Showing 12001 words to 15000 words out of 35375 words

Chapter 5 - Aure Da Haihuwa Book Complete Hausa Novels by Surbajo.txt

30 Nov 2024

1522

Rayhan yaje kofar dakin na safna yace cikin dakewar murya.
"Ki bude kofa ki fito mu tafi kotu Dan yau alkali yabada mu hallara agabanshi ina jiranki a mota"yana kaiwa nan yayi fucewarsa abunsa


Safna jin maganar tayi kamar saukar Aradu,yau itace Rayhan yakai kara kotu?wannan wacce irin masiface.
Tunda ya fada tasan dagaske yakeyi,Dan karya bata daya daga cikin halayensa.


Jiki asanyaye ta janyo hijab tasaka,ta zura takalmi ta fito.bayan ta kulle dakinta.


A motar ta sameshi yana cika yana batsewa,ba me cewa shine Rayhan din ta me yawan murmushi.


A harabar kotun suka samu doctor Amina ma ta iso ita da maaikatan da suka gudanar da aykin.


Karasawa gunta Safna tayi suka gaisa,inda doctor Amina tace"Safna kinga kaddara ko?"
Hawaye ne suka gangaro daga idon Safna masu zafi sannan tace"doctor ina cikin tashin hankali"


Karasowar Rayhan gurin ne ya katse musu hirar,inda ya dakawa Safna tsawa da cewa "wuce mutafi".ba musu tabishi abaya suka shiga cikin kotun.


Bayan kowa ya hallara ne me gabatar da kara yatashi ya gabatar da karar da Rayhan Hashim ya shigar agabanta,yana me kalubalantar doctor Amina,da sauya kwayoyin halittarsa Dana wani ta sawa matarsa,Wanda hakan ya janyo matarsa ta dauki ciki,yana me rokon kotu datasa matarsa ta zubar da cikin,kuma yanaso kotu me adalci da ta bi masa hakkinsa.


Bayan an gabatar da kara ne alkali ya bukaci ganin doctor Amina,jiki asanyaye ta karasa inda aka tanada domun tsayuwar Wanda ake tuhuma taje ta tsaya.


"Munaso ki gabatar mana da kanki"cewar alkali,


"Sunana Amina Galadima,likita,kuma mamallakiyar Asibitin Galadima special hospital"


"Kinji korafin da aka shigar akanki shin haka akayi koko kina da ja game da hakan?"alkali yasake jefo mata tambayar.


"Duk abinda aka fadi ranka ya Dade haka ne,sede ba nice da kaina na gudanar da aykinba, kuma kuskuren suna aka samu ta hanyar kamanceceniyar suna,ina me rokon kotu datai mana sassauci".ta kwashe komai ta sanar da kotu gamida mika takaddu na bincike da kuma duk wani Abu daya shafi dashen tun kan ayi har zuwa bayan anyi,


Alkali ya bukaci maaikatan da suka gudanar da aykin dasu gabato gabansa,suma suka amsa sune suka yi,


Bayan dogon rubutu alkali yafara magana,"Bayan nazari da bincike,wainda ake tuhuma basu wahalar da sharia ba kotu ta gamsu da duk bayanan kowanne bangare,kuskurene babba suka aykata,Wanda dole ay musu hukunci,Na farko,kotu ta yankewa doctor Amina hukuncin biyan Tara ta dubu Dari,bisa laifin daukar maaikatan da suke sakaci da aykinsu,su kuma wainda suka aykata laifin,kotu na umartar da akaisu gidan gyaran hali na tsawon wata guda,ko zabin Tara,ta dubu goma goma"kotunce ta hargitse da surutu,kamin alkali ya tsawatar akai shuru, sannan yaci gaba


"Kotu na kira ga Rayhan da yayi hakuri bisa faruwar wannan Lamari,sabida kotu bazata sa Safna ta zubar da cikiba, Wanda aykata hakan zunubine,kuma shi wannan Abu daya faru,shima kuskuren ne babba, duba da tabbaci da aka samu daga bakunan maaikatan na cewa cikin an sameshi bada kwayoyin halittarka ba,kuma kamin ayi an tabbatar da bata da ciki,bayan anyi kuma baka kusanceta ba seda aka tabbatar da ta samu cikin,hakan ya tabbatar da cewa cikin jikinta ba naka bane,Dan haka kotu ta sallami wannan karar"


Gaba daya kotun ta kaure da hayaniya,Safna kuka take kamar ranta ze fita, wannan kaddara dame tai kama.


Haka ta mike tabi bayan Rayhan din daya fita afusace,


Sede kamin ta karaso tuni yaja motar sa yabar harabar gurin,Dan shi Sam ba haka yaso ba,so yayi asa safna ta zubar da cikin, sannan adaure doctor Amina, amma gaba daya ba hakan akayiba,


Hakanne yasa shi tunanin anya ma kuwa alkalin yasan aykinshi?


Muje zuwa


Surbajo for life.
11/14/21, 12:47 PM - MY MTN 2: ��������
*AURE DA HAIHUWA*
��������


*Zahra Surbajo*


*Inna Ibrahim kime alkhairin Allah yakai miki, ina alfahari da haduwa dake arayuwata.*


*19*


Doctor Amina ce ta karaso inda take ta dafata, da sauri ta waiga taga waye,
Ganinta ne yasa ta rushe da kuka ta fada jikinta tana fadin,"doctor ki taimakeni banason rasa aurena,Ina son mijina sosai"tayi shuru sakamakon kukan dayaci karfinta.


Jan ta zuwa mota doctor tayi sabida jamaa sun fara taruwa akansu,da gudu ta fice daga harabar kotun.


Safna ko se aykin kuka take,har suka iso kofar gidan Rayhan din,bude mata kofa tayi ta fito,sannan tace"gobe zan dawo in mijinki ya fita Dan musan yadda zaa bullowa da abun ki kwantar da hankalin ki"


Jiki ba kwari ta tura kofar get din tashiga ita kuma doctor taja motarta ta bar gurin.


A harabar gidan tasameshi tsaye yana huci,kamar wani maciji,bata bi takanshi ba tayi hanyar shiga ciki,wata tsawa ya daka mata sai da cikinta yayi juyi ta waigo a firgice,.


Tsayawa tayi cak a inda take,har ya karaso,cikin fushi yake magana "Safna koda wasa ban dauka zaki ketare maganata ba,nadauka son da kikemin na gaskene,shiyasa na baki umarnin zubar da ciki amma kika ki,to ni bazan iya zama dake ina kwasar bakin ciki ba,Dan haka zan baki zabi wallahi sede ki zaba ni ko cikin jikin ki?"ya wurga mata tambayar batare da shayin komai ba,


Cikin kuka Safna ta tsuguna agabanshi tafara bashi hakuri"don Allah Rayhan kayi hakuri, kasan ina sonka, wlh nafi sonka akan cikin jikina,fushin Allah ne kawai banason na fada,sakamakon zubar da cikin,don Allah ka fahimceni"ta karasa maganar cikin kuka.


"Zabi na baki malama ni ko cikin jikin ki?"yafadi batare daya tausaya mata ba.


Rokonshi take da duk iyawarta kan yayi hakuri amma fafur ya kafe,ganin bata da mafitane yasa ta mike tsaye ta share hawayen ta tace asanyaye "na zabi cikin jikina Rayhan"


Kallon mamaki yay mata sannan yace "to kije na sauwake miki aurena dake kanki,na sakeki saki daya"ya yi saurin barin gurin sakamakon kukan dakeson kubce masa,yana son matarsa,yayi iya yinsa Dan yaso abinda ke cikinta amma yakasa,shiyasa ya sake ta gudun kar zuciya takai shi halaka.


Safna ji tayi duniyar tai mata nauyi,rasa abun yi tayi kawai seta kife agurin tana kuka,ta jima tana kukan kamin ta rarrashi kanta ta mike,ta shiga cikin gidan,dakinta ta shiga,ta hada kayanta na sawa se Jakarta ta hannu,


Ta janyo akwatin ta fice,daga falon tana kuka.


Shima dake tsaye ta window yana kallonta kukan yake kamar yabita,sede hakan da yayi shine masalaha agareshi.


Tana fita, taxi ta dauka drop zuwa jabi park, tana isa motar Daura ta hau,fasinga daya dama suke jira Dan haka direba yaja motar suka nausa kan titi.


Muje zuwa


Surbajo for life
11/14/21, 12:47 PM - MY MTN 2: ��������
*AURE DA HAIHUWA*
��������


*Zahra Surbajo*


*Kwana biyu bani da lafiya ne shiyasa kuka jini shuru,kuyi hakuri,yanzunma de na daure ne kar shurun tai yawa*


*Page 21*


Bata farka ba se wajen karfe goma,baki ta wanke sannan maimuna tasake bata wani abincin taci.


Bayan ta kammala ne shima jinjirin ya fara kuka alamun yunwa yakeji.a sanyaye maimuna tace.


"Safna kibashi nono yasha tunda ya iso duniya be sha ba fa"


A hankali safna tace "To"
Ta mika hannu ta amsheshi,sannan ta Ciro nonon a kunyace ta bashi,ayko kamar me jira ya cafke yafara ahankali.


Duk da zafin da takeji amma bata hanashi ba,har seda ya cire Dan kanshi ya koma bacci.


Maimuna ta amsheshi sannan ta dubi Safna cikin tausayawa tace"Husna lokaci yayi da zaki nemi uban Dan nan,Dan wanke kanki,daga zargin da ake miki"


Hawayene ya zubo ma Safna sannan tace"a bayanin likitar ubansa ba Dan kasar nan bane, maimuna a ina zan gano shi Nide kawai na dauki kaddara"ta karasa maganar hawaye na bin fuskarta.


"Ki kwantar da hankalin ki,ki bari in kikai arbain seki je gun likitar acan Abujar ta fada miki inda yake "cewar maimuna tana rarrashinta.


A haka sukabar hirar,maimuna ta rakata gida,sabida son ganin kwakwaf matan gidan sukai ta shigowa kallon jinjirin,ayko kan magriba tuni kauyen ya dauka ta haifo Dan larabawa tabbacin shege ne.


Unguwa unguwa akai ta zuwa ganin Dan na safna wacce bakin ciki yasa ta goye Dan tasa hijab ta hana kowa ganin shi.


Haka akai ta tsine mata,masu dungure mata kai nayi,masu dukan kanta nayi wai tayi asarar rayuwa zina da balarabe.


Duk yadda Safna taso danne wannan tozarci takasa,tayi kukan tayi kukan har ta rasa hawayen a idonta ,ko ina ba dadi,har dare jamaa zuwa tsine mata ake,gashi ba Wanda ya hanasu shigowa,


Da misalin karfe daya na dare ta hada ina ta ina ta ta fice daga gidan goye da danta tana kuka batare da tasan ina zata nufa ba, ita de kawai ta fice.


Muje zuwa


Surbajo for life.
11/14/21, 12:47 PM - MY MTN 2: ��������
*AURE DA HAIHUWA*
��������


*Zahra Surbajo*


*Page 20*


Da laasar ta sauka a kofar gidan su,sede dandazon mutanen da ta gani ne a kofar gidan ya daure mata kai,tana kokarin Neman hanyar da zata sada ta ne da cikin gidan taci karo da mutane na fitowa daga gidan dauke da makara da gawa aciki.


Da sauri taja baya, tana binsu da ido,kanin babansu ne karshen fitowa,suna hada ido yace "Safina ya muka ji da hakuri,sabuwa kuma sai yayi,Allah yajikanta"


Safna daskarewa tayi a tsaye tanajin maganar kamar a mafarki,innarta ta rasu,.batasan sanda ta yanke jiki ta fadi agurin sumammiya ba.


Matan dake cikin gidan ne suka hango faduwarta,da sauri sukazo suka dauketa zuwa dakin mahaifiyarta, aka shiga yafa mata ruwa ana mata fifita,ta jima kamin ta farfado.


Wani kuka tasaki me tsuma zuciya, wannan wacce irin rayuwace,miji ya korota asanda take tsaka da bukatarsa,mahaifiyarta ta rasu a lokacin data iso gareta domin Neman mafaka.


Rarrashinta makwabtansu ketayi,dan su kishiyoyin mahaifiyarta ko ajikinsu sabgar gabansu kawai sukeyi.


To haka rayuwa taci gaba da garawa,har Safna ta dauki danganar mutuwar mahaifiyarta,


Matan babanta ne suka sata agaba da tambaya me yasa mijinta bezoba ita kuma bata koma ba shine ta shaida musu komai bata boye ba,


Ayko kan kace kwabo garin ya dauka Safna cikin shege tayi agidan mijinta ya korota,duk inda tabi zunde da munafuncinta akeyi.


Ta rasa ina zata sa ranta taji dadi, maimuna kawarta ce kawai ke tausarta,kasancewar katangarsu daya da gidan da tai Aure.


Rayuwa tayiwa Safna tsada,ga matan babanta ba me bata abinci se ta wahalta masa shima bame yawa ba zaa bata.
Maimuna ke ayko mata wani lokacin.


Tsawon watanni bakwai kenan da mutuwar Aurenta,Wanda tuni cikinta watan haihuwarsa ya kama.


Kullum cikin fargaba take amma ta fawwala Allah,Dan ba me taimaka mata,se shi din.


Cikin dare yau ta tashi da ciwon nakuda,tayi kukan ta kira sunayen matan gidan Kansu zo su taimaketa amma ina ba Wanda yabi takanta,


Cikin hukuncin Allah ta haifo danta santalele ita kadai adaki,gefe ta koma tana kallon shi kwance akasa cikin jini yana ta rusa kuka,yana cilla kafa,


Ahankali ta matsa kusa da akwatin kayanta ta bude ta dauko zani,ta dauki jinjirin da mahaifar duka tasaka aciki ta nannadeshi sabida rawar sanyin da yakeyi.


Jin dumin da yayi ne yasa ya dena kukan,ya koma yayi lub,jin shurun tayi yawane yasa Safna saurin bude masa fuska,ta haska da fitila,ido cikin ido suka hada ita da jinjirin Nata, ko a wasa bata taba ganin jinjiri me kyau irin nashi ba,hasalima tafi ganin irinshi a kasashen ketare.karewa Dan kallo take sonshi na shiga zuciyarta,tana tunanin waye ubansa,


Mikewa tayi dakyar taja wani zanin ta daura,sannan ta bude kofar ta fice rungume da danta.


Gidan su maimuna ta nufa,batare da tsoron komai ba,taita bugawa,har mijin maimuna yaji yazo ya bude mata ta shiga,


Tana shiga maimuna ta fito Dan taji muryarta,tana tambayar ta lafiya.


"Maimuna haihuwa nayi kuma baa yanke cibiya ba,su inna kuma sunki taimakamin"cewar Safna a sanyaye.


Da sauri maimuna ta amshi jinjirin daga hannunta ta kamata suka shige daki.


Reza ta dauko sabuwa da zare, ta yanke jibiyar,sannan, ta kwantar da Dan koda ta fito tsakar gida tuni mijinta yajima da hada wuta ya Dora ruwan wanka,tunda yaji duk hirar tasu.


Kamin asuba tuni maimuna ta kimtsa Safna da jinjirin ta,cikin kayan sanyin danta datake goyo. Ita kuma ta bata kayanta tasaka.


Dumamen tuwo ta bata me zafi,tasa mata manshanu ta bata taci ta koshi.


Allah sarki bingirewa tayi agurin tana baccin gajiya.


Maimuna jinjirin tasa agaba take kallo,tana tasbihi ga Allah sabida irin kyau da kyautata surarsa dayayi Wanda ko a mafarki bata taba ganin halitta me kyansa ba.


Muje zuwa


Surbajo for life.
11/14/21, 12:47 PM - MY MTN 2: ��������
*AURE DA HAIHUWA*
��������


*Zahra Surbajo*


*Page 23*


Share wasu hawayen tayi sannan tace, "iyayena sun rasu mijina ya sake ni,yan uwana kuma sun gujeni,shiyasa na baro gida Dan in je inda zan samu abunyi"ta karasa maganar tana kuka.


Dafata Sarah tayi cike da tausayi tace "mu baki ne a kasarnan taku,watan mu biyu da zuwa nan din,wannan asibitin sabone da Dan uwana yazo ya Gina afadin jihohi talatin da shida da kuke dasu,babban reshen asibitin na Abuja,bamu da mugun nufi akan kowa,inde zaki iya zama damu na tsawon watanni goma masu zuwa mu zamu kaiki gidanmu ki zauna ki kula da babynki, zuwa lokacin zamu San abunyi"ta karasa maganar tana kallon mijinta.
Gyada mata kai yayi cikin nuna goyon bayan shi,yace"Zamu kula dake insha Allahu"


Tsugunawa tayi har kasa tana musu Godiya,cikin kuka,


Dagota Sarah tayi ta rungumeta,tana shafa bayanta.


Fitowa sukayi Sarah rungume da jinjirin, Safna nabinta a baya har zuwa harabar asibitin. Se alokacin Safna ta lura da sunan Asibitin Wanda aka rubuta da manyan Baki.


*FARHAN BIN ABU SARAH SPECIAL HOSPITAL*


"Farhan"Safna ta maimaita sunan aranta,haka kawai taji sunan ya mata dadi,


Mota suka shiga mijin Sarah yaja suka nufi unguwar rimi,layin latatumbai.


Gidane daya gaji da haduwa,fadin tsarin kyan gidan da haduwarsa,zeja lokaci me tsayi baa gama ba.


Safna kanta da suka shiga gidan seda ta tsorata,da ganin kyawun gidan,Dan ko zaman ta da Rayhan bata taba shiga gida me kyansa ba.


Dakin da suka mallaka mata a mazaunin Nata dakine na alfarma, sekace agidan sarauta.


Seda suka tabbatar da ba abinda take da bukata sannan suka barta ta huta.
Safna kan gadon ta haye bayan tayi wanka tayiwa babynta,sun kimtsa,nono ta bashi yasha,ya koshi,kwanciya tayi itama agefen Dan nata tana nazarin fuskar Dan Nata,itade ko idonta ne,amma wani hoton balarabe data gani manne a falon gidan,kamar yana kama da jinjirin ta,da sauri ta kawar da tunanin a ranta.


Zafafan comments samun next page akan kari.


Muje zuwa


Surbajo for life.
11/14/21, 12:48 PM - MY MTN 2: ��������
*AURE DA HAIHUWA*
��������


*Zahra Surbajo*


*masu karanta littafinnan na other groups ina godiya Allah yabar zumunci*


*Page 22*


A gigice direbar motar ta fito bayan ta tsaida motar,tayi kan Safna tana fadin "Ya Allah!!!!"
Mutanene sukayo chaaaa Kansu,aka dago Safna, ko kadan ba numfashi atattare da ita,se jinjirin bayanta dake ta tsala kuka,
Cikin harshen turanci matar data bugeta take rokon mutanen gurin asa mata ita amota takaita asibiti,


Da ike gurin be rabuwa da jamian tsaro,Dan sanda guda daya ne yashiga motar rungume da jinjirin na Safna dake kuka,ita kuma aka kwantar da ita a bayan motar matar taja sukabar harabar gurin.


Tuki take amma hankalinta gaba daya nakan Safna, tana fadin"ya Allah, ya Allah"


Tun kan ta karasa asibitin maaikatan asibitin na harabar asibitin suna jiran karasowarta kasancewar tayo waya atanadi komai.


Duk abinda yakamata shi akayi mata kasancewar asibitin mallakin larabawane,shiyasa komai bisa tsari akayishi.


Tasamu buguwane sosai,wacce ta haddasa mata suma,amma da taimakon Allah zata koma Dede.


Doctor Sarah itace likitar data bige Safna da mota akan hanyarta ta komawa gida bayan ta tashi daga ayki,Balarabiyace ,shiyasa ko Hausa bataji.sede turanci.


Jinjirin Safna ita Dan sandan yaba,sannan yatafi,zama tayi kan kujerar dakin da safna ke kwance tana karewa jinjirin kallo sosai tausayinshi yakamata se turo harshe waje yake alamun yana Neman nono..


Matsawa kusa da safna tayi wacce ke baccin wahala,ta yaye rigarta,ta kafama yaron nonon abaki ayko Yakama har lumshe ido yakeyi.


Wata ajiyar zuciya tasaki,se alokacin taji tadan samu natsuwa..


Seda yasha ya koshi sannan ta cireshi,ta rungume shi a kirjinta.


Wayar ta ce tai kara,da sauri ta daga wayar,dagacan bangaren akace cikin harshen turanci


"Sarah meke faruwa ne,baki dawo gida ba har yanzu?"


Cikin damuwa ta labartawa me tambayar tata abinda ya faru,shima gigicewar yayi ya kashe wayar.


Baayi minti ashirin ba yakaraso asibitin,sosai shima yatausayawa Safna, jinjirin ya amsa dake bacci yay ta kallonsa yana mamakin kyanshi.


Motsawar safna itace ta sa suka yi kanta gaba daya suna mata sannu.


A hankali ta bude idonta, tana karewa inda take da mutanen dake gurin. Kallo.dakyar tace da turanci,cikin muryar mara lafiya"me nakeyi anan?"


Murmushi Sarah tayi sannan tasa hannu tana shafa kan Safna tace cikin kwantar da murya.


"Kinsami accident ne a hanya,shine nakawoki nan"daga haka ta kwashe komai tasanar da ita daga karshe,ta kare maganar da Neman afuwarta bisa bige ta da tayi.


Murmushin karfin hali tayi sannan tace asanyaye"bakomai wannan kaddarace"


Tsawon sati guda Safna ta kwashe a asibitin karkashin kulawar doctor Sarah da mijinta.inka gansu ita da jinjirin ta,awannan lokacin bazakace a asibiti take ba sabida kyau da kumarin da suka yi.sosai Sarah ke kulawa dasu.


Yau aka sallami safna,sede gaba daya Safna batason barin asibitin, sabida bata da gun zuwa.


Zaune take kawai tayi tagumi tana rike da jinjirin ta,tausayin Kansu na Dada kamata.yanzu in sun bar nan ina zasu.


Shigowar Sarah da mijinta ne yakatse mata tunanin,inda tace mata"ki taso mukaiki gidanku muyi musu bayani,ba dadi tsawon sati guda basu da labarinki"


Hawaye ne ya zubowa Safna tasa hannu ta share sannan tace murya na rawa"ni marainiyace banida kowa"


Kallon kallo Sarah da mijinta sukayi,sannan suka maida hankali su kanta Dan Neman Karin bayani.


Muje zuwa


Surbajo for life.
11/14/21, 12:48 PM - MY MTN 2: ��������
*AURE DA HAIHUWA*
��������


*Zahra Surbajo*


*page 24*


Da gari ya waye zaune suke dukansu a falon gidan kasancewar ba ayki ranar.


"Mu baki fada mana sunanki ba bare na babynki fa?" Cewar sarah tana dafa Safna,


cikin murmushi Safna tace"sunana Safna, babyna kuma baayi mishi hudubaba,kasancewar babanshi be tare damu"


Murmushi mijin Sarah me Suna,Taufeeq yayi sannan yace "to ni bari in masa huduba,Dan baze ta zaman jiran babansa kamin yasan sunan shi ba," gaba daya suka yi dariya,Safna ko murmushi tayi tace "na baka damar yin hakan kuma nagode"


Daga haka yadauki babyn yay masa huduba,sannan ya dago yana murmushi yace "na sa masa suna batare danaji raayin ki ba"


"Ba komai nasan me maana zaka sa masa"cewar safna


"Kwarai kuwa me maanane yaci sunan FARHAN,"


Sosai taji dadin sunan,cikin walwala tace"sunan yayi dadi,amma ko meyasa ka zaba masa wannan sunan,naga kamar asibitin Ku ma irin sunan ke gareshi,ko kuna da alaka da me sunan ne?"ta karasa maganar fuskarta dauke da murmushi.


Murmushi Taufeeq yayi sannan yace"Farhan sunane me matukar muhimmanci agareni,"mikewa yayi ya karasa jikin hoton balaraben da Safna ta ke ganin yana kama da Dan ta, ya shafo fuskar hoton sannan yaci gaba da cewa,"ni Dan talakawane,soyayya ta kullu tsakanina da Sarah,wacce takasance ya ce ga prime minister kasar mu,muna son juna,amma munafukai sun shiga ciki sun hana mahaifin Sarah amincewa dani,mun wahala iya wahala,kamin Allah ya turo mana da Farhan, yaya. Agurin matata,Sarah, shine ya fahimtar da mahaifinsu talauci na Allah ne,daga karshe

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login