Showing 1 words to 3000 words out of 108906 words
Chapter 1 - MIN-QALB Book Complete Document Hausa Novels By Mamuhagge .txt
MIN-QALB
_Mamuhgee_
1
Bismillahir-rahamanir Raheem.
Qoqarin durqusawa takeyi ta dauki busashen biredin dataga wani yaro yazo ya zubar a babbar bolar bakin anguwar wadda za'a Kira da qaramar kasuwa sbd hargitsi da cunkushewar anguwar da manya da qananan kwatocinda suke cike taf da ruwa da ledoji tareda qananan abinci na wanke wanke dasuke biyowa,
Daukar biredin tayi tana kakkabewa tareda kaiwa bakinta daya gama bushewa yayi fari fat harya Fara yayyankewa alamar ko yawun bakinta sun gama bushewa ta gutsura kadan ta Dan tauna taji zai shiga
Da sauri ta qarasa turasa cikin bakin tana taunawa da sauri jikinta na rawa tareda hanjinta dasuke qugin jin wani abu ya saukar musu bayan kwanaki dasuka Dan dauka a na'de.
Ganin wani almajiri yayo gurin Yana kallon biredin a yunwace Shima Dan ko gabansa baya kallo idonsa nakan biredin ko kyaftawa bayayi yasa tayi saurin miqewa tana qara tura biredin cikin bakinta da sauri sauri tana kallon almajirin karya iso gurinta Bata cinyeba ya kwace sbd wannan shine Abinda yake faruwa a bolar qwacewa daga marasa qarfi Wanda a duniyarma hakane duk me qarfi shike qwace Abinda yakeso gurin masashi,
Batada uwa batada uba,
Batasan kowa aduniyaba Wanda zata ce nata ne,
Ita aduniyarma gaba daya batasan komaiba face yawon bola da tsince tsince.
Almajirin na isowa gurinta yayi wuf da qarfi ya qwace biredin hannuwansa na rawa Shima yakai bakinsa yanaci da sauri sauri Yana hadiyewa ko taunawa bayayi sbd sauri yakai bakinsa.
Kallonsa takeyi tana hawaye tana lashe sauran Dan gari garin biredin dake hannunta tareda uwar dau'dar dake tafin hannuwan nata dasuka sauya kala sbd dau'da.
Tana kallo ya cinye biredin ya dago Yana kallon hannuwanta ko zaiga wani abin naci sbd yunwar dakeci hanjinsa yakai ko numfashi baya iyayi ko mushe yagani zai iya ci sbd qarfinsa daya gama qarewa gurin yawon bara.
Ganin yanawa hannuwanta kallon yunwa yasa ta juya ta tafiyarta zuwa tsakiyar bolar tana bincikawa ko zata Kuma samun wani abin.
Yarinyace qarama sosai Yar kimanin shekaru bakwai saidai yunwa da wahala Sunsa ta matse sosai kamar Yar shekaru shida,
Dau'da tasa fatarta takoma baqiqirin ko tantance asalin kalar fatarta ba'ayi
Ga gashin kanta daya gama tsinkewa sbd dau'da da zamansa a bude.
Gangarawa tayi yafito cikin bolar tana qoqarin bude gwangwanin data samu cikin bolar fuskarta na nuna 'dokin son ganin me tasamo.
Bakin shagon alhajiyat me abincin bakin titin ta zauna daga can gefe inda ake Mata wanke wanke ta faki idanuwansu ta dauki wata matacciyar butar tsarkinsu ta Dora baki tafara kwankwadar ruwan da sauri sauri wani sanyin rahama na sauka cikin hanjinta ita batamasan wani abu qazantar ruwanba burinta dai su sauka a cikinta.
Fizge butar akayi da qarfi tareda jefarwa cikin masifa matar tasaka qafa ta tureta gefe tana cewa'"
Wannan yarinya wlh anyi muguwar mayya,
Yarinya saikace kafira ayita korarki Amma kullum saikin zo.
Kallon matar takeyi tanason yin kuka Amma Sam takasa sbd tunda ta taso batasan wani abu waishi so,qauna,kulawa ba ko gata bare tasan zafin rashinsu hartayi kuka.
Tunda tafara wayo daga ita sai kakarta kurma suke rayuwa a wani mataccen kangon shaguna wadda ita a wayonta batasan shin kakartace kokuma mahaifiyarta
Itadai tasan itace komanta gashi kurma ce bataji Bata iya mgn ga tsufa ahaka suke rayuwar Bara da yawon bola neman rubabben abincinda zasuci idan dare yayi sukoma shagunan dasuke kwana su kwanta duk da Basu kadai bane shagunan duk mabaratane da nakasashshi,
Koda iya tsohuwa tayi kwanaki kusan ashirin a kwance batada lfy tana gani tana kalla 'yarinyar ke fita yawon bola da bara tana ciyo abinci dame kyau da Mara kyau,
Wani lokacin ma idan ta ciyo Mara lafiya tana gani zatazo tayita amai da zawo Amma ahaka take sake fitarta tasake samowa Koda a bolar ne taci abinta,
Ciwo da yunwa da tausayin ganinsu ahaka yasa jikinta yin tsanani matuqa ahaka ta rasu batareda jamaa suna ankaraba ita Kuma batada wayon dazatasan meke faruwaba ahaka gawar tayi kwana biyu da yini take layin yafara daukar wani mugun wari wanda yasa sukasan akwai gawa.
ahaka kullum da daddare itakam take zuwa ta kwanta gefen gawar tayi kwanciyarta tayi bacci gari ya waye ta fita.
Koda aka gano gawar take suka Kira Yan sanda akazo aka bincika gawar suka tabbatarda rasuwa tayi ba wani alamar kasheta akayi suka kwashi gawar akai daji da ita acan aka binne a wata qaramar baqabarta.
Tundaga lokacin rayuwarta tasake gararewa sbd ankorosu daga waincan shagunan yanxu duk inda dare yamata acan take kwana saidai kasancewar shagon abincin alhajiyat na sabuwar anguwar data fado masu dafa Mata abinci anan suke kwana shago yasa itama ta fake anan bayan shagon take kwanciyarta tayi baccinta.
Bayan qawace butarda matar tayi komawa tayi gefen shagon daga inda suke watso ruwa ta zauna tafara qoqarin bude gwangwanin Amma Bata iyaba takasa.
Kokuwa takeyi da gwangwanin tana saka farcenta tana budewa da qarfi Amma takasa sai jin tayi ankwace ta dago da sauri taga almajirin daya qwace Mata biredi ne da sauri ta miqe tana kallon gwangwanin hawaye na cikowa idonta tace"
Abuna ne kabani inaso"ta qarasa tana Kai hannu zata karba ya tureta ya juya da gudu Yana qoqarin budewa Shima.
Zaunawa tayi agurin tana hawaye daganan bacci yayi gaba da ita dama gashi yamma tafarayi.
Cikin bacci tasaki fitsafinta Wanda tsumman kayan jikinta suka shanyesa ko gangarowa beyiba.
Mangariba bayi ta farka tazo ta zauna gefen qofar shagon tana rarraba idanun samun Abinda zaa jeho waje.
Ahaka har akayi ishai qarfe Tara tayi Bata samu komaiba ta miqe tana Sosa kanta dake danqare da dau'da Takoma bayan shagon tayi kwanciyarta.
Gari ba wayewa ta miqe ta kama hanya neman Abinda zataci.
Yauma duk Abinda tasamu almajirin jiyane ya qwace Mata ya cinye Kuma duk inda tayi kusan Yana biyeda ita sbd ga dukkan alamu shi sabon zuwa ne kamar baisan ko inaba kamarma baisan ya ake hakurin yunwaba sbd shi komaima yasamu ci yakeyi gashidai Shima zasuzo sa'a daya danshima bazai wuce shekaru bakwai dinba.
Abun mamaki almajirin Nan saigashi gurinda take kwana Shima anan yake kwana idan gari ya waye tatafi duk inda tayi Yana biyeda ita.
Ganin haka yasa yanxu tana samun Abu take rabawa biyu tabasa Rabin tun bai qwaceba ya cinye.
Ahaka harsuka Saba sosai lokaci yaza sosai duk inda zasu tare suke zuwa harsuka samu wata roba a wata babbar bola da ita suke zuwa bara.
Yau Kam ranar babu wata sa'a acikinta sbd ko ruwan dazasu sakawa cikinsu Basu samuba duk inda sukace korarsu da hantararsu akeyi sbd bayan wari da zarnin fitsarin tareda tsamin dau'da babu Abinda sukeyi.
Kwanciya sukayi cikin bacci tafara jiyo sheshekar kukansa tayi saurin tashi zaune cikin tsoro ta kallesa tagansa zaune riqeda cikinsa.
USMAN?????? takira sunansa cikin sanyin maryar dake bayyanarda itama a galabaice take sbd yunwa.
Dagowa yayi ya kalleta da ido sharkaf da hawaye yace"
Amah cikina ciwo sosai.
Tashi tayi tareda kallonsa kafin ta juya tana cewa'"
Zansamo ruwa saimu sha.
Tana juyawa wasu manyan samari su biyu dake boye suka fito tareda toshe Masa baki suka dagasa cak suka wuce dashi suna zuwa motarsu suka bude da sauri suka jefasa da gudu suka bar gurin.
Cikin sanda ta Isa qofarsu alhajiyat ta dauko butarsu dake cikeda ruwa ta sidado ta dawo da sauri saidai tana zuwa taga babu usaman din cikin sauri ta ajiye butar tafara duddubasa koina tana Kiran sunansa.
Har kusan asuba Bata gansaba tadawo ta zauna shiru tareda qurawa robarsu ido,
Akaro na farko arayuwarta bayan iya tsohuwarta data samu wani arayuwarta Wanda taji ayau tanason karya tafi koina ya tsaya gurinta suyita yawon neman abinci atare,
Tasaba da usman sosai sbd a yanzu Koda Basu samu Abinda zasuciba sunada junansu damuwarsu kadance tunda suna debewa juna kewa.
Har gari ya waye Rana ta fito Bata gansaba tayi yawon duk inda suke zuwa bara tare Amma Bata gansaba ga yunwa ga gajiya ga qishirwa ga Rana haka ta dawo agajiye da daddare ta kwanta bayan Tasha ruwan butarsu alhajiyat.
Cikin bacci gaji motsin mutane tana bude ido taga wasu su biyu sunzo gefenta sun anjiye Usman din sun jiya da sauri sun tafiyarsu.
Da sauri ta tashi tana cewa''
Usman Ina kaje??
Bai motsaba sbd ko numfashi baya fitarwa
Ta juyoda fuskarsa tadan bubbuga tana sake Kiran sunansa har lokacin bai motsaba.
Ganin kamar bacci yakeyi yasa ta gyara Masa kwanciya tareda juyawa ta kwanta tanajin Dadi akaroro na farko a rayuwarta sbd usaman yadawo.
Koda gari yayi haske ta tashi har lokacin usman be tashiba ta dawo gabansa tana Kiran sunansa ya bude ido ya kalleta idanuwansa jawur jikinsa nata wani irin rawa atake taji tsoron ganinsa cikin yanayi da sauri tace'
Usman menene? Kanajin yunwane haryanxu? Cikinka na ciwone haryanxu ma??
Ahankali ya nuna Mata duwawunsa Yana hawaye da dasasshiyar murya yace"
Sunmin wani abu anan zafi yakemin sosai''sai kawai ya fashe da wani irin kuka Yana dafe gurin sbd tsananin azabar dayasha agurin dasuka dannesa sukai amfani dashi.
Ganin irin kukan azabar daya keyi yasa itama tafashe da kukan ahankali musamman dataga jini a wandonsa tasan ciwone suka jimasa duk da basanma menene Abinda sukayiba.
Wasa wasa sai zazzabi ya rufe usaman sosai har jikinsa na wani irin mazari duk saita rude takamasa suka kutsa cikin kasuwa neman bara.
Suna shiga kasuwar taji wani me magani da lasifika Yana cewa'
Idan duwawunka ba ciwo baka iya miqewa bayan bahaya to kazo Muna mafaninka,
Idan kanajin fitsari baya fita sosai Shima kazo munada maganinka.
Da sauri taja hannun Usman dake tafiya a duduqe sbd ciwo da zazzabi sukazo gaban mutumin ta kalli maganinsa tana nunawa tace'"
Wannan zaka bawa Usman yaji ciwo a duwawu.
Kallonta me maganin yayi kafin ya kalli Usman da kyau Yana tauna goro da jajayen haqoransa ya washe baki tace'"
Ku kawo kudi' yana miqa musu hannu.
Kallon hannunsa sukayi kafin ta dago ta kallesa ta girgiza Kai alamar ita batamasan meyene ba.
Dari diyar ya fidda tareda nera dubu daya ya budesu ya nuna musu Yana cewa"
Kuje ku samo wannan ko wannan ku kawo nabaku magani yanasha zai warke.
Kallonsa tayi tana sake kallon kudin hannunsa kafin suka juya jikinsu a sanyaye sukabar kasuwar.
Kwana biyu jikin Usman babu wani sauqi gashi itama qarfinta yafara qarewa dole ta fakaici idon mutane da daddare tashiga shagon alhajiyat ta sato irin kudinda me magani ya nuna musu har guda uku.
Tana fitowa suka boye tunda safe suka shiga kasuwar neman me magani cikin saa suka Ganshi tabashi kudin duka tsabar zalinci saiya karbe duka dubu ukun yabasu canjin dari biyu tareda maganin Dan kanoma yafada musu su siya Koko susha dashi.
Kokon duka Darin biyu tasiya musu Usman yasha maganin ta shanye sauran kokon jikinta na rawa.
Dayake Shima Usman din harda yunwa dake cinsa yasa jikin tsananin
Saigashi sun samu qarfin jiki bayan sun shanye kokon take suka kutsa kasuwa bara.
Da daddare yauma batada zabi bayan sake sato kudin
Tunda safe suka sake siyan Koko yau harda qosai.
Sannu ahankali sata tashiga jikinsu
Tun alhajiyat Bata ganewa ana Mata sata harta gane tafara saka ido sosai akan son kama barawon.
Cikin saa takamasu aikuwa tasa akayi musu mugun dukanda Saida suka fita hayyacinsu Kuma tasa aka koresu daga anguwar gaba dayama.
Wata sabuwar anguwa suka fada wadda tafi wadda suka baro hargitsi saidai wannan din 'yan ta'addane sukafi yawa acikinta sbd gasunan koina suna shaye shaye.
Cikin saa nanma suka samu wata tsohuwar makaranta suna kwana aciki sauqinsu daya makarantar nada megadi shiyasa sukejin saukin kwana.
Ranarda suka cika kwana shida a sabon gurin cikin dare suna dawowa wasu maza biyu suka taresu.
Saurin riqe hannun juna sukayi suna ja da baya sbd yanzu sunfara wayo sosai.
Damqo amatu dayan yayi da qarfi Yana cewa'"
Kai saketa ka ware daga Nan gun.
Dayan hannunsa yasa yaqara riqeta Yana girgiza Kai alamar aa.
Wani wawan Mari dayan ya sakar Masa Wanda yasashi ihu.
Suka toshe masa baki tareda matsesa
Shikuma dayan ya fizge amatu tareda kwantarda ita qasa da qarfi.
Kuka tasaki tana miqawa Usman hannu tana Kiran sunansa itama da sauri dayan ya rufe Mata baki Yana qoqarin cire wandonsa.
Kuka sukeyi duk su duka musamman Usman dayaga irin Abinda akai masane zaayiwa amatu Kuma ya dandani tsananin azabar hakan bazai Bari amatu ta dandana ba.
#mamuh.
#Zafafa biyar#
Saran boye
Billyn Abdul
Abin dake zuciyata
Hafsat rano
Kibiyar AJALI
Miss xoxo
Siradin rayuwa
Safiyya huguma
Min qalb
mamuhgee
Pay@
09033181070
Or
09032345899
6/17/21, 8:01 AM - ': *_MIN QALB 3_*
_mamuhgee_
_Min qalb Na kudine_
Daki 'daya ya dauka iyami da amatu suka dauka daya
Sabuwar rayuwa suka Fara a gidan inda ake zaman rashin nasiha da ragawa juna,
Sam gidan kowa ta kansa yakeyi Babu Mai ta6uwa kowa ka taba Babu sauki sai masifa.,
Hakan yasa suma ahankali rayuwa ta koya musu yanda take,
Sunaji suna gani itama amatu ta ajiye karatu suka fada gwagwarmayar neman abin rufawa Kai asiri,
Amatu da iyami suka bazama neman ayuka
Ita iyami tasamu aikin abincin wata makaranta amatu Kuma tasamu aiki bookshop din wata iyamura.
Bata wani jima tana aiki gurinba saigashi Shima Usman aka kamasa aka rufe kusan wata biyu ga iyami ma tana fama da ciwon diabetes sai kawai tace Mata ta ajiye aikin abincin makarantar kada taji ciwo al'amarin yaqara lalace musu.
Hakan yasa nauyi yahau kanta na kulada iyami damuma nauyin ci da shansu.
Rayuwa da lokaci sune suka koyar da ita darussa da dama wanda ayanxu take musu kallon fahimta,
Tunda lalurar nauyin ahalinsu tadawo kanta Bata taba samun Wanda yadubeta da fuskar taimakawaba kowa da wata mummunar manufa yakeson taimaka mata,
Ansha niyar lalatar Mata da rayuwa tana tserata,
Ansha wulaqantata akan ana Mata kallon fandararriya Mara asali,
A ranarda wani yayi niyar lalatar Mata da rayuwa ta dole da niyar zai taimaka musu aranar ne zuciyarta ta gama qanqansewa da duk wani alamarin mutanen duniya
Shiyasa take Kiran kanta da furen kan juji.
Iyami ma hakan yasake busar Mata da zuciyar zata nemi kudi kota yayane Banda haram,
Babban Abinda ke qara kawo tabarbarewar zaman lafiyarmu shine hukunci akan Wanda hukuncin laifinsa bai Kai ba shike kawo sauyawar tunani da zuciya,
To kusan hakance tafaru da ahalin kawu,
Bayan fitowar Usman tuni zuciyarsa ta gama kangarewa sbd rufesan da akayi suncire Masa tsoron gidan yari Kuma,
Rayuwarsu tadawo sabuwa,
Burinsu shine kudi,
Farin cikinsu shine kudi,
Mafarkinsu shine kudi,
Mafarkinsu shine kudi
Idan har kudi suke Hana Dan Adam wulaqanta da tozarta tareda azabta Irin wadda suka taso suka rayu acikinta to tabbas sun shirya samun kudi Koda na wani ne.
Basu sake jinjinawa alamarin kudi ba Saida sukayi belin kawu da kudi naira dubu dari bayan yayi shekara daya da wata Tara gidan yari.
Babban al'amarinda ya shallake tunanin abokan zamansu na gidan hayan shine qarmashewar da zuciyar kawu tayi fiyeda ta kowa acikinsu game da kudi,
Yana fitowa gidan yari Abinda yafara fada afili shine'"
Idan har kudi sune maganin wulaqanci da toxarci tareda maganin wani baqin ciki to tabbas burina yanxu shine kudi,
Kudinma ba qananun ba manya nake buri.
Shekaru sunja sosai alamura sunyi haske sosai a rayuwarsu sbd kowa yanada hanyoyin samun kudinsa,
Acikin gidansu dake cike tab da 'yan haya to tabbas Babu me masifa da fitinar kawu,
Bayada sauki ko kadan Dan babu ubanda yake ragarwa a gidan ciki kuwa harda alhaji mande me gidan,
Duk masifaffun gidan suna shafawa kawu lafiya sbd fitinarsa Amma shikuma iyami ce kawai daidai dashi sbd ko atsakaninsu basawa juna nasiha ko sauqi.
Damuwa,kuka,kunci,baqin ciki,takaici,tuna baya
Wainnan duk wasu abubuwane dasuka binne a bayan rayuwarsu,
Sun koya su ciyar da kansu tun basusan kan nasuba,
Sun koya tsayawa da qafafunsu da junansu tun basusan meye duniyar ta qunsaba,
Sunyi yaqi da wahala da yunwa tareda azabta su kadai batareda wani ya tallafesuba,
Sun yakice tsoro tun basusan meye tsoronba
Dan haka su aduk yanda rayuwa tazo musu yanzu basuda damuwa da ita sbd sunsan babu wata gwagwarmayar data fi wannan din.
Wannan shine rayuwarsu,
Rayuwar 'yancin Kai rayuwarda baduda burin komai cikinta saina suji Dadi su dawwama da juna acikinsa.
AMATULLAH yanxu rayuwarta takeyi cikin jin Dadi da walwala,
Babu Abinda ya dameta face taji dadin rayuwa tareda ahalinta data keda burin su samu duniya suji dadinsu,
Duk inda tasamu aiki Bata jimawa ake watsewa sbd halayenta na Babu Abinda ya dameta bayan shiririta da yin duk Abinda taga dama
Duk Wanda yayi gigin shiga huruminta kuwa Yara take sawa qanana su koyawa mutum hankali kokuma usi Wanda beda aikin yi yanxu sai yawon banza sai idan ansamu na sanfewa a sanfe.
Amatu kyakkyawar cikakkiyar budurwace yanxu wadda tagama hada komai musamman kyawun jiki da fuska.
Maza ko gigin zuwa nemanta basayi sbd a duniya idan akwai Abinda ta tsana fiyeda komai to mazane idan aka cire usi dinta da kawunta.
Kana cewa kana sonta zata saka ahada maka jini da majina Wanda usi ne me aikin shida wasu abokanansa.
Ayanxu Kam sunsan duniya sunkuma darassantu da iliminda tabasu shiyasa akoda yaushe ashirye suke da duk sabon darasinda zata kawo.
AMATULLAH K SALEH shine cikakken sunanta Wanda kawu yabata aranar da yafara kaita makaranta,
Usman K saleh 'dan uwantane da aduniya babu Abinda takeso da qauna sama dashi,
Zata iya sadaukarda rayuwarta data Bari wani abu ya samesa,
Hakama zata iya sadaukarda komai sbd shi sbd sunawa juna kallon uwa daya uba daya suke ko kawu baitaba sanin ba uwa daya uba dayane ya haifesuba duk da Shima bakowane yasan cewa bashine mahaifinsu ba musamman da kusan halayen amatu duk nasa ne na rashin hakuri ko kadan,
Acikin su hudu kuwa baasan waye yafi wani son kudi da abun duniyaba shiyasa ake musu laqabi da dangin tsamiya.
Arayuwarta tayi aiki kala dabam dabam zai Kai goma koma fiye Wanda takeyi yanxu a restaurant shine kusan na sha daya
Hakama kawu yayi sanaoin harya gaji Amma yaqi kudi shiyasa ya tattara ya watsar yakoma zaman saka ido da jiran Wanda tsautsayi zaisa ya tabasa yaga masifa tareda siyan radio yakoma Shan waqe waqen gargajiya wanda kowa naji ba halin mgn sbd Shima ubanda zai tanka dinyake nema Amma haka kowa ke dannewa sbd azauna lfy duk da gidan kullum cikin fada da hayaniya ake.
****
Qarar waqar sani sabulu ce ta _duniya wandon roba_ ta cika gidan ta karade wane daki da saqo na gidan sbd qarar muryar radio din da aka Kai qarshe gaba daya.
Hankalinsa kwance yake yana Shan waqarsa Yana sakace haqoransa da tsinke
Daka gansa zakasan babu Abinda ya damesa.
Dukkanin mutanen gidan 'dai 'dai suka ringa fitowa rayukansu a 'bace da takaicinsa na kullum Wanda inda sabo sun Saba da dabi'arsa ta tayardasu kullum da sautin radionsa da muryarsa Bata qasa
Gashi bamai ikon mgn 'yar gaban goshinsa da shaqiyin dansa suce ba Wanda ya isa
Amma rshin arzikinsu babu kalar Wanda basa fafatawa dashi wanda kallo daya zakayi musu kasan su din abin mamaki ne,
Rayuwarsu abin kallo ce sbd sudin abin mamakine.
Yana ganin mutanen gidan sunfara fitowa ya sake dauke Kai sama Yana jiran yaji wani Mai shafaffun Mai akai