Showing 3001 words to 6000 words out of 60852 words
Chapter 2 - 'YAR BARIKI Book 1 Complete Writing by Rufaida Umar .txt
"Babu ranar da wannan fatan naki zai tabbata kuwa,zan maki uzuri da alama bakisan alfanun jinsi ba sai nan gaba."
Baby tayi murmushi mai had'e da jan numfashi
"Ba halina bane,baya daga abunda nake sha'awar aikatawa. So,in sha Allah bazan tab'a bin wannan hanyar ba."
"Ja'irar kaya,ashe har yanzu kinsan da sunan Allah? Toh ba laifi muje zuwa."
Abun sai ya bawa baby dariya,ta d'an dara kafin ta mik'e tayi hanyar fita
"Momi kenan,na barki lafiya."
******
Mutum ne matsakaici,mai dogon fuska,yana da matsakaicin hanci saidai akwai magana(idanu). Girarsa a cike kuma bak'i wuluk,kamar dai yanda sajensa da gashin kansa yake. Fari sol,zubin Fulani.
Zaune yake a ofis yana aiki akan Laptop. Hankalinsa gaba d'aya ya tafi ga aikinsa,kallo d'aya zakayi mishi kasan yana hutawa. Daidai lokacin aka bud'e kofar gami da yin sallama. Ba tare daya kalli mai sallamar ba ya amsa ciki ciki kasancewar ransa a b'ace yake dashi. Ya k'araso da fara'a ya zauna
"An gaida mutumina,ba fad'a mai ya kawo gaba kuma? Ace har ka iso garin nan saidai don rashin mutunci ko waya bakayi domin sanar dani ba sai a bakin kanwarka na tsinci labarin."
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(05)
Har ya gama maganarsa baice mishi komai ba. Ganin haka ya buga tebur wannan yasa shi watsa mishi wani irin kallo kafin ya karkato yayi juyi da kujerarsa yana fuskantarshi. Fuska a daure yace
"Kana da kunyar takowa ofishina bayan wulakancin kayimin?"
Cikin rashin fahimta,KB ya zuba mishi ido kafin ya tambayeshi
"Me kake nufi wai Haris? Nifa bansan takamaiman laifin dana aikata ba."
Ya dubeshi kadan kafin ya girgiza kai
"Jiya,(around 6:00pm),na had'u dakai anan wajejan sultan road. Saidai abun mamaki nayita hon baka tsaya ba saida kyar,karshe ma don rainin hankali kak'i fitowa daga motar. Saidai a yanda ka nuna yanzu ya tabbatar min ba kaine cikin motar ba saidai tabbas lambar motarka ce. Na soma tunanin direbanka ne,toh a gaskiya ka chanja direba,domin bakayi dace ba wallahi da zan ganshi zai sha mari ne...."
Kb ya katseshi
"Tsaya don Allah,gayamin menene ya faru?"
Haris ya labarta mishi,ya k'arashe da cewa
"Mercedes Benz dinka ce, kada kaso kaga gudun da direbanka ke...."
KB ya katseshi a kunyace
"Oh,Baby ce a ciki fa."
Haris ya yamutsa fuska
"Who the hell is Baby?"
Kb yayi murmushin basarwa
"Wata cousin d'in Mamina ce,ta ari motata ne tun kusan (last two days.)"
Haris ba don ya yarda ba,sai don kawai bai fiye bin kwakkwafin abunda bai shafeshi bane,ya gyada kanshi
"Ok."
Daga haka suka bar zancen suka fad'a hirarsu.
*****
Kabir Idris Babangida da Haris Aliyu Kazaure. Aminan juna ne,wadanda amintarsu ta samo asali tun daga iyayensu maza wadanda suma a baya can makwaftaka ta had'asu tun suna kauyensu na Kazaure kafin Allah Ya azurtasu a garin Kano. Kowannensu yayi gini na gani na fad'a ya dawo birnin Kano da zama.
Makaranta d'aya Haris da Kabir sukayi. Har ya zamana sun karanci course d'aya,wato business.
Kabir shi kad'ai ne d'a a wajen mahaifinsa Alhaji Idris. Shi kuwa Haris,su biyar ne. Saboda zumunta dake tsakanin iyayensu wadda bata wasa ba,ya sanya Alhaji Aliyu daukar Haris tun yana d'an shekara biyu ya damk'awa Alhaji Idris da matarsa Hajiya Jamila. Sunyi murna matuk'a domin Allah Ya sani,tun Haris na jariri suna matukar kaunarsa,kai bama su kad'ai ba. Mutane da yawa suna kaunar Haris saboda kyawu da farin jinin da Allah Ya bashi. Hajiya Aisha kuwa,mahaifiyar Haris mace ce mai alkunya wannan yasa ko kusa bata nuna damuwarta akan wannan kyautar ba tunda ga YASMEEN da sauran yaranta uku a gabanta.
Haka Kabir da Haris suka taso cikin kaunar juna da tsananin gatan da ake nuna musu. Rayuwarsu saita burgeka na yanda suka shak'u.
A fannin halayya kuwa,nan suka bambanta domin Kb mutum ne mai matukar son 'yan mata,karshe ma ya fad'a harkar nemansu. Abun bai k'ara gaba ba saida sukaje Malaysia karatu.
Duk abunda yakeyi yakanyi kaffa kaffa gudun kada Haris ya sani saidai kuma ba'aje ko'ina ba ya ganeshi. Yasha fama dashi kwarai dagaske domin har k'ararsa yakai wajen Alhaji Aliyu. Nan ya kirashi yayi mishi tas kafin daga bisani Kb ya daukar mishi alk'awarin ya dauka,nan ma ya daukarwa abokinsa alk'awarin dainawa. Hakan kuma bata canza zani ba,domin da abun ya bunk'asa sai ya zamana ma hatta da shaye shaye,KB yana gwada aikatawa.
Haka dai har suka kammala karatu suka dawo,saidai fa tun dawowarsu KB ya dora ido akan Yasmeen yaga yanda ta koma cikakkiyar budurwa. Nan ya shiga tura kanshi gareta. Ga Yasmeen kuwa,tuni itama ta mato akan kaunar Yaya KB. Wannan ya sanya ta bashi kai,soyayyarsu ta k'arfafa. A karshe iyayensu sukaji daga bakin Kb,ran Haris baiso 'yar uwarsa ta auri Kb ba. Ba wai don bai kaunarsa ba saidai tsoron halayensa a ganinsa tamkar bazai fasa ba.
A haka dai iyaye sukayi na'am,aka sanya ranar aure da zarar Yasmeen ta kammala secondary,idan yaso ta k'arasa a dakinta. Kafin auren ya iso,tuni Kb fa Haris kowanne ya kama aikinsa. Inda Alhaji Aliyu ya d'ora KB a matsayin manajan babban kamfaninsa dake a garin Abuja. Wannan mukamin da Alhaji Aliyu ya bawa Kb,ya bawa dukkan yan uwan Alhaji Idris mamaki,karshe suka k'ara ganin girma da kimar Alhaji Aliyu. Shima Abba yace baza'a barshi a baya ba,nan ya d'ora Haris a manajan kamfaninsa a Kano. A cewarsa baza'a yiwa danshi wannan son kan ba. Ba karamin karfi hakan ya sanya zumuncinsu ya k'ara yi ba. Shakuwa sosai da fahimtar juna. Ya zamana Kb baya dawowa garin Kano sai weekend. A haka har Allah Ya daukakasu.
Bayan aurensa da Yasmeen da shekara daya ya siya gidansa na kansa a garin Kano. A cewarsa nan iyalinsa zasu dinga sauka ba sai sunje gida ba. Shima Haris yana da hadadden gidansa mallakinsa a garin Kano.
Babbar damuwar iyayen,auren da Haris bashi da niyyar yinsa. Wannan ba karamin daga musu hankali ba musamman ma ga mahaifiyarsa wacce tafi damuwa ainun. Ganin ya nuna shi kam baiga matar aure ba saidai ko nan gaba wannan ya tsoratasu,suka tashi da addu a zatonsu aljana ce ta auri d'ansu.
*****
HADUWAR BABY DA KB NA FARKO........
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(06)
Haduwarsu ta farko a Nightclub ne. Kb yana zaune da abokinsa,Nas. Bai jima da isowa wajen ba,ya hau kallon gayun wajen domin ganin ta inda zai samu wacce tayi mishi. Shi kam a farko ya raina matan kano,ganinsa basu da wani wayewa na azo a gani. Wannan yasa yafi yin shegantakarsa a Abuja.
Maza da mata ne,kowannensu babu mai shigar kirki,ga kid'an dake tashi tamkar zai fasa wajen. Rawa sukeyi marar kyawun gani,a gefe kuwa wasunsu zaune suna iskance iskancensu basu ko damu da idanun mutune ba. Cikin nishadi ya tsiyaya barasa da niyyar kwankwad'a,yana niyyar kaiwa bakinsa ne ya hangota zaune cikin shigar kananun kaya kamar sauran matan wajen. Taci ado har ta gaji da had'uwa,shisha take sha hankalinta kwance. Tamkar bafulatana saboda hasken fatarta mai kama da madara,ga wani dan iskan rigar dake jikinta wanda bai rufe komai nata ba kasancewarsa shara shara.
Nas ya lura da hankalin abokinsa bai tare dashi,hakan yasa shi juyawa don ganin abunda yake kallo. Murmushi yayi kafin ya juyo ya taimaka wajen tura kofin hannunsa bakin KB,sai lokacin KB yasan ya lula tunani. Nas ya gyada mishi kai hadi da daga gira
"Baby tasleem sunanta,kaf bebs dake nan gurin babu wacce zata nuna mata komai na halitta. Ina gayamaka tana ji da kanta,gata da class. Ba kowane guy take mu'amala dashi ba. Kada ka kuskura ka tunkareta domin ba karamin aikinta bane ta disga ka a gaban kowa ba wajen nan."
Kb yayi murmushinsa,ya sanya hannu ya k'ara kwantar da sumar kanshi.
"Dats my girl,haka nakeson mace. Sha kuruminka kayi kallo."
Nas yana kokarin dakatar dashi saidai tuni shi kuma ya mik'e ya nufi inda baby ke zaune. Wannan yasa Nas tsayawa kallon ikon Allah tare da fargabar irin wulakancin da za'a yiwa abokinsa.
*****
Kb yana zuwa ya nemi kujerar dake fuskantar baby ya zauna. Baice da ita komai ba,sai kallonta da yakeyi itama ta kalleshi sau d'aya ta maida kanta ga abunda takeyi. Murmushi yayi kafin ya rik'o shishar hade da hannunta. Wannan ya sanyata dagowa a fusace tana dubanshi,saidai tunda baby take a rayuwarta bata taba cin karo da wanda dubansa ya sanyaya jikinta ba sai Kb. Tayi makwas bata iya hanashi abunda yake niyyar aiwatarwa ba. Rike da hannunta ya zuki shishar kafin ya d'ago ya dubeta. Ta kauda fuskarta,bazaka fahimci yanayinta ba sakamakon bata daure fuska ba kuma bata saki ba. Ta janye hannunta,ta mike tayi hanyar fita. A sannu take tafiya har ta kawo titi,saidai wayam ba motoci,gashinan manal bata gama shagalinta ba balle saurayinta ya maidasu gida. Hon taji ana yi mata,bata ko kalli motar ba,saida ya iso daf da ita ya faka ya fito. Ta saci kallonsa,shine dai. Ya bude mata mazaunin kusa da direba yana mai mata nuni a ladabce cikin murmushi
"Ba girmanki bane ranki ya dade,a ganki war haka a tsakiyar titi kin rasa abun hawa. Idan babu damuwa kizo ki shiga motata duk da nasan matsayinki ya wuce ki hau jagwal dita."
Ta dubi motar.babbar harka ce kwarai,range rover. Saima ya bata dariya,wannan ya sanyata murmusawa.
Lahaula! Tuni ta k'ara kashe Kb,ya sanya hannunsa akan murfin motar yana dubanta cike da murmushi,jinsa yake duk babu laka a jikinsa. Har ya fidda rai bazata shiga ba saidai ga mamakinsa yaga ta shiga ta zauna,cikin jin dadi ya rufe motar ya shiga ya zauna. Sai lokacin ya dubeta bayan ya matso daf da ita,murya kasa kasa yace
"Fatan zan samu rakiya gidana?"
Ta juyo ta dubeshi,numfashinsu na bugun juna,ta kauda kanta tana murmushi wannan ya bashi tabbacin amincewarta. Da gudu yaja motar, bakajin komai sai kid'a dake tashi ga sanyin Ac.
*****
Tun daga wannan ranar Kb da Baby suka dinke,dinkewa kuwa bata wasa ba. Su kansu su manal sunyi mamakin inda baby ta samo hadadden guy har haka. Karshe har gida ya sanya aka gyara musu,kudin kuwa da yake aikawa baby abun yaso ya baci. Ga sauran manyan da take harka dasu suma ba'a barsu a baya ba wajen cika mata account. Karshe Kb ya hanata mu'amala da kowa,acewarsa shi kadai ya isa dauke mata nauyin komai. Baby murmushi kawai tayi ta bishi a hakan,saidai kuma abunda bai sani ba,duk sadda yasa kafa ya koma Abuja babu irin tsiyar da bata shukawa da manemanta. Mota kyauta ya bata,wasu lokutan idan taga dama koda baya gari,zataje gidansa ta huta ta fita da motar da takeso. Babu wanda yake cewa uffan cikin ma'aikatan sanin matsayinta a wajen ogansu. Saidai suyita gulmammakinsu tare da rok'awa maigidansu shiriyar Allah.
******
Ta gama komai na tarar mijinta,ta gyara gidanta da jikinta. Jiran dawowarsa kawai takeyi.
Tana cikin sanyawa diyarsu,Nasreen,ribbon a jelar kitsonta,taji shigowar motar mai gidan. Nasreen ta kwace kanta daga wajen maminta tayi waje a guje.
"Daddy oyoyo,daddy oyoyo."
Haka tayita fad'i har takai ga jikin motarsa. Ya fito ya daga diyarsa cak yana sumbatar kumatu da goshinta cike da farin ciki ganinta.
"Bebin daddy oyoyo,I miss you soo much."
Tana ta dariya haka suka shiga ciki. Ya ajiye nasreen,daidai lokacin Yasmeen ta karaso tana duban mijinta cike da so da kauna saidai fa a sanyaye take sanin da tayi waccan zuwan nashi bai wani saki jikinsa da ita ba. Abu kadan da baikai ya kawo ba zai soma gayamata magana.
"Sannu da zuwa."
Ga mamakinta taga ya amsa tare da rungumeta. Ta saki ajiyar zuciya gami da hamdala a ranta.....!
Rufy: 'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(07)
Ya dagota yana mai riko kafad'unta
"Ya dai na ganki haka a sanyaye? Ko bakiyi murna da zuwana ba na juya?"
Ya saki kafadunta ya soma tafiya da baya, da hanzari ta riko hannunshi tana dariyar farin ciki
"Wace ni na guji prince dina? Barka da zuwa."
Ta ja hannunshi suna murmushi har zuwa d'aki,Nasreen tana biye dasu.
Yasmeen mace mai biyayya,ta taimaka mishi ya gyara jikinsa ya sanya kayan shan iska. Sannan suka fito ta zuba mishi abinci yaci.
Ranar kam sun farantawa juna saidai ko kusa zuwa yanzu bayajin dadin mu amala da kowacce mace sai Baby. Yau dinma tausayin matar tashi ne ganin yakan jima bai kusanceta bane.
*******
JUMA'A,5:00pm
Baby ce tafe cikin motarta,tuki takeyi cikin kwarewa. Kallo daya zakayi mata kasan tana cikin nishad'i. Dawowarta kenan daga gidan gonar Alhaji Ridwan Naira,wanda kusan sati yayi yana magiya da rokonta akan don Allah tazo gareshi. Sai a yau baby taga damar amsa kokensa bayan ta jera satuttuka tana lashe kud'ad'ensa.
Kai tsaye gidan Kb ta nufa duk da cewar tasan bazai shigo Kano wannan satin ba gudun kaucewa zargin iyayensa da matarsa. Yau kam a gidansa take sha'awar kwana don tasan koda ta koma bazata samu su Dalal a gidan ba. Manal tana Kaduna,yayinda Hibba da Dalal ke tare da mutanansu a gidajen shak'atawarsu.
Tayita hon saidai maigadin yayi nisan kiwo,wani maigadin ne daga makwafta yazo ya bud'e mata ta shiga. Ta fiddo 'yar bigmama dinta da wayoyinta ta rufe motar ta shiga ciki. Bata da matsalar mukullaye kasancewar tana da safayar kowanne mukulli na gidan a wajenta duk saboda mukamin data samu a wajen Kb. Wanka kawai ta fad'a sakamakon gajiyar data kwaso.
Daidai lokacin ya shigo layin,duk a zatonsa aminin nashi ya shigo gari kamar yanda ya sanar mishi a waya cewar watakila ya shigo. Hon yayi har sau uku,maigadin har lokacin bai kusa. Wanda ya bude kyauren da farko shine dai ya k'ara zuwa,Haris ya sauke gilashi ya yafitoshi da hannu. Yazo cike da ladabi ya kwashi gaisuwa,haris ya amsa gami da tambayar
"Mai gidan yana nan?"
Maigadin ya dubi gidan kafin ya dubeshi
"Eh toh,inaga dai yana nan don Hajiya bata jima da dawowa ba ni na bude mata kofa."
Haris ya dauka kanwarsa Yasmeen ce, yaji dadi domin yayi kewarta sun kwana biyu basu hadu ba saidai gaisuwa ta waya. Ya jinjina kanshi
"Taimaka ka bud'emin mana."
Da azama ya bud'e mishi ya shiga ciki yayi fakin. Bayan ya fito ya tsurawa motar da baisan da zamanta ba a gidan ido,cike da mamakin mamallakin motar ya dubi gidan kafin kuma ya tunkari cikinsa.
Fitowarta kenan daga wanka,tana shirin goge jikinta taji sallama a falon gidan. Farin cikin ya k'aru,ashe daman zai zo gari shine bai sanar da ita ba duk da wayar da sukayi? Cikin sauri sauri ta nufi hanya ta fita.......!
'YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(08)
Tana fitowa falon,wayam! Hakan ya tabbatar mata daga falon k'asa ne. Sai ta soma shakku akan anya kuwa Kb ne? Don bai tab'a tsayawa k'asa ba sai ya k'araso falon sama.
Haris jin da yayi sallamar ba'a amsa ba,kawai ya tunkari falon sama yana fadin
"Little,ina kika shiga ne?"
Baby ta tsaya cak daga bakin matattakalar,kafin takai ga yunkurin kaucewa har ya nufo benen. Ido hud'u sukayi,duk da batasan ko waye ba saida ta d'an tsorata. A gefen Haris kuwa,kallonta yayi tun daga k'asa har sama,bai k'ara marmarin kallonta ba. A fusace ya juya kanshi yana mai kokarin korar shaidan daga zuciyarsa. Cikin kakkausar murya yace
"Who are you?"
Cike da mamakin yanda gayen ya juya baya daga barin kallonta,baby ta kalli jikinta. Tawul ne ko cinyoyinta bai gama rufewa ba. Ita kam bata taba ganin namijin daya ganta haka ba harma ya iya juya mata baya ba sai a yau.
"I said who are you?!!! Mekikeyi a gidan nan?!!"
Ta razana matuka,tunda take wallahi ba'a taba yi mata tsawa har irin haka ba