Ummi mun rabu saboda Fa’iz, Zaneerah mun rabu saboda Aliyu, shin me zan koma in yi a Giwa? In ina da zuciya kare bai cinye ta ba daga yau na bar Hajjah Hadiza Giwa, zan koma gidanmu, ko da uwata da ubana za su kasheni ne tunda Hajja ba ta so na. Zanirah da Fa’izu ta fi so tuntuni.
Wannan haka yake ‘ya’yan Baban Kaduna take so, domin shine mai kudi, shine mai huce takaici, wato masu gidan rana. Yana kaita Hajji duk shekara ko ya ya ne? Shin ma wai me nake tsinta a kauyen Giwa ne da babu a Zaria? Zariar ma muhalli irin (Area One). Ba komai bane illa sabo da su Ummi. Tunda rayuwar ta zo da guguwar sauyi kowa ya koma gaban uwa da uban shi.
Yaya Aliyu! Yaya Aliyu!! Yaya Aliyu!!!
A kullum na tuno irin soyayyar da muka gudanar, a gaba dayan tsayin rayuwarmu, kulawar da ya yi mini, wahalar da ya sha a kaina, sai na yi kuka na gode Allah. Hawayena sun kafe, na kama kukan tunkiya, wanda babu hawaye sai sauti.
Babu abin da ya firgita ni kamar migraine (ciwon kan barin kai guda) da ya same ni a kowanne dare, ga wani zazzabi-zazzabi mai zafin gaske da nake kwana da shi da safe ya wartsake. Ban karanta ba, amma na kan ji an ce wadannan alamu ne na ciwon hauhawar jini (hypertention).

****
Ranar da muka zana takardar karshe wadda ta kasance ‘Islamic Studies’ na daga hannuwana sama na yiwa Allah godiya da ya nufe ni da kammala makaranta lafiya ba tare da na taba karya doka ko guda daya da makaranta ta kafa ba, ba tare da na taba batawa kowa da zama ya hadani da shi ba a kan sani, sai bisa ajizancin dan adam, kamar yanda ban taba yin laifin da aka dauki bulala aka shimfida a fatar jikina ba tsayin shekaru uku.
Na dawo hostel na shiga rarrabar da kayana ga juniors dinmu, na rabar da komai nawa har sutturar da nake amfani da ita a makaranta ban bari ba. Ban bar komai ba sai ‘hankici’ na da sutturar jikina wanda ya zame min tamkar jarabi. Na rufa shi a fuskata a wannan ranar, na yi kwance bisa gadon boarding school kwanciyar dana kira kwanciya ta karshe a sakandire.
Na juya rigingine al’amuran na gifta min tamkar majigi, kamar yau ne Yaya Aliyu ya kawo mu QUEEN AMEENA COLLEGE KADUNA. Yau ga Allah ya kawo mu ranar barin ta. Shekaru uku tamkar kwana uku.
Kwanakin, satittikan, watannin da shekarun sun shude ba za su kuma dawowa ba. Sai dai al’amuran dake cikinsu masu yawa ne a gare ni da ba zan iya mantawa dasu ba. Tunanin tashin hankalin da zan je in taras a gida gobe ya addabe ni.
Kowa ka gani a harabar makarantar ‘yammata ta Sarauniya Amina a washe gari bakinsa har kunne yake, farin ciki ya wadace shi. Sabanin ni da ta kasance bakar rana a gareni. Duk da dimbin tarihin da ranar ta ajiye min mai dadi ga iyaye da ‘yan’uwana.
Baya ga kyautar wadda ta fi kowa Da’a da kulawa da al’amuran addini (Amirah). Ni Fa’izah Ahmad Abubakar Bamalli Giwa, na karbi kyautar dalibar da ta fi kowa iya harsuna biyu mafiya shahara a duniya, wato Turanci da Larabci.
Wannan duk karami ne a kan yabon da na samu a kan kananan rubuce-rubuce na ‘Literature’ Littafina ARE VOWS MEANT TO BE BROKEN? Gwamnatin Kaduna ta saya akan kudi masu yawa, Sarkin Zazzau ya saya, dansa Yariman Zazzau Mansur Modibbo ya saya a kan kudi masu firgitarwa. Galadiman Zazzau ya saya, Iyan Zazzau ya saya duka don rabawa a labiraren makarantun sakandire na jihar Kaduna.
Wai-wai-wai. Ni Fa’izah na ga hasken camera a wannan rana, kamar ta bikin sallah. Haka na hau steps na rungumo kyaututtuka da award dina na literature. Babu abin da ya daga min hankali kamar rashin matallafi ko wani da ya shafe ni da zai karbe ni ya nuna min kauna cikin dangina da ya fito daga dimbin mutanen da ke hall din. Wannan ya tabbatar min daga Giwa har Kaduna da Zaria babu wanda ya zo mana.
A yayin da na ke saukowa daga ‘steps’ din saukowar na tafiya ne dai-dai da bugun zuciyata, hardewa nake ina rangaji kamar zan ci da baki. Kafafuwana da hannayena baki daya sun sage. Ko kowa bai zo ba na zaci Yaya Aliyu zai yi kokari ya zo a wannan rana.
A yayin da nake cikin wannan hali na takaicin rashin ‘yan’uwana, a yayin ne Ummi ta ratso daruruwan mutanen ta iso gareni ta tallafeni ni da kyaututtukana duka ta rungume mu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login