Showing 1 words to 3000 words out of 142497 words

Chapter 1 - NI DA YAYA SADAM Complete Document by Binta Umar Abbale.txt

NI DA YAYA SADAM


NA
BINTA UMAR ABBALE


1


*JIGAWA STATE*


Jahar jigawa Akwai wani 'karamin gari mai zaman kasan a cikin jahar, sunan Garin *Dabi* 'karamar hukuma ce guda wacce ta tara fulani usul a cikinta, Garin bashi da yawan mutane sosai Amma Allah ya albarkace su da gona ki da abubuwan more rayuwa don duk wanda ya shiga garin sai yayi sha'awar shi saboda dad'in sa suna da wuta da ruwa sannan suna da makarantu na boko da isilamiyya da allo Gaskiya Mai wakilatar garin yana kula dasu sosai, Jama'ar dake cikin garin *Dabi* suna da wayewar kai babu laifi sai dai idan suka fito cikin gari ne suke komawa 'yan kyauye mussaman idan suka shigo garin *Kano* sai suji tamkar a saudia suke saboda tsabar murna. Yawancin jama'ar garin 'yan uwan juna ne shiyasa suke zumunci sosai da sosai sam baka ta'ba jin wata 'baraka ta fito daga cikin 'karamar hukumar saboda suna da had'in kai kuma suna aiki da Iliminsu dai-dai gwargwado.


Wata 'katuwar 'kofa na kutsa kaina ciki na fara rarraba idona.


Kofafin na gani sun kai ashirin da wani abu kuma ko wace 'kofa akwai mutane a cikinta can na hango wata Matashiyar budurwa ta futo daga wata 'kofa a guje! tana nema ta bugeni nayi saurin kaucewa ina binta da kallo naga ta nufi babbar kofar da zata sada ka da ainihin 'kofar gidan gabad'aya.....Kafin in dawo daga tunanin da nakeyi na hangoshi yana talle mata 'keya tare da haurinta da takalminsa irin na sojoji ita kuma sai murza ido take tana zum'bura baki.


Nayi saurin 'buya bayan gatanga har suka wuce inda nake la'be sai na fito a hankali na bi bayansu.


'Kofar da yarinyar ta fito nan naga sun nufa sai na rufa musu baya domin inga 'kwal Uwar daka.


Tana zaune tana gyara fitilar 'kwai irin mai kamar a ci balal d'in nan sai mita takeyi tana fad'in "Marka kinga ja'irar yarinyar nan ko sai dai ta fasa min 'kwan fitila sannan taji dad'i."


Marka dake zaune a kofar d'akinta tana kad'in lagwani tace"Aifa! Ladidi kin manta halin Sayyada kenan nazo fitowa daga 'bandaki naga ta farara da gudu tana dariya sai kace wacce tayi abin arziki."


"Ki rabu da ita Marka ai yau sai na zane mata jikinta wallahi ki duba ki gani 'kwan fitila ta ya kai shekara guda a jiki amma sai da tayi sanadin sa har sauran kalanzir d'ina sai da ta zubar."


Marka tana kad'i tace"Kamar gaske ai ba zaki iya dukanta ba humm! sau nawa Sayyada nayi miki laifi kice zaki hukunta ki kasa Allah dai ya kyauta mutum d'aya ne yake maganin Sayyada."


Tace."To ki zuba ido kisha kallo yau sai na hukunta ta kan 'barnar da tayi mi........Kafin ta 'kara maganar ta sai suka jiyo gunjin kukanta daga soro!


"Wayyo na shiga ukana!! Wayyo baba Ladidi Wayyo Baba hiiiiiiii!hiiii! Wayyo Allahna baba Ladidina."!!!!!!!


Ai da sauri Baba Ladidi ta mi'ke don har zaninta ma ya kusa fad'uwa tayi sauri ta gyara tace" Marka kin gani ko ta futa an zalince ta kai! jama'a mutane basu da tsoron Allah yanzu daga futar ta ko minti biyu bata yi ba har an doko t.......Maganar ta ta katse lokacin da ta hango shigowarsu yana talle mata 'keya tare da rankwashinta aka.


Komawa tayi ta zauna tasha kunu! tana hararasa.


Baba Marka ta washe baki tana fad'in"Maraba lale sannu da zuwa soja marmari daga nesa sannu da zuwa sannunmu zauna ga gurin xama na gyarama ka." Tafada tana shimfida masa tabarmar dake kusa da ita a jinge ne.


A nutse ya cire takalmin sa ya zauna cikin nutsuwa yana gaisheta.....Baba Marka ta amsa cike da walwala da farin ciki tace"Ashe ka shigo gari shiyasa naji waccan kafirar tana kuka dama ai yanzu yanzu nake fad'in kai kad'ai ne maganinta."


Ya kalli gefan da suke zaune Baba Ladidi ta tsuke fuska sam! ta'ki dariya ballanta ta sakar masa fuska saboda ya doki 'yar gidanta.


Fuskar nan a had'e yace."Baba na same ku lafiya."?


Tace"Yo da baka sameni lafiya ba ai ba zaka ganni a zaune da'kau! ba haka kawai daga saukar ka sai ka fara cin zali ni bana son haka wallahi."


Shiru yayi yana kallonta tsawon minti sai ya girgixa kansa kawai ya mai da hankalinsa kan Baba Marka suka cigaba da hirarsu.


Sayyada ta zauna kan 'kafafun Baba Ladidi tana shar'bar majina tare da kuka wiwi "Allah ya saka min Baba wai me nayiwa wannan ne ya tsaneni! kullum sai ya dakeni Allah ya isa ban yafe ba."!!! Tana kuka take wannan maganar fuskarta duk tayi jage-jage da hawaye.


Ya juyo yana kallonta Tayi sa'ke_sa'ke! kan lanjararrun 'kafafun Baba ladidi wanda da 'kyar take tafiya dasu amma saboda tsabar so da sangarta ta bari Sayyada na tumurmusar su........Sarkin Zuciya da miskilanci kawai sai ya mi'ke! a fusace ya zare blet din 'kungunsa ya shiga tabka mata a jiki.


Daga Sayyadar har Baba Ladidin gigicewa sukayi Baba sai kare Sayyadar take wai kar ya daketa shi kuma yana sane ya dinga labta mata blet din ta ko ina!!


A guje! ta mi'ke ta nemi hanyar tsira bayan Baba Marka ta 'buya tana makyarkyata!


Baba Ladidi ta saka kuka tana fad'in" Wannan rashin imani da yawa yake Wallahi tallahi Sadam! zanyi maka Allah ya isa kan kana dukan 'yar nan zan iya bar muku garin gabad'aya mu koma wani gari ina dalili umm! me yarinya tayi maka kawai zaka tsane ta babu dama ka shigo gari shikkenan hankalinmu ya tashi yau har dani ka had'a ka doka tom zamu bar muku garin *Dabi!!."* Tana gama maganarta sai ta dingisa kafafu ta shige d'akinta tana share hawaye.


Sayyada ta mi'ke zata bi bayanta ya buga mata wata razananniyar tsawa"Koma ki zauna munafuka 'kazamiya kawai."!


Ta koma ta zaune tare da sunkuyar da kanta 'kasa! duk rawar kanta tsoron sa takeyi mutum sai kace mala'ika mugunta a cikinsa har da ta siyarwa gashi tunda take dashi bata ta'ba ganin dariyarsa ba.


Mi'kewa yayi fuskar nan a murtuke ya nufi d'akin Baba Ladidi.....Ya shiga ya tarar da ita tana had'a kaya cikin wata tsohowar akwati.
NI DA YAYA SADAM


NA
BINTA UMAR ABBALE


2


Ganin inuwar mutum a tsaye a kanta yasa ta d'ago kanta suka had'a ido sai tayi saurin mayar da kanta 'kasa ta cigaba da harhad'a kayanta.


Ya lalla'ba a hankali ya shiga d'akin ya samu gefan gadon karfenta ya zauna yana me sassauta fuskarsa, yace."Baba Ladi."


Banza tayi masa ta cigaba da harhad'a kayanta.


Sai ya sakko daga gadon 'karfen ya gurfana gabanta tare da ri'ke hannunta yana kallonta a marairace yace."Wai me yasa yanzu kika daina sona ne."!?


Da hanzari tace"Saboda kana zalintar marainiyar yarinya."


Ya sassauta muryasa tare da fad'in"Wannan ba zalinci bane Baba gata ne wallahi idan kikayi sake da Sayyada a haka watarana sai ta sanya ki kuka wai me yasa kika sakar mata take abunda take so macace fa duk rintsi aure zakiyi mata amma kawai saboda sangarta kin sakarwa yarinya tana shashanci har yanzu ta'ki hankali."


"Au! Abunda zakace kenan Sadam."!? cike da mamaki ta fad'i maganar.


Yace." Ai gaskiya na fad'a Baba yanzu a irin wannan shashancin da yarinyar keyi cikin 'kauyen nan waye zai aureta anya ma tana zuwa makaranta kuwa."!?


Baba Ladidi ranta ya 'baci da jin abunda yake cewa tace"Wato har ka manta al'kawarin dake kanka kenan har kakewa Sayyada maganar aure da wani."


Ya mutsa fuskarsa yayi yace."Wane al'kawari ne a kaina? na fad'a miki tun wuri ki daina wannan maganar abunda ba zai ta'ba faruwa bane."


Baba tace"Dama ai nima bance dole ya faru ba amma me yasa ka d'auki al'kwari kasan baza ka iya cikawa ba."?


Yace."Kawai saboda in kwantar mata da hankali yasa na d'auki al'kawari amma ni ko a mafarki banta'ba tunanin zan auri waccan shashashar ba."


Baba tace"To wannan abun kunyar baza'ayi shi dani ba a wannan garin wallahi tattara nawa zanyi in bar muku garin dama kun saba da abun kunya."


Yace."Ke yanzu kan Sayyada sai ki bar mahaifarki? garin da aka haifi iyayenki kan wata 'karamar alhaki sai ki bar tushen ki."!


"Idan ta kama hakane zai faru."! tafada tana kokarin rife akwatin tace" Kaga ma na had'a kayana guri guda Duk sanda Mahaifinka yazo muka tattauna kan maganar naga ya baka goyon baya sai in dauketa mu bar muku garin."


Miskilin murmushi yayi ya d'an kishingid'a kan fillo yana kallonta tana surutai ta gama ta futa daga d'akin tana fad'in "Mutukar kai da mahaifinka kuka karya al'kwari kun ci amanarmu."


Babu kowa a tsakar gidan don Baba Marka ta d'auki kayan kad'in ta ta nufi gidan d'anta dake cikin kofar wannan damar Sayyada ta samu sai ta fuce daga gidan gabakid'aya ta fara bin gidajan mutane tana musu 'barna da shirme duk gidan data shiga in ta dame su zasu koreta idan taji haushi kawai sai tara dutsinan wuta ta hau jifansu dashi tana zaginsu


Baba Marka na zaune a soron gidan d'anta mai suna Kawu Tanko Sayyada ta shigo a guje har sai da ta take mata 'kafafu ba tare da ta juyo ba ta afka cikin gidan tana 'kwalawa Amina kira "Ke Amina kina ina! ki fito kiji."!!!


Matar Kawu Tanko mai suna Iyatu tace" Ke Sayyada baki da hankali zaki shigo a guje kina ganin Baba a zaune amma kika bi takan 'kafafunta."


Zum'bura baki tayi tace"Baba Iya Wallahi Baba Marka muguwa ce ita ta ri'keni wannan mugun mai ba'kar fuska ya dakeni da blet shiyasa ina sane nima na take mata kafarta." Ta karasa maganar tana wata iriyar dariya."


Amina ta shigo da bokitin ruwa a kanta a guje Sayyada tayi kanta ta ru'kunkume ta tana ihu! kafin kice kwabo sai gasu a 'kasa ruwan ya rube a jikinsu sun ji'ke jagab! Sayyada ta mike tana kyalkyala dariya dankwalinta ta cire duk yawan gashinta sai da ya jike duk ya kwanta a gefan fuskarta doguwar rigar ta ta jike sai digar da ruwa take 'kananun nonowanta da suka fara fitowa suka sake tsini duk shatinsu ya fito hatta da nipples din sai da suka nuna alama duk da cewar doguwar rigar ta atamfa ce.


Baba Marka ta girgiza kai tace"Wannan yarinya ban san irinta ba wallahi yanzu yanzu fa Sadam! ya daketa amma da yake jikinta na ice ne har ta wartseke tana ibilici Shashasha mara nutsuwa ai zan sanya Sadam! din ya sake zane ki tunda bakya jin magana."


Amina tace"Baba da gaske kike Yaya Sadam! ne yazo."?


Baba Marka tace"Kaji ni da yarinya dama ni ina karya ashe."!?


Sayyada ta kyalkyale da dariya tace"Baba bakya 'karya sai dai ki fad'a ba dai-dai ba." hahahaha ta karashe maganar tana dariya.


Baba Iyatu takaici ya isheta sai ta dauki takalmi ta nufe dashi tana fad'in "Don 'kaniyar ki Uwar tawa kike 'karyatawa a gabana."


Sayyada ta ruga a guje han fita ta nufa tana dariyar hauka had'e da tsalle-tsalle.....Da sauri Baba Marka ta janye 'kafafunta tana fad'in"Yanzu sai tabi ta kaina ba hankali ne da it.......Kafin ta 'karasa maganar da takeyi taji bururut!burut!!! Sayyada ta sakar mata tusa a kanta a guje! tayi waje tana dariya.


Baba Marka ta toshe hanci! tana yun'kurin tashi ta bar gurin saboda tsananin warin tusar....Baba Iya kuwa dariya ce ta su'buce mata tayi mai isarta tana nemawa Sayyada shiriya gurin Ubangiji.


Amina a gurguje ta sanja kaya ta bi bayan Sayyada can Kofar Baba Ladi.


Karo suka buga ita dashi kirjinta ya daki kirjinsa....A gigice ta kwallara 'kara ta d'ago kai tana kallonsa rintse ido tayi tana tsalle had'e da harfar da hannuwanta kamar wacce ta 'kone fad'i take "Wayyo Allah na! Wayyo 'Kirjina wayyo 'kirjina Na shiga ukuna."!!!


Ya zuba mata ido yana kallo jikinta a ji'ke jagab! babu abunda bai gani ba a jikinta ga 'kirgar dangin ta nan yayi cibir dashi a tsaye yayi saurin kauda kansa daga kanta....Ita kuma bata fasa ihun da takeyi ba, Tsawa ya daka mata " Ke don ubanki yi min shiru."!!


Tsit! tayi tana kallonsa da idanunta masu rikita masa lissafi


Ya dauke kansa yana cizan lips dinsa na 'kasa mugun haushin yarinyar yake ji wallahi ya rasa wane irin horo zaiyi mata wanda zatayi hankali sai kaje mai sarkin aljanu aka.


"Hiiiiiii!! Wayyo Kirjina zafi suke min wayyo nan d'ina wayyo Baba Ladidinaaaa!!!! Sosai ta 'bare baki tana kuka sai hawaye ne yake shatata da alama dai da gaske take 'kirjinta zafi yake.


A dake! yace." Ina ne yake miki ciwo a 'kirjin naki."?


Nonowanta ta nuna masa duk guda biyun.


Yayi sakare yana kallonsu da mamaki a tare dashi Ina abun yake? da har dan an zunguresu zasuyi ciwo yanzu dai idan ya fahimta had'a 'kirjin da sukayi ne ya sanya take wannan kukan kamar wacce aka yanka.


Cike da mugunta ya kai hannunsa kan brest din ya murd'e da 'karfi! "Wayyyo! Wayyo! Allah."!!! Sai ta zube a gurin tana wani irin jan numfashi.


Ya tsugana gabanta tare da tsira mata lumsassaun idanunsa yace." Duk sanda kikayi laifi zan dinga hukunta ki da wannan tunda naga duka baya d'aukari dan uwarki! zan dinga murd'e miki nono sai kiyi kukan da hujja."! Ya mike tsaye ba tare da ya bi ta kanta ba ya nufi 'kofar su Kawu Tanko domin su gaisa yana so ya koma da wuri karo suka ci da Amina.
NI DA YAYA SADAM


NA
BINTA UMAR ABBALE


3


Amina na hangoshi ta nutsu cikin nutsuwa take tafiya har suka had'u ta saki fuska sosai tace"Ya Sadam! ashe kazo sannu da hanya yasu Kawu da Yaya Sule dasu Muniba."?


Yace."Kowa lafiyar sa lau Amina dafatan na same ku lafiya."?


''lafiya kalau wallahi."Tafad'a tana sinne kai. tsai yayi yana kallonta ya lura yarinyar na jin kunyarsa ya rasa kuma meye dalili hankalinta da nutsuwarta yana mugun burgeshi ba kamar waccan mahaukaciyar ba Sayyada.


Yace."Ina fata dai kina zuwa makaranta."?


Tace"Eh ina zuwa a boko ma nice nazo ta d'aya Isilamiyya kuwa sai da aka bani kyauta saboda na haddace izifi biyar da ka."


A take ya saki fuskarsa sosai tamkar gonar audiga yace."Babu shakka nima ta 'bangarena dole in miki kyauta Aminatu kin burgeni gaskiya da zan koma kaduna yau amma saboda ke zan zauna inyi kwana biyu ina so in saurari karatunki idan anjima da daddare."


Amina tayi murmushi tace"To shikkenan Yaya Sadam!.


Yace."Bari in shiga mu gaisa da mutan gida ko."


Tace."To." Ya wuce ya barta tsaye a gurin Amina bata dauke kanta daga kansa ba har sai da taga ya shige kofar su sannan ta wuce ta tafi.


"Wai Sayyada wannan kukan da kikeyi na menene."!? Baba Ladi ce tsaye kan Sayyada wacce ke zaune a dokin 'kofa tana kuka harda majina.


Baba tace" Wai ba magana nake miki ba kinyiwa mutane shiru wallahi Sayyada ki bar ganin ina kyaleki kan abunda kikeyi min ina tara ki ne akwai ranar da zan zane ki da bulala da kaina ai banji takaicin dukan da Sadam! yayi miki haka kawai saboda tsabar rashin ji kika fasa min 'kwan fitila shekarar abina biyu amma kinyi min sanadinsa." Baba Ladi ta dage sosai tana mata fad'a irin wanda bata ta'ba yi mata irinsa ba. Sayyada ta kwanta a kasan gurin tana kuka lokacin ne kuma Amina ta shigo.


"Baba wai me akayi mata take wannan kukan."!? Amina ke tambayar Baba Ladi.


Baba Ladidi na 'kokarin kad'e tabarma tace" Oho mata ai ta saba laifi idan anyi mata fad'a tazo tana kuka."


"Nifa Baba ba haka bane ba za'a tsaya a ji ta bakina ba sai kawai ayi tayi min fad'a."!! Sayyada ke wannan maganar lokacin da take dafe 'kirjinta da hannunta.


Baba Ladi tace" Ai sai ki fad'i dalili ba ki zauna kina kuka ba."


Tace."Baba nan d'ina ne yake min ciwo."! nononta da ya murd'e take nuna mata.


Baba Ladi ta aje ta barmar ta karasa inda take kwance tace"Tashi zaune ki nuna min."


Sayyada ta mi'ke da kyar tana nuna mata brest din nata wanda yafi ciwo tace"Yaya Sadam! ne ya murd'e min."!! Baba Ladi ta buga salati tana tafa hannu tace"Kika ce Sadam ya murd'e miki nono kan wane dalili? ai wannan mugunta ce kowa ya sani idan mace ta fara 'kirgar dangi sunayi mata zafi idan ba so yake ya kashe ki ba kan wane dalili ma zai ta'ba miki jiki bayan ance ya aure ki ya'ki."!!! Baba Ladi ta shiga sirfa bala'i inda ta nufi kofar d'akinta inda mayafinta yake rataye a kofa ta nan nad'e shi ta d'ora aka sai kace wacce tayi gammo wai ita nan yafa mayafi tayi sai ta nufi hanyar fita tana d'ingisa 'kafa "Wannan ai kafirci wato yaje yayi mu'amula da turawa 'yan bana bakwai sun 'bud'e masa ido da iskanci shine yazo zai dinga latsa yaran mutane to kuwa zai ci ubansa."!


Bayan fitar ta Amina ta Kalli Sayyada dake goge hawaye tace" Wallahi Sayyada 'karya kikeyi kice Yaya Sadam! ya ta'ba miki nono wallahi kiji tsoron Allah meye abinda zai burgeshi a jikinki mutum da yake mu'amula da 'yan gayu yaje 'kasar waje yayi karatu yayi cud'anya da turawa masu kyau da ilimi shine har zaki ce ya ta'ba miki nono ni dai ban yarda ba."


"To kada Allah yasa ki yarda mana dama ai ba so nake ki yarda ba aikin banza kawai kamar yanda yake dan uwanki nima haka yake dan uwana harda zaki wani tare masa ai dake ya ta'bawa ba zakiji dad'i ba ke ko kishina ma bakya yi wallahi nasan irin zaman da zanyi dake."


Amina tace"Ai halinki na sani na sharri da shirya magana sai kiyi ta rantsewa kan abunda ba'ayi ba wallahi Sayyada kiyi hankali ki daina abunda kikeyi."


Sayyada haushi ya sanya ta soma zagin Amina kafin kice kwabo sun kaure da fad'a har da kokawa Sayyada tayiwa Amina lilis ta zaneta tace"Idan kinje kice yazo ya rama miki shi wanda kike tarewa fad'an."


Amina na kuka ta nufi 'kofar su....Ita kuwa Sayyada sai ta kama hanya ta fice daga cikin kofar gabad'aya gidajan amare ta fara bi tana musu wanke wanke da shara yayi al'kawarin ba zata dawo gidan ba sai dare sai ta tabbatar ya bar garin sannan zata dawo.


Baba Ladidi ta nufi kofar su Kawu Tanko saboda tayi ya'kinin yana can aikuwa samunsa tayi zaune kusa da Baba iyatu da Marka suna hira ga 'kwaryar fura a gabansa yana sha.


Tana shiga ta sauke mayafin dake saman kanta ta rataye kan igiya.....Tace."Kai ja'iri gurinka nazo yanzu zan tona maka asiri ehe! wato dama abunda kaje ka karanto kenan iskanci."!


Sadam! Ya aje ludayin dake hannunsa ya had'e fuskarsa sosai yasan hargitsi irin na Baba Ladidi shiyasa yaci mur yana kallonta.


Ita kuma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login