Showing 9001 words to 12000 words out of 17786 words

Chapter 4 - Tawa Ta Same Ni Book 3 Complete pdf by Halima Abdullahi k Mashi .txt

shige dakin Haj
Maska, nan muka kwanta katifa daya ni da Jamila ita ta
kwanta dayar,bayan na rufo kofata.cikin dare naji
wayata nata ringin na tashi na san yaynmu ne dan na
sa mishi ringin din shi daban,cikin yanayin barci nace
yaynmu yace iyen ba kice ke barci ma kike?nace to ya
zanyi yaynmu yace ban san nayi kewarki ba sai da
nazo kwanciya gsky nayi missn dinki a lot nace gara
kai ga maman daddy nan, ya juya ya dubi mimi da taki
ko kissing dinta yayi wai tana kishi sai ynxu ya san da
ita,sai yace min mmn daddy jego takeyi nace to ynxu
ga shi gari ba kusa ba bare nazo gareka yace me zan
samu ynxu?nace komai ma yace kiss kafin ya karasa
fadi na mishi yace Allah ya bar min ke kina cikin aikina
haka mukayi ta hira har asuba sannan mukayi sallama
dan haka da nayi sallar asuba sai na koma barci.Goma
na tashi da zazzabi na sha panadol jamila ta mana
Break har ina mata jinjina nace Jamila mama tayi
kokari har kin iya girki?ai ko ina cin dankali sai amai,jiki
yaki ko da yaynmu yayi waya ban sanr dashi halin da
nake ciki ba Jamila ce tayi wa Mama waya, da yake
komai namu yana hannun Kabir sai Mama ta mishi
waya, sai da yazo ya dauki Mama suka zo gidanmu ko
zama ba na iyawa yaya Kabir yace mu je Asibitin da
yaynmu yayi Family Card Garkuwa Hosp, nan muka je
bayan likita ya dubani sai ya bani gado yayi ma su
Mama bayanin ina da shigar ciki sai dai yana bani
wahala,sati na daya a hosp amma su Mama sun hana a
gayama Yaynmu don sunce bai dade da tfy ba, sai dai
duk san da ya kira sai Haj Maska ta dauka tace ina
barci,ranar da aka sallameni ya kira ina kwance akan
gadona na dauka a wahalce nace yaynmu......ya
katseni ke ba wani yaynmu me kike nufi da kin daukar
wayata nace bari kaji wlh ya katseni dama na kirane in
kin ga dama kin dauka ince maki kin kyauta sai dai
dadin abin ba ke kadai gareni ba bare abin ya dameni
sai ya kashe wayar,ni ko da yake bani da lfy ban damu
sosai ba.tun daga ranar bai sake kirana ba nima ban
nemeshi ba,yau lfy gobe ciwo har muka shiga wata na
biyu da rashin lfyr rannan da jiki yaki sai da aka kuma
mai dani Asibiti na sha ruwa leda uku,Kamar daga sama
sai gashi yayi min waya na dauka nace yaynmu ka
huce ne?dan Allah kayi hakuri ka saurareni yace ina
jinki nace sanda kake nema na a waya bani da lfy ina
hosp sati na daya su Akhj sunki a sanar da kai don kar
kace zaka dawo gashi baka dade da tfy ba ynxu ma ina
gadon asibiti yau kwanana uku kuma yau za'a
sallameni,sannan duk tsawon kwanakin da ka dauka
kana fushi dani bani da lfy da sauri yace wanne irin
ciwo ne?nace nima ban sani ba sai dai ka tambayi
yaya Kabir ko Doc din yace to zaki iya jina ko wanne
lokaci mukayi sallama, cikin tashin hankali ya yiwa Doc
waya bayan sun gaisa Doc ya sanar dashi ciki gareni
sai dai yana bani wahala,washe gari na fito wanka
kenan sai na samu mutum a bakin gado,yaynmu ne
zaune ya zuba tagumi da sauri na isa gareshi nace
yaynmu yanxu kazo?ya dubeni hannuwanshi ya bude
naje na shiga jikinshi yace Allah sarki babyna duk kin
rame sai farin ciwo ko?na sunkuyar da kaina yace ina
Haj Maska nace tana dakinta ya su Dady yace suna
gaisheki nasan dai ya fada ne nace bari na samo maka
wani abun yace a'a gurin likita zamu koma dake shirya
na shirya nasa gyale wai nasa hijabi na cire gyalen
nasa hijabina.
Muna zaune gaban likita yace ma likita yana so ne a
cire min wannan cikin da sauri na dube shi ban gane
ba ya dubeni ke ba zaki gabe ba ki jirani,suka fita da
likitan da yake dama abokinshi ne yace Maska cire ciki
ba aikin mu bane sannan kayi kuskure da ka fada a
gabanta yaynmu yace Doc Salihu taimakona zakayi
mahaifiyata ta gindaya min doka mai tsanani akan
yarinyar nan sharadin da ta gindaya min tace na zabi
daya na kuma zaba, na farko tace ko in saki yarinyar
nan wanda sakin da zan mata yana nufin barin gidanmu
da mahaifiyata zatayi (wato mahaifina yace muddin na
saki yarinyar mahaifiyata zata bar gidansa)na biyu ko
ta tsine min na kuskura nabar yarinyar ta haihu,a son
ranta kar na kusanci yarinyar kuma ba zan iya ba tunda
ina tsananin sonta na zabi ba zata haihun ba to ynxu
tun bamu je ko ina ba gashi ta samu ciki,Dr Salihu yace
kaima ka san dole ne tayi cikin tunda ba wani mataki
ka dauka ba sannan zaka cutar da ita in har kace ba
zata haihu ba akwai nau'in zalinci,yaynmu yace naso a
dan dauki lokaci ne sannan na san yanda zanyi na
shawo kanta na san bai kamata nabi son rantaba na
saba ma Allah, amma ina son na ganar da ita a
hankali,Dr ya ce gashi ka soma magana a gabanta yace
wannan ba wani abu zan shawo kanta, ni kam lokacin
na kifa kaina a tebir din likita sai kuka nake yi, cikin da
na kwallafa rai shi ne yaynmu yace a cire min ko da
yake ba mamaki tunda dama yaynmu ba wai yana sona
ba an dai bashi ne,soyayyar da yayi ta nuna min don ya
mori albarkatun kirjina ne,ina wannan tunanin suka
shigo yaynmu ya zo gurina ya kamani muka ida
komawa kan wata doguwar kujera,Na dubeshi fuskata
taf da hawaye nace yaynmu ciremin za'ayi yace kiyi
hakuri kinga cikin na baki wahala nace ynxu ai naji
sauki ina sonshi dan Allah a bar min yace ba ki isa
haihuwa ba ki bari sai nan gaba, nace zan iya dan Allah
ku barmin ina sonshi yace nima ina so to amma dole
ne a cire ai bana so in rasaki ne Iman,na dube shi ya
soma ban haushi nace yaynmu kona mutu in dai gurin
haihuwa ne nayi shahada pls kar ku cire min ina son
babyna,sai na ga yaynmu ya daure fuska gami da
hararata gashi in ya sha mur ko kai wanene dole ka
saurara dan haka sai nayi shiru ya kira likitan ta waya
da yake fita yayi ya bamu guri yazo yace to kazo ka
mata inaji ina gani yaynmu ya kwantar dani a jikinshi dr
Saluhu ya danna min Allura har biu sannan yace mu
dan zauna dan tana da karfi ,lokacin duniya ya isheni
na mike nace ni gida zanje sai jiri duhu ya mamaye min
ido na sulale kasa daga nan ban kuma sanin komai ba
sai dai na farka naga Mama da Haj Maska,sai Yaynmu
dake gefen gadon jina nayi sharkaf da lema ko ban
duba ba na san jini ne na soma kuka yaynmu yazo ya
rike min hannu ina ne yake miki ciwo?ban kula shi ba
mama da Haj Maska suna min sannu nace Mama me
yake zuba a jikina?ta dubeni yau me zan gani ni
Habiba?wannan ai jini ne haka jini ya tsinke sai zuba
kan kace kwabo har na fita hayyacina likitan kanshi ya
rude da ganin jinin dake zuba daga jikina ya ma wani
likitan waya yazo sun hadu su biyu a kaina suka ce su
Mama da Yaynmu su fita,Yaynmu hankalinshi a tashe
yama rasa me yake mashi dadi sai safa da marwa yake
yi a kofar dakin tunanin shi in na mutu shine
sanadi,dana sani da nadama kawai yakeyi dan da ya
san hakan zata faru da bai bi san ran Hajiyan shi ba.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Awa daya,awa biyu,har awa hudu basu fito ba sai da
aka kira magriba Mama ta matso gurin shi tace
Abdulrahman kaji masallaci ana kiran sallah yace mmn
Sagir ba zan iya salla cikin nutsuwa ba gara in sun fito
sai nayi tawa,Mama tace ka daure ka je sai kayi addu'a
kaji ko? Haka nan ya tafi ,yana dawowa sai yaci karo
da Dr Salihi,yace yawwa Maska dama kai na fito nema
ynxu mun shawo kan matsalar da kyar sai dai jini muke
so leda hudu zamu duba,yaynmu yace a'a gani ka
gwada nawa in yayi sai ku diba ko laida nawa kuke so
Dr yace biyu zamu diba a naka yaynmu yace Allah duka
za'a diba haka kuwa akayi Mama tayi ta yima yaynmu
fada wai ya zai kwanta adibi jini har leda hudu?yace
mmn sagir mu dai yi fatan samun lafiyarta haka aka sa
min jini hannu biyu sai da na kwana biu bansan inda
kaina yake ba sai da na farka jinin ya kare sai
ruwa.Dishi-dishi nake gani ban san su waye a dakin ba,
hasalima dakin shiru sai karar fanka a hankali idona ya
soma washewa naga Mama da anty Yagana,sai Babana
da Alhj, sai kuma Malam. Nakai dubana kusa da kaina
Yayanmu ne daf dani da ganin shi yasa komai ya dawo
min sabo a raina nace abin da kake so shi yake
wahalar da kai,hawaye suka shiga yimin zarya sannan
ne yaynmu ya gane na farka da sauri yace Iman kin
tashi ne?ya kamamin hannu su Mama suka zo suna
min sannu gami da yiwa Allah godiya,wasa wasa kwana
na sha daya,Yau monday na fito wanka ina zaune a kan
gado yaynmu ya shigo Mama da Haj Maska suka fita
bayan sun gaisa ya dubeni Iman ya jiki?nace da sauki
fuskata babu walwala yace iman ki min afuwa na san
nine sanadin sakaki cikin wannan halin amma ki min
hakuri bana son rasa ki ne shi yasa,ni dai shiru na
mashi nasan duk dadin bakine yake min yanxu na gane
in mutum yace baya sonka tun farko ba zai taba sonka
ba,sai dai wani abu to shima yaynmu na gane
albarkatun jikina kawai yake so ba wani ni ba dama
nasan ni ba ajinshi bace shishshigi nayi
Ya tabani Iman tunanin me kikeyi ne?na zame na
kwanta hawaye ya soma min zarya abin da yafi bani
haushi yanda har ynxu zuciyata take matukar son
shi,har ynxu son na nan ba zan iya fdama wani ainahin
abinda ya sameni ba,Likita ya shigo bayan dube dubene
aka sallameni sun yanke shawarar Mama ta wuce dani
gida don haka gida muka tafi shi kuma yaynmu su
babana suka ce ya koma,ranar da zai tafi ya shigo
tunda na gaishe shi ban kuma magana ba, ba yanda
baiyi ba in yi magana naki daya matsa min sai na sa
kuka, ya kifa kanshi akan gwiwoyinshi na dube shi duk
ya rame a raina nace duk kai kaja ni ynxu don son da
nake maka zanci gaba da zamada kai baya ga haka da
sai dai ka sakeni ya mike to Iman na tafi sai kin jini a
waya ko motsi banyi ba bare na tashi nace Allah ya
kiyaye hanya yadan dubeni sai kuma ya tafii,Tunda ya
tafi kullum zai min waya sau uku,amma daga gaisuwa
bana kuma magana har mama ta gane sai fada take
min tanacewa ai ba shi ne ya dora min ciwon ba in
kuma cikine ai Allah ke badawa dan ya zube sai na
zargi mijina.Na warke sarai jikina ya dawo nayi kiba
mama tace na koma dakina nace nidai tunda Haj Maska
ta koma Maska sai su yaynmu sunzo zan
koma,watanshi uku da tfy suka dawo saboda zuwan
watan Ramadan nan da sati daya, ina falo ina kallo naji
ana masu oyoyo duk da son ganin yaynmu da zuciyata
takeyi sai naki tashi,dakin Haj Yaya suka yada zango
sai daga baya yaynmu ya shigo dakinmu, na dube shi
kullum dai yana nan dan gaye dashi jikin nan sumul,
yace gimbiya ina gajiya nace kunzo lfy,yace lafiya,ina
mmn Sagir?nace tana Sallah mama ta fito suka gaisa
da har nace ni ba ranar zan koma ba mama ta bude
min wuta dole na bisu, Yaya Kabir yasa an gyara gidan
an share shi,na zauna a falona ya shigo kusa dani ya
zauna nayi kamar ban ganshi ba yace Iman kin canja
min sosai yanzu ba kya kula dani kamar da shiru na
mishi ya jawoni jikinshi tashi muje dakina mu kwanta
nace kayi hakuri ba zan iya kuma kwana dakinka ba,
yace kina hauka ne ko? nace ba hauka yace ya zaki ce
ba zaki kwana dakina ba alhalin ina mijinki? nace
yaynmu ina ganin girmanka kar kasa na gaya maka
magana, yace gara ma ki gaya min dan shiru shirunki
ya soma cutar dani ya cigaba ina matukar bukatarki ba
zan iya jurewa ba, na soma kuka ina fadin dama nasan
jikina kake so hakika iyayenmu sunyi kuskure da suka
zata kaine zaka rikeni amana ashe ba haka bane.......
Ya tare ni wayace miki ban sonki? fadin son da nake
miki kauyanci ne kin gani in za kiyi magana ki daina
kawo maganar so....da kana sona da ba kaini an cire
min ciki ba ina son abina kila ma shi ne kadai kwaina a
duniya tunda baka sona shi yasa baka son hada zuria
dani,yace ba zaki gane bane shi yasa amma ynxu na
yarda komai kika ce ki min afuwa nayi kuskure,shiru
nayi mishi gami da shigewa bedroom.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Har azumi ya riskemu bamu jituwa da shi,yayi
naki,karshe ma ya shareni,ina komai,girki da sauran
aikace aikace, girkin ma nawa nakeyi tana na ta, kowa
ran girkinta ta sama mijinta,duk da yaynmu yana
kokarin ganin kar Mimi ta gane sai da ta gane,don haka
take ta shigewa yaynmu gami dayi min kallon
banza,yaynmu yayi siyayya irin na neman lada su
gero,suga, madara ya aika kowanne gida,wato gidan mu
da gidansu Anty Mimi kai harda babana,haka har sallah
ta gabato ya mana siyayar kayan sallah ya sai ma yan
uwa da abokan arziki sannan ashe ya biya musu
ummara shi da Anty Mimi,ko ita ma bai gaya ma ta ba
sai da abin ya gabato, murna ta dinga yi tana waya
tana gayawa kawayenta da sauran danginsu,ni ko sai
nayi kamar banji taba dama ranar nice da girki,yana
shan ruwa a falona ni kuma na idar da sallah ya dubeni
kiyi hakuri ba zamu je umra dake ba sai wata shekarar
in Allah ya kaimu,bace Allah ya sanya alkhairi na
tashi,da za su tafi yace komai na dangane da abincin
sallah yaya Kabir zai kawo sannan ya bani kudi nace to
ka san dai da sallah zani gida da gidan babana har
gidan kawu malam ya dubeni ban ce ki fita ko inaba,
haushi ya kamani, dama ina ciki gashi sai yayi ta jan
Anty Mimi suna wani soyayya a gabana dan naji haushi
ni ko sai na tashi na basu guri,na dubeshi gsky zanje
yawon sallah tun da nazo gidan nan ban taba fita ba
sai sanadin ciwo kusan shekara sai ka ce matar kulle
yace tun da ba matar kulle bace ki je ai zan ji lbr na
kara fusata nace ba fa siyana kayi ba hasalima ba gori
ba ganina kayi kawai an kawo maka shi yasa kake
wulakantani,yace Zauna ki gaya min me na miki?
kuskure daya na san na miki kuma na baki hakuri ni
nan da kika ganni kece mace ta farko bayan uwata da
na taba ba hakuri kuma kin ki ki hakura dadin abin ba
ke kadai gareni ba,abinda kike rowa ki jika ki sha ga
tsinuwar malaiku da kin bari ma cikin da kike fushi
kanshi da yanxu kin maida wani,raina ya kuma baci na
shige bedroom ina kuka.Tunda suka tafi kullum sai yayi
man waya wata rana in dauki wata rana na ki dauka,
dama dady wajen Haj Yaya suka kaishi,ko shekara bai
yi ba watan shi tara amma yana tfy.Da sallah ina zaune
gida dan ma yan yawon sallah sunxo min sosai Jamila
muna tare da ita tana tayani aikin sallah,shima yaya
Kabir yazo da Zee dinshi,babana ya aiko min da kudi
da kaji har da zannuwa ni da Anty Mimi har da Yaynmu
ranr baba uwa tazo da yaranta biu sun min wuni, Mami
da Amira rana daya suka zo min,mun sha hira har
dare,ita bikinta bayan sallah da Gidadonta,Sallah ta
wuce da kwana goma sha daya yaynmu suka dawo ko
waya bai min ba ranar ina daki ina karanta littattafan
da na ba Amira ta siyo min,na fito zani babban kicin ne
sai naga mutane baje a falo,na tsaya ina mamaki
araina nace lallai yaynmu,ya dubeni yace kin tashi?ko
ba barci kike ba,ko tanka mishi banyi ba.Da daddare ya
shigo ya kawomin tsaraba na ce ya barshi na gode
bana so ga mamakina bai tsaya roko na ba yace to shi
kenan ya dauka ya fita.Satinsu daya suka soma shirin
komawa nace tab ai ko wannan karon za'ayita, tunda
Anty Mimi ta gama makaranta to ita ma sai dai ta
zauna amma barina jira ya kare dan wulakanci sai da
ana saura kwana biu su tafi sannan ya sameni a
bedroom yace ke jibi zamu koma don haka sai ki
rubuta abinda babu,na mike nace to ai nima na gaji da
zaman gidan sai ka maidani ga iyayena ko ka nema
min makaranta sai da ya harareni sama da kasa
sannan yace makaranta ki daina tunanin ta kin gama
karatunki ki tind na baki dama tun ba yau ba na
lallasheki amma kika ce ke aure,dama na ce kiyi kuka
da kanki dan haka ai aure kika zaba shi zakiyi,nace to
haka ake aure?yace tambayi kanki ya juya ya fita na
fada kan gado sai kuka.Shima dakinshi ya nufa yaya
zaiyi da yarinyar nan?shi dai yana sonta tsananin
bukatarta ne ya ke hana shi zama kusa da ita yayi
lallashin ya bi ta fada a banza to wai shi yaya zaiyi
ne,ranar da zasu tafi ko kofata ban bude ba ina jin
yaynmu yayi ta dukan kofar amma naki budewa a raina
kuma na kuduri aniyr in dai ya tafi to zan shiga
makaranta abuna sai dai in ya dawo ya sakeni,Alhj yayi
mashi waya lokacin suna tare da mama yace yayi sauri
yaje fita zaiyi kasuwa yaynmu yace ku tafi inaga sai
gobe tafiyar nan,sai gobe! Alhj ya bukata yacigaba
dama vakuyi bookin jirgi bane?yace nayi bookin din sa
Alh matsala ce a gidan nake son warwareta kafin na
wuce Alhj yace kai da waye?ni da Iman ba ma wata
babbar matsala bace,Alhj yace Iman?to menene?
yaynmu yace ka bari ba wata matsala bace mai girma
alhj yace to tunda ka dage kan cewa ba wata matsala
bace to baka da gsky yaynmu yace ina dai zuwa suna
aje waya mama ta dubi Alhj tace me yake faruwa dasu
iman din?Alhj yace shirmen abdulrahman ne jiranshi na
tsaya yi muyi sallama don jiya bamu hadu ba ynxu na
mishi waya yana cewa warware wata matsala yake son
yayi tsakaninshi da Iman nace wace matsala ce yaki
fada shine nace bashi da gsky,mama tace kar kace
haka tukunna ina zuwa ta fita sai dakinta,layin yaynmu
ta kira tana tambayarsa abinda yake faruwa yace mata
ba komi dama yana sonyi sallama dani ne kuma na
kulke kofa naki na bude,mama tace yayi tfyrshi yace ba
dama na tafi ba tare da nayi mata sallama ba,mama ta
samuAllhj ku saukeni gidan Iman din dan nayi waya da
yaynsu ynxu bansan me ake ciki ba.sai naji waya tana
ringin na tashi na dauka sunan mamana na gani na
dauka nace mama,tace bude min kofa,Jikina ya soma
rawa gabana na gaduwa nace to ina bude kofa mama
ta shigk yaynmu ya biyo bayanta kafin nayi magana sai
jin saukar mari nayi gau!mama ta sakar min gami da
fadin ashe baki da mutunci?kin kama kofa kin rufe
ashe kece ma mijin?haka na koya miki?ko haka kika ga
inayi?ni kam sai kuka nakeyi ta kuma tasowa tana
kokarin cire wayar cd na ruga bayan yaynmu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login