Showing 108001 words to 111000 words out of 139085 words

Chapter 37 - KALLON KITSE Book Complete Document by Halima k Mashi .txt

a zuba ruwan alwalar, idan ya yi sallah sai ya yi wanda da su amma a buta za'a zuba ruwa."


"Na fahimta, nago..." Katse shi ya yi da cewa "Kar ka fara min godiya, in ba haka ba maganin ba zaiyi ba ma, ko ka manta wanene kai a wuri na?"


Dariya malam Ali ya yi ya mik'e, saida ya shiga cikin gidan su ka gaisa da matan kafin ya fito ya samu dreban nan su ka wuce da cewa sai sun zo suma wajen bikin Nura, kamar bai je ko ina ba sai gashi ya dawo ko rana bata gama haska duka gari ba, jika maganin ya yi da wannan ruwan kafin ya shiga wata sabgar ba tare da ya fad'awa kowa ba.




*Yamma* lik'is Khadija ta fito bayan ta biya ta karb'owa Bilal sabon d'inkin shi sannan ta zo gidan, ta na sallama kam gida dama ya samu hallarar dangi har an fara d'ora tukunyar abincin d'aurin aure, nan fa kowa Hajia Khadija Hajia Khadija, sosai ta gaisa da mutane kafin ta wuce d'akin Hajia, abun mamaki sam Hajia kasa had'a ido ta yi da ita sai haka suka gaisa cikin kunya, su Hassana ma da Rabi'a haka, sai ma wani sabon al'amari daga gare su na kowa ya na son ya mata magana, wurin zama suka samar mata tare da kawo mata ruwan sha da lemu, sai dai suma ba kowa ke kallon ta ba, ita kam ko a jikin ta sai dai ba ta sakar mu su fuska ba, kuma ta zo gidan nan dan ta ga malam ta bashi wannan maganin, dan ita bata san yanda za ta sa shi ya yi wanka da shi ba, ganin sun baibaiye ta ya sa ta fito tace su yi aiki, sai lokacin Bilal ya shigo Khadija ta tambaye shi ina malam? A cewar shi ya na k'ofar gida tare suke da shi ma, aika shi ta yi ya yo ma sa magana, a soron gidan su ka had'u da malam in da ta bashi magungunan ta fad'a mi shi duk yanda akayi, murmushi malam ya yi ya mata godiya tare da fatan alkairi, ciki ta koma ta yi zaune su na b'are tafarnuwa, malam kuma na fita ya kira Usman a waya ya na d'auka yace "Duk abin da ka ke ka zo gida yanzu ka same ni."


Usman da ke tsaye gaban gado ya na kallon Haseenah ta na shiri zai kai ta can ne yace "To malam, dama yanzu za mu taho gidan."


Datse kiran kawai malam ya yi yayin da ya bi wayar da kallo, kallon Haseenah ya yi da ta mik'e ta saka hijabin da ya dace da kayan ta haka ma jaka da takalmi, a gaskiya ta yi kyau sosai cikin wani bak'in leshi mai ji da kud'i da kyau, kwalliyar da ta yi kai kace yau ne bikin kuma ba aiki ne za ta tafi kamawa ba, wayoyinta biyu ta d'auka duka a hannu ta rik'e suka fito, da kan shi ya bud'e mata k'ofa ta shiga kafin ya ja suka bar gidan yamma ta k'ara yi sosai.


Daga nesa ne aka fara kiran sallah hakan ya sa Khadija tashi ta yi alwala ta shiga d'aki dan yin sallah, ta na shiga d'aki ta kabbara sallah ta ji sallamar Usman, saida gaban ta ya fad'i kafin ta saita nutsuwar ta ta ci gaba da sallar ta, gaisawa ya yi sosai da mutanen da ke wajen in da Haseenah ke gaishe da mutane ciki-ciki, fita ya yi tare da malam ysu ka yi alwala in da malam ya tara ruwan shi ya aje suka nufi masallaci, mata ma alwala suke su na sallah, Khadija na fitowa daga d'aki Haseenah za ta shiga, dukansu gadara su ka nuna in da Haseenah ta had'a da girman kai da raini, babu wacce ta matsawa wata dan ta wuce hakanne ya sa su ka bangaji kafad'un juna su ka wuce, tsaki Haseenah ta k'ara da shi wanda ya sa Khadija jawo hijabin ta ta kalli fuskarta tace "Kamar tsaki na ji kinyi ko? Da ni ki ke?"


Cikin nuna isa tace "Sake min hijabi malama." Dawowa Khadija ta yi cikin d'akin yanda ta ke fuskantar ta da kyau, k'ara shak'o hijabinta ta yi za ta yi magana Hassana ce ta shiga tsakani tace ma Khadija "Dan Allah yi harkar gaban ki, kinsan sai ka kula kashi ka ke jin warin shi, kare kuma ai ba ya haushi shi kad'ai."


Kallon ta Khadija ta yi tace "Ta ci albarkacin ma su albarkaci." Ta na fad'a ta fito daga d'akin ta na mu su sallama, Haseenah kam kallon Hassana ta yi wato ma ita ce karyar? K'wafa ta yi a ran ta ta zauna ko sallah ba ta yi ba, ta na kaiwa k'ofar fita malam ya tiso k'eyar Usman zuwa d'akin shi, tsaye ta yi su ka yi sallama da malam Usman kuma idon shi na kan cikin ta dake cikin hijabi ya ke ganin kamar gizo, shigewa malam ya yi Usman kuma ya tsaya bakin k'ofar k'ik'am, rab'awa Khadija ta yi za ta wuce sai kawai ya had'a ta da bango ya rufe kamar zai rumgume ta, kallon fuskar ta ya ke cikin wata irin murya yace "Me na ke gani a jikin ki ne haka?"


Fuska a had'e ta kalle shi ta na sake gyara hijabinta tace "Me ka gani?" Hannu ya zuro zai tab'a cikin ta yi saurin bige hannun shi ta ture shi ta kalle shi tace "Ka zama mai d'a'a mana, haka kawai sai ka tab'a jiki na."


Za ta fita ya rik'o hijabin ta yace "D'a'a? Ni ne marar d'a'ar?" Kafin ta yi magana ya fizgo ta ya had'a da bango, saida ta rintse ido tace "Ashhhhh." Saboda zafin da taji, hannu ya sa cikin hijabin ta ya na fad'in "Bara kiga rashin d'a'a, ke da kinsan ba na da d'a'ar kuma ki ka aure ni? Yanzun ma fitsara za ki min kenan." Da sauri ta rik'e hannun shi da ke shirin shafa cikin ta, kallon idon ta ya yi yace "Ban sani ba ko gizo ne ido na ke yi min, amma sai na ke gani kamar ciki ne a jikin ki."


Shiru ta yi ta kasa d'ago kai ta kalle shi, hannunta da ta rik'e na shi hannun ya kama yatsunta sosai ya na murzawa tare da juyasu son ran shi, tun ta na jurewa har ta fara matse ido saboda mugunta ce yake mata, jin idon ta na neman kawo ruwa ne ya sa ta kalli cikin gidan tace mi shi "Malam fa na jiran ka."


Da sauri ya saki yatsunta ya d'an ja baya ya juya ya kalli cikin gidan shi ma, ta na ganin haka ba ta b'ata lokaci ba wajen takawa da sauri ta bar soron gidan, juyowa ya yi dan ya kalle ta sai ya ga wayam, cije leb'e ya yi tare da k'wafa yace "Wato ni za ki rainawa hankali ko, ki na d'auke da ciki na amma ki na b'oye min, wallahi na tabbatar da gaskiya sai ran ki ya yi mugun b'aci, sai kin gane ba'a min haka a zauna lafiya."


Ciki ya shiga ya samu malam a d'akin shi, abun mamaki shine izini da malam ya masa ya shiga ban d'akin shi ya yi wanka da ruwan da ke cikin bokiti, idan ya gama sai ya d'auki wanda ke cikin buta suma ya yi wankan da su, yanda fuskar malam ke had'e ya sa dole bai iya tambayar komai ba face shiga ya yi abin da aka ce, tunda ya yi wanka da ruwan cikin bokitin nan ya ji kan shi ya masa bala'in nauyi, jiri ne ya dinga d'ibar sa har saida ya rik'e kan panpo kafin ya ji ya fara masa sauk'i, butar ya d'auka ita ma ya kwararo ruwan daga sama har k'asa, rawa ya ji jikin shi ya d'auka kamar mazari, bala'in da yake ciki ne ya sa ya kasa sako kayan shi sai towel d'in malam da ke rataye ya d'auro ya fito, malam na zaune ya na jiran shi da kaskon garwashin wuta, har zaiyi zaune saboda abin da yake ji sai malam yace "Dakata."


Tsaye ya yi malam yasa maganin nan ya na kewara shi da shi, Usman da hatta numfashin shi ya fara canzawa kasa tsayuwa ya yi sai kawai ya fad'i k'asa kwance ya na rawar d'ari, k'amk'amewa ya yi sosai ya na rawar d'ari, sunkuyawa malam ya yi yace "Fodio lafiya ko? Me ka ke ji?"


Cikin hard'ewa da hak'oran sa keyi ya iya had'a kalmar "S...ss..an..yi...na..ke.ji." Aje kaskon malam ya yi ya shiga uwar d'aki ya d'auko mi shi bargo ya na zuwa ya rufa ma sa, d'auko wannan garin maganin ya yi ya zauna k'asa kusa da shi ya bud'e ledar ya dangwalo da yatsunshi biyu ya kara masa a hanci yace "Shak'a, shak'a Fodio kaji."


Shak'awa ya yi duka hudar hancin shi kafin yaja zanin rufar ya sake rufe kan shi, mik'ewa malam ya yi amma shi kan shi saida ya yi atshawa guda hud'u, Usman kam da ya kama atshawa tun ya na yi daga zaune har saida ya bud'e rufar ya tashi zaune, atshawar da ya yi ba iya ka kafin ta tsagaita mi shi, jingina ya yi da kujerar da ke bayan shi ya na dafe da kan shi, da k'yar ya fara furta "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, la'ilaha illalah, Muhammadur- rasulillahi sallalahu alaihi wassalam."


Matsowa malam ya yi kusan shi yace "Fodio ya ka ke ji yanzu?" Ya na dafe da kan shi cikin yamutsa fuska yace "Gaba d'aya ji na ke kamar ba ni ba, kamar na farka daga wani mummunan bacci na ke ji."


"Alhamdulillah, Allah kai ne abin godiya." Cewar malam kafin ya mayar da kallon sa ga Fodio yace "Ka tashi ka saka kayan ka sai ka samu ka je gida ka kwanta ka huta ko, amma dan Fodio a daina wasa da addu'a, ba zance sakaci da addu'a bane ya ja abin da ya faru, saboda kuwa na sanka sosai ba ka wasa da ibada, amma dai ka sake zage damtse ka ji."


Mik'ewa ya fara yi da k'yar yace "Insha Allahu Baba, amma wai me ya faru da ni ne?"


"Idan ka je gida ka huta mayi magana wani lokacin."


Jiki a matuk'ar sanyaye ya sanya kayan shi ya fito daga d'akin wanda ya yi daidai da fara kiran sallah isha'i, haka ya wuce ba tare da ya kula kowa ba saboda abin da ya ke ji, a k'ofar gida ya samu Bilal zaune akan tabarmar malam ya yi alwala, shi ma alwalar ya yi suka nufi masallaci tare, bayan sun fito ne Usman ke tambayar shi "Wai ina sarauniya ne ban gan ta ba?"


D'aga kai Bilal ya yi ya kalle shi kafin yace "Mummy na na gida ba ta jima da tafiya ba." Ji ya yi sam babu wani abun da ya ke iya tunawa ma a kan shi a halin yanzu, kallon Bilal ya yi yace "To ni yanzu gidan zan tafi, za ka je ne ko kuma na barka?"


"Um um, Mummy tace na zauna nan sai an gama bikin kawu Nura." Shafa kan shi ya yi yace "To shikenan ni zan tafi, ka kula da kan ka kaji ko."


Saida ya sunkuya ya sumbace shi kafin ya shiga motar shi ya wuce gidan shi saboda tunanin shi Khadija na can,πŸ˜‚ tsohon zance, ai kuwa da ya je dai bai samu samu kowa a gidan ba, kiran Khadija ya yi yace "Ki na ina ne?"


Da mamaki Khadija tace "...


*Lokacin Haseenah fa ya fara fan's, yanzu nasan za ku ji dad'i.*




_Ma chérie *Hakeema* barka da samun k'aruwar 'ya mace, Allah ubangiji ya raya mana ita akan sunna, zafa musha shoki yan uwa😎 nasan baku tab'a gani na ina kwaso shoki ba._
01/03/2020 Γ  14:18 - πŸ’‹πŸ˜˜πŸ’‹: πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘




_SAMIRA HAROUNA_




*Litattafan marubuciyar*




*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._


*SADAUKARWA GA*


_MATAN FARKO_ πŸ§•πŸΌ *(UWAYEN GIDA)*




πŸ‡ΈπŸ‡¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_πŸ€œπŸ€›


```Fatan alkairi masoya```


_Wannan page ta ki ce ke kad'ai mahaifiya kuma maman mu da tafi kowa, my sweet and lovely ki bayar da wannan page ga *Momy na*, Allah ya k'ara girma da lafiya mai anfani._


_Bismillahir rahamanir rahim_




*34*




"Ban gane ina ina ba?"


Cikin tausasawa yace" To ranki shi dad'e Hajia uwar yarima ina aka je ne?


Saida ta furzar da iska tace "Ka fad'a min abin da ya sa ka kira ni amma ba wannan ba."


A hankali yace "Nana Khadija ina k'ofar gida yanzu haka kuma babu kowa a ciki, sannan daga gidan su Hajia na ke ba kya can, yarima yace min kin zo gida amma kuma ban same ki ba, ina ki ka je ki fad'a min?"


"To me za ka min da ka damu da sai ka ganni?" Ta fad'i hakane saboda tasan in har cikin jikin ta to fa ta shiga uku, dan sai ya yi mata abin da yace zaiyi, shi kam a cewar shi "Ina son ganin ki ne, ki fad'a min ina ki ka na je na d'auko ki tunda na ga motar ki aje."


Haushi ne ya kamata tace "Kaga malam ina d'an wani aiki, sai anjima." Datse kiran ta yi ya bi wayar da kallo, a hankali ya furta "Me ya samu Khadija ta ne haka? Ba ta min irin haka fa."


Shawara ya yanke ya kira wayar Hajia, ta na d'auka yace "Hajia Khadija na ce ko ta na nan gidan?"


Da mamaki Hajia tace "Khadija kuma, ai ko da ta yi sallahn magriba ta tafi gida."


"To Hajia kuma gani a k'ofar gidan ba ta nan, na kira ta kuma ta k'i fad'a min in da take."


Yanda ya ke maganar cikin damuwa ya sa Hajia cewa "To ka shiga cikin gidan mana sai ka tambayi Hajiar ta, ita ai ba za ta kasa fad'a ma ka ba, ita ma nasan ba ta fad'a ba ne saboda ta na jin haushin ka."


Da mamaki fal a fuskar shi yace "Hushi da ni kuma? Hajiar ta? Hajia wai me ki ke fad'a ne? Ban gane ba sam wallahi."


Fahimta da Hajia ta yi akwai abin da ya faru ne ya sa tace "Yanzu dai in ganin ta ka ke so ka yi ka je gidan su, ni kaga ina wasu harkokin."


"Hajia wai me ta ke yi a gidan su? Dan Allah ki fad'a min ko na ji sauk'i, wallahi ji na ke kamar na tashi a bacci."


Shiru Hajia ta yi ta na tunanin abin da za ta fad'a ma sa, kamar zaiyi kuka yace "Hajia ki taimaka ki fad'a min mana, dan Allah ki ce ba wani mugun abu na yi wa Khadija da har ya sa ta tafi gidan su, Hajia kinfi kowa sanin Nana ita ce rayuwa ta, dan Allah ki cire ni a duhun nan."


Cike da k'aguwa Hajia tace"Fodio, na ce ka je godan nasu ka same ta ko."


Ikon Allah sai kawai Usman ya ji hawaye a fuskar shi, cikin rawar murya yace "Hajia sakin ta na yi?"


Jin muryarshi ya sa Hajia jikinta yin sanyi, tabbas sunyi kuskure a baya da su ka nunawa Khadija k'iyayya, gashi alamu na nuna cewa Khadija dai ita ce rayuwar d'an su, jin shiru ya sa yace "Hajia na shiga uku idan sakin ta na yi, Hajia tun yaushe ta ke gida?"


Kashe wayar kawai Hajia ta yi ta aje gefe ta fito waje su ka ci gaba da harkokin gaban su, sai dai kuma hankalin ta ya koma kan Usman da abin da ke faruwa, Haseenah na d'aki zaune ba aikin fari bare na bak'i sai kallon mai bisa ruwa takewa kowa, Usman kam daga nan baiyi k'asa a gwiwa ba wajen wucewa gidan su Khadija ya na addu'a a zuciyar shi "Allah ka sa ba wani abu nayi wa Khadija ba, Allah na rok'e ka kasa ba fad'a mu ka yi ba." Wani lokacin kuma mamakin kasa tuna komai ne ke damunshi, da haka ya isa gidan ya paka mota a k'ofar gidan, zai sallama sai ga Bashir zai fito daga ciki, gaisawa su ka yi cikin mutumta juna kafin yace ya wuce ciki Hajia na nan shi zai fita ne, ba musu ya wuce dan dama ba tsayawa zaiyi ba, Hajia na zaune tsakiyar less da atampopi ya sallama tace ya shigo, zaune ya yi k'asa kamar yanda ya same ta a k'asa ita ma, gaisawa su ka yi kamar kullum kafin ya d'anyi shiru ya na tunanin ta'inda zai fara, shiru ne ya ratsa d'akin kamar ba kowa a ciki, a hankali Hajia ta kalle shi da murmushi tace "Komai lafiya dai ko?"


Saida ya rarraba ido kafin yace "Mama, wani abu ne ya ke faruwa da ni da na ke so na samu amsar tambayoyi na anan, dan Hajia ta ma k'i saurara ta bare ta fad'a min me ke faruwa, dan Allah Mama ki taimaka ki fad'a min ina Khadija take? Sannan meya faru tsakani na da ita da har ya sa take zaune gida?"


Jim Mama ta yi ta na tunanin to in har iyayen shi ba su fad'a mi shi ba me zaisa ita ta fad'a, murmushi kawai ta yi ta kalle shi tace "Ba komai Usman, ka wuce ta na ciki yanzu mu ke zaune tare da ita ta shiga ta yi sallah."


Damuwar kan fuskar shi ce ta k'aru yace "Mama, dan girman Allah ki fad'a min meya faru tsakanin mu, Mama idan ma sakin ta na yi wallahi tallahi bansan na yi ba, shi ya sa na ce mu ku wani abu ne ke faruwa, gaba d'aya na kasa tuna komai ji na ke kamar daga dogon bacci na tashi."


Ganin kamar zai mata kuka ya sa ta saki fuska tace "Kar ka damu Usman, ba wata babbar matsala ba ce, ka shiga ka same ta a ciki ku yi magana, idan har

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login