Showing 15001 words to 17786 words out of 17786 words

Chapter 6 - Tawa Ta Same Ni Book 3 Complete pdf by Halima Abdullahi k Mashi .txt

ce min big gal tunda yanxu ka daina sona,ya taso
yana dariya yana fadin to ai yarinyar ma tace bata sona
na mata tsufa,na dubeshi idona tam da hawaye nace
kaine za'ace baa sonka bayan kana da kyau da kudi?ya
jawoni jikinsa gaskene wai bata sona nace mata tazo
taga biga gal a gidana nima na fasa,da na kula
tsokanata yake sai naje na kawo miasi abinci.Rigima
kala kala na dinga mishi yana lallashi gami da
zolayata,ya basu kudi masu yawa amma har ynxu suna
nan suna ja mishi rai a cewar su sai sun ja mishi aji
gami da sashi ya sakeni yaje ya basu hakuri bisa
tursasawar mahaifiyarsa nan suka rufe shi da masifa
ita da uwarta bai tanka ba sai da suka gama sannan
yace ni dai ina baku hakuri ne tazo mu tafi,Haj Laure
tace sai ka je ka saki wannan matar taka! Ya mike da
sauri Momi me kike fada?tace nace ka saki Iman, yayi
mata duban kinyi kadan sannan yace Momy ki sake
sabon tunani in har sai na saki Iman Mimi zata koma
gidana to ta zauna dan ko mutuwa da ina da yanda
zanyi da ba zan bari ta dauki Iman ba,zan iya rabuwa
da kowa a ciki harda ku da dai na rabu da Iman, ya
wuce fuuu!!yana fadin in ta ga dama ta dawo in kun ga
dama kar ta dawo, yatafi ya kashe dukkan wayoyinshi
dan ma kar a kirashi.Ina kishingide ina tunanin maganar
Babana da ya ce inyi tunanin irin kasuwancin da zan
fara a bani kudi, sai naji an rungumeni ta baya da sauri
na tashi yaynmu ne yayi wata wawuyar ajiyar zuciya
nace guy lfy?yace sonki ne naji yana son ki ne naji yana
son faso min zuciya ya fito waje, dadi ya kamani nace
guy nima ina sonka ina tuna wata rana zaka iya min
halin maza ka sakeni sai in ta kuka,yace big gal auran
mu yafi auran zobe karfi ya shafi zoben hannuna tun
wanda ya bani yace ki kalli cikin zoben nan me zaki
gani na tsura masa ido(AA)nace AA ne a ciki yace to
Amina Abdulrahman for ever zaki gani cikin zoben ta
baya,kafin na kuma magana sai naji bakinshi cikin nawa
ya mantar dani duniyar da muke.
Mimi ta kalli haj Laure tace gaky momy nifa zan koma
gidan baban Dady tunda kin ga an samu wancan
maganin yayi yazo duk abinda muka ce yayi ni kuma
Iman in shiga ba sai in san yanda zanyi waje da ita baz
Haj Laure tace shikenan tunda kin dage ai sai ki koma
dan dama ni nufi na in karbar miki yanci,da sanyin
safiya munyi lako lako ni da guy dina muna kari sai
mukaji sallama tun kafin su gama shigowa muka gane
su su Anty Mimi,ne nan da nan na ga yaynmu yayi kicin
kicin da rai ya ajiye kofin hannunshi ya ja tsaki, nice na
amsa musu sallamar su gami da gaishe su, basu amsa
min ba sai suka nufi dakin Yayan mu ya yi dakin nima
nayi nawa dakin.Sun danyi fushin su da juna na kwana
biu suka shirya, sama sama take min magana nima
bata gabana, kwata kwata kwananta uku yaynmu yayi
shirin tfy, Haj shi taso ya tafi da Mimi sai yace shi ba
zai tafi da kowa ba saboda wani club zasu siyeshi
kuma bai san yanda abin zai kaya ba, tunda ya tafi ta
tsiri yawo kullum ba ta nan,ni dama ban cika fitowa ba
tunda abinci kowa nashi yake yi,yana kirana a waya
musha hirar soyayya ya sanr dani wani club sun
sayeshi miliyoyin kudi, kafin wata uku kowa ya san
yaynmu yayi kudi gidan su ma ya sha gyara
musamman dakin Hajrshi da dakin Alhj, motoci uku ya
sai musu. Muma ya soma gina mana namu gidan a
malali na gani na fada, tsarin gidan ma abin fda ne sai
da ya turo da kudi kabiru yake gabatar da komai
,yanuwa da abokan arziki aiken kudi da tufafi kowa sai
sa albarka yake.Ranar da zaizo bai fada ba zuwan
bazata yayi,ni kadai ce a gidan Aunty Mimi an tafi
yawon bin bokayen da aka saba, lokacin ko tunanin shi
na keyi sai naji ana kwankwasa kofa cikin faduwar
gaba na bude dan bansan kowane ne ba ina budewa
sai naga yaynmu ban san san da na daka tsalle na
dane ahi ba shima cikin murna ya rungumeni muka
shige cikin daki ya sauke ni akan kujera yace me ya
same ki ne big gal?kinyi wani ciwo ne?naga kin rame?
tunaninka guy shine ya ramar dani ya kuma rungume ni
tare da yan wasanni yana gayamin yayi missn dina a
lot,bai tambayeni Aunty Mimi ba,na shirya mishi abinci
ina fadin ban san kana hanya ba guy dana shirya maka
abinci na musamman amma gobe kace ma abokanka
suzo lunchn ya ce to shi kenan big gal
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Da daddare na shirya mishi farar shinkafa da miyar
dambun nama,yana ci na ajiye mishoi coke mai sanyi
na gwangwani,ya dubeni tun yaushe Mimi ba ta nan?na
ce dazu ta fita bai sake magana ba, muna tare har
goma bata dawo ba na tsuke cikin riga da gajeren
wando ,albarkatun kirjina duk sun fito,hakika kwalliyata
ta firgita guy,dan na lura ya nuna kwalamar shi a
fili,duk da fitar da Aunty Mimi tayi ta mugun bata mishi
rai sai yace big gal zamuje dakina na ce guy dakinka fa
kace me zanyi a ciki cikin zolaya nake magana yace
lada zaki samo ko ba kya so? nace ina so mana amma
sai dai ka goyani,ya ce abu mai sauki zo ki hau ya
duka ni kuma na dane bayan shi muka fita muna
dariya,mun kai tsakiyar falo sai ga Aunty Mimi ta
shigo,ganinmu ya bata mamaki musamman ma da bata
san yaynmu ya dawo ba,jakar hannunta ta fadi shi ko
guy sai yayi tamkar bai ganta ba ya shige dakin shi,kan
katifa muka fada ya nuna min karshen soyayya dama
gashi tunda ya tafi ko yaushe cikin kitsa kaina na ke
yar borno da yar arab suna kawo min kayan harka ga
na Anty Yagana,Mama ma tana aiko min dana ta a
gefe,rudewa yaynmu yayi ya gigita wane irin abu na bai
min ba haka bayan nutsuwa tazo yace big gal dama
kina bina bashi yau kam wannan rana nasa ta a cikin
ranakun tarihi sannan duk wanda nake bi bashi ko nawa
ne ranar yana tafe na dubeshi sai dariya nake yace au
dariya ma na baki washe gari har tara na safe muna
manne da juna yaki i tashi wai sai nayi barci jiya banyi
barci sosai ba,zan shiga da kaina in hada miki ke dai
Allah yayi miki albarka me zakici?na dauka wasa ne
ashe da gaske guy shine yayi mana break shi ya min
wanka sannan nayi kwalliya muka fita sai gidanmu,can
muka samu Aunty Mimi ina zaton kara ta kawo,kwana
biu mun sha soyayya dan guy karshe ne ya iya tsantsar
soyyaya, Aunty Mimi ta amshe shi suna tafke rigima
sosai har yayi sanadin dukanta,bata dai tafi ba dan ya
ce kuma in ta sake fita bai sani ba ta tafi kenan yace
yana son ya tafi dani ne yana tunanin Hajiyarshi ,amma
zai gwada yi mata maganar da na ga bai kuma
maganar ba har tazo na san ba sa'a.bayan tafiyar shi
na shiga laulayi kin gaya mishi nayi ko ya yi waya sai
dai na daure mu sha hirarraki, ko asibiti naki yarda
naje, nayi sa'a wannan karon ya dde sosai dan sunyi
wasanni,ga na Nigeria da zasu yi na gasar cin kofin
duniya,ni kaina ban san ko wata nawa bane amma har
ya fito,Anty Mimi tunda taga cikin sai hankalinta ya
tashi,suka shiga shige shige sai ga Aunty Mimi wai tana
iya cin komai tayi ta lallashina naki karba ta rasa
yanda zatayi dani kamar ta min dura can ta aje kwanon
tace ina zuwa bari in aika direba ya kai dady gidan
Haj..
Tana fita na aje mata kwanon a kofar daki na kulle
kofata, ina kallonta ta window tana juya abincin tana
magana ita kadai, tin da naga haka sai da nayi kwana
uku ban fito ba,ina da komai na a kicin dina.Yau
saturday;zaunenake ina kallon wasansu yaynmu na
karshe, kuma wasane tun karfi ,suna wasa ne
Brazil,ganin yanda Nigeria ke musu wasa ai suka shiga
dukan su da wayo,kusa da raga wani dan Brazil ya
sakarma yaynmu kafa a kirji, nan duka haushi ya
kamani nace kai bari yaynmu ya dawo ni dai gara ya
bar kwallo tunda duk abinda yake nema ya samu, sai
kuma ya kama wata harkar tunda yana da kudi, duk da
ture ture da kuma dukan da suke ma su yaynmu sai ga
shi Allah ya basu sa'a sun lashe kofin,murna ba'a
magana. Mutane suka yi ta bugo min waya suna min
murna,Amira ma daga Yola sun kirani ita da
mijinta,Babana ya kira yayi mana murna,bayan minti
talatin na kirashi yace big gal kin kalli wasan mu ne?
nace dole ne guy mun godewa Allah sai dai wanda ya
bige ka a kifjin nan ya bani haushi, yace ka da ki damu
wasa ne.Patyn da aka shirya musu a Abuja nace zanzo
sai yace kar nazo baya son ana kalle mishi ni,yaynmu
akwai kishi.
Da kyar ya bari na bisu Mami zuwa yola gurin
Amira,cikina sai girma yake ko su Mama basu san ina
dashi ba, tunda sanda muka je Yola bai fito ba sai a
bikin Saudatu suka ganshi, Anty Yagana kece min
watan sa nawa ne?nace ban sani ba suka ce banje
Asibiti bane nace sai yaynmu ya iso jibi bikin saudatun
ma mama na ma waya kuma ta mishi waya.
Haj Yaya zaune a gaban boka tace gafarta malam so
nake ka bani maganin da zamuyi amfani dashi yaron
nan da yazo ya saki amaryarshi ya zauna da yar
uwarshi,Boka yace ai Haj aikin gama ya gama dazu yar
uwarki tazo ita da yarta sun amshi maganin da zasu
kasheshi su zubar da cikin Amaryar su ci gado,Haj
Yaya cikin tsoro tace kuma ka basu Malam?yace na
basu ba aikin kudi bane kuma sun bani kudi sosai,Haj
Yaya da tsoro da mamaki suka hanata magana can
tace to ai malam ni ce mamarshi don dana ne shima,
Bokan mamaki ya kamashi yace ai danki ne?tace dana
ne wllh yace shine kike biye masu kuna mashi asiri
lallai baki da hankali in ya mutu wanene da asara?
Yarta zata auri wani kefa zaki haifi kamar shi?to aikin
gama ya gama sai ki tashi in kinci sa'a basu bashi
wani abinci ba ko abin sha, ki samu ki hana shi
karasawa gidan ma don ko gidan ya taka sai yayi wani
mummunan rashin lfy, maryar kuma in ta tsallaka kofar
dakin cikin zai zube,ke kuma in kika amsa sallamar yar
uwarki Haj Laure to zaki mutu, ai bata bari ya karasa
ba ta tashi da gudu da gaggawa ta isa gida ta daga
murya ta kira Kabir tana fadin Kabir kuna ina ynxu?
Yace na dauko yaynmu ne yanzu mun isa gidanshi ta
fasa ihu wayyo Kabir na shiga uku kada ku shiga gidan
hannunta rike da wayan tana fadin kar ku shiga zai
mutu idan kun shiga ko har kun shiga? yace eh,sai ko
ta fadi sumammiya,Mama ta fito tana salati ruwa ta
shafa mata, sauran kishiyoyin suna tsaye ta farko tana
dubansu sai ta ganta a jikin Habiba nan ta soma kuka
tana fadin ya mutu ko? Suka ce wa? tace yaynsu Haj
Laure ta cuceni sannan ta fasa kuka mai karfi ,cikin
kuka take masu bayani tana rufe baki sai akaga
yaynmu da Kabir don har sun kunna kai cikin gidan
sukayi waya da Haj don haka a rude suka shigo tana
ganinsu tace ka shiga gidan? yace a'a menene? nan
tayi musu bayani, tsaki yaynmu ya ja yace ai gara in
mutu in huta da wannan balain,Hajiyata kin bani
mamaki ya juyo ta ruko shi ina zaka? wllh ba zaka
wannan gida ba yace matata can tana cikin hatsari sai
in tsaya,Mama ta dube shi kar kaje itama Allah zai
kareta,yace haba mmn Sagir daina wannan magana,Haj
Yaya tace Kabir jeka zo da Iman gashi ance kar ta
tsallaka kofar dakinta,yaynmu yana min waya ina
babban kicin ya ce kizo gida ynxu ko me kike kar ki
koma daki na ce cikin tsoro lfy yaynmu? yace ba kalau
ba,kar fa ki shiga daki!ki jira Kabir a waje zai zo.Sai da
ana kwashe komai sannan na fita cikin tsoro kun sanni
da rudewa,duk muna dakin Haj Yaya tana mana bayani
cikin kuka ta soma rokon Mama gafara,Mama tace
dama ban rike ki ba,ta dubeni yar nan kiyi hakuri nace
ba komai Haj,kamar daga sama mukaji sallamar Haj
Laure ba wanda ya amsa mata,kowa yayi shiru tace
Murja! Murja!! Murja!!!
Sai ta sa ihu, kafin kace haka hauka tuburan,nan akayi
waje da ita.can sai ga Aunty Mimi da Dady tana jina
abinda ya faru sai kuka,yaynmu yace wa zakiyi ma
kuka? Na sake ki tunda har kin amince ku kasheni sai
a bar mana gida,Ummanki na gidanku sai kije kuyi jinya
bani dana,ya amshi dady,
Ni da yaynmu duk muna gida bamu koma can gidanmu
ba, Haj Yaya anyi nadama tunda ynxu dakinta nake
kwana, ta hanani naje dakin Mama, yaynmu dadi kamar
ya kasheshi.
Na fito wanka ina zaune a bakin gado ina shafa mai
yaynmu ya shigo sai kallona yakeyi,yace Big gal yau fa
zamu fita ina cikin takura fa masu aikin gidannan har
ynxu ba su gama aikin ba duk kudin da nake turawa
dan a takure nake,
Na harareshi ka kara hakuri guy ina jin kunyar su Haj
Yaya da Mama,yace zan tambayar maki nace kaga ina
da ciki ba zan iya maka komi ba yace ai hakan ma kinfi
bani sha'awa bari haj ta shigo nace a'a guy ba
ruwana.... muryar Haj ta hanani karasawa tace menene
naji ana cewa bari inzo?ya sosa keya yace
am..in...dama zamuje unguwa ne tace ina ce yace ba
nisa tayi murmushi kawai,mun fito na leka nace mama
mun fita,ashe daki ya kama a Hamdala Hotel nan da
nan sai gamu,lallai yaynmu yayi missing dina muna nan
har tara nace mu tafi yace ina zuwa,ya fita can sai
gashi da kaya niki niki ya dubeni yace duba kayane
kala uku da takalma nace na menene yace siyowa nayi
a waffa road don kwana uku na biya na zaro ido su
mama fa da Haj? Yace karki damu ai sun san muna
tare kuma tun da suka bani kesun san me zanyi ba
gama cikina nan ba,nayi shiru kawai.munyi soyayya
mai dadi cikin kwanakin bana zuwa ko ina gara shi in
nace ina son wani abu ya kan fita nema min,ranar da
mukaje gida kunya don kunya na kasa sukuni,yaynmu
kam ko a jikinshi ba wanda yace ina muka je dama
wayata ya kashe ta ma.
Wata na biu a gida 'lokacin yaynmu ma ya tafi ' aka
gama gyaran gidanmu komai na cikin gidan babana ya
zuba mana, Yaynmu yazo muka koma sabon gidan
karshen haduwa ya hadu,kwananmu arbain na tashi da
nakuda naso kada yaynmu ya tashi amma ina da ya
kaini asibiti sam yaki fita daga dakin haihuwar duk in da
nace wash nan sai ya rike mun da haihuwa tazo shi da
likita suna rike dani gam na sukuto yar babyna mai
kama da yaynmu tamkar kwabo da kwabo.
Gida aka maidani dakin Haj Yaya,naga gata ganin idona,
ranar suna yarinya taci sunanta Murjanatu!sai muke ce
mata Haj. Amira dasu Mami duk sunzo mana da danta
Ammar, Amira da tsohon ciki.Bayan suna da sati daya
yaynmu ya koma da niyar yin ritaya daga
kwallo,Satinshi uku da tfy ya dawo,tsam ya rungumeni
zamu kasance da juna big gal,ynxu wane abu zan fi mai
da hankali a kai,nace kana da gurin sai da motoci kana
da manyan stores sannan kana da gidan mai sai ka
zaba.Haj ta shigo ganin muna rungume da juna tace
yau naga ikon Allah kai kana da hankali? jego fa take yi
ke kin zauna ya shigo maki da dan labubun jariri ta fita
sai fada takeyi,nace ka gani guy na bani ya zanyi da
kunya,yace dama zata koro mani ke da na huta da
zaman kadaici,kai mata daya matsala ce dole na sake
aure, nace dan Allah kar ka yi min haka guy yace to ba
Haj tace kar ki shige min ba,nace ai a nan ne amma in
mun koma gidanmu ai ka gane..na daga mishi gira
yace naki wayon sai nayi amarya ya fita nace pls guy.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Kasuwanci,shago babana ya bude min kan titin maf
road,kayan dubai nake saida wa yaynmu ne ke sa ana
kawo min don yaki naje,shi kuma kasuwanci ya amsu
ta ko ina,sannan ya fada harkar siyasa abin da ya
karanta, mutane suka matsa sai ya fito takarar dan
majalisar jiha, ni da ban amince ba sai da kyar,cikin
sa'a ya cinye, lokacin Haj Baby nada shekara,Dady ya
shigo mamy kizo papanmu yace kiyi sauri nace yana
ina?dady yace yana dakinshi nace ina baby haj?yace
tayi bacci a falo nace muje ku kwanta bayan mun
kwantar dasu daki na koma na tsuke cikin riga karama
ko cibi bata kai ba gabamta igiyoyin ne dama
albarkatun gasu nan a fili sai gajeran wando ya dameni
na gyara kaina na sa turaruka, yana bakin gado yana
duba wasu takardu yana duba na yayi jifa da takardun
kan durowa ya mike tsaye sai da nazo daf dashi sai
kuma na daure fuska na juya da sauri yace menene big
gal?nace cikin shagwaba ba kace sai kayi aure ba?yace
wasa ne big gal ba zan iya aure ba ke kadai ce na juya
na rungume shi yace yawwa big gal dina zaki kashe ni
da soyayya ya ja igiyar riga ta sai warware ta baya ya
fada katifa nima na bishi.............Pens Uppp,cewar
Auntyn mashi, Alhamdulillhi,Aunty Allah yakara Basira
da Arziki, yakuma raya zuri'a,saikuma ni dana
rubutamuke nakemuku fatan alkhairi,tsawon lokacin
dana daukan kapin kammalashi nasan lallai na batawa
wasu kamar yanda nasan nima wasu sunbatamin,
saidai ta bangarena nayafemuku inna fatan kuma
kuyafemin.
Jinjina gareku Admins namu,Allah yabar zumunci,Allah
yakara hada kawunanmu. Sakon gaisuwa ga dunbin
Masoya dake min magana, inna alfahari damu,sanna
Dan Allah gamasu kallona abai bai Musamman yayin da
sukamin magana ban amsaba Dan Allah kusani inna
sane daku, wasu lokutan abin kefin karfina, nagode
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347






DOCUMENT CREATED BY
ZAHARADEEN SHOMAR
WHATSAPP 08168575100

4
5
6

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login