Showing 15001 words to 18000 words out of 30185 words

Chapter 6 - AUREN TAGWAYE COMPLETE DOCUMENT Book .txt

Unknown   

29 Nov 2024

1280

gudan d'akin yabarta, da wannan tunanin bacci 6arowa yayi awon gaba da ita.


Sanye yake da best da short niker, farare 'kal jikinshi sai tashin 'kamshin turarensa yake me suna *story of love* yanufi d'akin.


Ganin d'akin da haske ya tabbatar mai da Hussaina batayi bacciba, da sallama yashiga jin bata amsaba yasashi dubawa kobata d'akinne, can ya hangota kwance kan lafiyayyen gadonta tanata sharar bacci hankalinta kwance, karsa shiga yayi cikin d'akin sannan ya maida 'kofar yarufe, kafin ya isa gareta ya'karemata kallo, yanda rigar baccin jikinta take sharara ba abinda be bayyanaba na surar jikinta, take yaji wata matsananciyar sha'awarta ta kamashi rage Hasken d'akin yayi tare da kunna masu fitila me sau'kin haske, ya haye gadon ya rungumota gaba d'aya jikinsa.




















Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ» Shoki πŸŠπŸ»β€β™€β›„
[11:06AM, 2/11/2017] Zee Mmn Kd: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*






*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* πŸ‘©πŸ»






Page......................21






A hankali yafara shafa lallausar fatar jikinta, yayinda ya tsinci kanshi cikin wani irin farin ciki marar misaltuwa.
Can cikin bacci Hussaina taji Alamar mutum kusa da ita ahankali ta bud'e idonta, tozali tayi da jabeer Wanda ya lula cikin duniyar 'kaunarta yana aikamata da sa'konni soyayya masu wuyar fassarawa, wani irin dad'i taji cikin ranta wanda ita kanta batasan dalilin hakan ba, 'kara shigewa tayi jikinsa tare da sakar mashi duk wani sashe na jikinta, shikuma yacigaba da sarrafata da kwarewarsa da gogewarsa, Hussaina kuwa mamakin jabeer ne yacikamata zuciya "wai dama haka jabeer ya iya soyayya ya iya salo daban-daban amma lokacin kafin suyi aure yake nunamata shi ustaz ne kullum beda magana sai wa'azi da nasiha.
Da wannan tunanin kawai ta ida mallakamashi kanta, a daren sukasha amarcinsu ranar jabeer yasan Hussaina mace, kuma ba 'karamin farin ciki yayiba na yanda ya sameta cikakkiyar budurwa.


Hussaina kuwa banda kuka babu abinda takeyi saboda zafi da rad'ad'in datakeji, jabeer kuwa rarrashinta yari'kayi, dan wani sabon shau'kin sontane ya'kara kamashi.


Tashi yayi yanufi toilet yayi wanka ya tsarkake jikinsa, sannan yahad'a wani ruwa me d'umi ya dawo ya d'auki Hussaina yanufi toilet d'in da ita, zaunar da ita yayi cikin ruwan dan tad'an gasa jikinta, sannan yafito ya gyara gadon tare da canja masu bedsheets, bayan yagama yakoma toilet d'in lokacin Hussaina tagama wankan zuwa yayi da niyyar ya d'aukota amma saita kauce ta ma'kale kafad'a bataso, be matsamataba tunda ta nuna bataso hannunta yakama suka fito tana taku ahankali, kan gado ya taimaka mata ta kwanta sannan ya 'kuremata a.c d'akin kasancewar lokacin ana zafi.


Komawa yayi toilet ya d'auro wata sabuwar Al'wala sannan yazo ya kabbara sallah, nafila yari'ka jerowa saida yafarajin bacci sannan ya sallame ya dad'e yana kwararo addu'a kafin ya shafa, sannan Yakoma kan gado ya kwanta ya rungome matarshi yanajin wani sabon sonta da 'kaunarta na 'kara kamashi, a zuciyarshi yace "Allah kenan da yanzu bani bane angon dazesha amarci wannan daren yanda Hussaina tanuna tsana da tsangwama agareni batare danayimata wani laifiba, dayake Allah ya nufa nine mijinta yau gata jikina kwance numfashina na gauraya da nata, Allah nagodema....


Da wannan tunanin bacci 6arawo yayi awon gaba dashi.
_{Nikuma Zee danike biye dasu ina kwaso maku labari nace asuba ta gari, *Oya overy body shoki lol*}_




*Washe Gari*
Da misalin 'karfe tara na safiya me napep ya sauke nusaiba 'kofar gidan Ya Jabeer kamar yanda take kiran sunanshi, Hannunta d'auke da wani babban kwando da kuloli masu kyau a ciki, nocking tayi me gadi yace "waye
Nusaiba tace nice "to ina zuwa da Sauri yanufi get d'in yabud'emata 'karamar 'kofa tashige.


A falo ta zauna tanata doka sallama, jabeer ne yafito jikinsa sanye da jallabiya milk colour me gajeren hannu "A Nusaiba kece da wannan safiyar, "nice yaya ina kwana
"Lafiya lao.
"Gashi Mama tace akawomaku, kai amma mungode.


"Yaya ina auntyn tamu mu gaisa sauri nake zankoma na tsaida me napep, tana ciki bari na gayama, yafad'a tare da nufar d'akin baccin nasu.


Kwance ya isketa idanunta bud'e ba bacci takeba, "kizo ga Nusaiba nan tazo Mama ta aikota zaku gaisa wucewa zatayi,


Wani yamutsa fuska tayi "haba tunda safe kuma, nikam ba yanzu zan fitaba kawai kacemata tabari mun gaisa wani lokacin idan tazo.
"Sabodame bazaku gaisa yanzuba tunda tazo,
"Ni kawai fitarce yanzu banyi niyyaba kozan fitane saboda 'kanwarka.
"A'a amma kinsan ba dad'i mutum yazo har inda kake kuma ya bu'kaci ku gaisa kice a'a.


Cikin fushi tatashi zaune tare da d'agamashi Hannu "dakata Malam nifa banison abinda kakemin 'kanwatace dazakace dole saina fita mungaisa da ita da wannan safiyar, kaida take 'kanwarka kaje kun gaisa to kace nace ta gaida gida, banison yawan magana tana kaiwa nan a zancenta takoma ta kwanta.








Love u all my Fan's πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
[11:07AM, 2/11/2017] Zee Mmn Kd: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*






*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* πŸ‘©πŸ»






Page......................22










Duk abinda suke fada kan kunne nusaiba saboda yanda Hussaina take d'aga murya, Haka jabeer yafito jiki a sanyaye cike da fara'a nusaiba ta kalleshi "Halan aunty tamu bata tashiba, idan tatashi a gaishemin da ita nizan wuce,
"Wani busasshen murmushi jabeer yayi dan yasan Nusaibar tajiyosu kawai dai basarwa tayi, "to shikenan Ki gaida Mama ga wannan ki sallami me napep d'in ya mi'kamata d'ari biyar guda tasa Hannu biyu ta kar6a tare dayin godiya sannan tafice a gidan.




Da misalin 'karfe goma jabeer yafito cikin shiri, kafad'arsa rataye da jakar laptop, d'akin Husaina yanufa dan ganin kota tashi, wani babban abin takaici shine yanda yanda ya isketa kwance har yanzu kayan baccine jikinta, batada niyyar tashi.


'Karasawa yayi gab da ita sannan yad'an bubbuga gadon, juyowa tayi ta kalleshi "lafiya Malam,? Ta tambaya cike da rainin wayo.
"Lafiya lao na shirayane zan fita, yakamata ace kintashi ga break fast can Mama ta kawomamu kiyi serving d'ina sauri nake zan fita office muna ayyuka dayawa gashi harnayi latti yafad'a yana kallon had'addiyar agogon dake d'aure jikin hannunsa.


'Kara gyara kwanciyarta tayi tare da juyamai baya, "kaga Malam idan zakaje kayi break d'inka kawai kaje kayi dan naga Alamar yunwa kakeji ni ba yanzu zantashiba dan bansaba kalaci da wuriba.


"Yanzune da wuri kiduba kiga yanda rana ta fito...
"Kaga malam kaje kawai dan Allah banison hayaniya, tafad'a tare da jawo wayarta wacce takashe tun jiya ta kunna.
Message's ne suka ri'ka rige-rigen shigowa, wanda yawancinsu duk jiyan akayoamatasu sakamakon jin wayarta kulle.


Jabeer kuwa falo yakoma ya bud'e kulolin wacce d'aya take d'auke da wainar shinkafa sai miyar alayyahu, sannan gudar kular dake d'auke da farfesun hanta, sai plask shikuma d'auke da kunun gyad'a Wanda yaji tsan-tsar madara yayi fari kal.


Zubawa jabeer yayi a gaggauce yaci sannan yazuba kunun gyad'ar duk da son dayakemashi wanda yasha befi Rabin cup ba saboda saurin dayake.


Jakarsa ya d'auka sannan yafice, Har yanzu Hussaina na d'aki tanajin lokacin dame gadi yabudemar get yafice sannan itakuma tafito.


Kulolin data gani ajiye tashiga bud'ewa, take taji tsohuwar yunwar data tara ta tasomata da sauri takoma d'aki tasheka wanka, tazo gaban mirror ta murza lotion da powder sai man le6e tasama lallausan le6enta sannan tanufi wadrope ta d'auko kaya riga da siket na atamfa tasaka, fitowa tayi tazuba wainar tacika cikinta sannan tabi da lafiyayyaen kunun gyad'a Wanda dad'insa saida ya ratsata har tsakiyar kanta, tana gamawa tami'ke takoma kan three seater ta kishingid'a batare data kauda kayan dataci abincin ba.


Wayarta tajawo tafara karanta text messages farko massage d'in Hafiz tafara karo dashi, inda yake cewa.
_Haba babyna banyi tunanin akwai abinda zesa kirabu daniba, duk irin so da 'kaunar danike nunamaki kin d'aukesu 'karya kinje kin auri wani bayan kinriga kin dasamin bishiyar 'kaunarki a zuciyata, kin yaudareni Kin cuceni kuma kinci amanata, wama yasani ko inmutu saboda 'kaunarki, amma kisani idan har haka ta kasance Allah baze barkiba. Kihuta lafiya *Hafiz*_


Tana gama karantawa wasu zafafan hawaye suka zubo a idanunta, tasa hannu ta goge, tana cewa "ina sonka Hafiz ina 'kaunarka banta6a jin son wani namijiba a duniya bayan kai, ko yanzu ina tare dakai bazan gujekaba komin rintsi.


Sunanshi ta lalubo sannan ta danna kira bugu d'aya ya d'auka nan tashiga bashi ha'kuri "dan Allah kayi ha'kuri Hafiz wallahi ba yaudararka nayiba, har yanzu sonka yana cikin zuciyata ba abinda ya canja, kaine kaja Hafiz da farko na d'auka karabani da budurcina saida naba wani namiji kaina sannan na tabbatar dabahaka bane, kaja na mallamakama wani namiji kaina bakaiba.


"Kada ki damu babyna ni inasonki haka kuma zan iya kasancewa dake akowane hali kike, kedai kawai kicigaba da 'kaunata kamar yanda nike 'kaunarki.


"Kada kadamu babu wani namiji a zuciyata sai kai, tafad'a tana goge hawayen dake fuskarta, to shikenan yimin murmushinnan naki me sanyayamin zuciya, wani 'kawataccen murmushi tasaki kamar Hafiz d'in yana gabanta, wani lafiyayyen kiss yasakarmata ta wayar Wanda yaratsa dukkan sassan jikinta, taji inama kawai taganta tare da Hafiz yanzu ya shayar da ita zumar 'kaunarsa.












Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ» shoki πŸŠπŸ»β€β™€πŸ˜³
[11:07AM, 2/11/2017] Zee Mmn Kd: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*






*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* πŸ‘©πŸ»






Page......................23








Da misalin 'karfe hud'u na yamma me napep ya sauke Zuby 'kofar gidan Hussaina, megadi tafara yima magana sannan ya bata izinin shigowa bayan yanemo hakan daga gurin matar gidan, da dallama zuby tashigo 'kawataccen falon, mutuwar tsaye tayi saboda yanda falon yayi amasifar burgeta, batayi tunanin zata tarar da 'kawarta cikin wannan daular ba tunda taga Auren ba cikin shiri akayishiba.


Hussaina ta katsemata tunaninta ta hanyar yimata "welcome my friend, tafad'a tare da kamo hannu Zuby ta xaunar da ita kan d'aya daga cikin luntsuma-luntsuman kujerun dake zagaye da makeken falon.


Bayan sun gaisa Hussaina ta gabatarma da zuby da ruwa da lemu, nan zuby ta zuba lemun tanasha amma duk hankalinta nakan yanda aka kashe dukiya aka 'kawatama Hussaina d'akinta, nan take wani 'kululun ba'kin ciki yazo ya tsayama Zuby a wuya, a zuciyarta tace "tabbas dole inyi yanda nayi na raba Hussaina da gidannan, idan bansamu Hafiz ya aureniba, zan dawoma jabeer, 'karama jabeer d'in ai dan yafi Hafiz kamun kai da kamala, nasan idan har nayi nasarar rabashi da Hussaina nikuma zanyi yanda nayi ya aureni inyi zamana cikin jindad'i da farinciki nima inhuta da l'ikema yayan masu kud'i danikeyi, muddin idan nasamu nasarar auren jabeer zan mallakeshi kota halin 'ka'ka sannan dukiyarsa sai yanda nayi da ita nima lokacin zan faso gari 'ya'yan talakawa zasu ri'ka likemin kamar yanda a yanzu nake li'kema wasu........
Wani shu'umin murmushi tayi dan lokacin har hangota takeyi zaune a wannan babban falon a matsayin matar gidan tad'ora kafa d'aya kan d'aya ga yan'aiki durkushe gabanta tana bada owk.... _lol_




Zuby ta lula duniyar tunani Hussaina nata faman yimata magana amma ko Alama batajitaba, saida Hussainar ta ta6ota "lafiya 'kawata Tunanin me kikeyi...


Saurin dawowa zuby tayi daga duniyar tunanin data Lula, "a'a ba kome kawai ina tunanin halin rayuwa, yau gidanmu tashi mukayi bamu d'ora tukunyaba ga babanmu bayada lafiya, tana kaiwa nan ta fashe da kuka.


Wani irin tsananin tausayinta Yakama Hussaina dan tasan abinda Zuby tafad'a ba 'karya ko yanayin gidan dasuke zaune kad'ai ya Isa ka gane suna cikin Halin rayuwa.
"Kada kudamu inshaAllah idan jabeer yadawo zansa ya taimaka maku.


Zuby ta'kara fashewa da wani kukan munafunci kamar da gaske "nagode 'kawata Allah saka da Alkhairi, "ba kome 'kawata kada kidamu ai munzama d'aya tafad'a tana bubbuga kafad'ar zuby alamar lallashi.


Suna cikin haka suka jiyo sallamar suduka suka maida hankalinsu ga 'kofar tare da amsa sallamar, Jabeer ne yashigo da sallama, ko kallon inda yake Hussaina batayiba saima kauda kanta datayi gefe tana danne-danne a wayarta.




: Da sauri Zuby ta sauka daga kan kujera ta dur'kusa har 'kasa ta gaida Jabeer da Fara'a ya amsa "Zuby ce yau a gidanmu kice kinzo gun mutuniyar taki kenan, "eh wlh munzo shan manshanun amarya tunda haka akayi Auren ba gayya sai dai kawai mukaji a sama, murmushi jabeer yayi yace "wlh kuwa kinsan Al'amarin ubangiji muma yanda abin yazomaku haka yazo mana, mudai fatanmu atayamu addu'a.
"To Allah sanya Alkhairinsa yakuma bada zamanan lafiya, "Ameen ya amsa sannan ya wuce bedroom.


Saida Zuby ta tabbatar da shigewarsa sannan ta kalli Hussaina "kawata amma yanaga kamar baki murna da dawowar angon naki naga ko irin tarbar nan ta sabbin ango da amarya bakiyimashiba.
Yamutsa fuska Hussaina tayi "ai wannan tarbar sai idan akwai soyayya tsakani akeyinta, nifa yanzu babu soyayyar jabeer ko d'igo a cikin zuciyata, dan wallahi daze sakeni danafi kowa farinciki.


Saida Zuby tad'an razana dajin maganar Hussaina a zuciyarta tace "nifa ta fad'i gasashshiya dan naga Alamar raba Wannan shashar da Jabeer abune mai sau'ki, amma a zahiri sai tadafa kafad'ar Hussaina cikin tsananin nuna damuwa tace "Amma Hussaina sabodame kike son rabuwa da jabeer, yanzu kina tunanin akwai macen dazata samu gwarzon namiji kamar jabeer tayi fatan rabuwa dashi? Amma bansaniba wai hausawa sunce duk wanda ta 'kone rumbunsa yasan inda toka ke tsada..... Bansaniba ko kinada wanda yafishine.


"Yauwa 'kawata anzo wajen, inada Wanda yafi jabeer nesa bakusaba,
"Waye wannan? Zuby ta tambaya.
"hafiz mana, shine namijin da babu wani namijin daze maye gurbinsa a cikin zuciyata.


Wani sanyi Zuby taji ya ziyarci zuciyarta, dan tasan 'kawar tata zatayi ba one ba one, dan kuwa tasan Halin Hafiz sarai baze ta6a Auren Hussainaba, tunda hartayi aure kuma wani namiji ya jusanceta bashiba, dan itama abinda tahanshi aurenta kenan dan tariga tabashi kanta, shikuma tsarinshi baya auren macen da yasani a mace kafin aurensu, yasha fad'ama zubyn haka lokacin datake kwakwar ya aureta, to barantana kuma wacce wani namijin ya kusanta bashiba.


Kallonta zuby tayi, "wow 'kawata nafa manta da wannan guy d'in, gaskiya dole kike rud'ewa ki susuce akansa dan ya matu'kar iya soayayya, ga kuma iya........


Alamar tafiyar dasukaji yasa zuby yin shiru, jabeer ne yafito cikin shigar 'kanan kaya bakin wando da milk d'in riga sai 'kamshin turarensa ke tashi da Alama shigarsa wanka yayi, ganinshi yasa Zuby mi'kewa to 'kawata nizan wuce sai wani lokaci kuma.


Saurin tashi Hussaina tayi "d'an jirani mana, kallon jabeer tayi bako fara'a a fuskarta inason magana dakai, batajira amsarshiba tawuceshi zuwa bedroom, binta yayi daga baya, basufi minti goma da shigaba saiga Hussaina tadawo hannunta d'auke da bandir d'in yan d'ari biyar-biyar Sabbi fill tami'kama Zuby "kawata ga wannan akaima Baba, amsa Zuby tayi hannu na 'kyarma "nagode 'kawata nagode "kada kudamu 'kawata kunzama d'aya.


Nan tayimata sallama ta tafi tana mamakin sakarci irinna Hussaina ace kasamu miji wanda zaka juya haka amma har kana 'ko'karin rabuwa dashi.
Wani shu'umin murmushi tayi tare da cewa "Ni zuby zanyimaki Hankali Hussaina sai kingane ni *Makira* ce (na Fiddausi sodangi) wataran sai kinzo gidannan namiki korar kare......














Love u all my Fan's πŸ’ƒπŸ» shoki πŸŠπŸ»β€β™€πŸ™†πŸ»
[11:07AM, 2/11/2017] Zee Mmn Kd: πŸ‘­ *AUREN TAGWAYE* πŸ‘­
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•ΈπŸ•Έ
πŸ•Έ
*Written & Story by*
*Zee Elkaseem*
*{Mmn khady}*






*Dedicated to All member's group of Ciwon "ya mace* πŸ‘©πŸ»






Page---------------------- 24








*Bayan Sati biyu*
Hassana tana zaune gidan jabeer ne kawai amma babu wata kyautatawa irin ta ma'aurata dake shiga tsakaninta dashi daga 6angarenta.
A nashi 6angaren kuwa be tauyemata komeba, dan ba abinda tanema tarasa, abinci kuwa har jabeer yasaba da cin na restaurant dan ko sau d'aya Hussaina bata ta6ayin girki da sunan faranta ranshiba, kullum sai dai tadafa dai-dai cikinta tazauna taci idan tagama tatashi tabar plate nan, kullum haka zatabar gidan kace-kace hatta da gadon dasuke kwana batasan tagyaraba, duk da wannan abubuwan datakema jabeer amma bata Hanashi kanta idan yabu'kaci hakan, sauran abubuwanma tanayinsune wai kozeji haushi yasaketa amma ko kad'an beta6a nuna alamun ze rabu da itaba sai dai idan abin yademeshi ya zaunar da ita yari'ka mata nasiha,


zata zauna ta saurareshi yana gamawa zatace "Allahu Akbar, kaga Malam idan wa'azi zakayi kaje masallaci akwai masu bu'katar haka dayawa bananba inda bazeyi wani tasiriba, nifa ba dole akayima akan saika zauna daniba idan bazaka iyaba ka sauwa'kemin, ni wallahi da saki a hannuna yake da tuni

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login