Showing 18001 words to 20639 words out of 20639 words
Chapter 7 - A JININSA YAKE PDF BOOK 2 COMPLETE Writing by Zulaihat Sani Kagara .txt
Ta bi shi da
kallo, sannan ta juya bisa lemu, ta tsura masa
ido,"Menene dalilin bani lemu in sha da tsohon
dare? Kashe ni kuma yau zai yi? Gara ya kashe
ni ma kowa ya huta, shi kenan an raba
gardama." Kwalla suka tsatso mata, ta goge su.
Kan ta tsaye ta kafa gwangwanin lemu ta yi sha,
har ya kare. Tayi zuru gefen gado tana jiran
abinda zai biyo baya. "Yan mintoci kadan ta fara
hamma, idanuwanya su ka yi nauyi. Kafin ayi
haka, ta rasa duniyar da take, nan ta wuce
lauuuuu........bisa shimfida warwas! Minto 10
tsakani ya dawo dakin, ya zura mata ido. Sai
kuma ya ji tausayinta ya kama shi. "Tabbas
kwayoyin nan sun fi karfin jininta ga shi yayi
mata (Over dose)." Ya gyara mata kwanciya, ya
dafa goshin ta yayi addu'a. K'arfe shida na
safiya, ya shigo dakin Zarah rike da carbin sa,
yana ja. Ko gaisawa ba su yi ba, ta ce,"Ban ga
amarya ba, bari in duba ta." Ya ce,"Barci take
yi, tunda ta tashi tayi sallah, ta zube kamar
matacciya." Wayyo, gajiya ce, bari in kyale ta, ta
huta baiwar Allah. Tun da ka yi haihuwar nan
bata yi sukuni ba? Ya zauna kusa da ita ya
ce,"Ke ba kya gajiya da wasa amarya."Ta watso
masa harara ta ce,"Me ye na ka a ciki? Ya
langwabe kan sa a kafadar ta ya ce,"Babu komai
Antin amarya. Ni matsala ta na yi missing din ki
da yawa, yaya bayanin yake ne? Ta janye
kafadar ta, ta ce,"Koma dakin ka yanzun Umma
za ta kwaso ruwan wanka." Turo mata fuskar sa
yake yi kamar zai cinye ta, kawai muryar Umma
suka ji daf da kofar daki tana fadin,"Jama'a, wai
yau ina Nusaiba ne? Yayi zumbur ya suro Ameer
yana girgiza shi," Kai sarkin kuka ne ko? Ka
hana mutane barci da sassafe kuma ka tashi.
Dariya ta kullewa Zarah ciki, da kyar ta kirne ta
ba Umma amsa,"Barci take yi Umma." Ta
ce,"Allah sarki, gajiya ce, komai sa ta ce ita ce
za ta yi." Ta dire bahon wanka Zarah ta miko
mata kujera da kayan sabulu. Naseer ya miko
Bebi, sannan ya tsugunna ya gaishe ta, ya samu
ya sulale ya koma dakin sa. Agogo ya fara duba
wa kafe 7 sau kwata. Yayi kasake yana
tunani,"Kai 'yar mutane fa shiru? Ya tambayi
kan sa. Ya zubara ya fito. Kofar ya murda a
hankalu ya bude. Kwance ya hango ta yadda ya
bar ta, tun kiran sallar farko. Ya shigo ya maida
murfin a natse ya rufe. Ya matso ya shiga
bubbuga ta, "Ke! Tashi! Ba ki san gari ya waye
bane? shiru ka ke ji. Malam ya ci shirwa.Tsoro
ya fara kama shi, bai san lokcin daya haye
gadon ya tarairayi ta ba, ya dan bubbuga kuncin
ta,"Ke Nusaiba! Ke! Can cikin sambatu take ta
surutan da bai san abinda ta ke cewa ba. Tayi
lauuu.....ta fada bisa filo. Idon Naseer fa ya
raina fata. Bayi ya shige ya debo ruwa ya
tarairayo ta, yana shafe fuskarta, yana kira tare
da bubbuga kuncinta. Da kyar ya samu ta dan
budr ido jajur! Ta dube shi,"Ki tashi aka ce, gari
ya waye, kowa sai tambayarki yake yi." Ahaf,
ashe duk surutun banza yake yi, zurun da tayi
ma sa a cikin barci ne. A hankali ya ga idon ya
karasa rufewa. Ya dafe goshi, ya runtse ido, ya
ce,"Na shiga uku.!" Da ya rasa na yi, sai ya
gyara mata kwanciya, ya rufe ta ya bar dakin.
Mota ya dauka ya nufi gidan Yakubu ya dauki
doki ya bazama filin sukuwa yayi ta zagaye, ba
ji, ba gani, saboda damuwa. Ba shi yasan halin
da yake ciki ba, sai da ya ji shi cikin ciyayi yana
birgima. Yayi lamo kamar ya mutu. Wasu
mutane 2 suka dago shi suna tambaya,"Ba ka ji
ciwo ba? Ya mike ya na fadin,"Ban ji, ba na
gode." Ya kar6i akalar dokinsa a hannun su, ya
taka ya haye, nufi Tudun Jukun. Karfe 10 saura
kwata, yake fakin, ya shigo gidan yana fargabar
me zai shiga ya ji? Yana yin sallama kuwa.
Umma ta kwala masa kira. Ya nufi gunta
ajikinsa a sanyaye,"Ga ni Umma."Ta ce,"Nusaiba
barci har tara da rabi, da kyar muka tashe ta ni
da Zarah. Wane irin barci ne haka, yarinya bata
ko iya tsayuwa? Ya zaro ido, ya ce,"Ina take
yanzu? Ta ce,"Tana daki, ta ce kanta ma ciwo
yake yi, shine na ce ko asibiti za ka kai ta? Ya
wuce da sauri, yana shiga falo yayi karo da
Zarah ta fito kicin,"Yayanmu, barcin amarya yau
ya ba mu tsoro, kamar wacce ta sha wani abu?
Tana nan kai na faman ciwo." Tana daki ne?
Tana nan akwance." Ya wuce dakin, ya bude ya
shiga. Tana kwance Idanuwan ta rufe, ya tsaya
kan ta yayi kira,"Ke! Ki tashi aka ce a kai ki
asibiti." Ta bude ido jazur, ta dube shi, wani
sabon takaici ya lullube ta, hawaye suka cika
idanuwanta fal, ta ce,"Na sha magani, ya
daina." Umma ta ce,"A kai ki asibiti, ta so mu
tafi mana." Tayi shiru tunani ya rufe ta, bata
ta6a zaton Naseeer yana kin ta haka ba, sai
yanzu ta tabbatar da bata da makiyi kamar sa.
Shi yasa tunda ta wartsake, ta tantace halin da
take ciki, ita ma ta fara tsanar sa, irin wanda
bata ta6a ji ba. Tayi kuka cikin bayi, ta kuma
roki Allah yayi mata sakayya, idan har akwai
cutarwa a cikin abinda Naseer ya yai mata. Yayi
sauri ya kauda kai, jikinsa ya k'ara la'asar. Ya
kama hanya da sauri zai bar dakin. Zarah ta
kawo kai." Asibitin za ku? Ya ce," Ta ce bata
zuwa." Saboda me? Ta wuce gun ta, "Amarya!
Me yasa? Ta goge kwalla ta ce,"Na sha Panadol
Antina." Ta ce,"Ai yanayin barcin da ki ka yi ba'a
gane masa ba, shi yasa Umma ta ce ki zo a kai
ki."Tayi shiru bata da niyyar tashi. Can ta jiyo
muryar Umma,"Ina Nusaibar? Nan da nan ta
sakko daga gado, ko kafin Umma ta karaso cikin
dakin, ta dauko hijabi. Ya ce,"Kin ce ba za ki
ba?" Za ni Umma, hijabi zan sa." To ki je yana
jiran ki a mota." Suka fito Zara ta rako ta bakin
kofar gida. Ta shiga mota. Suka tafi, babu mai yi
wa wani magana. Sun iso cikin asibitin. Nusaiba
fa ta kafe ta ki fitowa daga mota. Yadda bai ce
mata fito ba, haka ita ma bata motsa ba daga
inda ta ke zaune ba. Haushi ya kume shi, yana
ganin kamar tana son ya rarrashe ta ne." "Lallai
yarinyar nan ta raina ni." Hannu yasa ya zaro
wayarsa, ya danna (Ear piece) yana jin gindan
Rediyon (Queen FM). Ga hotunan Ameer yana
kallo hankalin sa kwance. Kusan minti 30 suna
zaune, ita ji take kamar ta fice daga motar tayi
tsuntsuwa ta ganta gidan iyayen ta. Da ya ga
abin na ta da gaske ne, sai ta buga tsaki. Shi
take 6ata wa lokac, sai ya buga tsaki yayi wa
mota key, ya figeta a guje. Yana yin fakin kofar
gida, ta bude ta fito ta shige cikin gida. Ya bi ta
da kallo, kafin ya ce aran sa,"Duk su Zarah su ja
siyo min raini." Yayi tsaki ya fito ya shiga ciki.
Suna tare da su Umma suna tambayar ta yadda
aka yi? Yana isowa, tana fadin,"Babu komai
Umma, dama maganin barci na sha, don un
sami barci, ashe ya fi k'arfin jini na, amma
Likita ya ce ba komai zai sake ni." Umma ta
ce,"Ai shi ke nan, sai ku kiyaye shan
maganunguna haka kawai. Don Allah kar ki
sake, kin ji? Ta ce,"To Umma." Yinin nan guda,
bata iya cin abincin kirki ba. Saboda tsabar
tunanin kaddarar da Allah ya sauko mata.
Washegari ta tambaye shi zuwa Kaduna.." A
dawo lafiya." Ya ce da ita. Da kan ta ta tuka
motar ta tafi.."Can ta wuni tare da Umman ta,
suna hira ta ji dan sanyi a ranta. Kamar kar ta
dawo ta rink'a ji, shi yasa ta rink'a nuk'u-nuk'u.
Yamma tayi sosai. Abban ta kuwa ya ce ba za ta
kwanan ba. Direba yasa, ya ja mata motar ya
dawo da ita. Shi ya koma a ta haya.
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~ Sannu a
hankali Zarah tayi arba in. Kodayaushe Ameer
na wajen Nusaiba, ita ke masa komai, ta shaku
da shi sosai, kuma tana son Yaron, duk da irin
cin kashin da Baban sa yake mata. Wanda har
yanzu abinda yai mata, yana cikin ranta. Ta sa
ido ta ga ko zai sake kwantawa, amma baiyi
gigin k'arawa ba, saboda shima al'amarin ya
dan sanya shi nadama, bata dai isa ya nuna
mata ba, balle ya bada hakuri. Saboda haka
suka ci gaba da zaman da suka saba tuntuni.
Kwanan Ameer 50 dai-dai, yayi wayo ya kumua
shiga ran kowa. Da asuba Zarah ta farka tana
mamakin irin barcin da tayi. Lallai Ameer ya sha
kuka, bata ji ba. Domin tayi tunanin tun lokacin
da ta bashi nono take barci. Tausayin shi ya
kamata, ta tashi ta dauki shi. Kara bude ido tayi
sosai, don sai taga kamar. Gaba daya jikin sa ya
sandare Tsoro ya kamata, jikinta ya dauki rawa
ta dan girgiza shi, ina rai ya riga yayi halinsa, da
sauri ta diro daga gado tare da shi ta nufi kofar
dakin Naseer ta bubbuga, ya fito ya bude mata.
"Duba Yaron nan ka gani ko motsi ba yayi.
"Inna-lillahi"wa-Inna-ilaihir-raji'un! Haka yake ta
faman fadi yana girgiza shi. Tuni Nusaiba ta ji,
sai ga ta a gigice. Naseer yayi waje da shi, suka
biyo bayan sa, suka dunguma sasan su Umma.
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
Ajininsa yake 2-04
Posted by ANaM Dorayi on 08:19 PM, 20-Nov-15
Under: Ajininsa yake
_______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______
Abba ya kar6e shi, ya rungume a jikin sa ya
ce,"Ku yi hakuri. Allah ya kar6i abin sa."
Nusaiba ta sulale nan hawaye suka tsinke mata.
Zarah kuwa dakin ta ta koma ta zauna bakin
gado tana sallallami. Shi kuwa Naseer kafewa
yayi kai da fata aje asibiti a duba masa Yaro,
k'ila suma yayi. Ya dube shi ya ce,"Hakuri fa za
ku yi Naseer, wannan yaron ya riga ya rasu,
babu abinda za'a iya yi masa. Kujera ya zauna
dabbas! Idanuwansa suka bushe kamas! Kirjinsa
na bugawa.
Abba ne ya iya gayawa duk wanda ya kamata
ya sani. Nan da nan jama'a suka taru. Umma
tayi masa wanka, aka shirya shi, cikin likafanin
sa, suka sallace shi, aka wuce da shi makabarta.
Naseer bai iya zuwa ba, saboda ba zai iya
jurewa ba, yana kallo a cusa masa Ameer cikin
rami. Yana zaune kai cikin guiwa a falon Abba,
ya rasa abinda ke masa dadi a duniya. Ji yayi an
dafa kansa, ya dago a natse, yadda ya bi wanda
ya dafa shi. Alh.Basheer ne a gabansa, yayi
mamakin da bai ji sallamar su ba. Ya mike yana
masa sannu da zuwa, ya amsa, ya ci gaba da
fadin." "Zauna ka ji?" Suka zauna tare, ya gaishe
shi. Bayan yayi masa gaisuwa, ya ce, "Umman
ku ta ce an je kai shi ko? Ya ce,"Sun tafi tun
dazu." Ya ce,"Allah ya kara mana hakurin rashin
sa. Tare muke da Ummin Nusaiba, tana can
sasan wajen Umma." Ya ce,"Bari in je mu gaisa."
Ya mike ya fice. Alhj na masa kallon tausayi.
"Yan mintoci kadan ya dawo, ya sake zama. Bai
iya cewa k'ala ba, har zuwa wani lokaci, kafin
Alhj ya katse shirun,"Naseer! Ya dan dube shi ya
amsa. Ya ce,"Don Allah ka daina yawan tunani,
komai ya sami bawa da izinin Allah. Ba kai kadai
ba ne, Ubangiji na jarabtar bayin sa da masifu
iri daban-daban. Amma idan bawa yai hakuri,
ya jure komai wucewa yake yi, tamkar bai ta6a
faruwa ba. Abinda na ke son ka da shi shine. Ka
k'ara yawaita sadaka da addu'a, domin ita
sadaka tana yaye masifa da damuwa. Sai kuma
hamdala ga Allah. Ko wane yanayi ka tsinci kan
ka, to ka gode wa Allah. Ubangiji na wadata mai
yawan yi masa godiya. Ba wadatar kudi kawai
na ke nufi ba, har da wadatar zucci. Ka sani
idan zuciya ta wadatu da imani, duk abinda zai
zi wa bawa, zai kasance mai mika wuya ga
Allah. Kar ka damu, ka ji? Ya sauke numfashi ya
gyada kai, ya ce,"Na gode." Sun jima. Alhj
Basheer na yi masa nasihohi kafin su Malam
Balarabe da sauran jama'a suka dawo daga
makabarta. Nan ya bar su ya fita,Suka yi
sallama da jama'a, yayi masu godiya kowa ya
kama gaban sa. Aka bar su su 2 da Sageer.
A hakikanin gaskiya Alh.Basheer na son Naseer,
shi yasa duk ya damu da irin halin damuwar da
ya shiga, tunda yayi aure. Yau wannan, gobe
wancan. Shi kuma Naseer na masa kallon duk
matsatsin daya shiga. Alhj ne sila, don haka
babu wani dadin bakin da zai masa. Ya fadi,
kunni yaji, amma aiki da shi ba zai ta6a zama
dole ba. Naseer kenan.
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~
Wata 2 da rashin Ameer. Bikin Sageer da Fa'iza
ya rage saura sati 2, ka na Kausar tsakanin su
sati 1. Watau na sati 3 ya rage. Angwaye da
amare na ta fafutikar shirye-shiryen biki, ita
kuwa Nusaiba wani abu ke daure mata kai, mai
kama da al'amara. Al'adar ta d'if, ta dauke
wata 2 kenan. Ana neman a shiga na uku. Ga
wani ciwon kan safe da take fama da shi, yawan
kasala da taruwar miyau a bakin ta. Bata gane
kan gadon ta ba, ko alama sai dai bata fidda
shakkun ciki take dauke da shi. Ta runtse idonta
tamau? Ta dauki salatin Manzo ta yi wa Allah
tasbihi mai yin yadda ya so." Watau rabon Da,
ya kawo ni cikin gidan nan kenan? Ta dan yi
murmushi, domin take nan ta tsinci soyayar
abinda ke cikin ta.Tana so ta nuna wa Antin ta
alamomin da za ta gane, amma tana jin tsorin
kar Naseer ya sani. Watakila ba zai so haihuwa
da ita ba, tunda baya sonta. Kar ya munafunce
ta da wani abin, ya zubar da cikin. Saboda haka
ta ci gaba da 6oye yanayin ta, babu wanda ya
fahimce ta, illa tsiyar k'iba da Antin na ta
kullum take yi mata. A haka suka sha bikin
Sageer. Amarya ta tare kusa da gidan su Sageer
din, ya kama hayar gida karami dakuna 2, kicin
da bayi. Sageer ya kama angwanci, babu kama
hannun Yaro. Sati da ya zagayo tun ranar
alhamis Nusaiba na Kaduna, ko dama duk ta
kosa ta sami 'yar damar da za ta gida, ta dan
kwana 2. Tana like jikin Umminta, dadi ya ishe
ta, ga madarar Holandia mai sanyi take ta
faman sha, tun isowar ta. Haka Ummi ke cikin
farin ciki ganin yadda Nusaiba tayi k'iba, ta
k'ara haske sosai. Tana ta kallon ta, tare da lura
da yanayin ta, ita kuwa Nusaiba ta k'i yarda
wani abu yanke a bakin ta, kar miyau ya taru,
kamar dai yadda take yi a gida Zariya. Bikin
Kausar yayi armashi kwarai da gaske, angonta
Injiniya Abdul-Malik yayi bajinta. Haifaffen
Unguwar Sarki, amma yana aiki da hukumar
gida da ke Lagos.Ta tare a makeken gidan sa da
ke (Abuja Road) kafin lokacin da za su d'aga
Lagos. Ranar asabar Zarah ta zo, kuma ta so
kwana. Kiri-kiri Naseer ya hana, ya kasa, ya
tsaye da yamma dole ta biyo shi, ya dawo da
ita. Nusaiba kuwa sai da ta kai litinin.
Alh.Basheer yayi ta ciwon baki, yana wa Ummi
fada yana ganin kamar da hadin bakin ta
Nusaiba ta kai Mondy. Karfe 4 kayanta an gama
kintsa su a mota. Direba zai maida ta. Tayi tsaye
tsakar falo tana kallon iyayen ta, kamar kar ta
tafi. Hawaye ya gangaro kafadarta,"Kuka za ki yi
shagwa6a66iya? Ta tsura masa ido, hawayen
suka zubo shar-shar! Yasa hannu ya goge su, ya
sake cewa,"Menene abin kuka? Kin ga kama
hanya ku tafi. Allah ya kiyaye hanya. Ki kula da
kanki da kyau. Kin ji? Ga katon 4 nan na
Holandia, na ce a sa miki a but." Umminki ta
ce,"Yanzu shan ta ki ke yi sosai ko? Ta dan
sadda kai kasa. Yayi murmushi, ya dago
ha6arta,"Haka Umminki ga gaya min, ga ta dai
a tsaye, ko ba ke ki ka gaya min ba? Ta wuce
shi da gudu ta koma gun Ummi, rungume ta. Ya
ce,"Ummita, sai mun yi waya." Kafin ta ce wani
abu, ta bar wajen da gudu, ta fita. Me za su yi,
ba dariya ba, kamar almara ta ga Naseer na
fakin a harabar aje motici. Ta ja tsaya, tana
kallon sa. Mamaki ya ishe ta. Daga bayan ta, ta
ji muryar Abbanta na fadin , "Ah , ga ma mijinta
nan ya zo." Ya zo ya wuce ta, ya nufi wajen
Naseer da ke fitowa daga mota. Da sauri ya
tsugunna. Alhj ya mika masa hannu tare da
sallama. Ya mika na sa yana amsawa. Sannan
suka gaisa, kafin Alhj ya ce,"Ashe za ka sami
zuwa? Ai tun jiya na tambaye ta, ta ce min ka
na da.(Exams), ba za ka zo ba." Kan sa tsaye ya
ce,"Mun fito da wuri, shi ne na ce bari in zo
kawai in dauke ta." "Yayi kyau. Dama fitowar na
ta kenan zu su tafi. Bari direba ya kwashe
kayan, ya mayar but din ka." Ya bude but din.
Direba na juye kaya, shi kuma ya shige cikin
gidan, don gaisawa da Ummi. Ko dama Nusaiba
tuni ta koma ciki, kan ta daure, tana tambayar
kan ta." Wai ashe maza ma sun iya kisisina?
Kurame sak! Suka zama cikin mota, yadda ya
like kunnensa da Ear piece haka ta manne na ta
da sauraren tafisr din Marigayi Sheik Jafar
Mahmud Adam Kano.
(Allah yajikan Mallam Ja'afar na Gadon kaya me
Ahlussuna, tare da iyayenmu baki daya
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100