Showing 21001 words to 24000 words out of 31162 words
Chapter 8 - Matar Police Book Complete document .txt
su, Amira ta ce, "Jidda ina gidan mu zakije?"
Jidda ta ce, "Aa ni akai ni gidanmu bazani gidanku yayanku mai tusa, yata dukana ko ya harbeni ba. "
Haka kuwa akayi Jidda aka fara kai wa gida kan aka kai su Amira da Amir.
Jidda na shiga gida kuwa ta tarar da Mumy (Hajiya maryam) ta zo suna ta hira da Hajiya Iya.
Mumy ta ce, "Kakata andawo kenan, ya baki bi su Amira da ba, ai da anjima driver ya dawo da ke."
Jidda ta ce, "Ni Um-un bana son gidanki Wannan Yayan dukana ya ke, dazu ma ya min wanka fa tab."
Murmushi Mumy ta yi ta ce, "Ayya Sorry Kakata ki yi shiru kinji ko, in kara dukan ki ni zan rama miki da kai na."
Jidda ta ce, "Yawwa, ni yunwa Nakeji iyatu abincina, wayyo cikina."
Mumy ta ce, "Je ki gun Antynki Mariya ki karbo abincin ina jin ai ta kammala."
Da gudu Jidda ta shige kicin , "Anty Mariya Yunwa na ke ji mai aka dafa."
Mariya ta ce, "Taliyace ga tanan in zuba mi ki ne?"
Nan ta ke ba magana Jidda ta baje a kicin din kasa ta fara kuka, "Wallahi bazan ci taliyar ba, ni tuwo zanci ni innaci taliyar zukyemin jini ta ke, wayyo Allah na."
Da sauri Iya da Mumy su ka nufi kicin ba shiri, hatta Mama da ke daki ma sai da ta fito, sun zata wani Abu ne ya same ta.
Suna shiga Mariya ta ce, "wai ba za ta ci taliyar ba."
Iya ta fara surfen masifa, "Ai daman wannan salon mugunta ne kawai ace safe taliya rana taliya taya abinci zai zauna acikin mutum to Wallahi tun wuri adafa ma ta tuwo yanzun nan ko kuma ni na shiga kicin din in dafa."
Da sauri Mama ta shige ta na, "Bara in daura Mariya ki min jajjjage."
Jidda kuwa tashi ta yi ta fice waje abinta.
Ta na fita ta ga yaron makota na wasa ta ce, "Kai zonan."
Yaron ya zo da akalla bai zarce shekara biyu ba.
Ta ce, "Mamanka ta ma wanka kuwa ?
Ya ce, " Aa."
Nan ta ke Jidda ta fara tubeshi ta kai sa gaban famfom da ke kofar gidan ruwan sanyine sosai Amman ta tasa yaron mutane gaba tin bir ta na jikashi.
KHALEEL ne ya zo wuce wa amota daga office zai je wani aiki.
Hango Jidda ya yi tana ta faman dirzan jikin Dan mutane, kaman zai wuce sai kuma ya tsaya.
Urs Xayyeesherth
[11/24, 10:58 AM] Xayyeesherth: °°°°°° _*MATAR POLICE*_ °°°°°°
24November 2020
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*🤝
__________________________________________________________
_We Are Here To Educate,Motivate, And Entertain Our Readers._
__________________________________________________________
_*Matar Police kirkirarren labarine mai cike da barkwanci, fadakarwa,nishadantarwa tare da sabon salo na mussaman domin farantawa masoya littafaina*_
_*LABARI DA RUBUTAWA*_
_*AISHA MOHAMMED SANI (Xayyeesherthul-humaerath)*_
_LITTAFAN MARUBUCIYAR_
1- _BABU RUWAN SO_
2- _KUCHAKAR KISHIYA_
3- _WASA DA SO_
4- _AZZAWAJUL-MUKADDAR_
5- _JAMEEL (Nafseen)_
6- _KWADAYI 2020_
AND NOW *MATAR POLICE*
_LITTAFINA NA KUDINE INDAI KI NA SON CIGABAN ZA KI TURO KATIN 200 KACAL TA WANNAN NUMBER 08103080717 SANNAN KI YI SCREENSHOT DOMIN TUROMIN DA SHEDAR BIYA_
_*BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM*_
*_FREE PAGE 30/31_*
****************
************
******************
Dago glass din Motar ya yi, ya kalleta sannan ya fito.
Ya na fitowa saukar rankwashi kawai Jidda ta ji a kanta, tun kafin ta dago kai ta ga waye ma ta fara, "Allah ya Isa na Wallahi, mugunta kawai."
Dagowa ta yi suka hada ido da KHALEEL ta yi saurin kawar da kai ta na, "Yaron nan fa ya ce min Mamanshi ba tai mai wanka ba shine na Ke mi shi."
KHALEEL ya ce, "Ke din ma kin Iya yiwa kan ki ne bare Dan wasu? Kuma bakya ganin ana sanyi ne? Na Lura Ke kam dai mahaukaciya ce, Shashasha."
"Ni dai ba mahaukaci....
Kan Jidda ta karasa magana sai ga mahaifiyar yaron nan ta fito ta na kumfar masifa.
Banda iskanci A sanyin ki jikamin yaro da ruwa, wannan ai iskancine ba yarinta ba.
Ta na karasowa ta maka wa Jidda Mari afuska, Jidda ta ce, " Mugu Azzaluma kawai."
Nan fa ran MATAR nan ya kara baci hakan ya sa ta saurin harzika tare da Fara jibgar Jidda.
Ban da Ihu ba abin da Jidda Ke yi.
Ta fara , "Yaya Dan Allah ka ce ma ta, ta barni haka Wallahi daga yau bazan kara mi shi wanka ba, ni ba ma ruwana da shi."
Kallonta KHALEEL ya yi,tare da yin dogon tsaki, ko kala bai ce ba ya yi wajen motarshi ya bar wajen nan ta ke.
Mata kuwa sai da ta jibgi Jidda son Ranta kan ta kyaleta, ba shiri da gudu Jidda ta shige gida ta na haki.
Mumy ta ce, "Kakata ina kikaje ne haka tun dazu an gama tuwon Amman an dubaki ba a ganki ba?"
Jidda ta ce, "Umm ni ma ban San inda aka kai ni ba kawai gani nai nadawo."
Ta shi ta yi ko wanke hannu ba tai ba zata fara cin tuwon.
Mumy ta ce, "Aa dai aje awanke hannunku."
Ta shi tayi tana tsallenta ta shige toilet ta wanke kan ta fito ta fara zakar tuwo.
Tunda ta fara cin tuwon nan Mumy Ke ganin ikon Allah har sai da Jidda ta take tuwon nan tsaf abincin da mutane uku za su iya ci Amman ga yarinya nan yar shekara Tara ta cinye tas.
Ta na gamawa Mumy ta ce, "Sannu Fa Jidda, Yawwa Hajiya Iya wai ya maganar yan Jigawane Malam Adamu?"
Iya ta tabe baki , "Yoo ina nasan ma yadda ya ke mutumin da ya manta da mu gabadaya, ina so Ibrahim dai ya zo ya kira min shi asalularsa asanar da shi Maganar Auren Mariya in ya yi niya yazo shi da iyalan na sa."
Mumy ta ce, "Ah yakamata kam ya zo gaskiya."
Malam Adam 'Dana ga yar uwar Hajiya Iya kasancewar Iyayensa sun rasu tun yana yaro hakan ya sa Iya ta Rainasa tare Alhaji Ibrahim,Malam Adam ya na da matukar son abin duniya arayuwarshi ya dage sai ya yi kudi ya zarce Ibrahim, duk da kasancewar shima ya na da rufin asiri dai-dai gwargwado Amman ya fi hange kan na Dan uwansa,hakan ya sa ko waiwayen Hajiya Iya ba ya yi bare kuma Alhaji Ibrahim.
Mama ce ta fito daga daki ta na, 'Yawwa Mumy daman Alhaji ya ce inya dawo daga tafiya za mu je siyayyen kayan bikin, kin ga kwanaki na ta tafiya gashi mu ne dangin Amarya kuma dangin ango."
Mumy ta ce, "Hakane kam Uncle dai kam ai ya yi sa'an uban gida, ya rainesa kuma ya bashi kyautar 'ya, kin ga ai sai mu tafi duka da ni, da Ke, da mariyar, har ma Da Hajiya Iya, kin San yaran yanzu da su ake zuwa siyayyen komai na zamani ya chanja."
Karaf kuwa Iya ta ce, "Ai kuwa dai, ni fa lokacin Aurena, ko Iya hada ido da iyayena ba na iyayi, Amman yanzu Ku tsabar rashin kunya ma naga da yaran kuke shawara, gaskiya duniya ta zo karshe, ko gobe ko jibi sai ku Iya jin ance tashin alkiyama ne."
Mumy ta ce, "Hajiya Iya gobe talata jibi laraba fa kuma ai Ran juma'a ne za ai tashin alkiyama."
Iya ta ce, "Au ki na so ki cemin ba ma juma'an ba ne yanzu? Lallai to ni azatona ma ai yau juma'an ne duniyarce duk kun bi kun rikitata."
Dariya Mumy ta yi ta tashi ta na fadin
, "Wai yaushe ne Alhajin zai dawo?"
Mama ta ce, "Ina jin gobe ma insha Allah."
"To Allah ya kai mu, bara kiga na huce gida nasan su Amira kadai ne agida sai dije mai aiki."
Cewar Mumy da ke kokarin fita daga gidan kenan.
Mama Ta tashi za ta bi ta Iya ma ta tashi za aje ayi munafurcin ba to muje tare kanwa uwar gami.
*******WASHE GARI
Dassafe Mama ta sa Jidda ta shirya domin driven su Amira na hanya zai zo ya kai su skul.
Sabon uniform din da aka dinka ma ta,ta kalla kawai sai ta fara kuka , "Ni Wallahi bazan sa wannan dangalallen guntun sket din ba, ai ni ba yar iska ba ce, Wallahi bazan sa ba."
Iya ta ce, "Ina bayanki walle Dan haka ke ba yar iska ba ce ba Wanda ya isa ya saki ki sa wannan danalallen skilen kamar mai tallan jikinta, kalan ma ki fita ace mi ki karuwa, to Wallahi ahir din ki Zainabu Jidda ba za ta sa ba ah to na dai Fada mi ki, ki ma fice min da gani tun kan na tsine mi ki na tsinewa kankan kakarki."
Ba yadda Mama ta iya da Hajiya Iya haka ta fita, sai wata shawarar ta zo ma ta, ta kira Baba ta sanar da shi, ya ce ta kai wa Jidda wayar.
Da ke Mama tasan halin Iya ta na shiga ta ce, "Hajiya wai Gashi za Ku gaisa da babansu."
Da sauri ta fizge wayar ba ni naji Dana.
Ta kafa ta akunne kamar zata manne awajen Baba ya gaisheta ta amsa sai washe baki ake, ya ce, "Ah ya na ji kamar muryar Jidda ne ko ba ta je makaranta ba ne yau."
Iya ta ce, "Ina fa zataje makaranta bayan ankawo ma ta kaya wani irin na yan iskan zamanin fir'auna."
Baba ya ce, "Ayya Iya Kiyi hakuri ta sa ba kayan yan iska bane uniform ne, na yara kuma haka ake yin sa, Amman inna dawo za asan yadda za ayi."
Iya ta ce, "To shikenan ba ra dai mu gani."
Ta mikawa Mama wayar, Mama na fita.
Iya ta ce, "ai in sun San wata ba su San wata ba, ni dai bazan barki da shigar iskanci ba dauko ki sa ki ga wani Abu."
Da Jidda ta sa uniform din nan ba karamin kyau ya ma ta ba tamkar Dan jikinta akayi.
Nan ta ke Iya ta dauko wani tsohon zanin leshinta ta ce, "Yawwa matso nan in daura mi ki, tunda su yan iska ne ai mu ba ma biye ma su ba."
Haka Jidda ta fito ga uniform ga zani daurin kirji, zama ta yi ta zabga uban kwalliya kamar me tafiya tashi, sannan aka sa sandal da safa, tafiya ta farayi kamar wadda kwai ya fashewa aciki adole ita ta yi kyau.
Mama na ganin Jidda daga sama har kasa Dan takaici bata San lokacin da ta fara dariya ba, Mariya ma na fitowa ta fara zabga dariya harda rikye ciki.
Iya ta ce, "Iskancin banza iskanci wofi, mu za agayawa iskanci ai mun nuna ma Ku mun fi Ku iyawa ne."
Mama dai tai tsit.
Mariya ta ce, "Dimple Queen ina zuwa haka? Kamar mai zuwa tashe Amman dai ba makaranta za ki ba ko?"
Jidda ta murguda wannan bakin da ya sha Dan Jan baki kamar manja ta cigaba da tafiya ta na rankwasa ta ce, "Makaranta ma na ai ni ba yar iska ba ce."
Ta na fita sai ga driven ya zo, shi kan shi sai da yayi dariya ganin shigar da Jidda ta yi, Amir da Amira ma ban da dariya ba abin da su ke.
Ita kuwa Jidda ko ajikinta ga ni ta ke ta yi shiga tare da kwalliyar kera sa'a.
Suna shiga Makaranta ban da kallon Jidda ba abin da ake ana dariya Amman ita hakan fa ko ajikinta, malamai sun yiwa Principal magana Amman ya ce abarta.
Fita break aka yi Jidda da Amira su ka fito waje suna cin abinci.
Wata yarinya ta zo wucewa kawai ta taka wa Jidda kafa, Jidda ko na tashi ta wasketa da Mariya nan ta ke yarinyar ta fadi aka sa.
Jidda ta ce, "Laaa Amira yasin Aljanune da wannan yarinyar fa kin ga ta fadi."
Amira ta ce, "To kin ga mu tashi ba ruwanmu."
Jidda ta ce, "Tab Wallahi ni sai na mata magani Hajiya Iya ta koyamin yadda ake rukiya."
Amira ta ce, "To nidai ba ruwana Wallahi."
Jidda ta kama kunnen yarinyar ta na gwaranci, ba abin da bata, har A,b,c,d da 1,2,3 ma sai da suka sami damar shiga.
Chan dai jikin Jidda ya fara Duran ruwa taga yarinya ba ta da niyar farkawa, chakulkulu ta fara ma ta ta na, "Wallahi Ku saketa na Fada ma Ku Ku saketa in ba haka ba kakata za ta tsine ma Ku."
Ashe daman yarinya iskancine tana jin an fara chakulkulu ta fara motsawa.
Da guji Jidda ta bar wajen sai da zanin ta ya fadi akasa tsabar gudu wai ajanune Ke bin ta abaya.
Ita ko Amira ban da dariya ba abin da ta ke...
Haka Jidda ta koma gida, ba zani, Iya na ga ni ta fara salati da sallallami, "Ni kuluwa na shiga hamsin ya na ganki tsirara?"
Jidda ta gwalalo ido, "Aljanu na gudunwa shine su ka zaremin zanin ni ban ma San ya fadi ba sai da muka koma aji."
Iya ta kyalkyale da dariya, "Ke ki ka San shakiyancin da ki ka yi dai, Babanki ma ya dawo tashi muje."
________Bayan kwana biyu.
Tun ranar da KHALEEL ya rankwashi Jidda bai kara zuwa gidan ba ko ince ba su kara haduwa ba sai yau da yake weekend ne kuma bai da aiki a office, Hajara ya dauko daga wajen salon kasancewar motar ta ta sa mi matsala, hakan ya sa shi cewa ta rakashi ya gaida Mama kan su wuce gida da kamar ba za ta yarda ba, da kyar dai ta yarda su ka shiga.
Ya na shiga ya Tarar Mama na fama da Jidda ta tsefe kan ta ta ki yarda fir, wai ai satin kitson biyu kuma sai ya yi wata kan ta tsefe.
Da shigarsu Tsawa KHALEEL ya ma ta, nan take Jidda ta fara fitsari awajen tana kuka, Iya na ganin Jidda na kuka itama ta fara, da sauri ta tashi ta shige daki ta kwaso kayansu ahargitse ma ta kulle azaninta, kuka ta ke bilhakki da gaskiya,ga kaya aka da ta daura ta fito ta na, "ke kina mata shima ya zo ya na mata ni na gama lura da Ku in ba kashemin ita kukayi ba bazaku taba jin dadi ba, yau zan bar ma Ku gidannan daga ni har ita sai Ku ta yi," in ta yi magana daya biyo sai goge majina da saman zani, ana kara kakkalo wani hawayen.
Janyo Jidda ta yi tana , "Muje."
Daga Mama har KHALEEL summan tsaye su kaj awajen har ma sun ka sa motsi bare magana.
Hajara kuwa Jan gefe ta yi tana danna wayarta hankali kwance.
Suna fita sai ga Baba ya shigo Mama ta kirashi awaya, da ya ke bai yi ni sa ba.
Ko kallonsa Iya ba tai ba ita dai yau sai sun koma kauye.
Jidda kuwa ta ji dadin zaman birni har ga Allah bata son komawa.
*SHIN YA KUKE GANI? YA DACE ACE JIDDA DA IYA SU KOMA KAUYE, KO KUWA ZAMAN BIRNIN DAI ZAI FI??? MAJORITY CARRY D BOTH*
Urs Xayyeesherth
[11/26, 10:03 AM] Xayyeesherthul-humaerath🥰: °°°°°° _*MATAR POLICE*_ °°°°°°
26November2020
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*🤝
__________________________________________________________
_We Are Here To Educate,Motivate, And Entertain Our Readers._
__________________________________________________________
_*Matar Police kirkirarren labarine mai cike da barkwanci, fadakarwa,nishadantarwa tare da sabon salo na mussaman domin farantawa masoya littafaina*_
_*LABARI DA RUBUTAWA*_
_*AISHA MOHAMMED SANI (Xayyeesherthul-humaerath)*_
_LITTAFAN MARUBUCIYAR_
1- _BABU RUWAN SO_
2- _KUCHAKAR KISHIYA_
3- _WASA DA SO_
4- _AZZAWAJUL-MUKADDAR_
5- _JAMEEL (Nafseen)_
6- _KWADAYI 2020_
AND NOW *MATAR POLICE*
_LITTAFINA NA KUDINE INDAI KI NA SON CIGABAN ZA KI TURO KATIN 200 KACAL TA WANNAN NUMBER 08103080717 SANNAN KI YI SCREENSHOT DOMIN TUROMIN DA SHEDAR BIYA_
_*BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM*_
*_FREE PAGE 32/33_*
😂 *ARADU KAMAR AN TOFE LITTAFIN NAN YAWANCIN FANS DIN SA OUT OF 100% , 80% MA SU SUNA AISHA NE😂 ABIN DA MAMAKI FA TAKWARORINA NE MASOYA, WANNAM FEJIN SADAUKARWA NE GAREKI NAMESY AYSHA SHU'AIB, TARE DA AYSHATUL-HUMAERA, DA KE MA AISHA🤣DA AYSHER🤣BAN MA SAN YANDA ZAN BANBANTAKU BA WALLE😂KAWAI DA MA DUK WATA MAI SUNA AISHA INA YIN KU IRIN SOSAI DINNAN🥰🥰*
****************
************
******************
😂😂 *NA LURA MASOYAN DOMPOL KON BA SA SO TA KOMA KAUYE, DAMAN GWADA KU NAI AI ZAMAN BIRNI YA ZAMA DOLE GA JIDDA, TUNATARWA DAI FREE PAGES NA DAF DA KAREWA DAN HAKA DUK WADDA TA SHIRYA SIYA TA MIN MAGANA*
Baba ya durkusa gaban Iya ya na, "Dan Allah ki yi hakuri ko me aka mi ki daga yau basa a kara ba,in sha Allah, ki ya fe ma na."
Iya ta ce, "To ban da fitsara da iskanci ga ta tsarkin yan tsafta za ta addabarmin diya wai sai tai kitso, ana dole ne? Na ga ita kan ta lokacin da ta aureka a yar gajarta ta ke, ga kai kaman hammatar yan iska, ai ko gwanda jiddan ma ta gajemu tai gashi sak kamar na yan indiya, shine ake bakin ciki ko, hnmm za asha mamaki fa agidannan."
Mama ta karaso" Hajiya Dan Allah ki yafemin na tuba, bazan kara ma ta magana akan komai ba."
Iya ta kada kai tare da fadin, "Yoo ina ma kika ganmu bare ki kara tursasata yin wani abun, na Fada ma Ku fa ba abin da zai hanani barin gidannan Yau."
Daga Mama har Baba ba su San sanda hawaye ya fara zubowa daga idanunsu ba, mussaman Baba da ya San Iyah za ta Iya rabuwa da kowa ma indai akan Jidda ne.
Janyota tai suka cigaba da tafiya ta na hama min masifa, KHALEEL da ya tsaya kallon ikon Allah ne ya yi saurin shan gabansu.
Shima durkusawa Ya yi kamar yadda Baba ya yi, "Hajiya Dan Allah ki yi hakuri, ba za akara takurawa Jidda ba, ai ni na za ta ma kitson kan na ta ya kai shekara ne ba a tsefe ba, da nasan sati biyu ne ma ko magana bazan yi ba."
KHALEEL na magana hanjin cikin Iyahtu na motsawa domin duk a tsorace ta ke gudun kar ya dauko bindiga ya ce zai harbeta cikin sauri ta ke fadin, "Yawwa Dan Albarka daman nasan da ka sani ai bazaka tabamin jikalle ba ko? To Yanzu dai ina bakazo da bindiga ba?"
KHALEEL ya fahimci tsoron bindiga karara afuskar Iyah hakan ya sa shi fadin, "Aa Amman na barta amota ko in dauko mi ki ne?"
Ta na ji ya ce ta na mota ta yi wata irin ajiyar zuciya da ya kai karshen maganar kuwa
Wani irin zaro ido Iyah tai tare da fadin, "A'a A'a Dan Allah ka bar ta ni inna