Showing 12001 words to 15000 words out of 15857 words

Chapter 5 - Tawa Ta Same Ni Book 2 Complete by Halima Abdullahi k Mashi .txt

ganin abin rabawa na
buga jaka na buga bokitai na roba sai na buga agoguna
har fada mama tayi min wai naje ina amso kudi masu
yawa haka shi kuma ya biye min,nace to mama kiyi
hakuri ni ban yana cewa in basu isa ba zai kara min
wasu wai dan ni kadai yake neman kudi,mama tayi
tsaki ta shige daki mu da Amira ba muje shirya gurin
da zaayi sisters day din ba dan gudun rikici sai bayan
an gama komai an soma kai kawaye sannan muka
shirya,jan material dan dubai shi na dinka riga da siket
nasa duk yanda mutum ya kai ga hassada ba zai
kusheni ba a wannan rana takalmi da jaka bakake nayi
amfani dasu kafin amira ta gama shiri na shiga gidan
mu na fito wata mummunar faduwar gaba naji sanda na
hangi yaynmu a kofar dakin yaya Kabir shi da Nasir
sanye yake da wando jeans baki da riga fara ta kama
jikinshi kyau annuri ne ke fita a fuskarshi yana da kyau
na karshe fatar shi ta kara zama smooth giran gashin
shi kuwa abin birgewa ne,kamar na juya sai na dake
tunda bai ganni ba gara na nuna ban ganshi ba sai da
nazo daf da su sai Nasir yace kai Iman wannan dauke
kai haka?na juya da sauri ango ban ganka ba ne,na isa
wurinsu na dubi yaynmu wanda yayi wani kicin kicin da
fuska nace sannu da zuwa yaynmu kunzo lfy?a ciki
yace lfy duk sai naji ba dadi dan haka sai nace Nasir a
kirata ne?yace a'a ba gurinta nazo ba sai na wuce
ciki,ganin yaynmu sai tsohon ciwona ya tashi wutar
sonshi ta soma ruruwa a cikin zuciyata ranar dai sai a
hankali mun isa gidan yaynmu sai naga ma ashe duk
yanda suke bada lbr haduwar gidan ya wuce nan gefen
da ake sister day lambu ne yanda suka shirya yayi kyau
Amare kaya iri daya suka sa tunda muka zauna bamu
tashi ba sai da aka soma liki sannan ne na shiga nima
na bada tsoro da kudi na fito,anty mimi tayi kyau sosai
cikin farin tattausan leshinta rigar fitet ce don haka
cikinta ya dan fito dan das daga mun hada ido sai ta
dalla min harara har Amira ta lura da ita tace ke kefa
matar can take harara nace tayi ta gama abinda yasa
ma bata neme ni da rigima ba dan tasan yanxu bama
shiri da mijinta ko ince an samin rana shiyasa Amira
tace haka ne kam,wayata ta soma ringin na duba sunan
yaynmu na gani gabana yayi mummunan faduwa na
dauka yace ina jiranki a falon gidan nan cikin in ina na
ce ban san hanya ba ki tambaya sai ya kashe wayar na
dubi Amira kinji yaynmuda rikici ko wai na sameshi
falonsu bayan dazu da ya ganni sai ya wani daure
fuska Amira tace kije mana nace to ai tana kallona
matarshi Amira ta ce to zauna ina ruwana,na mike na
nufi hanyar waje nan na kirashi nace ban gane hanyar
ba gani a gurin bakin gate,yace ni kenan kike nufin in
zo ko?sai ya kashe,gun mai gadi na nufa nace mishi
dan Allah ina kofar falon,ya nuna min sannan na nufa
sanyi da kamshi da kuma laushi su naci karo dasu ina
shiga falon,yana zaune yana shan coke na isa gurinshi
har ya canza kaya daga bakin jeans zuwa blue da yar
shirt,na dan rusuna gefenahi yace tashi ki zauna kan
kujera na tashi nabi umarninsa yana kallona kamar hoto
ko TV yana shan coke na gaji kar matar shi tazo sai
nace gani yace na ganki sai yaci gaba da abinda yakeyi
da danne dannen waya,can sai yace ke kamar ni nazo
garin nan ace ki gagara zuwa ki gaisheni?sannan da
muka hadu sai kika wani dauke kai ke kin girma wai
shekarar ki nawa ne?nayi shiru dake nake na dubeshi
fuskata a daurena kauda kai,ba kya jina nace sha
takwas yace to me na miki kika kasa gaidani?nace ban
gane kaba ne shiyasa shi yasa kika manta dani ko?baki
taba yi min waya ba tun da natafi me yasa?nayi shiru
can nace to kayi hakuri,aikin ki kenan bada hakuri to
na hakura menene shirye ahiryen na ki bikin?na
dubeahi ni bani da wani shiri yace ki dai fada tun da
wuri kinsan ance mai kwarmin ido da wuri yake sa ma
kuka nine uban Amarya kuma nine abokin ango,haushi
ya kamani nayi kicin kicin yace to menene na bata ran
kamar ba ke kika zabi mijinki ba?sai ya canza magana
baba kwana biu ban kirashi ba kuma tun da nazo banje
ba amma zanje mu gaisa nace dama kana kiranshi ne?
sai ya share zancen,kun zan jarabawar?munyi,to Allah
ya bada saa amin ina yan waige waige yace me kike
kallo ne ki saki jikinki gidana kike ba na wani ba ni ko
yaynki ne,Amira da Mami sai doko min waya suke ina
cewa gani nan yaki sallamata,har suka tashi sai ga
mutane na mike da sauri harara ya sakar min ba shiri
na koma na zauna a raina nace kai dai kana shaawar
kowane biki sai ka sani a problem,sunyi mamakin
ganina sosai fuskar anty mimi a kaina,Nace don Allah
zamu tafi shi kuma sam ya ki sai da yayi raayi sannan
yace to wa zai kaiku?nace mashin yace bana son kina
hawan mashin fa nace to nabi motar Nasir ni da
Amira,to sai yaushe nace ai yanzu kuna nan zamu yi ta
gaisawa ko yaushe yace shi kenan,washe gari lunchn
tun safe ba hutu sun tafi gyaran gashi ni kam da bani
kona gashi sai na tafi kitso biyar daidai kowa ya shirya
sai mu kawaye da Amarya ake jira dan har an soma
dibar kawaye bayan na shafa mai sai inner wears na
dakko less wanda ya amsa suna less kalarshi ba zaa
kirashi milk ba kuma ba zaa kirashi yellow ba shi kuma
ba light brown ba yana dai tsaka tsaki na saka shi
sannan nayi shafe shafe kai ni kaina nayi mamakin
kyan da nayi sai da na gama shiri tsaf sannan na fito
kai Iman inji Mami gsky ko ni amarya kin fini haduwa
gsky cire inji Mami nayi murmushi nace ba wani kyan
da nayi,kafin tayi magana sai ga su Amira da sauran
kawaye kowacce sai da ta raina kwalliyarta ynxu burina
inga yaynmu shima inji ta bakinsa mun fita harabar
gidan mu yan mata ne tsantsam nan kallo ya koma
kanmu Adams ne tsaye suna magana da sauran abokan
ango yana hango ni sai kawai ya wani washe baki yana
kallona amira tace iman ji mutuminki nace naganshi
share kawai,ya iso gurinmu Amarya gsky ba tare da
ango zamu kaiku ba sai dai ya haura ma kanshi daga
baya,Mami tace saboda me kace haka Adams?Ya nuna
ni yace ga yar gidana da Amira ku zauna tare a motata
don ni ne zan tuka ku na juya zan mishi magana sai
wata masifaffiyar hadaddiyar mota ta kunno kai
harabar gidan duk mutanen dake gurin sun raja'a ga
ganin motar, baka ce wuluk haka gilashin ta ni kam
shashancewa nayi ina duban motar dan tunda nake ban
taba ganin mota irin wannan ba,Adams ne yace sai
Maska dai dai lokacin da yayanmu ya fito cikin wata
shadda galila yar gaske sai maiko take,hatta
numfashina sai da ya dauke na yan dakiku sannan ya
dawo daga nesa damu yake amma kamshin sa har
gurinmu,Adams ya ce sai Maska yaynmu ya dago mishi
hannu ya mishi alamar yana zuwa 'yan mata suka bishi
da kallon birgewa yayin da wasu suka kyasa
A hankali nayi ajiyar zuciya sannan nace Adams kun
damu mu fito ga mutane ba'a gama kwashe su ba ya
za'ayi mu tafi?ya ce to ynxu ya za'ayi kenan? Amira
tace don Allah ku gama kwashe su mana sauran
abokan suka ce to,yaynmu ya kuma fitowa gurin
motarshi ya nufa Adams ya bishi ya bude mota suna
magana da Adams ko me suke cewa oho?sai Adams ya
dawo shi kuma ya shiga cikin motar sai kuma ya fito
ya dubi gurinmu da hannu ya yafito ni gabana ya fadi
nace Amira yayanmu yana kirana mami tace karki dade
fa banko iya magana ba na nufi gurin motar sai na
samu kaina da canza salon tfy cikin isa da kasaita na
iso gurin motar gefen kusa da dryva ya bude dan haka
sai na zagaya nayi magana sai naji yace shigo ba musu
na shiga kamshi da sanyi sukaimin sallama cikin isa da
jan aji ya tashi motar ba tare da ya dubeni ba cikin
gwaninta ya fusgo motar da gudu sai da muka hau titin
Bako Road sannan ya kara sautin wakar p square cikin
wakar su ta no one lyk u,na jingina da kujera ina
sauraro wakar na zata gurin lunchn zamu je sai fa naga
mun dau wata hanyar ban ankara ba sai gamu gaban
gidan yaynmu dake Yakubu Avenue gabana ya fadi
sannan tsoro ya bayyana a fuskata yaynmu ya dube ni
sai ya fito da waya yana yan danne danne shi ban sani
ba ashe hotona yake dauka ban sani ba,na rufe wayar
sannan yace bisimillah mu shiga nace me zan yi
yaynmu?kasan fa gurin Lunchn zamuje,yace nima
bazaniba dan haka kema ki hakura da sauri na dubeshi
cikin damuwa nace mami ba zata ji dadi ba fa yanda
muke da mami ban kyauta mata ba,dubana kawai yake
sannan yace to mimi taje mana ni dake dan haka ynxu
ma ni yunwa nake ji mu shiga ki min abinci na dubi
fuskar shi ba alamun wasa amma duk da haka sai da
nace bai dace matar gidan ba ta nan ba na shigar mata
gida ya daka min tsawa gami da cewa tsaran ki ne ni
kike yi min musu?bayan mun shiga ya tsaya da motar
na fito shine a gaba ina binshi a baya har falo ya zauna
nace inane kicin din bi nan ya nuna hanyar,na tafi
komai na kicin da ake bukata akwaishi dan haka na
shiga aiki gasky na raina tsaftar matar gidan banyi
karambanin gyra mata kicin ba nidai nayi iya aikina
farar taliya da miyar kwai da hanta nayi mishi a
gabanshi na jera komai na koma na zauna ya dubeni zo
mu ci kai kawai na girgiza dai dai lokacin da naji ringing
a cikin jakata na ciro wayar har ta katse na duba 11
miss call na duba su Mami ne da Adams na dubi
yaynmu dake faman cin abinci nace su mami na jirana
ya dubeni kin san bana son nacin magana ko?ya
kamata ki rike wannan ya cigaba da cin abincin shi sai
da yayi dam sannan ya shige dakinshi wanda an rubuta
master bed room a jikin saman kofar dakin da yellow
din kala kamar minti biyar ya fito zo muje
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
A ranar haka muka yi ta yawo a gari dan mugunta har
magariba kuka ne kawai banyi ba dan haushi wai ace
biki kamar na mami bana guri ai da takaici gashi ya
amshe wayata ya kashe na rasa irin wannan ikon,
gidan shi muka koma ya tafi masallaci ya barni wai
nayi sallah cikin dardar na zauna sai bayan ishai ya
dawo ko sallar ma banyi ba ya kuma daukata ya shiga
gari sai tara ya maidani gida lokacin an tashi daga
lunchn din dan haka dakinmu na wuce na fada gado ko
da mami ta shigo da fushi ganin ina kuka sai ta sakko
tana tambayata menene?cikin kuka nakece mata
yayanmu ne ya daukeni sai yawo yake dani ya hanani
zuwa gurin lunchn dinki tace ba komai kila shima yana
da dalili nace wanne dalili?shidai burinshi ya ga raina a
bace nan dai ta shiga lallashina. Washe gari aka daura
wasu mami aure, da daddare aka kai mami gidan Nasir
dake unguwar sarki tun fara bikin sai yaune muka sake
nida Adams dan yayanmu ya kasa ya tsare yaki barina
na cashe ashe shi yana can suna yinta da anty mimi
yace ba zata zo ba ita kuma tace sai ta zo ya gama
shirinshi tsaf ta taso har gun mota ta biyo shi tana
cewa sai taje,ta shige mota itama tata kama murfin
motar yace sake min tace sai fa naje yace ke kina fa
cin darajar cikin jikinki ne bayan haka dakin san ina
fada kina fada ba zata yiwu ba amma zaki haihu ba zan
dau wannan iskancin ba wata macen arziki ce zata bar
gidan aurenta karfe goma kuma bata san sanda za'a
tashi ba to tunda lallashi baya miki zan biki da zafi yaja
murfin motar ya rufe sannan yaja motar,muna tsaka da
fira sai ganinshi mukayi tsakiya suka sani shida
Adams,Adams ya dubeni mun zata ba zaka zo dinner
kanwa ba?yace kasan mai iyali saida na lallameta tayi
barci Adams yana yayi kyau muma dai Allah ya kaimu
ga jarawa ,ni kam kumallon ya motsa don haka duk
haushi suka bani Adams ya dubeni yar gidana kina
gaya min kince zakuyi lunchn da mene?nace sai mun
zauna dasu Amira menene na sauri Adams da sauran
lokaci fa,yace ba wani lokaci gara ki fada min don in na
tafi sai ana sauran kwana daya biki zanzo in nasan
komi tun yanzu zaizo da sauki,na dubi yaynmu wanda
yake ta aikin danne dannan waya tamkar baya jin mu
nan ko yana sauraren komai nace to kafin ka tafi
zamuyi zancen, gobe fa zan tafi cikin kosawa da
maganar nace to baga waya ba Adams yace to shi
kenan ya canja zancen da hajiyata tana son jin
muryarki bari na kirata ku gaisa,nace haba dai daren
nan?ka bari sai da safe yace to na bari kinsan ni ba dai
cikin gimbiya ba nayi dariya nace to Allah yasa ka dore
ba sai naje gidan ba a canza min yace haba aini din
nan ko bawa kika samu kinsan yanda nake son ki
kuwa?kin san nutson da nayi a kogin kaunarki?in da
ace kinsan yanda jiki da jijiya da bargo da kashi da
tsoka........kai yaynmu ya daka tsawa ya cigaba haba
Adams ka tasa yarinya karama kana wannan
kauyancin?ai wannan soyayyar dace in kana sonta
idonka kadai ya isa sheda ba sai kanata wannan batun
ba ka gane wannan ai yar da girma ne da ga ni har
adams kallonshi muka tsaya yi sai da ya gama sannan
yace Maska kai komai naka daban ne kana da hali irin
na masu girman kai...yaynmu ya daga mishi hannu ya
isa yi tayi,Sai karfe sha biyu muka tashi daga dinner
washe gari muna sallama da Adams yace sam bikin
nan bai min dadi ba,dan naso muyi hotuna muyi hira
mai isarmu amma haka bai samu ba nace kar ka damu
tun daga waya maganar hoto sai na shiga na miko
maka munyi sallama nabashi hotuna ya diba son ranshi
mun rabu akan sai naji shi a waya haka muka
rabu,bayan gama bikin mami yaynmu bai kuma damuna
ba sam gaisuwa ke hada mu sai dai da naje gidan
babana ne yake cewa yayanmu yana zuwa yana
gaisheshi har yazo da mai dakinshi ya yabeni tare da
fadin kirkinshi,ranar ma muna zaune a falon babana
dani da Anty Maijidda sai ga yaynmu sun gaisa da anty
maijidda sannan na gaisheshi anty tace kije ki kira
babanki na tashi na dauki dan kwalina naje na sanar
dashi,yana fitowa naga ya soma fara'a ganin yaynmu
suka gaisa sannan yace yazo ne ya mishi sallama dan
gobe zasu koma sai kuma nan da wata hudu lokacin
bakina da abokinshi babana yayi mishi godiya gami da
sa albarka sañnan yace ga kanwar ka nan dama ta
dameni wai nayi sallar magariba na kaita gida don haka
sai ta tashi ku wuce,na ce sai gobe zani,babana yace
a'a ni kinga gobe kwatano ma zamu,na soma shagwaba
nayi takwa takwa da fuska nace nidai to ai baka sai
min abinda kace ba yace me nace zan sai maki?
computer yaynmu ya harareni na kauda kai babana
yace to in na dawo ranar sati monday sai na sai maki
shi kenan?nace eh yace to uwata maza tashi yaynki na
jiranki na mike ina fadin ko kana korata ne?ba zan sake
zuwa ba suka sa dariya shida anty Maijidda yace wane
ni na kore ki ban isa ba nayi kadan anty tace naje daki
na dauki kayana na dauka tace na gaida mamana,tunda
muka dau hanya ni da yayanmu ba wanda yayi magana
can yace gobe zamu koma sai kuma bikinki na dubeshi
to Allah ya tsare hanya na fada cikin karfin hali,tunda
muka zo gida muka samu haj yaya a harabar gidan na
soma tsuma,cikin tsoro nace gasu haj,to menene yace
yana fakin na fito da ido suka bini shi kuma ya nufi
gurin su ni kam gida na wuce,yace haj daga ina?ta
daure tace nan makwafta muka shiga barka ta cigaba
matarka tana jiranka ashe kai kuma kana nan kana
yawon banza daga ina kake?daga tudun wada,gurin
wa?gurin baban iman ta kuma dubanshi muje ciki gani
nan tana mamakin halinshi shi mutum ne wanda baya
shakka ko karya komai zai fada in dai gsky ne zai fada
sai dai a mutu
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Haj yaya fada take tana karawa tace eh dan shashanci
matrka ta na nan tana jiranka kai kuma ka tafi gidan
kanin ubanka yace to haj dan naje munyi sallama shine
damuwa?to kiyi hakuri ta dan sassauto kai baka da
tunani yanzu in kai wanine yaushe zaka bar Adamu
abokinka ya nemi yarinyar nan ga kannenka?yace
wadanne kannen kuma bayan sunyi aure?ko ba ma
haka ba ai matar mutum kabarinsa....tace nasan haka
amma ni na sha alwashin sai na hana auran Iman da
Adamu in dai ina numfashi yanda bana son ta rabeni
kaima bana son ta rabi na kusa da kai kaf yayana
wacce ce ta samu mai kudi dan mai kudi kamar
Adamu?babu dan haka itama ba zata aureshi ba,sororo
yayi yan dubanta sai da ta gama sannan yace to haj ke
me zakiyi akai?dan Allah ki bar maganr nan,tace nasan
abinda zanyi kai dai tashi ku tafi Allah ya tsare hanya
kana can zakaji lbr,yaso yayi mata nasiha gami da
shawara amma sai taki ta hau shi da fada,dan haka sai
yace to haj zan wuce ba zan samu dawowa da safe ba
saboda sammako zamuyi ta kano zamu tashi sakon ki
gobe in Kabir ya kaimu kano ya dawo zaije banki ya
amso maki kudin,ta ce zaka kara min dubu talatin akan
na da yace ba komai zai kawo maki ina Mimin mu
wuce,haj tace tana gidansu, ya dubi haj wa yace taje
jiya fa can ta yini haj tace ai ba'a gajiya da gida ka dai
biya ka dauketa yace Allah ba zan biya ba tunda ban
aiketa ba in ta dawo shi kenan in bata dawo ba ta
zauna,Haj ta dubshi gara da ka nuna na gani dama ta
kawo min kara kana wulakantata son ranka yace haj ni
kinsan abinda take min ne? bata san kula da miji ba
bata san darajar miji ba bare yanda zatayi biyayya son
jiki bata iya girki ba,ni nasan ina da mata amma sai na
fita yawon gidajen cin abinci,tace to ai komai dan
lallashine yace wane lallashi ne ban mata ba amma
nasan maganinta zata gane bata da wayo,ya mike mun
tafi haj tace Allah ya tsare kar dai ka yarda naji wata
magana.
Sosai su haj yaya suka hau shiga malamai duk wai dan
araba Iman da Adams ko ina ruwansu oho?nikam
bansan me suke ciki ba,muna hira da Adams yanzu na
sadaqar shine mijina kuma na hakura shirye shiryen
dasu mama keyi na bikin nan ba dama har dubai su
mama sukaje da anty yagana ga wasu jike jike da suke
faman dirkamin bansan ko na menene ba sunce ma in
saura sati biu bikin zamuje maiduguri a gyarani bansan
gyaran da za'a min ba tunda dai nasan nima ba dan
laifi baka ce amma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login