Showing 27001 words to 30000 words out of 44953 words
Chapter 10 - Zumuntar kenan Book 1 by Sumayya Abdulkadir Takori.txt
ni gare shi yana sona?”
Na ce, “Zanirah cewa nake Maman Kaduna da Baban Kaduna, Baba Na’ibi da Maman Yaya Aliyu, Yaya Hauwa da mijinta, su Baba Barau da Yaya Ibrahim, Sadi, Salisu, Sani, Aunty Rabi da Yaya Muftahu kadai sun ishe ki ishara. Zanirah babu yadda za ayi HAJJAH HADIZA GIWA ta hada aure ayi dana saninsa ko ayi dakacen wanzuwarsa, ko kuma ya zama mara dadi tsakanin ma’auratan. Sai dai ma daga baya a zo ana gode mata.
Saboda haka ki kwantar da hankalinki ( a ganina fa) Hajjah ba za ta kai ki inda za ki wulakanta ko ki tozarta ba. Insha Allahu babu komi cikin wannan auren face alkhairi. Ko ni da nake ganin zamu yi auren “So” da Yaya Aliyu ina gudun kada in zo auren bai mani dadi ba kamar na sauran zuri’ar A.B ba. Don haka har yanzu na kasa bawa Yaya Aliyu amsa”.
Ban juyo ba ina kallon ceiling ne dalili kenan da ban ga halin da kalamaina suka jefa ‘yar’uwata Zanirah ba. Ashe Zanirah fiddo ido ta yi warwaje, dafe kirji tare da bude baki duka a lokaci daya. Idanuwanta suka jirkice cikin dan lokaci tare da wuntsilowa daga cikin ‘sofa’.
Sai dai ‘yar’uwa ta gaskiya wadda ZUMUNCHIN har cikin zuciyarta yake ta yi kokarin controlling kanta ta hanyar komawa cikin sofa ta kalmashe ta runtse ido, tare da dafe kanta dake neman rabewa gida biyu saboda sarawa da juyawar bazata da ya yi mata.
Cikin sassanyar murya mai dauke da yankewar buri na rayuwa ta ce, “Wane Aliyu Fa’izah?”
Na mai da hannuwana baya na sarkesu na doshi taga a hankali na tsaya ina kallon waje ta tagar ina murmushi, na ce, “Aliyu nawa muke da shi cikin A.B. Zanirah? Baya ga Aliyu Haydar Na’ibi A.B Giwa?”
Na juyo gaba daya na fuskanceta ba tare da na gane rikicewa da gigicewar da Zanirah ta yi ba na isa ga jakata na zuge na fiddo wasikar Aliyu na mika mata ina fadin “Ban iya soyayya ba Zanirah balle kalamanta masu sanyi. Ban san soyayya ba Zanirah, ban san kalamanta ba. Na shafa duka duniyar kwakwalwata in nemo kalaman da suka fi kowanne dadi ga masoyi a duniya in rubutawa Yaya Aliyu na rasa baya ga (I love you too). Taimake ni ‘yar’uwa ki rubutawa Yaya Aliyu kalaman soyayyar da suka fi kowanne dadi da gardi a duniya ko da layi biyu ne kacal, ya san cewa ‘I do care for him too much’ ya san cewa ruhi, kalbi da gangar jikin Fa’izah gaba daya yana kaunar Yayanta Aliyu!”
Hawaye wani na bin wani sharaf-sharaf a fuskar Zanirah, a ya yin da take karanta wasikar Aliyu ga Fa’izah, tasa gefen rigarta ta share da sauri ta yagi wani gefe a karshen takardar ta ce, “Bari in rubuta maki amsa Fa’izah, ko dama can wauta ta hana ki gane Yaya Aliyu na mutuwar son ki, amma kowa ya sani. Ki rike Aliyu da kyau, ki yi mai rikon magnet.
Yaya Aliyu ba irin mazan da ake yiwa rikon sakaka bane. He has all the qualities and all the attribute to be love upon. Ina da kyakkyawan zaton cewa, muddin Yaya Aliyu ya zamo miji a gare ki babu ke babu ganin wulakancin namiji da ‘yan’uwa mata ke suffering, saboda Yaya Aliyu na daban ne. Babu ke babu kalmar nan da mata suke kira kamar ayar Alkur’ani wai “Duk wadda ta ce namiji uba ne.....” Domin Aliyu uba ne, uwa ne, aboki ne, dan’uwa ne, miji ne abin so da duk wata diya mace za ta yiwa kanta burin samu”.
Sakin baki na yi da kunne duka ina sauraron Zanirah. Me ya kawo duka wannan dogon sharhin? Ya ya aka yi muryarta ta canza haka kamar ba muryar Zanirar dana kwana na tashi da sani ba, tana magana cikin fidda rai da yankewar buri?
Na ce, “Za ki rubuta min amsar ne ko dauko diro zan yi in aje miki ki hau ki ci gaba da fadin how lucky I’m for having Aliyu as a husband?”
Ta yi murmushi ta ce, “Zan rubuta mana sister nah”.
Ta kammala cikin sakan biyu. Ta taso har inda nake tsaye jikin taga ta bani, ta juya ta shige toilet.
“If all my body is full of mouth, it’s not enough to expess the kind of love I had on you Yaya Aliyu”.
Na yi murmushi na rungume takardar ina fadi a cikin daga murya, “Na gode Zanirah.....”
“Da ta yi miki me?”
Gaba daya muka duba kofa ni da Walida, Yaya Aliyu ne!
Walida ta bude baki tana dariya, ni kuma na yi wuf! Na shige uwar daki cike da takaicin a yanayin sutturar da ya same ni na sanyo riga da zani da dankwali. Ina kokarin sanya dan kunne ya tsaya a bakin kofar sai na samu kaina da kasa hada ido da Yaya Aliyu a yau, sai sunkuyar da kai nake. Ya yi dariya ya juya yana fadin ina jiranki main falo.
Da ya fito dai-dai toilet sai na jiyo shesshekar kuka. La shakka Zanira ce take kukan da ba ta so a ji, ko a gani, shi yasa ta shige toilet take yin sa. Na tabbata ba zai wuce a kan aurenta bane. Ban yi mata magana ba, domin Zanirah mutum ce da ba ta son fadin damuwarta ga kowa, ba kuma ta son shisshigi cikin al’amuranta. Sai na fita falon a hankali duk jikina ya yi sanyi.
Yaya Aliyu ya dubi Kausar da Walid da suka yiwa cinyoyinsa dabaibayi ya ce, “Oya!” Ya fiddo alawar Zanirah a da (Bounty) ya mikawa kowannensu, ya ce, “A tafi wajen Yaya Abdallah ga shi can yana exercise kuma ku yi, ko kwa rage wannan kumburin naku”. Duk suka ware da gudu.
Abu ne da Hajjah ta raine mu da shi wato muddin bako ya zo kowanne iri ne abu na farko da zamu yi mishi shine, ba shi ruwa da lemo. Ban yarda mun hada ido ba har yanzu na yi kitchen na dauko lemon ‘Chivita’ da gorar ruwan ‘Faro’ masu sanyi da kofi na ja karamin center table gabanshi na aje mishi. Baya komi sai bina da ido, kamar yau ya fara ganina.
Na daga gorar ruwan da har raba take don sanyi ina budewa na soma tsiyayawa cikin tambulan, amma kallon da Yaya Aliyu ke bina da shi ya haifar min da karkarwar jiki, na tsula mai ruwan a cinya. Ya mike da sauri ni kuma na saki kofin bisa tayal ji kake taratsatsatsa.....
Muka yi tsaye cirko-cirko kamar zakaru, cikin murya mai sanyi ya ce, “Yaushe Fa’izah ta koma mara imani ne?”
Ban san sanda na saki dariya ba. Duk yadda Yaya Aliyu ya kular da kai sai ya san yadda ya yi ya baka dariya. Na ce, “Ni da imanina bai je ko ina ba. Bari in baka wani”.
Ya ce a harzuke, “Ke look! Bana bukatar ruwanki ba shi ya kawo ni ba. In shi ya kawo ni ai na san hanyar kicin din, kawai Malama ki bani amsar takardata. Da kuma dalilin wulakancin da kike min tsahon wata uku? Tun daga Legas na tako na kawo takarda a baki. An tabbatar min an bakin, to mene ne dalilin kin bani amsa just a single yes or no?
Duka cikin kwanakin aikina nake jele daga Legas zuwa Giwa don kawai na karbi amsar ki amma Fa’izah babu. Anya akwai sauran imani cikin ranki? Na ce kar ki bar Jabi Road sai na dawo daga Giwa, na je na tarar kin gudo nan. Nan din ma ban yi fushi ba na biyo ki kin jike ni sharkaf da ruwan sanyi, anya Fa’iza ke ce?”
Yadda yake maganar cikin sanyi, sai ya yi bala’in bani tausayi.
“Fa’izah magana nake fa?”
“To Yaya Aliyu ba ka zama?”
“Ba a zaman, kawai ki bani amsata, kin amince ayi aurenmu da zarar kin yi graduating?”
Na langanar da kai na ce, “Haba Yaya Aliyu”.
Ya yi murmushi ya zauna, nima na zauna, muka dubi juna, sai muka sa dariya a tare.
“Ke fa shu’uma ce Fa’izah, in mun yi aure zan sha wahalarki”.
Na kau da zancen cikin jin kunya da cewa, “Zanirah fa tana ciki Yaya Aliyu in kirawo ta?”
Ya ce, “In mata me? Ke, ina fa da abin yi, za ki bani amsata ne ko kuwa?”
Na yi rau-rau da ido kamar mai shirin kuka na ce, “Haka ake ba da amsar Yaya Aliyu kamar a fagen fama? Don Allah ka yi hakuri na amsa duka laifuffukana”.
Ya saki rai ya ce, “Ok!”
Na koma kicin na kawo mishi wani ruwan, har da cake da dambun naman kaza ya soma ci yana hararata ina share fasasshen kofin tangaram ina murmushi. Na kammala na koma daki na dauko takarda na dunkule a hannuna na fito.
Zuwa lokacin Yaya ya gama, na ce, “To Yaya Aliyu rufe idonka”. Ya mai da manyan idanunshi ya lumshe zara-zaran gassun girarsa. Ya bude su duka a kaina ya ce, “An ki a rufe, in rufe ki caka min wuka, tunda ba kya SO NA?”
Ido waje na ce, “Lalala! Sharrin da za ka yi min kenan Yaya Aliyu?” Na jefe shi da takardar na yi daki a guje tare da kullo kofar har da murza key.
Zanirah na tarar zaune bakin gado tana rubutu cikin karamin ‘DIARY’ din ta. Tana ganina ta boye shi cikin filo ta mike tana fadin “Fa’izah har yanzu Momi ba ta dawo bane?”
Na ce, “Nima na rasa abin da ya tsare su, amma lokacin dawowarsu har ya wuce tuni”. Ta ce, “Ke da wa kuke ta magana ne haka a falo?”
“Yaya Aliyu ne Zanirah, amma na ji tashin motarshi yanzun nan ya tafi, kina toilet sanda ya zo”.
Jikinta a sanyaye ta koma gadon ta kwanta tana fadin “Zan dan kwanta in samu bacci kafin kiran sallah, in sun dawo don Allah ki tashe ni”.
Wai Zanirah ta dauka kwanciyar nan da ta yi ban san cikin damuwa take ba. Damuwar ce ta yi mata yawa ba ta so na gane shine dalilin da yasa ta zabi ta kwanta din a dalilin dauriya da juriyarta sun kare. Umh! Na fa soma tunanin akwai wani abu tsakanin Yaya Aliyu da Zanirah, kai to mene ne.... kai babu komi.... to mene ne ma zai shiga tsakanin nasu? Oh! Ni Fa’izah! Anya ba son Yaya Aliyu Zanirah take ba??????
“..... Ina kammala makaranta zan kawo mata mijin..... Ki rike Yaya Aliyu da kyau, ki yi mai rikon magnet..... Yaya Aliyu ba irin mazan da ake yiwa rikon sakaka bane..... He has all the qualities and all the attributes to be loved upon.... ina da kyakkyawan zaton cewa, muddin Yaya Aliyu ya zamo miji a gare ki babu ke babu ganin wulakancin namiji da ‘yan’uwa mata ke suffering.... Saboda Yaya Aliyu na daban ne.... domin Aliyu uwa ne, uba ne, aboki ne, dan’uwa ne.... miji ne abin so da duk wata diya amce za ta yiwa kanta burin samu...... Imagine Fa’izah, yadda za ka zauna da wani alhajin zuciyarka da tunaninka, ruhi da gangar jikinka duka suna ga kaunar wani can daban.... Na tuno kalaman Zanirah!
Na tallabi kaina da hannayena biyu sakamakon wata irin kwankwatsa da yake yi min tamkar zai dare gida biyu. Ko da yake an ce az-zannu zambun, wato zato zunubi ne bai kamata in yi saurin gaskata hasashena ba, har sai na ga diary din Zanirah da take boyewa, sai na ga abin da ta rubuta dazu, sai na ga damuwarta ta shekara da shekaru wadda a kullum ke zane a fuskarta. Ko mene ne ni zan yi kokari in magance mata damuwarta in har ba soyayyar Yaya Aliyu bane, zan taimake ta insha Allah ta fita daga halin damuwar da take ciki.
...... Shigowar Walida ya katse tunanina. Ta ce, “Yaya Fa’izah, Yaya Aliyu ke kiranki yana cikin mota zai tafi”.
Duk da ina jin nauyin Aliyu ba zan iya kasa yi mishi sallama ba. Na rufe kaina da mayafi na bishi. Yana zaune cikin mota duka kafafunshi suna waje, ya jingina da makarin kujerar idonshi a runtse.
Har na karaso bai bude idon ba, sai da na kwankwasa gilashin kofar motar ya bude dukkan manyan idanunshi a kaina, sun kada sun yi jajir har sai da na ji gabana ya yanke ya fadi, ko amsar da na ba shi ne ya tayar da hankalinsa maimakon ya yi farin ciki?
Kallon juna muka yi cikin ido na ‘yan sakanni, kafin mu saki ajiyar zuciya a tare. Cikin sassanyar murya ya ce, “Abin da kika fada cikin takarda Fa’izah haka yake ‘heart and soul!”
Kunya ta rufe ni, na rufe ido da yatsuna goma ina dariya......
Ya ce, “Na gode, na gode kin ji Fa’izah. Ina fatan lokacin da na yanke ayi aurenmu bai zamo takura a gareki ba, wato watanni uku masu zuwa bayan kammala jarrabawar ku ta karshe?” na yi shiru.
“Akwai babban dalilin da yasa na yanke wannan lokacin duk da bana so na takura ki, akwai dalilin da yasa na yi hakan”.
Na kara yin shiru idona a kan kananan duwarwatsun da suka rufe harabar gidan, da gaske ne har zuciyata ban shirya aure yanzu ba. A ranar na cika shekara goma sha takwas. A ra’ayina in samu ko karamar Diploma ne in yi kafin aure. To amma bana iya yiwa Yaya Aliyu musu saboda matukar so da kaunar da nake masa, ina son shi fiye da tunanina, fiye da tunanin duk wani dan adam.
Bana iya musa mishi duk abin da ya umarce ni, don ina da tabbacin ba zai yi umarnin da zai zama cutuwa a gare ni ba sai wanda zai amfane ni. Har sau tari na kan ga kamar son da nake wa Yaya Aliyu ya ninka, ya dame ya shanye wanda shi yake mini.
Wani lokacin na kan yi tunanin muddin muka yi aure ba zan iya batawa Yaya Aliyu rai ba ko inyi masa ba dai-dai ba daidai da kwayar zarrah, ko da shi ya bata min abu kadan zai yi ya shafe laifin daga idanuna da zuciya, komin GIRMAN sa.
To amma dole in ji dalilin gaggawar tunda an ce ba a son garaje cikin aure, don gaggawar daga shaidan ce. Kamar wadda za ta gudu? Na ce, “Shin Yaya Aliyu to saurin na mene ne haka?”
Ya saita kwayar idanunshi cikin nawa cike da damuwa ya ce, “Saboda SONKI Fa’izah! Na kai na kawo a sonki da kaunarki da son ganin mun zamo abu guda, na mannu da fatar jikinki which is always hunting my dreams.....”
Na rufe fuska cikin jin kunya. Na ce, “Yaya Aliyu ai ba inda za ni, kullum muna tare. Ina laifin bayan candy da shekara daya? Bani da tunanin kowanne da namiji a duniya sai kai Aliyu Haydar......”
Sai bayan na fada na san abin da na fada. Juyawa na yi zan tafi, Aliyu ya riko gefen mayafina.
Ban juyo ba don haka ban san halin da yanayinsa ke ciki ba, ya ce, “Idan haka ne barshi a yadda na ce Fa’izah, watanni uku masu zuwa”.
“Saboda me Yaya Aliyu? Gaggawa daga shaidan ce”.
“What target do you have for making it longer haka Fa’izah? Wata babbar matsala ke neman fatali da farin cikinmu”.
Ban san sanda na juyo gaba daya ba, na ce, “Matsala? Wacce irin matsala ce Yaya Aliyu?”
Idonshi cikin nawa sun kada sunyi jajir, muryarsa a dushe ya ce, “Kina nufin baki sani ba? To Hajjah ke son in auri ZANEERAH!”
Ji nayi wani abu ya kwashe ni yuuuu! Zai maka da kasa, na yi kokarin kama hannun Yaya Aliyu dake jikin motar gam-gam na rike. Muryata na rawa harshena na sarkewa na ce, “ZA-ZA-ZANIRAH Yaya Aliyu? Haba! Biri ya yi kama da mutum....”
Na durkushe a gabansa kaina cikin cinyoyina, kamar in yi yekuwa a zo a tallafi rayuwata. Shi kansa Yaya Aliyu ya yi nisa a tunani, bai tanka min ba. Kowanne sakar da yake yi cikin zuciyarshi daban da na dan uwanshi. Kafin wata juriya da imani su shigeni ciki da bai dina.
Na dago a hankali idanuna taf da kwalla na ce, “Ka je Yaya Aliyu Allah ya kai ka lafiya”.
Ya dago ni daga durkushen da nake muka fuskanci juna. Don karfin hali irin na Aliyu murmushi ya yi min, nima ban san sanda na mayar mai da lallausar murmushi ba.
“Kada ki sa abin a ranki fa. Everything will be alright. Don Baban Giwa (Barau), Baba Sadi da Baba Ibrahim da Yaya Hauwa basa goyon bayan zancen sam”.
Na yi shiru ban yi magana ba, a zuciyata cewa nake, “Ni da kai kuma Yaya Aliyu ai sai wani babban ikon Allah, wanda in haka ta faru na tabbata na yi asara wadda ba mayarwa”.
Zuwa can na ce, “Wallahi ka je kawai Yaya Aliyu, ni ba zan damu ba”.
“How sure are you ba zaki damu ba.....”
Na ba shi amsa muryata na gab da barkewa da kuka.
“I am sure!”
Ya gyada kai. Ya sanya hannu cikin aljihun motarshi ya dauko daurin kudi ‘yan naira dari biyu sardauna sabbi kar ya miko min. Na bata fuska gab nake da rushewa da kuka, don ji nake kamar sallamar karshe muke yi ni da Yaya Aliyu, kamar babban shinge na shirin shiga tsakaninmu, kamar wata sabuwar rayuwa zamu bude wadda dukkaninmu bamu taba tsammaninta ba.
“Kada ki min musu, ki karba kawai. Ban da yau na taba dauko naira tsurarta na baki?”
Na mika hannu biyu na karba.
“Yaya Aliyu na gode, Allah ya kara budi”.
Ya yi murmushi a cikin kallona ya yi min alama da hannunsa in tafi. Har na juya na soma tafiya ya ce, “Au! Fa’izah!”
Na juyo hawaye shimfide a fuskata wasu na korar wasu.
“Kika ce ba za ki damu ba, to meye na kuka?”
“Ni ba kuka nake ba hawaye ne”.
Ya yi murmushi, “Hawaye?”
Nima sai na yi dariya, ga hawayen fal a fuskata.
“Su zuba kawai suke, kuka kuwa zuciya ke yin sa”.
“Na yarda dake”.
Ya miko hannu.
“Wannan kyakkyawan hankicin na hannunki za ki bani mana?”
Na girgiza kai na ce, “A’a!”
Da mamaki Aliyu ya ce, “Dalili?”
Na ce, “Wallahi haka nan kawai nake son hankicin bana son rabuwa da shi, ina son kamshin sa”.
“Wa ya baki?”
“A dakin su kawata Naja na ganshi a hostel dinsu cikin kayana, wallahi ban san na waye ba”.
“Mu gani?”
Na mika masa ya karanta rubutun (AHUBBIK (I love you!”)
‘WA ANA AIDHAN (me too)” Na mayar masa muryata na karkarwa.
Ya miko min hankicin na juya da gudu na karasa cikin gida, ban san tsawon lokacin da ya diba