Showing 60001 words to 63000 words out of 108906 words
Chapter 21 - MIN-QALB Book Complete Document Hausa Novels By Mamuhagge .txt
dama Salman ya tabbatar Mata da a irin wannan lokacin Modibbo na gurin Andi.
Modibbo ne yafara gabeta ya zuba Mata idanuwansa masu kwarjini da Khalil da MD suka dauko ta qaraso ahankali ta zube qasa gabansu sai alokacin Andi ya dago ya lura da waye.
Cikin tsananin biyayya da nuna damuwarta a fili tace"
Ina miqo gaisuwata ga Andi da Modibbo tareda neman afuwar babban kuskuren Dana aikata Wanda ya shafi 'da mafi biyayya da gujewa zuciyarku.
Kallon mamakin rashin tsoronta da gwarin gwiwarta suke Mata su duka din ta sauke Kai cikin nutsuwa da girmamawa tace"
Wallahi tallahi Dr khalil zabeera baitaba aikata laifin da kuke tunanin ya aikataba koma wane irine,
Taimako ya hadani da Dr khalil Kuma shine yasa yayita ajiyata acikin zabeera,
Ni marainiya ce kuma Yar bola kamar yanda kowa ke fada Amma Kuma banice nakai kaina bolarba harnayi rayuwa acikinta na tashi acikin
Rayuwa da jarabawar rayuwace takaini wadda itace tabaku girma da matsayi tareda sunan dakuke ganin yafi Dan Adam daraja,
Nayi rayuwar maraici da tozarci irinku masu arziki Baku dubemu ba kuka taimaka Mana saidai maigadin makarantane Wanda yake karban dubu bakwai a wata ya taimakemu,
Nayi rayuwar almajiranci Ina matsayin mace sbd kawai na rayu,
Nayi rayuwar wahala da qasqanci duk Dan sbd na rayu,
Munkwana da yunwa muntashi acikinta,
Lokacinda yaranku da jikokinku suke karatu mu bara mukeyi alokacin sbd muci,
Da kaina na koyi yanda zanyi yaqi da maza na qwaci kaina daga sharrinsu tun inada qananun shekaru
Shin nayi dukkanin wannan ne sbd nazama karuwa a rayuwa????
Nice na zabarwa kaina yin sata amaimakon karuwanci Dan kawai na rayu sbd sata Zan iya rokon me Abu ya yafemun wata Rana Amma Zina fa???
Dr khalil zabeera shine mutum me arziki na farko daya shigo rayuwarmu,
Yakawo Mana walwala da farin ciki a zukatanmu,
Talakawan bangarenmu wainda Dr khalil zabeera yakawo farin ciki akan fuskokinmu da rayuwarmu basa qirguwa,
Meyasa mutum me zuciya irinta Khalil maimakon ayi alfahari dashi za'ayi fushi dashi?
Shin Kuna tunanin ladar aikin Khalil kawai Bata Isa takawo qarin haske da walwala acikin zabeera ba??
'yayan da Allah yabaku dukkaninsu amanace agurinku Allah zaitambayeku alaqarku dasu idan da akwai cutatarwa,
'yayanku ne Amma Kuna gudanar da rayuwarsu kamarta dabbobinku kokuma bayinku,
Wasunsu da dama a tauye suke basa rayuwar farin ciki,
Zaman auren Dole da qunci sukeyi duk sbd bin umarni da qaidojinku,
Shin haramun ne neman farin ciki a wani gurin kokuwa musulunci ne ya hana?
Shi mutunci da girma Allah ne yake badawa Kuma shiya Baku
Idan Allah yabaku suna duk Abinda wani Dan Adam zaiyi bazai Bata hakanba Koda kuwa me zaiyi.,
Nazo zabeera ne sbd son kudina dakuma rashin sanin ciwon kaina Amma sbd tseratar da mutuncinku yasa ya karbi laifi da bacin sunan da baisan lokacinda aka hadosaba,
Wallahi niba karuwa bace,
Bantaba aikata zinaba,
Bansan ta Yaya ake aikataba,
Aikin gidajen abinci danayi nayine Dan neman halak Dina Wanda haryanxu Ina alfahari da hakan sbd Allah bai bani matacciyar zuciya ba.
Dagowa tayi da idanuwanta dasukai jajir ta ajiye katin Daurin aurensu cikin sanyin jiki tace"
Babban burinsa shine aurena yakawoni gabanku Dan neman yafiyarku da gafararku nikuma babban burin danakeson cika masa shine bashi kaina amatsayin mata dakuma sasantawarsa daku iyayensa,
Hawaye masu tsananin zafi suka gangaro Mata cikin daci da damuwa tace"
Dan Allah Ina roqan gafarar ku yafe Masa kodan kasancewarsa 'da me biyayya da gudun zuciyarku a baya,
Ku basa farin cikin dabai taba samu daga garekuba tun haihuwarsa....
Umme dake bayanta tuntuni a tsaye batasan lokacinda tafashe da kukaba tana sake Jin qaunar Amatu ta qaraso gabansu Modibbon ta zube itama cikin kuka tace"
Andi Dan Allah ku yafewa khalil kubarsa ya aureta wlh dukkaninsu ba laifinsu bane nice me laifin sbd nice na kawo Amatu zabeera da wata manufarda rashin wadataccen ilimina yabani.
Zayyane musu komai tayi sukai tsit Babu me motsi musamman Andi dashi maganganunsa Amatu ne sukafi shigarsa,
Shin dukkanin yawancin 'yayansu rayuwar kunci sukeyi sbd gudun zuciyarsu???
Tabbas tunda yake tsawon rayuwarsa Babu Wanda yataba kallonsa yafada Masa haqiqanin gaskia sai yau yaringa qanqanuwa daya Isa haihuwar ubanta koma kakanta ta kallesa tafada Masa quncin dayake saka 'yaya da jikokinsa shekaru wa shekaru.
Modibbo Kam dama tuni Amatu ta Dade dashiga ransa bazai iya nunawa bane sbd bacin ran Andi Amma tuni yajima da sanin yarinyace me fadar gskia batareda tsoro ko shakkaba.
Miqewa tayi ahankali ta juya ta fice tana share hawayenta daketa fita da gudu ta fada mota suka bar zabeera.
Kwance yake yau kwana biyu kenan ciwonsa nacinsa harya Fara cin qarfinsa ko fita daqyar yakeyi sai dare cikin duhu yake zuwa gidansu kawu sbd kada agano halinda yake ciki magungunsa yasiyo dasu inhaler Amma Sam kamar basa Masa aiki sbd kullum sanyi sake shigarsa yakeyi a gidan.
Yau laraba saura kwana daya Daurin aurensu Amma abin yaci qarfinsa tuni aka gano baida lafiya sosai sbd Koda Ibrahim yaje gidan tuni ya Dade da fita hayyacinsa hankali tashe ya kwashesa sai asibiti.
A asibiti Koda aka karbesa numfashinsa yayi nisa sosai cikin gaggawa akai emergency dashi ana qoqarin saka Masa oxygen.
Su kawu Ibrahim din yafara fadawa kafin yakira salman yafada Masa cikin qanqanin lokaci duk suka halarto asibitin hankalinsu duk atashe.
Kallo daya Amatu tayi Masa hankalinta yayi mummunan tashi sbd lokaci daya sanyi ya kumburasa
Numfashinsa Sam kwata kwata Babu saidai oxygen dinne ke janyo Masa ahankali idanuwansa a rufe fuskarsa tayi haske hakama bakinsa yayi haske sosai ya bushe.
Hawaye ne suka kufce Mata ta saki siririn kuka ahankali tana cewa''
Meyasa zaka boye bakada lafiya harsaida abin yayi tsanani haka?
Zaman rashin hankalin kurame sukeyi a asibitin daga ita har kawu da iyami duk suna asibitin da salman sai ummensa dasu Nuratu dasuka iso kowa cikin tashin hankali bama kamar umme datasha kuka idanuwanta sukai jajir.
Sunanan zaune har magriba saiga anty zarah da MD ZABEERA sun iso tana ganin anty zarah suka tsaya kallon juna cikin tsananin kewa da qaunar juna tazo da gudu tafada jikinta tana fashewa da sabon kukan datake ta riqewa tuntuni na ganin har lokacin sai Abinda yayi gaba ajikin nasa.
MD ne dakansa yaje yayi mgn da likitocin suka sake yimasa bayanin sanyine yayi mugun shigarsa Wanda yasa gaba daya jijiyoyin huhun Jan numfashinsa sun daskare ya tayarda ciwonsa gaba daya harya basa attack Sam numfashinsa yaqi dawowa ta oxygen dinma alamarin sai ahankali.
Tsorone yashigesa akaro na farko rayuwarsa
Dawowa yayi dakinda Khalil din yake ya tsaya akansa Yana kallonsa yaji zuciyarsa na neman karyewa da sauri ya juya fice.
Anan ta kwana asibitin itada ummensa da iyami har gari ya waye be farkaba zuwa lokacin Kam ko mgn basa iyayi da junansu sbd damuwa zazzaune kawai suke suna rarraba idanuwansu dasuka kode sukai zuru zuru.
Da yamma tayo alwalar magriba tazo gefensa ta tayarda sallah tayi tagama tana cikin addua taga kamar ya motsa hannunsa kadan ko shafa adduar batayiba ta zabura ta miqe sai taga idanuwansa a bude sunyi fari tas dasu cikin tsananin farin ciki ta fada kansa ta rungumesa tana sakin hawayen farin ciki.
Umme data fito toilet din dakin tana ganin haka tayo kansu da gudu har sanyin ruwan qafarta na zameta itama fadawa tayi kansa ta rungumesa
Ya lumshe ido ganinsu su biyun ba qaramin farin ciki yasashi ba yasake lumshe ido cikin azabar ciwo yanason motsawa Amma sun dannesa
MD daya shigo yayi gyaran murya itace tafara juyowa sukai Ido biyu tayi saurin dauke Kai tana maido da kallonta Kan Khalil cikin tsananin farin ciki tace"
Dr Dan Allah karka sake rufe idonka.
Qarasowa yayi ahankali Yana kallon fuskar Khalil din yau farin cikinsa dai Kam ya bayyana
Shima Khalil din shi yake kallo fuskarsa nason bayyana farin cikin ganinsa Amma azabar ciwo ya hana.
Cikin sautin murya me taushi yace"
Kun sakar Masa nauyi da yawa inaga.
Da sauri dukkaninsu suka dagasa kafin suyi wata Magana saiga Andi da Modibbo tareda alhaji qarami sun shigo salman yakawosu take umme da amatun suka saki hawayen farin ciki suna kallon fuskar Khalil din da idanuwansa suka nuna zallar farin ciki ganinsa hawaye masu dumi suka gangaro ta gefen idonsa
Andi da kansa ya matso gefen gadon ya dafa kansa yasaka tissue ya share Masa Yana jinjina Masa Kai.
Salman da MD ne suka tayar dashi zaune amatu ta hado ruwan zafi da towel suka gyara Masa jikinsa tareda Sanya masa shirt Mara nauyi aka basa tea yasha kadan har lokacin da oxygen a hancinsa Kuma har lokacin bai iya mgn sbd bai iya jan dogon numfashi.
Kafin dare yadan warware ba laifi sbd Yana Dan magana ahankali tareda zuwa toilet idan ankamasa.
Da kawu yaso daga Daurin auren a gobe Amma Andi yace abarshi kada a daga tunda anriga anyi sanarwa.
Da daddaren ranar duk yanda ta nace hanata kwana asibitin akayi akace Takoma gida Salman zai kwana dashi tunda washe garine Daurin auren Dole ta koma bayan tayi Masa bankwana yabiya da Ido cikin kewarta tun Bata wuce dinba.
A gida duk wani hidimar al'ada sunyi abinsu hatta lalle anyi Mata a blue fox anty zarah takaita akayo Mata tareda gyaran Kai dana jiki Daurin auren kawai suke jira a goben akaita zabeera.
Tunda ta kwanta mafarkin Dr kawai takeyi sai kawai ta tashi tayo alwala tazo ta tayarda sallar nafila.
Tunda gari ya waye takejinta batada qarfin jiki sbd barin gida dazatayi.,
Qarfe daya da rabi dubban JAMA'A suka shaida Daurin auren KHALIL ZABEERA da AMATULLAH SALEH Wanda ya bayarda tarihi me girma sbd itace mace ta farko da aka auro daga waje.
A asibiti dagashi sai MD ZABEERA ne Wanda yace zai zauna dashi tunda kowa na gurin Daurin auren.
Bacci yakeyi sbd alluran da akai Masa bada jimawaba sbd jikin daya dawo Masa sosai.,
Bayan Daurin auren JAMA'A duk asibiti sukaita zuwa dubasa sai yamma lilis ya farka cikin ikon Allah saiya tashi da qarfin jiki haryana iya Magana tana Kuma fita sosai.
Wanka MD ya taimaka Masa yayi ya sanya farar jallabiyar datai Masa kyau matuqa yayi sallolin da ake binsa yazauna kenan saigasu umme da Nuratu wadda idanuwanta sukai luhu luhu sbd kukan data kwana tanayi.
Abinci ta zuba Masa ta zauna gefensa ta miqa Masa kanta a sunkuye batareda ta kallesaba.
Karba yayi tareda sauke numfashi cikin sanyin muryarsa dake fita ahankali yace"
Nuratu inshallah zaki samu Wanda zai wadata rayuwarki da farin cikin Dana kasa baki.
Kallonsa tayi idanuwanta na cikowa da hawaye murya na rawa tace"
Meyasa kakeson Amatu???
Lumshe idanuwansa dasuke a 'dan galabaice ahankali yace"
Allah ne yasamin sonta fiyeda komai
Kuma Ina fatar zaki qaunaceta kodan sbd ni.
Murmushi me ciwo tasaki hawayenta na sake gudu tace"
Zangwada.
Murmushi shima ya sakar Mata tareda juyowa ya kalli MD dake amfani da wayarsa yace"
Kaifa MAHMOUD???
Zaka gwada qaunar matata ko Dan sbd ni?
Juyowa yayi ya zuba Masa idanuwansa batareda yace qala ba.
Abinci umme ta matsa Masa ahankali yaci kadan Tasha tea me zafi har zufa yadan karyo Masa aka kunna Masa AC kadan.
Ganin yanayin jikin nasa dakuma shi kansa daya nema sallama yasa suka sallamesa bayan sallar magriba zuwa ishai Koda suka Isa zabeera daidai isowar motacin dasuka je dauko amarya Amatu.
A gurin Andi aka kaisu duk su duka yayi musu nasiha sosai kafin aka wuce da ita gurin zamanta wato sashen Khalil din Wanda aka sauyawa komai sabo.
Iyami da kanta taredasu maman junior suka kawota har cikin dakinta suna jinjina arzikin duniya irin na familyn ZABEERA kafin aka maidasu gida.
Ahankali yashigo dakin datake zaune zugum bakin gado tana tunanin da batamasan tanayiba...
Ji tayi anzauna kusada ita ahankali ta juyo sukai Ido biyu dashi gabanta taji yafafi ahankali ta dauke Kai zata sunkuyar ya riqo fuskarta ahankali tareda girgiza Mata Kai ya rungumeta cikin jikinsa ahankali tareda sauke ajiyar zuciya batareda yace komaiba.
Sunjima ahaka kafin ya saketa tareda cewa ta tashi suyi nafila.
Tashi tayi Babu musu sukaje toilet din tare sukayo alwala suka fito yakama hannunta suka nufi dakinsa.
Bayan sungama sallar hannunta ya riqo cikin nasa ahankali yace"
Zakici abinci ko wani Abu?
Akwai abinci da umme da antynki suka kawo gashi can a dining.
Dagowa tayi ta kallesa ahankali kafin ta girgiza kai.
Murmushi yasake ganin yau itama tazama kurma kamarsa tunda yafara ciwon baya iya doguwar Magana.
Miqewa yayi tareda tayarda ita tsaye Yana zame Mata mayafinta kyakkyawar fuskarta ta bayyana da kyau cikin qarfin hali yace"
Alhamdulillah.
Sunkuyar dakai tayi tana qaqalo murmushi ya janyota ya sanya cikin jikinsa ya rungumeta Yana lalubar zib din goguwar rigar Julius Holland din dake jikinta me laushi ya bude rigar ta Fadi qasa tabarta daga ita sai farar bra din dake jikinta da farin under.
Saurin rintse ido tayi zata durqushe ya tareda tareda rungumeta cikin jikinsa baida qarfin jiki sbd ciwo Amma hakanan ya cirata tana qanqamesa ya kwantar da ita Kan lafiyayyan gadonsa tareda rage hasken wutar dakin ya zare jallabiyarsa ya hau gadon ahankali tareda jawota jikinsa Yana kallon fuskarta ya Dora bakinsa akan nata tareda 6alle hook din bra dinta Yana cillowa qasa.
Qarfe ukun dare taringa Jin wani irin Nishi sama sama cikin kunnuwanta ta bude idanuwanta ahankali tana kallon inda take saita tashi zaune da sauri tana kallon gefenta a firgice tagansa numfashinsa na qoqarin daukewa cikin tsananin firgici ta diro gadon ta zagayo gabansa tana Kiran sunansa cikin tashin hankali Amma Sam tayi nisa a kidime ta janyo jallabiyarsa ta zura sbd itakadaice zata shigeta alokacin sbd firgici
Sam Bata damu da tsakiyar darene ba ta fito da gudu tayi hanyar sashensu anty zarah dake kusa da nasu a kidime tahau buga musu kofa tana Kiran sunan anty zarah da qarfi.
MAHMOUD dake zaune daram acikin Daren yakasa ko rintsawa sbd tsananin ciwon Kai yafara jiyo bugun qofar ya sauko daidai itama zarah tafito daga dakinta Dan taji bugun qofar itama.
Shine yafara cewa"
Waye??? ta jikin qofar
Cikin sauri da tashin hankali tace"
Nice Amatu Dan Allah kuzo Dr ne......
Tun kafin ta qarasa ya bude qofar yanayin datake ciki yasashi Kama hanyar sashen nasu batareda tagama fadar Abinda zata fada din ba.
Koda suka iso tuni Dr khalil zabeera yayi nisa shima yau gigitar yashiga ya janyo wata jallabiyar da sauri ya sanya Masa ya daukesa da dukkanin qarfinsa yafito dashi suka biyosa
Zuwa lokacin Amatu kukanma takasa Yi suka fada mota Banda zarah dayace taje hafsatu ta Rakata ta fadawasu umme.
Koda suka Isa asibiti cikin gaggawa aka karbesa akai ciki dashi zuwa lokacin Amatu idanuwanta neman qanqancewa sukeyi kamar wainda ke bayansu saiga umme da Modibbo harma da Salman sun qaraso asibitin Babu me nutsuwa Hakanan yau ciwon nasa yasasu cikin wata irin rashin nutsuwa da firgici.
Dr ashir ne da Dr Fatima suka fito daga dakin emergency din idanuwansu kowanne jajir Dr Fatima tuni idanuwanta suka kawo hawaye rauninta na bayyana Dr ashir ya sauke Kai gaban Modibbo yace"
Saidai hakuri Allah ya karbi Dr khalil zabeera.
Wuta kowannensu ya dauke musamman Amatu da umme
Amatu qyafta idanuwa tayi kusan so biyu kamar zata makance sbd duhu dake mamaye idanuwanta suka yanke jiki a some kusan atare itada umme wadda Modibbo ya tare ita kuwa MD ne ya tareta ta zube jikinsa dukkanin jikinta ba saki.
##Mamuh#
6/17/21, 8:05 AM - ': *_MQ 31_*
MAHMOUD ZABEERA ma yau dukkanin jarumta da qarfin ransa ji yayi Yana kakkaryewa daga zuciya har gangar jikinsa, tarota kawai yayi Amma shima Jin yake kamar faduwar zaiyi,
Dr Fatima tayo gurinsa da sauri tana hawaye ta tattaro Amatun jikinta tana Kiran nurses da duk asibitin jikin kowa da zuciyarsa tayi sanyi da rasuwar Dr khalil zabeera Wanda ya zamto cikakken mutum sbd kyawawan halayensa dasukeda wuyar samu acikin mutanen yanzu.
Dr ashir kuwa ganin dukkaninsu kowa neman zauce musu sbd tsananin tashin hankali da sauri ya dauko kujera yakawo wa Modibbo daya tare ummen data Suma,
Kiran wasu nurses yayi aka Kama umme itama akai ciki da ita aka kwantar gadan dake gefen Wanda aka kwantarda Amatu cikin sauri aka Fara Basu taimakon gaggawa dansu farfado tinda suma.
Su Modibbo kuwa zaunar dashi MAHMOUD yayi dukkanin jikinsa na rawa idanuwansa sunyi jajir ko mahaifin nasu yakasa kalla
Jin yanda jikinsa ke rawa sosai yasa Modibbo dagowa da jajayen idanuwansa ya kallesa tareda dange hannunsa Yana rintse ido tareda jinjina Masa Kai alamar sai hkr.
Dr salman zabeera kuwa kuka yakeyi sosai kamar mace sbd rasuwar Khalil din tamkar saukar tsawa sukajita kwatsam Babu Wanda yakawo tunani ko zancen mutuwa yanzu ba'a kansaba kosu Andi dasuke tsofi Basu kawo tunanin mutuwa akansuba.
MAHMOUD ne yayi qarfin hali da jarumtar karban wayar Modibbo yakira Andi dake zaune cikin tsakiyar Daren Yana salati sbd baccin dayaji haka kawai ya dauke daga idanuwansa Kiran farko na asuba dayaji anyi yasashi miqewa zaiyo alwala yafara ko nafilfili wayarsa tadauki haske alamar Kira.
Juyowa yayi ya kalli wayar yana mamakin Wanda ke iya kiransa a wannan lokacin saiyaga sunan Modibbo
ya sake shiga mamaki ya dauki wayar tareda dauka cikin nutsuwa yayi sallama.
Daga can asibiti Saida MAHMOUD ya tattaro qarfin halin iya bude bakinsa cikin rawar muryar dabai taba ba arayuwarsa yace"
Muna asibine taredasu Modibbo da umme Allah yakarbi Khalil cikin Daren Nan.
Tsit Andi yayi tsawon mintuna Yana qoqarin kakkamo zancen dazai fada yafara da Kiran"
Innalillahi-wainna ilaihirrajiun.
Kashe wayar yayi tareda ajiyewa yakoma bakin gadonsa ya zauna Yana sake maimata taslima Yana jinjinawa al'amarin ubangiji dayakeyin yanda yaso alokacin da yaso,
Ya dauke Khalil bayan cika masa burinsa na kwana daya tal,
Wannan shine cikakkiyar ikon ubangiji da Babu Wanda ya Isa ya sauya sbd yau da ace dukiya da mulkinsu nada iko meya hada Khalil da mutuwa a ranar yau da ko awa ashirin da hudu aurensa baiyiba.
Astaghfirllah" yafara maimaita tawa Yana rintse idanuwansa ya sunkuyar dakai cikin tsananin jimamin rasa yaro me tsaftatacciyar zuciya da tausayi tareda tawakkali irin Khalil.
Allah yayi maka rahama yabaka hasken kabari da sakamakon gidan aljanna KHALIL.
Koda asuba tayi akai sallar asuba tuni rasuwar Khalil ta yada zabeera da familynta nako Ina da ko Ina tuni kuku ya sauka a zabeera sbd mutuwar ta girgiza kowa sbd Babu Wanda yayi tunanin mutuwa Kuma tasa adaren,
Koda gari yayi waye sosai tuni family suka Fara halarta zabeera tafara cika tun kafin akawo gawar tasa gida dama wainda sukazo biki Kuma dama Basu tafiba tunda a Daren jiyan aka kawo amarya Ashe basasu koma daga bikinsa ba saisunyi zaman makokinsa,
Duk Wanda ya iso saiyayi kukan wannan babban rashin na khalil zabeera sbd kowa Yana shaida kyawawan halayensa da nutsuwarsa wadda tasa yakeda jamaa ciki da wajen zabeera.
Ahankali tabude idanuwanta ta rufe tasake budewa tana qyaftasu
Da fuskar usi dake rungume da kanta tafaracin karo ta rufe idon ta bude taga shi din daine ta zabura da sauri ta tashi zaune har tana zamewa