Showing 3001 words to 6000 words out of 59456 words
Chapter 2 - YAR LESBIAN CE COMPLETE DOCUMENT BOOK.txt
cikin pant dinta tarinka murzawa nishi Kawai Suke Ahhhhhh washhhh kusan minti 30 Sukayi Ahaka feenat ta kankame ta Alamar Tasamu tayi riles.
ππππππππ
YAR LESBIAN CE
ππππππππ
By
Nadeeya Muhammad Ahmad
.
Whatsapp +2347010902548
Web http://arewapost.tk
In dedicated to
Xaynab Ummu mahbub
*da Bazarku Nake taka Rawaπππiyayena Abin Alfaharina Ina farin ciki daku Akowani irin Hali Allah yakaro muku Lafiya tare da tsawoncin Kwana me AlbarkaπLove you With all my heart mum and dadπ*
Page.....4
feenat ce daure da towel gawani karami A hannunta tana goge gashin kanta da Alama daga wanka tafitoh wajen makeken bed din dake tsakiyar Dakin ta nufa, Leemah Leemah tashi kishiga nafitoh. Haba Feenat kaina Sai yayi ciwo ni kibarni da Asuba Nayi Leemat tafada cikin muryar bacci Feenat bata Kara bi takanta ba ta dakko wata doguwar Riga tasaka tajawo darduma tafara gabatar da nafilfili Raka'a 4 tayi ta daga hannu Sama tana kwararo addu'oeh take! Abinda ta Aikata dazun ya bijiro mata Azuciya kuka mai tsanani tashiga Rairawa Tana, Ya Ubangiji ka gafarceni Kan Abin nan danake Aikatwa ya Allah Kasani Nauyina kan iyayena yake wajibine Su magancemun matsala ta Amma Suka banzatar Dani gashi nafada kan turbar Shedan Ina Aikata Abu mafi muni Agareka, ya Sarki mabuwayi mai Shiryar da bawaYayin da yaso ya Allah Kashiryar da Zuciya ta Nasani nidin mai girman Zunubice gareka Ubangiji ya Allah badan niba ka gafartamun Zunubaina kakuma ganar da Mahaifana,,,,, ya Allah narokeka Dan girmanka Dan Albarkacin fiyayyen Hallita Ka yaye mun yawan Sha'awar nan Ka Kara daurani kan Hanya maidaidaciya......wani Kuka ne ya kwace mata π΅π΅kuka take Sosai na nadama Abinda take Aikatawa,,,, Haba Feenat wan nan wani irin Abune kin Hanani bacci da ihun kukanki Leemat tafadi Rai Abace... Dan Allah Leemah kitaso Muyi magna feenat tafada cikin dashashshiyar murya Kinga ni ba'inda Zan Sakko kibarni nayi baccina tunda ke kika Jawoni, Abinda Zaki fada din yawuce kice kinyi Nadama Kuma Sau nawa kina Alkawarin kin bar lesbian,,,,,,wannan kukan naki dashi Gara babu ki tsaya idan Nadamar gsky Zaki kikai Zuciyarki nesa,,,,,,,,bare kuma Nasan ba nadamar bace Dan Wanda besan Halinki ba Shi Za'a ba labari. Toh nima dai NADEEYA ban San Halin Feenat ba kuma masu karatuma Zasuso Suji wacece feenat.......
SHIN WACECE FEENAT NE
Alhji Ibrahim dattijo mai dadtaku Tare da matarsa Nafisa Asalin fulanin yola ne Suna Rayuwarsu cikin jindadi da ganin girman Juna Sunada yawan Arziki SHANU RAKUMA da dai wani dabban kiwo na fulani Allah ya Azurtasu da haihuwar Yara 3 Nazir Shine babba Sai Aishatu Sai Sukai Auta Umar daga nan haihuwar ta tsaya musu, kusan kansu duk daya dan ita Nafisa Akai Akai take haihuwar ta, duk da cewa Fulanine Iyayen su basuyi kasa a quiwa wajen ganin yaran nasu Sunyi Karatun Islam dana Zamani ba, Sun taso da hazaka Nazir da Aishatu Aji daya Suke Inda suka wuce Umar da Aji daya,,,,,,, bayan Su Aishatu Sun Kammala Secondary dinsune Tasamu miji tayi Aure Anan yola inda yarage Nazir da umar wanda tun tasowarsu suke Son junansu Ahaka Nazir yaki ci gaba da karatunshi cewa Sai Umar ya Zana jarabawarshi ta Secondary Sucigaba tare,,,,,,,,,Masha Allah bayan lokuta Sun Samu addimetion Suka tafi makaranta a .A. B .U . Zariya,,,,, Hutu ke kaisu garin yola Suna matukar temakon iyayensu duk dacewa babu Abinda Suka nema Suka Rasa hutun Karshe dasukai Suka koma yola Anan ne Nazir yasamu mata yayi Aure yacigama da business Alokacin Aishatu tana da yara 4 duk Maza Anso Umar yafito da mata Ahadashi da Dan uwanshi yace Shifa Ina karatu mai Zurfi yake So yayi inda yasha banban da Sauran yan uwanshi kenan,,,,,,,Alhji Ibrahim bai cika takuraba indai wajen karatune Shiyasama ya Amince da Hakan, Umar kaduna yakoma don cigaba da karatunshi wanda da ker Nafisa ta Amince da Hakan yakanje ya dubasu Akai Akai, karatu yake Sosai wanda yasamu degree har biyu Anan ne ma ya yake Shawaran yafara business gun Wani Mahaifin Abokin Shi Alhji Aminu,,,,,,,,Suna gudanar da komai cikin Amana da gsky lura da Hakan ne watarana Alhji Aminu ya kirashi...... Umar badon komai na kiraka ba Nalurada irin Amanarka da Iliminka Da nagartarka Sannan Kwanakin baya dakuje yola da Sulaiman yabani labarin irin mutumcin iyayenka,,,,,,,,Don Haka na yake Shawaran Zan baka Auren Yata "Hafsat" Sai Asan nan Umar yadago Kai yace duk Abinda Ka yanke daidaine Baba Nasan bazaka taba cutar daniba Nayi matukar farin ciki duk dai Nasan cewa daman bazanji Kunya ba. Kaje Zanje yola muyi magana da Mahafinka Kafin nan Zaka fara Zance da Hafsa dan kufahimci Juna Yace toh Baba Alhji Aminu yaje yola Mahaifan Umar Sunyi farin ciki matuka Duk dacewa Sunso dan nasu yayi Aure a yola cikin yan uwanshi, Amma basu nunaba Sabida Alhji Aminu dattijon kwaraine bayan wata biyu Umar da Hafsa An fahimci juna inda Suke gudanar da Soyayya mai tsafta abinka da masu ilimi Acikin watan kuma Aka Saka Aurensu Ranar Wata juma'a misalin Karfe 10:00 dunbin mutane Suka Sheda Auren Umar Ibrahim da Amaryarshi Hafsat Aminu, Su Aishatu dasu Nazir duksunzo kaduna Kasancewar Agidan Alhji Aminu Ake gabatar da komai Hatta Su Hajiya Nafisa da Matar Nazir data haifa yara biyu mace da na miji duka suka dungumo Anci Ansha Anyi komai cikin Mutumci. Wani katafaren gida da Umar yagina A Unguwar Dosa Nan Aka kai Hafsa Gidane kato nagani nafada komai yayiπ
Bayan Shekara daya
Hafsace Zaune da katon Cikinta Tana duba wasu takaddu Sai rintse ido take tana cije baki daga dukkan Alamu batajin dadi Abun taga Saici gaba yake tayanke Shawaran kiran Mijinta Awaya. tana Sanar dashi yatawo Dan dama banisa yake da gidaba Sabi da ita kasancewar Soyayya Suke Sosai danko Sharokan Sai Haka lol Hafsa machace yar boko Ga Kyau Kota'ina ta hadu Ga iya Zama da miji Shiyasa Suke cin karansu ba babbaka. Yana ganin Halin da take Ciki ya temaka mata Suka Shiga mota Sai Asibti Cikin mintuna da bazasu wuce5 ba Aka fito da jariri Kato farisol kyakyawa dashi. Wayyo zokaga murna wajen masoyan nan biyu dama duk Wasu masoya nasu. Ahaka Aka Sallmesu Suka wuce gida cikin farin ciki Aishatu Ita tazo ta Zauna da Hafsa har'akai Suna Ranar Suna yaro yaci Suna NAZIR Sunan yayan dadyn shi kenan. Bayan watsewar taron Suna da dare yana Zaune Suna fira Ga yaronsu sun rungume daga yau dai Hafsa kin koma "Mumy" murmushi tayi tace kai kuma "daddy" ba Ahaka Zamansu yacigaba da tafiya... yaron yanada wayo Sosai Dan haka yana Cika 3years Suka Sashi makaranta dama gaba dayansu Burinsu Kenan yana kokari kuwa matuka Bayan yacika Shekaru biyar ne Mumy ta tashi da wani Zazzabi mai tsanani Ai ba bata lokaci Suka wuce Asibiti gwajin farko ya nuna tana dauke da Ciki Wata 4 Murna Sukai Sosai dawowarsu kenan daga Asibiti Aka kirashi daddy A waya cewa Allah yama maihafinshi Rasuwa gaba daya Nima danake Typing Saida naji Ajikina Kasancewar tsowo mai Mutumci yarigamu gidan gskyπ΅ Tuni Suka Shirya Suka dunguma yola Harda iyayen Hafsa watoh Alhji Aminu da Hajiya Amina mahaifiya gun Mumy Kenan. Sunje inda Achan wasu Sukayi dan koke kokensu bayan Kwana bakwai Kowa yadawo Akabar Inna Nafisa Achan Haka Suke kiranta. Sundawo gida lafiya inda mumy tacigaba da Rainon Cikinta daddy yana kula da ita.
ππππππππ
YAR LESBIAN CE
ππππππππ
By
Nadeeya Muhammad Ahmad
Whatsapp +2347010902548
Web http://arewapost.tk
In dedicated to
Xaynab Ummu mahbub
*page dina na farkon Wan nan Novle Nayi korafi Kan cewa yakamata mai karatu ya tsaya ya natsu kan karatu kamin yayi bakaar magana, Amma jiya Nasamu masu mgn kan cewa Zan bata tarbiyyar wasu, Amma Naji dadi danasama wanda Suka fahimceni fiye da masu Zaginπ‘ Sannan Zan kara dacewa duk wanda yaga bazai juri karanta book din nan ba Can leave it. Danni da Masoya littafin nan yanzu muka fara*πππ
Wannan page Nakune Masoya littafin "yar lesbian ce" love you allπ
Page......5
Bayan Rasuwar Alhji Ibrahim Kamin su daddy Sutawo bayanda basuyi da Inna Nafisa kan ta biyosu ba Amma firrrr taki, Acewarta inda Kasar mijinta take itama Nan Za'a Saka ta idan tasu tazo. bayan Wata Tara da Wani yamanci Mumy Suna Zaune Suna fira da Matar Sulaiman Aminin daddy kenan, Dan Su daddy Tare Suka taso Sunayin komai da Sulaiman da Wani Abokinsu Ahmad duk dacewa Ahmad ya Rigasu Aure Dan Saida yayi Aure ya haihu Δa Namiji Sannan daddy yayi nashi Auren Saikuma Sulaiman yaya Awajen Mumy kuma Aboki Awajen daddy Shima yayi Nashi Auren. Mumy Takasance irin matan nan ne masu tattalin miji wanda Ko Zumunci basucika yiba Sabida kula da mazan su dan Haka bata zuwa ko'ina daga gidansu Sai wajen Aikinta dan Cikakkiyar barrister ce, Tana dan Zuwa YOLA wani lokacin idan daddy Zaije, ba kasafe tacika Ziyartar Maryam Matar Sulaiman ba Saidai Ita maryam din ke yawan Zuwa mata, ko Sau daya Kuma bata taba tunanin Zuwa gidan Fatima matar Ahmad ba itama Kuwa fatiman tace bazatazoba harsai mumy taje mata,,,,,kullum cikin Sa Rana take Amma ina,,,,,,,,hakan ce takasance Ayau ma tare Suke da Maryam Wacce Nazir yarada ma UMMA Tana ma mumy korafi Wlh kedai Hafsa bazaki chanza haliba kullum kina gida Kamar daddawa da Anyi magana kice daddyn Nazir na Gari Kamar dan ke kadai Akai miji, Kai Maryam kedai kullum maganar ki kenan idan ban Kula da Shiba waye Zai kula dashi beda kowa Anan garin wanda ya wuce ni da Nazir Sai wannan Cikin Nawa Uhum Toh dan Allah badole na Zamemai gata gaba da baya ba? Kizama Shi yazama ke Kawai karshen magana kenan Maryam tafada tana gyara Zamanta,,,,,,,,, Bari Nakawo miki Abinci kici Amma maganar nazama Shi yazama ni na nawa kuma Ai munzama tsoka daya mumy tafada tana bin Hanyar kitchen,,,,,,,Kayattacen Abincin da ta dafa ma daddy Aciki ta iba ma Maryam, tanaci Suna fira, Umma ce tace wai kuwa kinsan Fatima ta Haihu yau kwana hudu kenan, Kai Haba mai Aka Samu? Tahaifi diya mace, kai tubarakallah Allah ya Raya.Amin Umma tace Sannan Takara dacewa Saiki kishirya Kije Barka, Kai Maryam bakida tausayi wan nan Cikin Nawa Haihuwa ko yau ko gobe Zakice naje barka, Uhum haka kawai ma Anki Ziyara bare yanzu da Akeda Hujja mai Karfi. Kyadai ji dashi Ai Zan kirata namata barka. Allah yasa. Ni Zan tafi, haba Maryam tun Yanzu? Eh Ai nafi Mara Zumunci, ki kwantar da Hankalinki nima Zanzo. Muna jiran Ranar da babu. dahaka ta tashi Mumy taimata Rakiya.
Cikin daran Ranar Nakuda tazo ma mumy, tun tana daurewa Har takasa ta tashi daddy dake bacci cikin Rudu ya dau key din mota ya temaka mata Suka fita yasata Amota yadawo ya dau Nazir dake bacci Sai SULTANA HOSPITAL dake nan Unguwar Dosa KADUNA Mumy tasha wuya A wannan haihuwan dan saida Aka kwashi Awanni tana Abu daya daddy Zufa kawai yake yana kaiwa da komowa, daker ya'iya daukan waya ya kira Sulaiman ya Sheda mishi daga bisani ya kira Ahmad, Kusan atare Suka karaso Sulaiman da Maryam, Sai Ahmad wanda matarshi ta Haihu badaman tazo, Zuwan Su Kuma yayi daidai da fitowar wata nurses tasheda musu Anhaihu diya Mace, Atare Suka Shiga dakin Suna ma mumy Sannu yayin da daddy ya dau yarinyar, SUBHANALLAH tsarki ya tabbata ga Allah wanda da ikonshi yake Samar da Abu mai Kyau da Mara Kyau, daddy ne yafada yana nunama Ahmad (Abba) dake kusa dashi babyn, Sunyaba da kyan babyn Dan Ajin farkoce wajen Kyau. Ahakadai washe gari Aka Sallamesu Sukayi gida, Kai Alhmdullah duk dacewa Mumy bamai Son Zumunci bace mutane Sai zuwa barka Ake, Sabida kyan jariryar ke rudan wasu yarinyar tun tana jaririya da farin jininta. RANAR SUNA yan YOLA duk Sun Hallara Mutane kota'Ina kowa farin ciki yake Anci Ansha taron Suna yatshi lfy inda Yarinya taci Sunan Kakarta mahaifiyar babanta wato NAFISA Zasuna cemataa (Feenat) Haka Rayuwa tacigaba Mumy na kokari wajen faranta Ran mijinta yara kuwa Tasamu wata dattijuwa Ladi ita ke kula dasu.
Lokacin da Feenat tacika Shekaru Uku Alokacin Aka Sata makaranta nursery "iman Academy" dake Unguwar Dosa, makarntar hade take da Islamiyya, Idan Sun tashi 12am Sai suke Shiga Islamiyya 5pm driver ke daukosu lokacin Nazir yana primary6 Mamah LADI itaa ke kula da komai nasu, Feenat tana Maida Hankali yarinayace mai hazaka aduka bangare biyu, Bawanda feenah ke Kulawa Dan ita din yarinyace marason Hayaniya, Kawarta daya Halima Itama Sabida kokarinta Yasa Abotarsu tazo daya da Feenat, BAYAN WANI LOKACI Abubuwa da dama Sun faru, Feenat Sun Zana jarabawar fita daga Secondary. Ayayin da Suka kara Shakuwa da Kawarta leemah Sosai, daddy ya tura Nazir Kasar Turkey Achan yake cigaba da Karatun inda yake Karatun Soja, Alokacin Feenat ta damu kan rabuwarsu da yayanta Sabida Shakuwar dake tsakaninsu, Leemah Itama tasanar da feenat cewa brother dinta yaje karatu America yana karatu Doctor, Mumy takara Haihuwa inda ta Haifa Twins, Mace da namiji namijin yaci Sunan kakanshi daya Rasu Ibrahim Suna kiranshi (Mubeen) inda macen taci Sunan Mahaifiyar Mumy Aminatu Suna kiranta (mubeena) Anyi Shagali Sosai. Haryanzu mumy batasamu taje gidan Fatima matar Ahmad ba............Feenat basu hada iyayensu Kawanceba ita da Leemah Acewarsu Koda Zasuyi Karyar fita yawo sarinka karya dazuwa dagidajen juna tunda kowacce Agidansu Ansan irin Shakuwar da kawayen biyu Sukayi
BAYAN SHEKARU.
Wata tsaleliyar budurwace wadda Aqallah Zatai Shekaru 18 duguwace ba irin Sosai ba,farace mai matsakaitan idanu Samanshi dauke yake da dogayen gashin idanu, girarta Aciki take ta kwanta lufff, Tana da diri batada kiba Kuma ba Arame Take ba, kirjinta cike yake idan baka Zata ba Zaka Iya Cewa Wata mai yawan Shekaruce. fuskarta dauke take da dogon Hanci yayin da pink din bakinta y kasance karami, kwance take kan makeken gadon dake manne jikin ginin dakin tana danne dannen waya da Alama Chat take Ringing..... dayar wayar dake kusa da ita tafara. Hello besty daga dayan bangaren Aka amsa Hy feenat ina hanya zan zo gidanku fa, dagaske? Allah da gaske,Saikin karaso ok. Ba'afi Minti20 tsakaniba Saiga ta tashigo, turo Kofar tayi, dasauri Feenat ta Sakko Suka Rungume Juna, leemah Shine Baki gayamun Zakizoba, Sorry Kawata magana Zamuyi, Inajinki besty, Hawaye tafara Feenat yanzu Rabuwa Zamuyi, Zaro ido feenat tayi tace Akan me?muda muka Shirya yanda Rayuwarmu Zata kasance,kokinmance cewa komai namu iri dayane kinsan matsalata nasan taki,ke kikace Hatta Ranar aurenmu Rana daya zekasance, Leemah kin mance Ranar da kikacemun Mu Auri miji daya kokuma Mu Auri wa' da kani duk Dan mukasance Tare. Leemah duk kinmance yau kikemana Zancen Rabuwa. dan Allah Feenah ki kwantar da Hankalinki Ki Saurareni. INAJINKI besty Abba nane yasmamin Wata School Of Nursing A Abuja Shine yace Zai turani, Sabuwar Makarantace yanzu take tashe Akace. Hmmm Ajiyar Zuciya Feenat tayi tace Dan wan nan besty Shine kika dagamun hankli indan Wannan Zanmawa daddy