Showing 48001 words to 51000 words out of 60852 words
Chapter 17 - 'YAR BARIKI Book 1 Complete Writing by Rufaida Umar .txt
akan yasmeen amintarsa da dan uwansa ke neman samun mishkila duk ta hanashi motsi,jin maganar Abba ne yasa ya juyo.
"Bansani ba Abba."
"Allah Ya tsare hanya toh. Matarka nace ta shirya kuje can gidanka idan yaso zuwa gobe saiku wuce Abujan."
Baiji dadin wannan hukuncin ba,saidai yasmeen ta biyashi data boye sirrinsa,tabbas idan yayi mata wani rashin adalcin bai kyauta ba. Ya amsa da toh kawai. Jimawa kadan ta fito suka wuce a mota sai janta yakeyi da hira ta basar dashi bisa hud'ubar mami da ta nuna mata ya dace ta d'an ja ajinta.
****
Da sallama ya shigo gidan,humaira aguje ta rukunkumeshi tana ihu
"Ga yaya! Ga Yaya!!"
Wannan yayi sanadin tashin tasleem dake bacci a falon sakamakon damuwa ta haneta bacci daren jiya da kuma shariyar da Mamma tayi mata tabar wani d'okin ganinta gaba daya ma ta chanja mata fuska.
Cak ya tsaya ita kuwa ta daure fuskarta tamau tayi azamar mikewa zata nufi falon sama,a guje yasha gabanta. Bakinsa na rawa,ya kasa gaskata cewar ita d'ince tsaye a gaban idonsa. Dakyar ya iya tab'a hannunta jin cewar ita d'ince yasa ya riko hannun hawaye sun wanke fuskarsa. Kawai sai ta soma kukan itama kafin ta warce hannunta tayi sama a guje har zuwa d'akin mamma da batanan tana dakin mijinta. Gadonta ta fad'a tana kukan tunowa da yanda yayan nata yayi mata korar kare daga gidansa. Muryarsa taji cikin kuka a kusa da ita
"Na rasa kalar godiyar da zan yiwa Ubangiji,da ace kin kara shekara baki dawo ba wallahi mutuwa zanyi ko nima a nemeni a rasa. Tasleem kin jefa yayanki cikin tashin hankali,nayi magana cikin fushi na zartar da hukunci ban tab'a zaton zakiyimin haka ba. Tasleem ina kika shiga? Ya za'ayi ni Abdullah na yankewa kanwata abar kaunata wannan hukunci mai tsauri. Ina sunan 'yan uwantakanmu? Wallahi kusan zaucewa nayi dana wayi gari naga da gaske kin gujeni...."
Mamma ya gani tsaye ta harde hannuwanta a saman kirjinta,hakanan ta zuba musu ido. Jin da tasleem tayi Abdullah yayi shiru yasa ta dago kai,taji k'arar rufe k'ofa wannan yasa itama ta dubi k'ofar. Mukulli mamma ta saka daman mijinta ya fita zuwa aiki,humaira tayi umarni ga gwaggo mai aikinta ta mik'ata gidan liman. Nura kuwa makaranta yake zuwa baya dawowa sai yamma sakamakon shirin jarabawar karshe na sakandire da yakeyi.
Gidan ya zamana daga Mamma sai yaranta mafi soyuwa azuciyarta. Fuska a daure ta zauna yayin data dubesu
"Ku zauna sosai."
Tasleem ta mike zaune daga kwanciyar da tayi,shima abdullah ya zauna gefenta a saman gadon,yayinda mamma taja kujerar gaban madubinta ta zauna idanunta a kansu. Ta dubi tasleem
"Kince sai yayanki yazo zaki fadamin abunda ya afku a rayuwarki ko? Yau kuma gani gaki,gashi muna sauraronki duka."
''YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(52)
Yau ba ranar boye boye bace, ita kam koda zata boyewa kowa matsalarta toh banda mahaifiyarta. Don haka ta russunar da kanta ta labartawa mamma halin data tsinci kanta tun rabuwarsu. Da kuma fyaden da Usman yayi mata wanda ya sanya mamma fashewa da kuka,Yaya Abdullah kuwa tsananin mamakin yanda akayi kanwarsa bata sanar dashi bane ya cikashi.
"Haba Tasleem,meyasa kiks boyemin magana har haka?"
Tayi murmushi duk da ruwan hawayen da take fitarwa
"Yaya baka nemi hakan daga gareni ba. A karshe ma saika kama maganar su Raliya ka yarda cewa na bawa wani budurcina. Haba yaya, wane talauci ne zaisa nayi haka?"
Ta ja majina kafin ta dora,haka har ta gangaro kan rayuwarta a hannun yayanta da kuma rud'in shaidan da yasa ta bawa rilwan jikinta da cikin data samu yayanta ya koreta. Haduwarta da Momi harma da barikancin data fad'a har zuwa taimakon da haris yayi mata bayan tayi hatsari da zuwansu nan. Hakanan bata b'oyemusu ko wanene haris ba saidai bata tonawa kb asiri ba.
Salatin da Mamma ta doka ne ya maido hankalinsu gareta,tuni kuma ta kife a k'asa sumammiya. Ihu tasleem ta fasa,Yaya abdullah kuwa yayi yunkurin fadawa bandaki ya debo ruwa. Baiyi wani jinkiri ba ya yayyafawa mamma amma ina bata motsa ba. Tasleem tana ihun kiran sunanta tana fadin "Mamma kimin aikin gafara,wallahi mamma ni ba 'YAR BARIKI bace yanzu. Mamma mutuwarki mutuwata ce..."
"B'udemin kofar nan da sauri."
Yaya abdullah ya fada lokacin da yake kokarin daukar mamma. Da gudu tasleem ta bude kofar,tuni yayo waje yana fadin
"Ki biyoni da hijabin mamma."
Ta wulk'a idonta,ta kasa gane hijabin ma kawai saita janyo farin abu dake rataye jikin hanger. Yaya abdullah ya ajiye mamma a baya jikinsa a sake yana kuka.
Ganin haka tasleem tayi azamar zagayawa ta shiga mazaunin direba ta tada motar. Da gudu maigadin dake kallonsu ya bude kofar ta fita shaf batajin radadin hannunta tama manta tana da ciwo saboda tsabar Firgicin da take ciki.
"Yaya ina ne asibitin,ka gayamin kada ka janyo mu rasa mamma."
Yayi ta maza ya dunga gwada mata hanya har suka iso. Da gaggawa aka amshesu akayi ciki da mamma. Tasleem kawai ta zube a bakin kofar ta hada kai da gwuiwa tana kuka sosai. Yayanta ya iso ya zauna kujerar dake gefanta,hakan ya bata damar kwantar da kai a cinyarsa
"Yayana na halaka!"
Ya dafa kanta ya shiga girgiza kai saidai ya kasa magana. Ta dago ta dubeshi
"Idan mamma ta mutu wallahi nima mutuwa zanyi. Rayuwata bata da amfani,dana sani da nadama sun dabaibayeni fin tsammaninka yayana,meya rud'eni da bariki? Menene shi? Mena d'and'ana cikinsa? Wallahi yaya abdullah rayuwata bata da amfani,wani wanda baida uwa da uban ya fini. Amma yayana kaima kasan bani da laifi ko? Khalid Ma'aruf waziri shine ya watsar dani. Bayasona,bai damu da sauke hakkin daya rataya a wuyansa a kaina ba. Wallahi bana sonshi,na tsaneshi nima. Bayamin fad'a,bayamin nasiha,ya kasa aurar dani. Na tsaneshi!!!"
Sai ta mike tana ihu kafin ta hau buga kanta da bango,yaya abdullah ya damk'eta a gigice,mutanen wajen ma sai salati sukeyi suna kiran lafiya kuwa? Kawai saita suma jikin yayan nata......!
''YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(53)
"Tasleem!!" Yaya abdullah ya fadi da k'arfi sannan ya dubi mutanen wajen gumi duk ya gama wankeshi hadi da hawaye kwance saman fuskarsa.
"Ku taimakamin don Allah."
Sai ga wata nos, tayi azamar kama tasleem ita da wata mace dake a layin ganin likita suka shiga ta kwantar da ita saman gado sannan ta kirayi likita. Nan suka soma kokarin ganin ta farfad'o.
Yana nan tsaye likitan dake tsaye kan mamma ya fito
"Alhamdulillah,ta farfado har ma tana nemanku. Kuna iya shiga,ina ita kanwartaka?"
Yaya abdullah ya numfasa yana hamdala kafin ya nunamishi d'akin da aka sanyata
"Ta suma ne amma likita yana tsaye a kanta."
Cikin damuwa likitan ya nufi dakin da baby take bayan ya damkawa abdullah takardar magungunan da za'a siyo ya kuma tabbatar mishi hawan jininta ne ya tashi amma da sauki,shi kuwa abdullah yayi azamar fad'awa d'akin da mamma take. Tana kwance ta kurawa silin ido,jin shigowar mutum yasa ta duban kofa kafin ta yunkura ta mike zaune,gaba daya tayi mugun sanyi ga hawaye na zubo mata. Abdullah ya zauna yana mai rike hannunta
"Sannu mamma."
Ta gyadamishi kanta kawai,kafin ta hau duban hanya, cikin rawar murya ta tambayeshi
"Ina tasleem?"
Ganin halin da take ciki yayi nufin rufeta,ta girgiza mishi kai
"Banda yau Abdullah,kabar k'ara b'oyemin komai ga rayuwarku. Idan ka boyemin taka,kada ka kara cutata da karemin damuwar diyata mace."
Hankalin abdullah ya tashi
"Ki gafarceni mamma,wallahi ban tab'a rufeki domin cutar rayuwar kanwata ba. Asalima bacin raine yasa na kori tasleem daga gidana wanda daga baya nayi muguwar dana sani bayan kuma da komai ya fito. Mahaifin rilwan ya sameni ya sanar dani batun wasikar,harma ya nemi a daura aurensu anan ne hankalinmu ya tashi."
Ya zame ya durkusa gwuiwoyinsa a k'asa yana hawaye jikinsa kuwa har kakkarwa yakeyi
"Ki gafarceni Mamma,bansan zan cuci rayuwar kanwata ba da ban aikata wannan mummunan laifin ba. Saidai ganinta da ciki ya rud'amin kwakwalwa har ma na kasa wani kwakkwaran tunani. Na tsoraci kada ta rusa aurenki ne,ganin da nazo nayi maki kina cikin kwanciyar hankali da walwalar dana jima ban riskeki cikinta ba mamma.
Bayan haka kuma ina...."
"Kiyi a hankali mana."
Jin muryar nos duk suka mayarda hankulansu ga kofar shigowar. Tasleem ce gaba dayanta a hargitse gashin kanta na usuli wanda bana k'ari ba duk ya barbazu a kafad'arta ko dankwalin babu. Ga bandaji da aka zagaye goshinta dashi sakamakon jinin dake fita daga goshin nata.Ta ja burki wanda ya janyo nos dinma tsayawa kafin kuma ta fita ta rufe musu kofa ganin kamar ba'a bukatarta a wajen. Kunya da nadama tsantsa suka kasa barin Tasleem k'arasawa ga mahaifiyarta. Meyasa alokacin data tashi yin wannan aika aikar na zina duk basu fad'omata ba? Babban tashin hankalin ma,mantawa da tayi da Mahaliccinta kuma alhamdulillah kullum cikin tuba take hakanan yanzu hakan ma haila takeyi. Zubewa tayi anan tana mai sanya tafukan hannunta ta rufe fuskarta tana kuka kamar ranta zai fita.
"Astagfirullah! Astagfirullah."
Tayi ta maimaitawa har babu adadi,mamma kallo daya tayi gareta bata k'ara ba. Koda taji tausayin diyarta da kaddararran rayuwar da tayi a baya batajin zata iya saukowa a daidai wannan lokacin da bacin rai da tsoron tambayar da Allah zaiyi gareta akan amanar daya damk'a mata na d'iya babu abunda ke yawo a kwanyarta. Ta saki hannun abdullah bayan data dubeshi
"Maidani gidan mijina."
Wannan ya tsayar da tasle daga kukanta,a gaban idonta mamma ta kunce dankwalinta ta d'an rufawa jikinta tayi waje. Abdullah ya dauki takardar maganin ganin mamma na shirin fita tayi saurin rike kafarta
"Don Allah mamma ki yafemin. Nayi kuskure bazan kara maimaita irinsa ba."
Bata ko saurareta na ta janye kafarta tayi hanyar fita,da sauri abdullah ya ciro takalman kafarsa ya ajiye kusa da kafafunta
"Ki sanya Mamma,kada ki fita haka."
Ta sanya tana mai k'ara jin kaunar yaran nata a zuciyarta. Saidai kuma sunyi laifi gareta. Tabbas ta k'ara hakikancewa Dr. Khalid bashi da amana.
Suka fita, abdullah saida ya bari mamma tayi gaba ya bude mata motar ta shiga kafin yazo ya rarrashi baby itama ta mike tayi gaba sannan yaje ya share bill nasu,likitan yana kara jaddada mishi cewar a kula da abunda zai k'ara tab'a zuciyar mamma saboda blood pressure dinta kada yayi high.
A mota shiru,ba wanda ya cewa wani uffan tsakanin mamma da baby domin mamma zaune take a gidan gaba. Abdullah ya dawo
"Ki gafarceni mamma,na tsaya karb'o magani ne."
Batace uffan ba yaja sukayi gaba.
Suna zuwa gidan sukayi kicibus da Dad yayi ribas zai fito,ganinsu yasa shi komawa. Suka fito ya nufosu a gigice yana kama kafadun mamma.
"Maman nura lafiya dai? Maigadi ke sanarmin kuna asibiti dawowata kenan."
Ya dubi abdullah sannan Tasleem yayi mamakin halin da suke ciki.
"Ita kuwa d'iyata menene ya sami goshinta?"
Da sauri Mamma ta tare
"Lafiya,hawan jinina ne ya d'an motsa shiyasa suka kaini asibiti ba'a hayyacina ba. Bakaga yanda yaran naka suka rud'e ba?"
Baby ta amshe
"Dad buguwa nayi wajen sauko da mamma daga steps."
Ya danyi murmushi ya amince da hakan
"Wayyo sannunki diyata." Ya maida dubansa ga matarsa wacce kallonta ke mantar dashi komai
"Nagode Allah da ya ceci ran abar kaunata."
Daga haka yaja hannunta zuwa ciki yana sannu sannu ba iyaka. Baby ta daskare tana dubansa cike da sha'awa.
"Tell me now my sister,ta yaya zan bari matsala ta b'ullo tsakanin dad da mamma?'
Ta dubi yayan nata wanda ke magana cike da matsanancin damuwa hannunsa rike da ledar magunguna. Hawayenta suka cigaba da kwaranya tayi murmushi mai ciwo
"Babu."
Ya numfasa kafin yaja hannunta
"Inason mu zauna mu tattauna dake sosai."
Daga haka yaja hannunta suka mara musu baya.
Sam mamma tak'i bawa tasleem damar yin magana da ita a keb'ance. Tun magrib tayi sashen mijinta domin yace ta huta bayason ganinta a kicin. Shima can ya tare a wajenta. Abdullah yace mishi sai zuwa gobe zai koma.
Tana zaune ta idar da salla ta zubawa talabijin ido inda humaira ke kallon tashar Disney na cartoons zallah. Ta lula cikin tunanin wannan shariyar da mamma keyi mata,Abdullah ya zauna kusa da ita saman kujera yayinda take zaune kan darduma ta takure.
"Biyoni." Ta bishi babu musu har zuwa d'ayan falon dake jikin wanda suke. Bayan sun zauna ya dubeta......!
YAR BARIKI
©Rufaida Omar(Hannu da Yawa Writers)
(54)
Saidai ya soma da bata hakuri laifin daya aikata gareta na korarta daga gida da kuma gargadinta da zuwa wajen mahaifiyarsu kafin yayi mata nasiha ya kuma nuna mata kurenta na rashin dacewar jefa kanta a karuwanci da tayi. Koda suka gangaro kan Mamma,ya shawarceta data koma gidan liman ta bari har zuwa sadda mamma zata sauko hakanan jininta ya daidaitu. Tasleem tayi na'am da wannan,saida ya kammala da wannan babin kafin ya kirayi sunanta wanda hakan ya sanyata dago kai ta dubeshi tana mai amsawa.
"Ya dace ki sassauta kiyayya ga mahaifinki."
Nan da nan ta daure fuska tamau,ya share kamar bai gani ba ya cigaba da magana.
"Mahaifinki a yanzu idan kika ganshi,kikaga yanda yake fama da ciwon sugar da hawan jini,zaki tausaya mishi saboda ramar da yayi tayi yawa,aikinsa tuni ya ajiyeshi gefe. Zakiyi mamaki idan nace maki kullum cikin zubar hawaye yake duk a dalilin rashin sanin takamaiman inda kike. Ban boyemishi dukkan abunda ya faru ba ya nunamin kurena,yace idan shi ya koreki ba'a hayyacinsa na meyasa zanyi wannan ta'asar? A karshe yace laifin nashi ne. Da ace bai koreki ba babu yanda za'ayi ki shiga wata rayuwa ta daban."
"Yaya bani labari mana game da abunda ya kawo chanjin Abba."
"Tun bayan tafiyarki da watanni uku, mummunan iftila'i ya fad'awa Usman na konewar babban shagon da baiyi ko wata biyar da bud'ewa ba,hakanan wasu b'arayin sun tareshi a hanya sun mishi duka har suka nakastashi suka kwace wayoyi da kudadensa. Abun mamaki kuma sati ba'a rufa na itama marigayi raliya akayi hada mata jini da majina a karshe aka watsar da ita a kofar gida. Jinyar da tayi kamar bazata tashi ba,gashi kuma wata kaddarar komai na Abba ya soma ja da baya Tasleem. Kamar wanda aka sanyawa hannu fitar ma da yake zuwa asibitinsa ya gaza. Hakanan raliya ta matsa mishi akan sai an fidda d'anta waje anyi mishi aiki saboda tuni matarsa tace bazata iya zama da nakasashshe ba ta ajiye mishi 'yar sa ta tafi. Akan dole Abba ya kashe makudan kudade wajen aikin kafar Usman ta hanyar fitar dashi waje saidai aiki baiyi ba wai a niyyarsu a sanyamishi kafafun roba saidai garin haka mutuwa ta riskeshi acan. Nan raliya ta hau ihu da zage zage,abun ne ya zame mata wajen goma ba. A gefe ga d'iyarta ta tsunduma kanta a harkar bin maza itama. Can kuwa nura ne ya kara lalacewa da bin mata. Matarsa ma ta gujeshi,hamza kuwa ya zamo mijin tace a wajen matarsa. Ke rayuwa fa tayi mata zafi ga mutuwar Usman,haka ta dawo ta rungumi jikokinta da suke a wajenta. Bata isa ta sanya Hamida da Hamid aiki ba suyi,kamar wata sa'arsu haka zakiga sunayi mata tsawa. Duk cikinsu,hindatu kadai ta fita daban,babu ruwanta ke sai kice ma ba daga jikin raliya ta fito ba. Nazo jana'izar Usman sannan na tattara na koma Abuja ina mai cike da dumbin mamakin ramar da Abba yayi sannan gaba daya duk yayi sanyi kamar bashi ba.
Wata biyu rabona dashi saidai nakan kokarta kiranshi na gaisheshi,wataranar juma'a ina zaune na dawo daga masallaci na amsa kiransa inda ya nemi nazo na sameshi da sauri. Ba shiri washegari na tafi a mota. Kuka sosai na samu Abba yana yi,cike da fargaba nikam na karasa wajenshi don gani nakeyi kamar zai yimin magana cikin fada fada kamar yanda ya saba. Ga mamakina naga ya rungumeni yana neman gafarata,yace a baya yakan damu idan yayimana wani abun ashe ba'a son ransa yakeyi ba Tasleem. Yace min ya iske raliya tana waya da bokanta inda takeso tazo ayi mata aikin da za'a kasheshi suci ragowar kudinsa saboda ta fahimci ya soma talaucewa ita kam bata tab'a ganin