Showing 57001 words to 60000 words out of 108906 words

Chapter 20 - MIN-QALB Book Complete Document Hausa Novels By Mamuhagge .txt

08 Jan 2025

4751

samun Bata kariya daga kowanne irin barazana.


Doguwar tafiya sukayi Mai Dan tsayi takaisu central din inda daqyar aka barsu suka Shiga sbd tsaro.


Yana yin parking suka fito kawu na qarewa gurin kallo cikin tsananin tashin hankali ace anan Amatu take zaune akan qanqanin laifi irin wannan Wanda ko zagi da bannar suna da gorin da mutane suke musu aka barsu dashi sun hukuntu,
Amma ace ankawota irin gurin Nan dasai masu laifin babbar kisar gilla ake kawowa sbd kawai tayi Abinda ba laifinta bane,
Wani irin kunci da bacin Raine ya cika zuciyarsa yanajin ba'a taba yimusu rashin adalci ba tun takaicinsu irin wannan,
Yarinya qarama mace budurwa za'a kawo irin gurin Nan?¿
Yanda yakejin tsananin bacin Rai wallahi daba mahaifiyar Khalil ce tasata a wannan halinba wlh dasai yayi shari'a da duk Wanda yake cikin zuriar zabeera sbd arziki ba hauka bane hakama talaka ba dabba bane.


Shi kansa Dr khalil Jin yayi dukkanin gwiwoyinsa na sanyi zuciyarsa na cika da baqin ciki da bacin ran ganin anan Amatu take,anan aka kawota cikin masu manyan laifuka sbd kawai tayi qaramin laifinsa baifi ayisa agama cikin gidaba...


Babu Wanda ya iya yiwa wani Magana acikinsu sbd halin tsananin baqin cikin dasuka Shiga na ganin irin cin zarafi da wulaqantawarda akayiwa Amatu.




Koda suka Isa bakin office din commissioner Saida aka Shiga aka isarda zuwansu shima sbd Khalil din 'dan Zabeera ne da Babu wanda zai Bari ko hanyar office din su Isa.


Daga cikin office din commissioner kuwa Bayan anzo ansanar Masa da zuwansu waya ya dauka ya dannawa alhaji qarami Kira Wanda akaci sa'a a lokacin Yana gurin Andi.


Shiru alhaji qarami yayi bayan yagama sauraran Abinda commissioner ke fada Masa cikin mamaki yace"


Ya akayi yayi saurin ganowa Bayan kabada tabbacin aqalla har maganar taje court bazai gano inda takeba.??
Yanzu dai Bari na sanarda Andi saina kiraka kafin ka gansu.


Aje wayar yayi ya kalli Modibbo kafin ya kalli Andi cikin nutsuwa da girmamawa yace"


Andi khalilu ne yasamu gano inda take Yana bakin office din commissioner ma yanzu haka.


Dagowa yayi ya kalli alhaji qarami din da mamaki a fuskarsa kafin ya kalli Modibbo cikin bayyanarda mamakinsa yace"


Me Khalilu yakeson komawa ne akan mace????


Shiru Modibbo yayi Yana sauke Kai cikin takaici da mamakin Khalil din.


Sake bayyanarda mamaki da takaici Andi yayi Yana cewa''


Tabbas khalilu Yana buqatar hukuncindazai dawo dashi hankalinsa tunda yazabi wulaqanta hukuncina akan mace..


Dan gyara zama Modibbo yayi tareda gyaran murya cikin girmamawa yace"


Allah ya huci ranka Andi Amma sai Inaga tunda yariga yayi nisa duk wani hukunci sake tsaurara abin zaiyi tunda Babu wani a zabeera daya taba take hukuncin Manya sai akansa gashi yanzu kowa yafara ankarewa da hakan da azo ayi Abinda zaisa agano bijiewa yayi yayi watsi da hukuncinka asamu masu Goya Masa baya abun yayi yawa.


Shiru Andi yayi Yana sauraronsa cikin qoqarin son fahimtar zancensa
Ya dago ya kalli alhaji qarami dakeson Magana shima yace"


Kaikuma meye naka hasashen?


Gyara zama yayi Yana tausasa murya yace"
Inaga akashe maganar a idon duniya ma'ana a janye qarar amatsayin munduba maraicinta mun qyaleta idan yaso sai commissioner su saka kudin belin da Khalil din bazai iya biyaba idan yayi yayi Dole zai hkr kokuma ace za'a biya kudin belin Amma saiyayi alqawarin rabuwa da yarinyar
Hakan shine mafita a yanayin da ake yanzu sbd Khalil idan baa janye qararba zai iya dagewa qarshe ya aikata Abinda zai saka zabeera kunya.




Jinjina Kai Andi yayi Yana na'am da bayanin alhaji qaramin yace"


A aikata hakan Amma kafin Nan ayau nakeson Modibbo dukkanin Abinda Khalil ya mallaka na zabeera a karbe.


Kallonsa Modibbo yayi da sauri saikuma ya sauke Kai Yana jinjina hukuncin sbd kaf 'yayansa bama shikadaiba kusan duk yayan zabeera da arzikin Zabeera suke tinqaho MAHMOUD ZABEERA ne kawai Babu qwandalar zabeera acikin dukiyarsa da guminsa da wahalarsa yatara arzikinsa,
Idan akace akwace komai na Khalil to motarsa ta hawa da kudaden account dinsane kawai zai tsira dasu Dan kuwa ko asibitinsa dayake tinqaho da ita MAHMOUD ne ya Gina Masa ita amatsayin tayasa murnar zama cikakken likita.




Koda commissioner yabasu izinin shiga bai nuna musu komaiba suka gaisa kafin Khalil yafara Masa bayanin Abinda yakawosu Babu dogo musu yacewa Khalil din an janye qara belinta kawai zasuyi akan kudi naira miliyan daya sai kudin tarar bacin suna miliyan daya da rabi duba da yanayin gidan da akayiwa bacin sunan.




What?????"""Khalil yafada cikin tsananin mamaki da yiwa commissioner din kallon rashin hankali yace"


Beli ne wannan kokuwa hukuncin Rai da Raine wannan???


Murmushi commissioner yayi Yana gyara zama yace"


Dr khalil zabeera zaka iya Kiran lawyer dinka zamu basa komai a rubuce sbd samun qarin fahimta.


Kallon bakinsa kawu keyi cikin yanayin tsoron dayafi mamakinsa miliyan biyu kudin beli?gwarama su fito su fada musu bada itane bazasuyiba.


Koda lawyer din Dr khalil ya iso aka miqa Masa takardun belin da aka bugo cikin qanqanin lokaci ya karanta yasake karantawa zuciyarsa na tafasa ko ba'a fada yasan shirine akayi Dan quntata Masa shida su Amatun,
Koma menene akayi Dan a cimma bazai taba rabuwa da Amatu ba,
Idan anyi ne Dan aga gazawarsa tabbas bazai taba gazawaba zaiyi komai iya iyawarsa zaikuma qwatar Mata mutuncinta da yancinta.


Dagowa yayi ya kalli kawu da idanuwansa sukai jajir sbd tashin hankali saiyaji zuciyarsa ta sake karyewa ya waiwayo ya kalli commissioner cikin yanayin na nuna rashin gazawa yace"


Ahada takardun belin su zama ready zuwa gobe zankawo kudin.


Kallonsa sukayi da sauri duk su duka commissioner na boye mamakinsa akan Khalil din yace"


Shikenan Dr khalil zabeera muna jiranka goben.


Miqewa yayi ya fice kawu da Barr Bashir na bayansa kowannensu cikin damuwa Yana Isa bakin mota ya tsaya ya juyo ya kalli Barr Bashir da idanuwansa dasukai jajir yabude busashen bakinsa yace"


Barr zankiraka gobe muhadu anan abasu kudin inshallah.


Kallonsa Barr yayi cikin kulawa da jimami Yana cewa''


Dr khalil kana ganin zamu karbi belin Nan ahaka?
Inaga muje can zabeera aroqi maganar tarar ajanye Mana ita zaifi....


Girgiza Kai yayi Yana qoqarin boye rauninsa yace"


Ba buqatar hakan zanhada kudin zuwa goben Inshallah.


Shikenan tunda zaka iya biya ba damuwa Allah yakaimu goben.


Suna Shiga mota yayi shiru cikin tsananin damuwa da tashin hankalin ta inda zai Fara hada kudin sbd dukkanin kudin account dinsa ya rabesu gurin case dinnan cikin kwanaki kadan
Duka duka abindake account dinsa baifi dubu dari bakwaiba Kuma gidan haya yayi niyar kamawa dasu ya ajiye Amatun.


Bayan kudin account dinsa da motarsa baida wata babbar kadara sai tsadaddun agogunansa da wayoyinsa,
Asibitin dayake tinqaho da ita bata cikin lissafi sbd tamkar alamar qaunarssuce me qarfi dake tsakaninsa da 'dan uwansa.


Kallonsa kawu yayi cikin tsananin damuwa da sarewa yace"


Khalilu kada ka takura kanka da hada wainnan kudaden daba haduwa zasuyiba,
Qaddarace wannan me girma ta samemu wadda Allah zai fitar damu inshallah.,
Zamuje muyita addua Allah yabamu ikon cinye jarabawa sbd koba komai munqara bambamce halaye irin na wasu masu arzikin Wanda bayan suna Babu Abinda suka damu dashi,
Farin cikin yayansu da walwalarsu bai damesuba kamar yanda sunansu da girman kansu ya damesu.


Ahankali yaja motar suka bar gurin suka kamo hanyar gida har lokacin bai iya cewa ko qala ba sbd nisa da yayi a tunani.


Koda suka Isa ajiye kawu yayi ya wuce zuwa zabeera.


Parking yayi daidai sashen Modibbo yafito ya nufi ciki jikinsa da zuciyarsa amatuqar sanyaye.


Sallama yayi palon yashiga cikin sa'a Modibbon na zaune shikadai Yana kallon labarai Koda yaga khalil din Saida yaji tausayinsa Amma bai nunaba sbd ya dauke Kai Yana cigaba da kallon labaransa.


Gabansa ya zube tareda sunkuyar dakai wasu irin hawaye masu zafi suka gangaro daga cikin idanuwansa akaro na farko daya nuna gazawa cikin wani irin sauti Mai tsananin sanyi yace"


Modibbo Ina roqon yafiyarku akan dukkanin Abinda yafaru Dan Allah ku sassautawa Amatu wlh batada laifi akan hakan kuskure ne da rashin sanin ciwon Kai wlh batayi Dan wata manufar Bata suna ko wani Abu ba dabam tayine kawai sbd kudi Wanda tsananin rayuwa yakaita ga hakan.,


Modibbo Dan Allah Ina roqon gafara da yafiyarku Dan Allah ku duba maraicinta kada ku tsaurara Mata.


Juyowa Modibbo yayi ya kallesa sosai ganin yanda babban namiji jajirtacce kamarsa ke kuka ya sauke ajiyar zuciya Yana cewa"


Khalilu zancenka ba'a hannuna yakeba Amma amtsayina na mahaifinka zanfada maka Abu daya,
Kada kayi Abinda zai kawo maka matsalarda bazaka iya tsayawa kaga wucewartaba,
Idan kanason yarinyar Nan tsakani da Allah Dan tallafawa maraicinta to tabbas na amince maka ka aureta sbd aurenta ne kawai zaisa Andi ya iya sassautowa tunda tariga tazama Zabeera Amma idan kasan tsakani da Allah yarinyar Nan batada nasaba to Ina baka shawara kayi gaggawar cireta daga rayuwarka shine kawai sauqi da mafita agareka..




Da jajayen idanuwansa ya dago ya kalli Modibbon Yana nazartar zancensa wani irin sanyin sassauci na shiga zuciyarsa sbd ya fahimci zancen mahaifin nasa take sabon qwarin gwiwa yasake shigarsa ya sunkuyar dakai cikin sanyi yace"


Nagode Modibbo Allah yaqara tsawon Rai.


Yana fitowa sashen ummensa ya nufa inda ya tararda ita zaune tayi tagumi kamar koyaushe cikin kwanakin tana ganinsa tayi saurin miqewa ya hanata ta hanyar mayarda ita zaune yana girgiza Mata Kai murya a mace yace"


Umme zanbar zabeera......


A firgice ta kallesa idonta na cikowa da hawaye zata fashe da kuka yace"


No umme karki manta kinmin alqawarin bazakiyi kukaba Kuma kinyi alqawarin bani support adukkanin Abinda Zan yanke.,
Umme albarkanki nake nema a rayuwar dazanyi wajen zabeera dan Allah umme kimin alqawarin bazaki saka kanki cikin damuwar dazata cutatar dakeba.


Kasa riqe kukanta tayi ta fashe dashi tana cewa''


Khalil Dan Allah kada kabar zabeera kabarni katafi Dani Nima
Wlh bazan iya zama baka nanba,
Katafi Dani duk inda zakaje zanzauna acikinku,
Zan zauna taredaku zanyi renon 'yayan dazaku haifa........


Kasa hkr yayi ya rungumeta Yana girgiza Mata Kai Yana cewa''


Umme Zaki zauna anan gidan aurenki sai mutuwace kawai zata fiddaki zabeera.


Aa khalil zanbika Dan Allah kada ka tafi kabarni.


Ganin yanda ta daga hankalinta yasashi zamewa da sauri ya fice Yana danne zuciyarsa dake neman fashewa yayi hanyar sashensa.


Kayansa ya diba a akwati tareda kwashe agogunansa da takalmansa masu tsada sosai da duk abubuwan dazai buqata ya saka cikin mota tareda dukkanin takardunsa yafito yaja motarsa yabar zabeera.


Daga zabeera gidan Ibrahim yaje yafara ajiye kayansa acikin dakin farkon Shiga ya rufe dakin da mukulli ya fito yarufe gidan ya wuce.


Tareda Ibrahim din sukaje gurin masu Saida agogo akayiwa agogunansa kudi kaf aka shiye suka hada kusan dubu dari uku daganan gurin Wanda zai siye motarsa suka nufa aka Fara cinikin saidai abin son Rai yayiwa mutane yawa Dan siyan wulaqanci sukaiwa motar har kusan mutum shida sukaiwa motar siyan wulaqanci qarshe Dole ya saidata miliyan daya da dubu dari suka karba ya hada hadda kudin account dinsa suka tashi 2.6.


Mashin yahau Abinda baitaba hawaba a rayuwarsa ya nufi gidansu kawu anan yafadawa kawu ya hada kudin daga iyami har kawu basusan lokacinda suka fashe da kuka ba.


Murmushi me ciwo kawai yasaki batareda yace komaiba anan yayi sallar ishai iyami tasashin tuwon Dole kafin yatashi yatafi.


Mashin yasake hawa yakoma gidan Ibrahim Yana Shiga Allah ya taimakesa ana kawo nepa Nan ya tube yayi wanka da ruwan rijiyar gidan da Ibrahim yacika Masa durum da kansa masu shegen tsananin sanyi Wanda Saida suka saka numfashinsa kusan daukewa daya watsasu.


Boxer da singlet kawai yasaka yadawo ya kwanta Kan sabuwar katifar da Ibrahim din yasiyo yau yakawo Masa.


Kiran salman ne keta shigowa wayarsa Yana qin dagawa sbd duk kwanakin ya tashe duk banyarda salaman zaishigo cikin Al'amarin sbd bazaiso laifin ko wani Abu yasamesaba kodan yanda Amatu ta daukesa kamar usinta.


Kiran MD ZABEERA ne yashigo wayar ya qurawa wayar Ido tsawon sakanni kafin ya dauka Yana boye damuwarsa Nan suka hau Maganar shi cikin sanyi MAHMOUD Kuma cikin nutsuwa da miskilanci.


Koda asuba tayi daqyar ya iya dafawa ya tashi zaune sbd tsananin sanyin daya Gama shigewa ya Kama dukkanin qasusuwansa.


Daqyar yayi sallah ya jingina da bango Yana makure jikinsa guri daya sbd kaf gidan gaba daya koina sanyi yake fitarwa sbd gaf suke kusada ruwa.


Daqyar yaga qarfe Tara na safe tayi ya miqe yasake zuwa bayi ya watso ruwan sanyin yafito jikinsa na Dan rawa yashigo daki ya shirya cikin qananan kaya masu Dan kauri ya bar gidan sbd Jin kamar zai iya suma da ciwonsa dake gaf da tashi.


A gidansu kawu yaci biredi da kunun tsamiya tareda waina da iyami tasiyo Masa me kyau ta shinkafa.
Kobai fadaba sungama gano halinda yake ciki sbd kada su qara Masa damuwa sukaqi yimasa maganar sai tattalinsa dasukeyi.




Qarfe goma da rabi a central tayi musu shida kawu suka zauna zaman jira har qarfe goma sha biyu commissioner bai buqaci ganinsuba sai daya da rabi Bayan anyi sallah anfito tukuna aka kirasu suka Shiga.


Barr Bashir ne yacire kudin beli da Tara ya bayar akayi rubuce rubucen daza'ayi aka gama kafin akace afiddo Amatun.


Lokacinda aka kawota suna ganinta kowannensu idanuwansa suka ciko da hawayen baqin cikin ganin halinda take ciki Amma ita ganinsu yasata qaqalo qarfin hali tana danne azabar cizon sauri da galabaituwar yunwa da dau'dar datake ciki Danma tunda tazo koda Wasa ba'a taba dukantaba Wanda umarnin Andi ne kada a daketa ko so daya.


Babu Wanda ya iya mgn acikinsu aka Bata gyalanta da takalmanta suka fito tana tafiya daqyar a galabaice.


Suna fitowa titi taga suna qoqarin taron adaidaita ta kalli Dr khalil din da mamaki Kan fuskarta saidai batayi maganaba suka tare adaidaita biyu ita dashi suka shiga daya kawu yashiga daya.


Ahankali ya juyo ya kalleta cikin tsananin kulawa da damuwa akan fuskarsa yace"


Are you ok?


Kallonsa takeyi tana mamakin sauyawar dayayi
Yayi duhu tayi Rama hakama kamar Wanda baida lafiya sai Nishi Nishi yakeyi kamar Wanda yayi aikin wahala.


Kai ta daga Masa ahankali tana lumshe ido a wahalce.


Koda suka iso gida tuni mutanen gidan suka rude da murna da yiwa Allah godiya take aka hada ruwan wanka masu zafi aka Kai Mata
Maman junior hadda tayata wanka kamar me haihuwa haka aka gasata tasamu 'dan qarfin jiki aka Bata abinci taci tareda magungunan da Dr Khalil din yasiyo Mata ta kwanta take baccin wahala ya dauketa.




Da daddare kafin ya wuce Bayan yaci tuwon iyami cikin nutsuwa ya zayyanewa kawu duk halinda yake ciki yanxu tareda gabatarda buqatarsa na auren Amatun
Kawu ya sauke numfashi me sanyi yace"


Khalilu ko bakayi mgn ba nayi niyyar aura maka Amatu kobabu danginka ko daya sbd aduniya Babu Wanda ya cancanta yazama Dole yazama mijin Amatu idan bakaiba Dan haka wlh khalilu nabaka Amatu amatsayin Mata ka shirya nida kaina zanje masallacin juma'a nayi sanarwa ranar juma'ar Nan Inshallah za'a daura muku aure.
##Mamuh#
6/17/21, 8:05 AM - ': *_MQ 30_*








Wani irin sanyin farin cikine ya Shiga zuciyarsa Wanda ya manta rabonsa dashi ya kalli kawun cikin girmamawa yace"


Nagode sosai kawu
Allah yaqara girma da Nisan kwana.


Amin Amin" yace Yana cigaba da yimasa nasiha akan hakuri da rayuwa komai lokacine dashi wata Rana komai zai wuce.


Bai jira sake ganin Amatunba yanayin sallar ishai a masallaci taredasu kawu yayi Masa Saida safe ya wuce.




Ahanya ya tsaya ya siya cardigan me kauri da sabon bargo me laushi kafin ya wuce gida.


Sbd sanyi hatta qafaguwansa da hannuwansa Saida ya sakawa socks bayan yasaka rigar sanyin ya dunqule cikin bargo Amma har lokacin yanajin sanyi na shigarsa hakanan ya daure har wahalallen barci ya daukesa.




Washe gari da safe ba laifi da kuzarinta ta tashi saidai kawai sauyi sosai data gani daga iyami har kawu Wanda ya tabbatar Mata da fushi sukeyi sosai da ita sai taji hankalinta ya tashi duk yanda taso Basu hakuri ko fuska taqi samu Saida Dr khalil yashigo ne taga sakewar fuskarsu ta kallesa da Ido ta nuna Masa fushi sukeyi da ita yasakar Mata kyakkyawan murmushi Yana nuna Mata Babu ruwansa
Suna Nan zaune saiga salman zabeera yazo Yana ganin Amatu cikin tsananin farin ciki yaqaraso Nan aka hau sabuwar fira inda anan ne takejin dukkanin Abinda yafaru hadda komai da Khalil din ya rasa bayan aikinsa da asibitinsa baida komai yanxu.


Jitayi sabuwar soyayyarsa tasake shigarta hartanajin ko bayada komai zata auresa ta zauna dashi Kuma alqawarine ta dauka saita shiryasa da familynsa ta maidasa cikinsu.




Koda maganar aurensu sati me zuwa ta bayyana tuni kowa yahau murna Nan aka Fara shirye shirye musamman iyami data bada himma gurin gyaran Amatun ga umminsa ma kusan kullum saitazo gurin duba Amatun taso taimakawa sosai Amma Khalil ya nuna kada tayi Masa komai zai iya iya qarfinsa shiyasa Dole tabari sai itama ta maida hankali gurin gyaran Amatun sbd 'danta yaji Dadi.




Sauran kudaden dasuka rage Masa yaso Kama wani gidan hayar dasu Amma duk gidajen babu Wanda zasu iya zama saiya aje kudin da niyar bayan daura auren Koda da sati biyune zaiyi qoqarin hada kudaden dazasu Samar musu gida me Dan kyau.


A bangare daya sanyi yayiwa jijiyoyinsa da qashinsa muguwar shiga a 'yan kwanakin sbd yanxu takai kowane dare Baya iya bacci daurewa kawai yakeyi cikin mutane baya nunawa Amma ciwonsa yatashi matuqa yanajin yanda lungs dinsa sukai mugun laushi baya iya Jan numfashi yanda ya kamata duk iya qiqarinsa yanayi Dan ganin ba'a fahimci halinda yake cikiba.






_GERMANY_


Kallon hoton katin Daurin auren da Khalil yaturo masa yakumayi da fararen idanuwansa dasukai wani irin laushi lokaci daya ya lumshe ido Yana sake kallon hoton katin ya ajiye ahankali tareda miqewa ya nufi gaban qaton window din dakinsa dake kallon swimming pool din gidan ya zuba hannuwansa cikin aljihun three quarter din dake jikinsa Yana qurawa waje Ido zuciyarsa na sanyi.


Tunani zuciyarsa keyi Amma ya yakuce hakan Yana lumshe ido
Tabbas zai halarta sbd ranar farin cikin Dan uwansa ce.


Juyowa yayi ahankali tareda dawowa yadauki wayarsa daya kashe sbd rashin son damuwa ya dannawa PA dinsa Kira Yana dauka Kai tsaye cikin muryarsa me sautin girma yace"


Ka shirya Mana komawa gida jibi akwai Daurin auren dazan halarta.


Done sir.


Kashe wayar yayi ya ajiye Yana sake karanta sunan dake rubuce 6aro 6aro akan hoton katin KHALIL DAHEER ZABEERA da AMATULLAH K SALEH.


sake dauke Kai yayi yana lumshe ido tareda sauke ajiyar zuciya ya juya yabar gaban labtop din.






_NIGERIA_


da kanta ta shirya tsaf Babu Wanda yasani ta fito suka fita da salman zuwa zabeera mansion.


A sashen Andi sukai parking tafito ahankali tana kallon koina komai na dawo Mata sabo tana tuno yanda tabar anty zarah dinta cikin kuka da damuwa take taji idanuwanta sun ciko da hawaye Bata damu da tsaidaduba Saida suka gangaro tasaka hannu ta gogesu ta nufi qofar shiga palon Andi din ta tura tashiga da sallama

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login