Showing 6001 words to 9000 words out of 20639 words
Chapter 3 - A JININSA YAKE PDF BOOK 2 COMPLETE Writing by Zulaihat Sani Kagara .txt
ga dama, mu hadu a can ,"Yanzu da gaske
kun dauko yarinyan nan." Haushi ya kama
Sageer, ya rasa me zai ce? Sai yayi tsaki ya
kashe wayar sa, ya ci gaba da tuki. Naseer ya
dubi agogo karfe shida da kusan kwata. Ya mike
da kyar, yayi mika, kansa kawai ya ji ya dauki
ciwo, ba kadan ba. A haka ya fito ya kulle dakin
ya shiga mota, ya nufi (Hanwa Low-cost). A
hanya ya kira wayar Umma, ya shaida mata
bakin sun iso. Nan da nan aka shirya kayayyakin
abinci kala-kala. Bus guda tare da 'yan tar6ar
baki suka tafi. Naseer na isowa. Jeep din Antin
Jordan na fakin. Ta fito da yaranta, wajen ta ya
nufa, ya dan rankwafa, yana mata sannu da
zuwa. Bakinta har kunne, ta bubuga kafadar sa.
"Angon Nusaiba. Angon Zarah. Ina ka shige, na
yi neman duniya, ban gan ka ba? Ya shafi k'eya,
ya ce,"Kira na aka yi nan Zariya, dole na dawo."
Anti ta ce,"Haka wannan abokin na ka ya ce,
"Dama an daura aure, ban ga ango ba, ko sau
daya, shi yasa na tambaya. To Allah yasa
albarka." Ya ce, "Amin." Ta wuce ciki, shi kuwa
ya wuce wajen su Sageer. Yana wa Allah godiya
da karyar sa ta zo dai-dai da wacce Sageer yayi.
Karfe 9 saura kwata aka kawo Zarah, a lokacin
bakin Kaduna duk sun juya, wadanda suka rage,
ba su fi mu2m 10 ba. Antin Jordan da kan ta, ta
jagorance su zuwa sashin Zarah. Bayan yan
kawo amarya sun gama ba ido su abinci, motoci
suka koma da su gida. Aka bar mu2m 3, suka
taya ta kwana. Haka ma Zarah ba karamin
mamaki ta sha ba da ganin dakin auranta. Ko a
mafarki bata ta6a tunanin irn sa ba, saboda
haka ta kwana yi wa Allah godiya tare da rokon
sa zaman lafiya dauwamanme. Washegari
safiyar lahadi, karfe 9 za'a gudanar da hawan
Yakubu. Sukuwa ta musamman wacce Yakubu
ya shirya. Filin sukuwa ya ci ka fal da Zaratan
'yan wasan tseren Polo daga ko'ina 'yan kallo
kuwa babu masaka tsinke maza da mata.
Alh.Basheer da tawagar sa ma suna wajen.
Tsofaffin 'yan wasa irin su Yakubu da shi kan sa
Yakibu su suka fara sharar fage, inda dokin
Yakubu yayi wa saura fintinkau. Daga nan
sukuwa ta ci gaba. Kowa na nuna bajintr sa,
abin gwanin sha'awa, sai wanda ya gani. Karfe
11 dai-dai, rana ta soma zafi, wasa ya zo
karshe, kamar yadda Yakubun ya shirya. Ango
shine zai rufe fili, don nuna farin cikin sa ga
dimbin masoyan sa da suka taru. Saboda haka
Yakubu ya mike ya dau lasifika yayi wa ango
kirari, ya kwarzanta shi, sannan yayi kiran sa,
"NASEER, ta so ka ja mu je! Yana mike wa, duk
wuri ya yamutse da hargowa da tafi, shi kuwa
kansa ne ya ji yana sara ma sa. Domin duk
lokacin da aka kira shi angon Nusaiba, ya kan ji
jinin sa ya k'ara hauhawa. Ya tsaya gaban dokin
da ya saba hawa, ya cire kuben da ke kan sa.
Yakubu ya dora masa ta kwano. Ya taka ya haye
doki. Ji ka ke tafi, ta ko'ina. Yayi karfin hali, ya
daga hannayen sa sama, yayi gaisuwa ga kowa,
sannan ya tsala wa doki bulala, yayi haniniya ya
zura a guje. Naseer fa bai san abinda yake yi
ba, gudun kawai yake yi kura na tashi., Rayuwar
sa gaba daya cikin kunci take har ya kan kai ga
lokuta da dama yana mancewa da tunaninsa.
Abinda ya faru da shi kenan a halin yanzun. Ya
sakarwa dokin sa linzami, ba san irin gudun da
yaje yi ba. Ai kuwa ba a jima ba, kafafuwan
dokin suka sarke, yayi haniniya, yayi sama, me
jama'a za su gani? Ango ya watso k'asa
warwars! Wuri yayi tsit!Na 'Yan dakikai, sannan
gaba daya jama'a suka dauki salati, yayin da
tuni jama'a da ke kusa da wajen, suka yanyame
shi. A sume suka wace da shi asibiti. Ba 6ata
lokaci aka kai shi (Emengency). Kowa ka duba,
hankalinsa tashe yake, musamman da Likita ya
ce yana da karaya 2, a hannun sa na dama.
Alh.Basheer zufa kawai ke keto masa, fadi ya
ce, "Inna-lillahi"Wa-Inna-ilaihir-raji'un! Ana cikin
halin haka, su Malam Balarabe suka iso, ba'a
jima ba Jeep din Antin Jordan ta aje su tare da
amare. Kowacce ido warwaje, ta sha kuka. Ba su
ma yi kuka ba, sai da suka ga angon su
magashiyyan a kwance, bai san halin da yake
ciki ba. Antin Jordan kuwa tunda ta iso ta tsinke
da fada, kamar ta ari baki, wai me yasa za'a
bar ango yayi sukuwa? Duk laifin na su Alhaji
ne, haka take ta fad'a. Sam ta mance haka
Allah ya kaddaro. Bai farfado ba, sai la'asar, ya
sha mamakin ganin sa a gadon asibitin. Wani
sabon bakin ciki ya sake turnike shi. Wannan
wace irin masifa ce?
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
Ajininsa yake 2-02
Posted by ANaM Dorayi on 11:41 PM, 11-Nov-15
Under: Ajininsa yake
_______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______
.
.Gaba daya an gur6ata masa rayuwarsa? Take
nan ya kara tsanar Nusaiba, ba wai a zuci ba ya
kadai ba, har cikin jinin jikinsa yake jin bai
sha'awar zama tare da ita...Lallai iska na wahalar
da mai kayan kara, domin Alhj ba karamin
hidima ya sha ba a asibitin nan da kudin mai
dorin gargajiya. Angwanci dai ya dawo asibiti.
Anan abokansa da suka zo daga nesa suka yi
bankwana, suka koma zukatan su cike da
tausayin Naseer. Baya magana da kowa, illah
iyaka eh, ko a'a, ko kuma ayi masa sannu ya
amsa. Hatta ita kan ta Zarah kallon ta kawai yake
da ido, domin haka ya fiye masa kwanciyar
hankali, kar a gane da ita kadai yake magana.
Kwanansa 3 a Shika. Likita ya gama tabbatar wa
Alh.Basheer babu wani rauni a jikin sa, sannan
aka sallame shi. Aka dawo da shi gida. Haka suka
wuni kar6ar baki, a cikin su harda su Lubabatu,
Hauwa'u da Maryam, watau mutanen Zarah na
makaranta. A daren wannan rana Zarah ta feso
wanka, ta sa wani dan karamin dinkin atamfa riga
da siket, ta fito ta leka sashin Nusaiba, ita ma
wankan ta shiga, saboda haka ta wuce sashin
Naseer. Bisa kafet ta same shi zaune, ya jingina
da bango, idanuwansa rufe suke, sallamar da ta
yi. Shi yasa ya bude idon, yana kallon ta har ta
zo kusa da shi, ta zauna. "Yayana tashi ka yi? Ya
ce,"Na gaji da kwanciya, jiki na duk yayi tsami."Ta
dan dube shi, ta ce,"Sannu yanzu me za ka ci? Ya
dan kada kai,"Ban jin yunwa." Suka yi dan shiru
'yan dakikai, ta dago ido ta dube shi. Ita shi ma
yake kallo, don haka tayi dan murmushi, ta sauke
na ta idon. Hannun sa ta ji ya riko na ta, jikin ta
yai sanyi, ta kasa motsi." "Zarah!" Ya kira ta a
wata siga mai taushi. Kunya kawai ta ji ya lullube
ta, ta kasa duban sa. Ya kara kwantar da muryar
ya ce,"Ki dube ni, na ce, ni ba angon ki bane? Ko
don kin ganni a karye? Hannun ta daya, ta dan
kare baki, tana murmushi. Ya kara runtse
yatsunta ya ce,"Kin ga irin ta, ba don kun jawo
min ba, ai da tuni na kauda wannan kunyar." Ya
kara bata kunya, kamar ta tsere. Ya jawo ta, ta
matso shi sosai, ya rungumo kafadarta ya ce,
"Zarah kullm ina yiwa Allah godiya daya ba ni ke,
saboda ke kadai na ke so a rayuwata. Sai dai
yanayin da na ke ciki, ya zame min wani jarabci,
wanda na ke ganin sai kin taya ni addu'a. Allah
ya kawo min iyakar sa. Allah yana gani, kuma ya
ga abinda ke zuciya ta, tamkar kan k'aya na ke
cikin gidan nan. Saboda haka na ke neman hadin
kan ki, ki taimaka min kullum ki kasance tare da
ni, domin ke kadai ke yaye min bakin cikin da ke
rai na."Ta sauke numfashi, cike da tausayi, ta
dan dube shi ta ce,"Kullum ina tare da kai
yayana, na sha gaya maka, ka daina damuwa. Ka
kuma daina daukan wannan aure a wani matsayi
na daban, face hadin Allah. Ba ka san abinda
Ubangiji ya 6oye a cikin sa ba. Ba wai ba na
kishin ka ba ne, ko alama ba haka bane. Ban ki
in kasance ni da kai a gidanka ba, amma na yi
imani da cewa, duk wanda zai yi jayayya da
shinrin Ubangiji. Tabbas yana tare da wahala, ga
kuma tarin zunubi. Domin daga nan ne mutum
yake fadawa muguwar hanya, saboda bakin kishi.
Na san ka na so na yayana, amma ka sa ni.
Nusaiba ma amanar ka ce." Shi fa ba ya ma ko
son ya ji an ambaci wannan sunan, sai ya ji
kamar ya kurma ihu. Yayi ta maza saboda Zarah
da ke kusa da shi. Ha6arta ya dago ta dube shi,
yayi murmushi sosai, ya ce,"Na ji maganar ki,
kuma zan yi iya kokari na. Abinda ba na so kawai
a rink'a saurin kama ni da laifi.." Ta ce,"Kamar
yaya? Ya kada kai, ya ce,"Wannan sirri na ne, ba
zan fada ba, na samu ana kallo na, kunya ta sa a
daina. Kinga na yi wa kai na." Ta sa hannu ta
dan buge hannun sa da ke ha6ar ta, ta kauda
fuska, tana 'yar dariya. Shi ma dariyar yake yi, ya
sake juyo fuskar ta, ya jingina gashin sa jikin na
ta, ya ce,"Kin min alkawari kullum ki na tare da
ni, me yasa za ki kauda min fuska? Ta kwantar
da ido k'asa, bata tanka ba." Kin sa tayi 'yan
sumbatar kuncinta,"Da ke na ke magana." Ta
ce,"Bari in kira amarya mu shirya yadda za mu
rink'a girki." Ta yunk'ura za ta mik'e, ba tare da
ta ji ta bakin sa ba. Hannun ta gam!Ya rike shi.
Ta juyo dauke da murmushi ta ce, "Don Allaj bari
in kira ta." Ya lumshe ido, yana girgiza kai,"Ban
ce ba." Ta dade tana kokarin kwacewa, amma ta
kasa. Motsin bude kofa suka ji. Tare da sallama,
ta dage da karfi ta fizge hannun a lokaci guda,
shi ma ya sake ta yayin da Nusaiba ta kawo kai.
"Bata fahimci komai ba, domin Zarah a tsaye
take. Shi kuwa dan gogan tuni ya dauke kai cike
da haushin Nusaiba, ta katse masa hanzari." Ke
za ni kira amarya, na lek'o dazu ki na wanka."
"Ta ce,"Ni ma na shiga, ina ta sallama, na ji
shiru. Ya jikin na sa? Na gan shi a k'asa ne." Duk
suka zauna suka sanya shi tsakiya. Zarah na
fadin,"Ni ma na shigo, na gan shi zaune ana. Wai
ya gaji da kwanciya." Ai da gajiya, kwanciyar."
Koma yau da bango ya jingina, ya rufe ido. Ta
ce,"Sannu." Da kai ya amsa. Ta mike ta dauko
filo, ta tsugunna gabansa,"Dan daga in sa maka
filo, zai fi maka dadi." Yayi shiru kamar ba i ji
ba.Yayin da Nusaiba ke fadin,"Shi ke nan gara da
ka sa baki. Da su Antina za'ayi min wayau." Ya
kalle ta a dage ya ce,"Kyale ta kawai, tashi ki tafi
abin ki." Ta kuwa mike za ta wuce, Zarah ta
rikota,"Wai sai ki tafin kuwa? Ta ce,"Me zan jira
Antina? Ai na yi ma ku hira, yakamata in je in
barci." Karfe 9?" "Eh mana. A kwanta da wuri, a
tashi da wuri." Fuska yamute ya ce,"Don Allah ki
kyale ta, ta wuce mutun na jin barci a hana shi?
Tana can tana kallon Naseer, ya 6ata rai ba sauki,
Nusaiba ta zame hannunta,"Allah ya ba mu
alkhairi. Yayanmu Allah ya karo sauki." Amin." Ya
fada a fizge. Ita kuwa Zarah ta kasa ma motsi
tayi. Tana kallo Nusaiba ta bar dakin. Dariya ya
kamayi, ganin yadda Zarah tayi sukuiti duk jikinta
ya mace." Ta nuna shi da yatsa ta ce,"Ka daina
sa mana baki idan muna magana." Fuskar ta
kunshe da shagwa6a. Dariya ya ci gaba da yi
mata. Suka ci gaba da hira. Karfe 11 da kyar ya
bar ta ta koma dakin ta, ta yo shirin barci ta
kulle dakinta, ta dawo wajen sa.
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~ Bayan kwana 2. Nusaiba
ta kar6i girki, a ranar kuwa gidan cike yake da
baki da 'yan dubiya har da iyayen su. Tare suka
hada suka yi girke-girken abincin su kuma tare
suka ji ta kula da bakin su.Kamar yadda suka
saba gwanin sha'awa. Zarah ta gaji tu6us! Don
haka tana yin ishha'i, tayi wanka ba ta jira komai
ba, ta bi lafiyar shimfidadden gadon ta, babu
6ata lokaci, barci ya sace ta. Nusaiba kuwa bayan
ta gama shirin ta, sashin Zarah ta soma zuwa,
kofar falon na garkame. Ta tsaya kame da
ha6a,"Ba dai hat Antina tayi barci ba? Lallai
Antina." Ta jinjina kai ta wuce wajen Mai-gidan.
Yana kwance, gaba daya dakin yayi masa
bakikirin. Babu abinda yake tunani illah Zarah,
abinda ke 6ata masa rai kuwa, yai ba ita zai gani
a dakin sa ba. Ko sallamar ta bai iya amsawa ba.
Ta zauna gefen gadon, tana fadin,"Ka san wani
abu? Wai Antina har tayi barci." Ya baki taso ta
ba? Ta kulle kofar falon ma Ya ce,"Yayi mata dai-
dai. Daga nan bai sake cewa komai ba, nan ya
bar ta zaune, a zaton ta ma barci ne ya sace shi.
Yana jin ta, ta rufe shi, sannan ya kwanta, sai da
tayi barci, ya jawo filon sa, yasa kasa ya dawo
nan ya kwanta. Karfe 2 dare, ta farka, don yin
sallar dare. Can ta hango shi bisa kafet Mamaki
ya kamata. Ta sakko ta tsaya kan sa tana kallo.
Kamar ta tashe shi, wata zuciya ta ce ma ta kila
ya fi son kwanciyar kasa ne. Don haka ta wuce
bayi, ta kama ruwa, ta yi alwala ta fito. Motsin ta
ya farkar da shi barci, amma san bai bari ta gane
ba. Ta daura zani, ta dora hijabi ta haye sallaya
ta fara sallah. Shi kan sa ta burge shi, da zai fadi
gaskiya. Ta jima bisa sallaya tana addu."a kafin
ta mike, ta nufo gunsa ta tsugunna. Yadda ya
kwanta a yaye babu lullubi, sai ta ga kamar sanyi
yake ji, don haka ta mika hannu ta janyo bargo
ta sake lullube shi. Ta koma gado tayi kwanciyar
ta. Naseer yayi shiru ya rasa me yake sakawa a
zuciyar sa. Har asuba bai koma barci ba, haka
kuma bai daina sake-saken iska ba cikin ransa
ba. ~~~~~~~~~~~~~~~~~~
Tsawon wata 1, Naseer yana samun kulawa wajen
amaransa da wacce yake so da wacce bai damu
da kulawar ta ba. A son ra'ayin sa ko sannu baya
buk'ata daga gare ta, shi yasa kullum yake jin sa
kamar bisa k'aya cikin gidan nan. Kuma bai san
dalilin da yasa kodayaushe k'ara tsanar Nusaiba
yake yi ba, duk da bajintar da suke nuna masa
ita da iyayen ta. Wani lokaci har tsoron zuciyar sa
yake ji, ta yadda ko alama ta k'i amsar Nusaiba.
Hannun sa yayi sauki sosai, domin har ya kan fita
ya je wajen iyayen sa, ya gaishe su. Bai ta6a
shiga sabuwar kerarriyar Jeep din sa ba, wace
Alhj ya sake masa, sai da Zarah ta goranta masa.
Shagon dinkin Sageer ya iso yayi fakin ya fito duk
jama'ar wajen idanuwan su akn sa. Idan ka dube
shi sai ka rantse da Allah wani hanshakain dan
kasuwa ne. Gaisuwa jama'ar wurin ya rinka
amsawa, sannan yayi sallama shagon. "Allah ya
kiyaye min na Zarah, angon Nusaiba." Ya wuce
shi ya zauna a kujera. Sauran yaran shagon suka
gaishe shi da jiki, ya amsa. Sageer ya biyo shi,
shi ma ya zauna kujerar gefen sa ya ce,"Duk na
zura ido in ga wa zai fito daga wannan
shimfidediyar mota, ashe Alhaji na ne, ka gan ka
kuwa?Ai za'a ce ka ba wata biliyan dari baya
mutumina." Ya ce,"Ka bari kawai, ni kai na tsoron
gidan nan na ke yi da motar nan. Zarah ce ta
matsa min na kinkimota." Yayi dan murmushi ya
ce,"Arziki. Kashi Naseer, ka riga ka tako kuma
kowa yana da hanyar da Allah ya shiryo masa
inda zai sami abincinsa. Allah ya kara hada mu
da masoyan mu." Ya dan nisa kafin ya ce,"Yanzu
tsakanin ka da Allah ba ka min kallon auran jari
na yi? Kyar Sageer ke kallon sa,"Me yasa kai ka
cika tsarguwa ne? To idan ma auran jarin ka yi,
ina ruwan mutum? Ina cewa shi ma mu2m ya
sami damar yin hakan, sannan zai yi? Naseer, ba
auran jariba, ko auran damfara ka yi, babu
ruwan ka da mutane kowa ta shi ta fishshe shi.
Abinda Allah ke duba ita ce zuciya, shi yasa ake
so a kodayuashe ta kasance tsarkakkiya." Ya dan
yi hucin zafi ya ce,"Na fahimce ka, amma kar ka
manta ba kowa ke da irin tunanin ka ba. Ni kuma
na tsani zargi, ina fitowa motar nan kowa sai
kallo na yake yi, har da gaisuwar gulma, dole in
na shiga wannan, ayi magana ta. Ka san ban da
hakuru, idan na ji ba za'a kwashe ta dadi ba,
komai gemun mu2m." Ya dan bubbuga kafadar
sa, yana dan murmushi,"Allah ya ki yaye min
angon amare, hakan ma ba za ta kasance ba.
Insha-Allahu. Ai yanzu ka wuce da ajin fada, sai
dai ka yi rabon na 'ya'ya a cikin gida ko ba haka
ba? Wani dan bazawarin murmushi yayi ya
ce,"Aje wannan maganar, ka san ina son yara,
kar ka tada min kwadayin su." Ko?" Sageer ya
tambaya, ido waje. Ya ce, "Ah? To mece ce ribar
auran?, Ita Zarah ma ta ki fara laulayi, sai ja min
rai take yi." Sageer ya fashe da dariya suka tafa.
Sannan ya nuna shi,"Zarah kadai? Har da
amarya, lokaci guda za su zazzage ma tagwaye."
Take nan ya sauya wani shafin." Ka san wani
abu? Na kusan fara zuwa koyon dinki, jira na ke
hannu na ya gama warkewa." Baki sake yake
kallon sa."Ina son ka ranar yanko zance, babu
seti. Mutumin da hidiman karatu ke gaban sa, ga
fita wasanni, yaushe za ka sami lokacin zama
nan? Lallai za ka sha mamaki, kai ba ka na
karatun ba, ka rinka koyon dinkin? Ya ce,"Ai na
ma riga na sha mamakin. To wai me yasa ka ke
son koyon dinkin yanzu?" "Ra'ayi na ne ya sauya,
yanzu kuma dinkin na ke so." 'Yar dariya Sageer
yayi,"Allah ya nuna mana lokacin." Ya ce ,"Amin.
Ya dan jima nan suna ta hira, sannan ya je ya
gaida Umma. Abba ya riga ya fita kasuwa. Daga
can gida su Zarah ya nufa, suka sha hira da
Innar sa. Haka yayi ta yawon sa a gari, ba shi
nan, ba shi can. Saboda yasan Nusaiba ke da
girki, bai koma gida ba, sai gab da Sallar
magariba. Suna zaune a falo, kowacce ta tsala
don mamaki. Yayi sallama ya shigo, suka amsa
dauke da fara'a, sannan suka yi masa sannu da
zuwa. Idon sa akan Zarah yake amsawa. Kan sa
tsaye ya wuce kujerar da take, ya zauna bisa
hannun kujerar, yayin da take fadin. "Haba
yayanmu, kuma tun safe har magariba ba'a ko
waiwayen gida? Haka ake yi? Kawai yadda take
motsa bakinya, shi ya tsura wa ido,, yake kallo.
Nusaiba ta ce,"Ai ni ban ma san abinda zance ba
Antina." Ya dan lumshe ido kadan, ya bude su,
kafin ya ce, "Na yi laifi kenan? Ta ce,"Tambaya
ma ka ke? Kodayake babu ruwana, tsakanin ka
da amaryar ne. Aron bakin ta na yi, na ci mata
albasa. Bari na yi haramar sallah." Ta mike za ta
wuce, yayi wuf ya cafke hannunta. Adon ta kawai
ke kidima shi, tayi masifar kyau,(Material) din ya
amshi jikinta sosai." Ta waigo a firgece, ta rasa
ma me za ta ce?" Zo in ji warin albasar da ki ka
ara ki ka ci." Ta dubi Nusaiba da ke kallon su,
tana dariya ta ce,"Au dariya ma ki ke yi, ba za ki
kwace ni ba, ki na kallo zai kar ya ni." Ta gintse
dariyar ta ce,"Duk zan iya jinyar ku." Ya janyo ta,
ta fada da karfi ta dawo inda ta tashi ta sake
zama. Ya matso ta sosai, ya ce,"Haba Fati na,,
daga shigowa ta kuma sai ki tashi, don me?