*(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎°•° *WASA FARIN GIRKI* °•°💎 {cigaban gidan gandu} 💎1~2💎 💎*sameemah point of view*💎 Inajin duk abinda baba umaru yake fada akan wai na maida komai ba komai ba, kuma nayi tawakkali,saidai da yasan abinda nakeji a cikin raina a lokaci da bayyi gangancin yin wannan furucinba,dan ji nake kaman na sha'keshi yah daina motsi dan haushi. Duk da gargadin danayi masa amma bai jiba sai ma cigaba da yayi da cewar, "Nasan Har yanzu kina jin haushi da kuma shiga yanayin damuwa saidai ina so nasanar dake cewa,hakan yah kasance a zanen kaddararki yahke,sannan ni nacika alkawarine na matata hajara dana dauka,wanda tah bani kafin tah koma ga gidan gaskiya" Saurin juyowa nayi na kalleshi jin yace wai wasiyyar ummah tah ce da ta bashi kafin ta rasu,kenan dama abinda ta fadawa baba umaru kenan ranar da ta ce mu fita tana shirin mutuwa,wannan tambayar ni kadai nayiwa kaina amma kuma banida amsarta. Tashi nayi domin fita a dakinnasa dan a halin yanzu bana bukatar abinda zai hadani da wani ma tukunna,dan na gano duk tsawon shekarun danayi a rayuwata a cikin duhu kai da jahilcin rashin sanin mai yake faruwa nayi ta dukka. Dakinmu na nufah koba komai naji dadin rashin ganin mutane a gidan domim kowa yah watse bayan kwana uku da biki. Wanka nafarayi badan nasoba dai dan yanda naji jikina yana hamami,rabona da wanka tun kwana uku da suka wuce. Kayan inna rabi nagani a gefen nawa kayan da alamun anan take zaune kenan tunda aka daura auren,kallon dakin nakeyi wani kululun bakin ciki yana cina a zuciyah,nayi niyyar gyarashi na zauna ni kadai ashe nima so suke su fitar dani a cikin gidan. Duk da cewa yanzu ba wannan ne a gabana ba,burina shine na san mai yake faruwa tsakanina da sameer dan yamzu nasan shidin ba jinina bane tunda aka daura min aure dashi. Kuma na dau alwashin nima bazanyi musu yanda suke so ba matukar basu fadamin mai yake faruwa ba. Dukkan gidaje guda ukun na amare babu wanda yayi wani doki da zuwan amaryar tasa,saboda duk abinda yake mararin zai samu daga wajen ta daren farko dama ya riga da ya karba a waje tun da dadewa,daya kuwa ma bazawara ce dan haka baya bukatar yin wani rawar kafah. Zainab ce tah kalli yunusa wanda yah ke kokarin saka kayan aikinsa na yansanda zai fita. "Yanzu dan tsabar rashin mutunci irinna maza,daga kawoni koh satin amarci banyiba kace min zaka fita wani aiki,kuma itama waccar uwartaka hadda cewa yau nice dayin tuwon gidannan?,,t Duk maganar da takeyi ta rike wani dan karamin kunkuminta mai kama da muciyah tana jijjiga shi,amma yunusa bai kukataba kaman tana magana da dutsi,sai ma cigaba da gyaran takalminsa da yayi. "Yanzu yunusa inaa magaan amma kaaman ka bawa banza ajiyata,toh wallahi tun wuri kaje ka fadamusu ba zaman yi musu tuwo nazo yiba,toh in ma tuwonne haka kawai daga zuwana koh sati banyiba har za'a dameni da nazo nayi aiki,saikace an kawomusu jaka koh?,toh wallahi bazan yiba nikam" "Ashe kuwa kema bazaki ciba,kuma ninan da kika ganni aradun Allah yau bazan sayo miki gurasaba,dan tah jiyama saida nayi bashi na sayo,kuma tunda na rakaki kwanan uku ai yah isheki koh,dan haka koh ki dafa su baki naki,ko kuma kice bazaki dafaba ki zauan haka kalass,danni kam bazanje nace musu ke ba jaka bace,amma tunda kina ganin sudin jakunai ne basu da iyaye koh kuma suma basuyi amarcin ba sai kije ki fada musu" Yana gama kawo nan a zancen sa yah dauki hukarsa yayi gaba kaman ba shine mai daukin auren ba kwana uku da suka wuce. Ajiyar zuciyah zainab tasake mai cike da takaicin abinda angonnata ya fadamata,dafe hannunta tayi akan goshinta dayan kuma ta rike kunkumi,abin duniyah duk yah fara isarta tun ba aje ko ina ba. Ganin ba sarki sai allah ne yasata fitowa daga dakinnata ta nufi sashen surukar tata domin gaisheta. Sun daga nesa take jiyo masifarta da babbar surukarta wanda duk cikin su tafi yi mata rashin mutunci saboda halinta na sanyi da rashin magana, "Dallah can ta shi Kuban waje,dan mijinnaki yakawo kudi sai akace kuma a baki kiyi yanda kika dama dasu,wato dan baku kuke nemowa ba kuma zaune saidai kici kusha sai kuma kashi a masai,toh bazan bada jaka biyun ba,wazobiyah (hamsin)ga tanan ki sayo masa ja da yalo(tetracycline),yasha,ba duk ku kuke jawo gudawar ba,ko ina mutum yah wice banda kukdaje da wari babu komai,duk kun cika gida da kazanta" Daga kai tayi tana kallon zainab wanda ta iso wajen ta zuba mata idanu sai masifah rakeyi babu full stop bare kuma comma, "Ke kuma miye kikayimin shekeke akai kaman wata wanda tasaka wandon karfe iyee" Saurin tsugunnawa zainab tayi tana jinjina masifa irin ta,inna laraba. "Inna Ina kwana" Saida ta yahtsina fuska kaman bazata amsaba kafin tace, "Lafiyah,nikuwa kawuna(yunusa),yah fadamiki zancen yau zaki dora tuwon dareko,dan in bai fadamikiba toh bari ba nanata miki,yau kece da ciga magirka,dan kowacce yarknyah idan aka aurotah toh kwana uku takeyi saikuma tashiga layin dafa abinci,dafatan kin fahimta" Saurin daga kai zainab tayi kirjinta yana bada lugufen duka,bata tsammaci abin haka yakeba sai gashi duk masifarta da raininta ta kasa yiwa inna laraba musu,sai ma wata karkarwa da jijinta yah debi yi.........hmm muje zuwa. Kwass kwass kwass kakejin karar takalimi mai tsini yana sakkowa daga kan beni. Hajiyah mairoce ta sha wasu arnan kaya ga kuma sarkar gold a wuyanta,tun daga bakin kofa salma ta kafeta da ido ganin irin shigar da matar tayi da kuma itah kanta tsadar suturar. Wannan shine kallonta na farko da hajiyah mairon,dan tunda yan gidansu suka kawota suka tafi koh wata halittar bata sake gani tah shiga sashenta ba sai mai kai mata abinci kawai,bare kuka uwa iba mijinnata rabinta dashi tun hirar dasukayi lokacin ana gobe daurin aure,sai kuma aikan da akayi mata akan maigidan yana kiranta sashen uwar gidan. Saida tah gama jijjuyawar ta kafin tah dawo kujerar da take facing salma tah zauna,wani kallo ta ke zifanta dashi na zaki sani yarinyah,tun kafin wani a cikinsu yah yi magana sallamar su sameerah da umaruje ya jiyarci dodon kunnesu. Ba laifi kam sameerah tayi shar da itah na kyallin amare,sai murmushi takeyi,a kasan kujera suka zauna,sameerah har wani sunne kai takeyi itah ga mai suruka. Dauke kanta daga kallon salma tayi ta miyar kan sanyi zuviyar tata da kuma matar da suka shigo tare, "Ina kwana mom" "Lafiyah son yakk" "Normal mom,yah abokiyar zamanki?" "Hmm gata gaka ai,saika tambayeni itah,ko duk aurenne yasaka ka haka" "Ahah kawai na tambaya ne" Itama sameerah ganin sun gama gaisawa ne yasakata cewa, "Ina kwana mom(uhmm a dole anji wani yah fada,duk da halin bakin cikin da salma take ciki saida taji kaman tah tuntsire da dariya)" "Lafiyah" Daga haka hajiyah mairo bata sake kallon inda sameerah take ba bare kuma salma wanda dama tunda suka zo wajen bata kulata ba,sai cigaba da magana da sukayi da danta. "Lah my son nikuwa yah tafiyah Dubai dinanan ne,yakamata kaje karisa karatunka sananan idan ka dawo maganata tana nan" "Mommy amma da sameerah zamu tafi koh,tumda wata shida zanyi acan bandawo ba" Wani sihirtaccen dadine ya jiyarci zuciyar sameerah jin inda zasuje ita da mijinnata,har ta fara hasasowa irin rayuwar dazasuyi acan din,bazama ta yarda su dawoba idan suka tafi can,maganar hajiyah mairoce tah katseta daga hasken tunanin da takeyi zuwa na duhun bakin ciki. "Bada it ah zaku tafiba kai kadai zakaje,so kake ka takura kanka ka kasa more jin dadinka,da budurwace ma ko kuma irin matanann na nuna wa sa'a sai ku tafi,amma banda wanda bata san komai ba kam tayi ta baka kunyah. Sannan maganar mu na auren ku da Suhaila yana nan sannan itama ta dawo Nigeria lokacin dazaka dawo,nariga na yanke hukunci nan da sati daya zaka tafi" Emotions guda uku ne yake yawo a cikin falon,umaruje kunyah ce ta kamashi,dan baiso mamar tasa tayu maganar auren da zayyi a wajen ba,itah kuwa sameerah tunda uwarta ta haifeta,da kuma duk irin tujarar da suke yiwa kansu a gida,bata taba jin disgawar da akayimata mai ciwo kaman wannan. Yayinda salma a bangarenta kuwa dadi yah kaman yah kasheta jin yanda kishiyar tata take cakawa sameerah magana mai zafi. Kowa dawowa yayi cikin hankalin lokacin ma har ummaruje yayi musu sallama yah tafi wajen abokanansa. Suma tashi sukayi zasu tafi hajiyah mairo tah tsaida su tareda cewa, "Bangama dakuba ai,inaso na sanar daku cewa na sallami dukkan yan aikin gidannan,daga yau kune zaku dunga yin komai na gidannan,na abincin mu da kuma na wanda ake fita dashi sadaka,ke zaki iyah tafiyah saboda ina da iko dake,ke kuma ki jira wanda yah kawoki yah tabbatar miki kiji da kunnenki,duk kuma wacce taga bazata iyaba toh yau basai gobeba zata koma gidan tsofi" Har salma tayi niyyar juyawa tayi mata musu sai taga tamkar zakine a gabanta yake bata umarni,hakan yasa jikinta yayi sanyi tah koma ta zauna,duk da bata ce komaiba. Itakuwa sameerah rarrashin zuciyar ta tayi ta bar sashen,zuciyarta sai bugawa takeyi tsoronta dayah kar asirin da take dan takama da shi ya karye ta,shiga uku gashi yamzu da gaske ta fara son umaruje aranta tun daren farkonsu yah kama zuciyarta. Basu fi minti uku a zaune ba bayan tafiyar sameerah alhaji bala ya fito daga dakinsa yana gyara hannun rigarsa,wajen hajiyah mairo yaje yah zauna yana wani yake hakorah. "Afuwan uwar gida sarautar mata,na barki a zaune kina ta jirana koh" Saida hajiyah mairo tayi wani rausaya da kuma kallon salma ta gefen ido wacce tah zama tamkar kungi ganin koh inda take alhaji bala yayi bare kuma yayi mata magana,"anya kuma shine koh kuma wani ne daban"tah fada aranta. "Babu komai honey kawai dai kasaka ni zamane har nakusan awa guda,nayi zaton koh kaki wankanne irin jiyah,ina shirin tashi naje na tayaka kuma sai gashi ka fitoma" Dad'i kasheni haka alhaji bala yaji kaman an saka shi a cikin lambun soyayya. "Ahah ahah karki damu gimbiyah mai tafiyah da ragamar rayuwata ,ina na isah nasakaki aiki bayan jiyah na saka ki,menene yake faruwa?" "Sakonna na umarnin daka kafa gidanna nake so kasanar da matarka dan taji da kyau,karma ta daukeshi da wasa" Kallonta alhaji yayi rai a bace kaman yaga kashi mai wari, "Toh ma saina sake fada mata,ai duk abinda kika zartar dadai ne kawai yin biyayyane aikinta idan tanason zaman gidan" Baki salma tasake tana kallonsu,musamman ma yanda alhaji yake wani cuccusuwa a jikin hajiya mairon,kaman wani mai shirin shan nono koh kuma mai kokarin komawa cikinta,koh kunyah basaji sai ka ce wasu yara. Cikin dashashshiyar muryah irin ta wanda yashaki bakin cikinnan salma tace, "Toh idan kun gama bani aikin dazanyi zan iyah tafiyah" "Eh kina iyah tafiyah,kaima alhaji yah kamata ka tafi aiki haka,nima fita zanyi yamzu" "Angama Ranki yadade" Dukkansu kowa barin falon yayi farinciki kal zuciyar hajiya mairo,burinta yana cika.Kiran hajiyah laila tayi tana fada mata aiki yayi kyau sosai,dan yanzu kaff mutanen gidan itace take da iko dasu. Inna rabice tah shigo dakin tah samu sameemah tah daga kayan aikinta tana shirin sakawa,aikuwa abinda bata sone yah faru dan kwaredede tah hada mata ganin abinda take shirin aikatawa. "Tabdijan lallai ma kam,ina kike kokarin zuwa haka da aurenki da komai,kina da hankali kuwa ? Toh idam baki tambayi baba karamiba(sameer) ba inda zakije a gidannan,dan shike da iko dake a yanzu ha............." "Wallahi karki sake kicigaba da cewa shike da iko dani,babi wanda ya isa yayi iko dani,nice nan nake iko da kaina,kuma zuwa aiki ba bashi ya dad'e bai bani izinin ba ina ga kuma wanda zai hanani fitah daga gidannan idan yah isa" Duk maganar nan da takeyi saida tah jiyo tah kalli inna eabi tukunna ta fada,dan ma tasan da gaske takeyi ba karyah ba. Saurin fita daga dakin inna rabi tayi da sauri dan gani takeyi kaman sameemah dukanta zatayi. Cigaba tayi da shiryawarta hankali kwance har ta gama tsaff kafin tah fito daga dakin,karo suka ci da baba umaru da kuma sameer wanda shima fuskarsa babu alamun walwala a cikinta,saidai hakan bai dameta ba dan shidinma haushinsa takeji kaman tah sha'keshi. "Yah isa haka wannan boye boyen, inna rabi tah fadamin cewa wai kin ce saikin fita,toh babu wannan zancen,indai akam abinda yah farune shekarun baya inshaallah yanzu zan sanar daku basai gobe ba,saidai daga lokacin zaki bi mijinki ku tafi wannan shine burin ummanki idan har kin dauketa da daraja kaman yanda kika fada. *fitowar farko kenan daga littafin WASA FARIN GIRKI(cigaban gidan gandu)* Sannan littafin zai dunga zuwa da,MADUBIN GANI (point of view),wato duk wanda aka sakawa shine zai dunga bada labarin mai yake faruwa,da abinda yake ransa da kuma abinda yake gani. Nashiryah fah tsaff domin kayatar daku fiyaeda littafin farko. Domin saida nayi nutso kana nayi linkaya kafin na fito muku da zakinsa coii. Amma ba'a bawa wanda bashida jaka guda a wajensa(200),dan haka saikuyi harama domin mallakar naku a hannu. Domin samun shigaban labarin dakuma yanda zata cigaba da kayawa toh ku biyoni tahanyar biyan kudinku nairah 200 kacal,ta wannan hanyar. Masu turowa ta asusun banki: 3131951977 Masu biya ta katin wayah kuma: 09035784150 Muna jiran isowarku domin cigaba dulmiyawa cikin cakwakiyar da take shirin kunnowa kai,ina yimuku tabbacin baku biyha kudinku a banza ba. Domin komai kuke bukata mun tanadar muku a littafinnan. Tun daga kan rashin mutumci, artabu, cakwakiyah, sarkakiyah, soyayya tausayi, harma da saka ku kuka,duk na shiryah. 💎Sadi-Sakhna💎_______✍🏼 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎3~4💎 Kowa samun waje yayi yah Zauna a tsakar dakin harda sameemah wanda koh kayan aikinnata bata cireba,da alamun har yanzu bata hakura da zuwa aikinba. Numfasawa baba umaru yayi kaman bayason fadin abinda yake sirrinne,saidai dolene yah budeshi yunda bukatar hakan tah taso. 💎*Baba umaru,a Madubin Gani*💎 Shekara talatin da biyar suka wuce,lokacin ina matashin saurayi mai neman na kansa,duk da yayuna da kuma babana suna iyah kokarin su akan komai naci da sha, har ma da aure idan mutum yaso niyyar yi. Saidai ni ban yadda da hakanba don nafison nakasance ina neman abin kaina bawai na dogara da abin wani ba. Hakan yasa na yanke shawara inda na fara bin babbaan yayanmu mai suna ABDULLAHI,ana ce masa malam Audu,wato shine kawunku kawu audu wanda yah rasu tun kuna kanana,sanadiyyar ciwon koda. Shikuma sana'arsa shine saida kayan fulani a garin bauchi a kasuwar wunti. Bayan wani dawowarsane nace nima zan bishi mutafi koh taimaka masa saina dunga yi,baiyi musu ba kuwa saima dadi da abin yabashi. Lokacin da muka tafi saida nayi shekara d'aya kafin na zo gida,inda anan ne na hadu da innarku hajara tana kawowa fura daga kauyensu zuwa garin mu,da farko nasha wahalar shawo kanta saboda macece itah mai kunyah dakuma sanin yah kamata. Lokacin da muka daidaita kanmune muka sanar da manyam suka shiga zancen,da yake aurene ba irin na yanzu ba sai an ja lokaci,wata d'aya mukayi sai gashi mun tare a dakin Da'aka yimana da kuma dan zagaye. Zaman aminci da ganin darajar kowa mukayi har tsawon shakera biyu kafin hajara tah samu ciki, DA take ni ba anan nake ba ina wajen Audu bansan me ake cikiba,ashe hajara wahala yake ji a wajen mahaifiyar mu kasancewar bata sonta,tafi son na auri y'ar kawarta aminyarta wato Ramatu,saidai duk abinda yake faruwa hajara tah toshe duk wata kofah da zansan abinda yake faruwa,har saida tazo haihuwa ne lokacin nazo akace bazata iyah haihuwa lafiyah ba saboda karancin jini da kuma rashin samun ishashshen abinci mai gina jiki. Abinne yaban mamaki ganin babu abinda aka fi karfinsa ,tun daga sannan na fara zargin ba lafiyah na musamma yanda naga tah rame tayi baki,mata fara da itah amma tah koma haka. Allah cikin ikonsa dayah dubemu sai hajara ta haifi d'anta na miji wata ranar juma'a bayan doguwar nakuda da kuma jin jiki da tayi,har masu karbar haihuwar suka ce bazata sake haihuwa ba ma saboda yanayin laushi da mahaifarta tayi. Ranar suna aka sakawa d'a suna SAMEER,bayan an yanka masa rago. Kasancewar ina nan nazo gidan saboda haihuwar matata,sai hajara taji dadi har tayi wankan arba'in dinta cikin walwala da kwanciyar hankali,duk da bata fadaminba amma nasan taji dadin jama danayi a tareda itah batareda na tafiba. Tun da IYAH taji cewar hajara bazata haihuba sai zakaminta nasan na auro inna ramatu yah tashi,aikuwa tun kafin haajara tayi arba'in tashiga ta fitah saida tah kawo ramatu gidannan,duk da bana son auren amma nayi na'am da cewar hakan yana cikin kaddarata. A zama na da ramatu babu inda na banbanta ta da matata hajara saidai sha'nin mata dakuma in sun samu daurin gindi daga wajen uwar miji,sai hakan yakara hura wutar tsiyar ramatu a cikin gidan. Tun kafin hajara tayi arba'in ramatu da samu ciki,wanda itah bansamu damar ganin haihuwar ramatuba sai saƙon haihuwarta daya sameni kawai. Ban tashi dawowa gidaba saida sameer yayi wata shida yayinda shikuma dan inna ramatu (manjo )yake da wata huɗu. Aikimmu kam alhamdulillahi yana karbuwa sosai,dan yanzu shagonmu yah cika da kaya,har na samu hayar daki ɗaya wanda zan iyah tafiyah da matata daya muzauna. Nan ma wani artabun aka buga ina na yanke shawarar yin wata shida da kowacce sai kuma tah koma wata tazo. Bayan shekara goma muna kasuwanci sai ciwo yah kama mallam Audu inda ya barmin kasuwamcin nakeyi,saidai nima banyi wata biyu ba akayi godabara kaya suka ce ɗibemu a hankali. Hakan yasa nayi niyyar komawa gida saboda komai yah kare,wannan zuwan da ramatu mukaje sai masifah takeyi wai an koma yin abinci marar daɗi,nida jinta kawai nakeyi dan banida amsar dazan bata a lokacin. Da muka isa gidanma wani tashin hankalinne yasameni, domin a kwance na samu hajara a ɗakinta rai a hannun allah,wai laulayin ciki takeyi tun wata uku da tafiyarmu,gashi bayason abinci barkatai sai wanda tah zaba tukunna. Nan nafara jinyarta gashi kuɗin hannuna bashida yawa sosai,ana cikin hakanne wata hajiyah ta turo saƙo akam idan inaso naje zata bani aiki na gadi a gidansu,kuma ta yaba da hankalina saboda ina yawan sayar mata da kaya,mun saba a wajen cinikayyah. Abinda nayi tunani shine aikin gadi sai an zauna a gidan,sannan indai za'a zauna toh fah wata rana za'a bata,idan kuwa na kuskura na tafi da ramatu toh a ranar za'a koromu,sannan kuma bazan iyah tafiyah na bar hajara a wannan halin ba,kuma halin da take ciki tana bujatar taimako sosai. Hakan yasa na yanke shawara babu wanda yahsani na cewa ramatu aikin dako zan tafi yi a wani ƙauye,kuma bazan iyah tafiyah da hajara ba bata da lafiyah,tsalle tayi ta dire akan bazata je wajen wahala ba saidai na tafi da hajara kk kuka nasan yanda zanyi,lokacin kuwa ta yaye ƴarta sameerah. Baƙaramin daɗi najiba dana samu nakashe wannan wutar. A ranar na fara yimana shirye shiryen kayan ita dai hajara kallona kawai takeyi,dan nasan idan zanyi shekara ina abu indai ba faɗamata nayiba bazata tambayeni ba. Ranar tafiyarne na kaiwa iyah kayan sameer saboda yana zuwa makaranta shi,kuma ma yayi girma a tafi dashi gashi bamusan wajen ba muma tukunna. Mun daɗe muna tafiyah a mota sai gamu a garin bauchin yakubu,hajara kam duk tah galabaita saboda jijjigar mota ,gashi dama koba mota amai takeyi inaga ta samu dalili. Mai adaidaitah sahu muka ɗauka zuwa anguwar rail way inda tayi mana kwatancen gidan. Shima kansa mai adaidaitan baisha wahala ba saboda gidan ba a lungu yake ba,kan hanyane inda kowa zai gane. Kuɗin na bashi kafin na ranƙwafo da hajara zuwa jikina muka fitah zuwa bakin gidan. Duba takardar ta take hannuna nakeyi sannan kuma ina sake duba gidan,"anya kuwa shine?" nafaɗa a raina,dan gaskiyah giraman gidan bayyi kama da wanda za'a gayyaci kamanni cikinsaba. Ganin ba sarki sai allah ga kuma matata tana bukatar taimako ne yasa kawai nayi shahada da tunkari kofar gidan,saboda mun riga mun zo kuma ai babu batu komawa. Wasu inyamuraine masu kayan sojoji suka buɗe mana kofar gidan,saboda tsabar tsoro bansan lokacin dana mika masa takardar hannu na ba,saboda dama tace idan nazo nabawa ɗayah daga cikinsu,zasu barni na shiga. Hakan kuwa akayi ina mika masa yabani hanya wuce ina mamakin toh wane irin aiki kuma zanyi,danni a iyah tunanin gadi nakawo da tace zata ban aiki a cikin gida kuka zan iyah zuwa da iyalina,toh kodai ba nan bane,dan nan kam suna da mai gadi,wanda koh kare bazai nuna masa gadin ba ,dan ga ganinsa a fuska ma zaka tantance. Nidai ban sare ba muka cigaba da tafiya a hankali saboda yanayin tafiyar hajara da bata sauri saboda rashin karfin jiki. A bakin wata kofah muka tsaya saidai itah karamace amma dai tafi kofar shiga ɗaki girma,da wata yarinyah muka,haɗu tah yimana iso zuwa ga matar gidan. Shiga mukayi tareda itah bayan tah dawo tacemana mu shiga. Tabbbb danƙari wani kayan sai amale aradu,ai ina arba da inda aka shigo damu na saddaƙar da cewa ba'a Nigeria nake ba kawai,dan wajen badai ado ba kam. A ƙasan wajen muka samu waje muka zauna inda mai aikin tacemana mu tsaya. Bata daɗe ba kuwa sai gata ta shigo bakaman sauran masu kuɗiba da zasu iyah barka a zaune har awa guda. Sallama tayi mana tareda nuna mana kujera akan mu zauna,nidai duk hankalina bai kwanta da zaman kujerar ba saboda kar mu bata musu,amma kasancewar ƙasan da sanyi ga kuma yananyin jikin hajara sai muka koma kan kujerar. Har ta gyara zama zata fara magana sai kuma tayi saurin kiran wata a cikin gidan,saida ta bayyana naga ashe wacce ta rakomu ce, "Yawwa blessing kawo musu abin sha da abinci mana,kinga har na fara cikasu da surutu kafin na bansu wani abu(juyar da kanta zuwa ga inda muke sannan tah cigaba da cewa). Afuwan malam umaru,naga mai ɗakinnka ma kaman batajin daɗi sainaga kaman ma ƙaruwa zamu samu,yamzudai bari na saka akaiku ɗakin dazaku zauna kuci abinci ku huta daga baya sai muyi magana koh?" "Toh shikennan babu matsala duk yanda kika ce ranki yah daɗe" "Kacemin madam kawai,itah kuwa tah kirani da sunana Maryam,allah bamu ikon zama na fahimatar juna" Daga haka ta tashi tayi hanyar wan beni,itah kuwa hajara tun gaisawa da sukayi bata ce komai ba sai murmushi da take kawai,duk wanda yaganta yasan akwai alamun gajiyah a tareda itah. Ɗakine mai matsakaicin girma amma yah ƙawatu kam matuƙa,gashi an shareshi tasss sai ƙamshi yake fitarwa mai daɗi da kuma sheƙi. Wacce hajiyah maryam ɗin takira da blessing ce tasake dawowa ɗauke da kayam abinci,godiyah nayi mata na ɗawainiyha damu kafin tah fita a ɗakin. Kallon hajara nayi wadda samu bakin gado tah zauna tana ɗan riƙe ciki. "Ciwo cikin yakeyi ne" Batayi magana ba sai jijjiga kai da tayi,nima bansake tambayarta ba nayi hanyar banɗaki domin ganin menene babu,saidai da mamakina naga komai yana inda yake gashi na zamani,dan ma allah ya taimakeni nasan yanda ake amfani da banɗakin zamani da hakan sai yaban wuyah. Ruwan mai ɗan zafi na haɗa mata a bahon wanka,wajen cin abine dai saida aka kai ruwa rana tukunna. Muna cikin hakanne kuwa blessing ta sake dawowa,ɗauke da magani inji hajiyah maryam na masu ciki,dayake itama cikinne da itha kuma bai girma sosai,dan zayyi wata ɗayah dana hajaran. Ina bata maganin kuwa tah fara baccin farin ciki wanda rabonta dashi har tah manta ma. Kwanan mu uku a gidan kafin hajiyah maryam ta nemi ganina a falon baƙi. Gaisheta nayi tah amsa batareda dogon jawabi ba tah shaidamin cewar aikina shine bayin fulawa safe da yamma da kuma kula dasu akai akai. Mamaki abin yabani jin ɗan karamin aikin da zanyi kuma aka bani muhalli da kuma albashi ga uwa uba abinci mai rai da lafiyah,dan kwanan mu uku har mun murmure daga ni har hajara,wanda yanzu tah koma kaman ba itab saboda. Magananin da ta ke sha da kuma samun abinci mai gina jiki. "Nasan zakayi mamakin ganin karamin aikin dana baka,amma bakomai bane dama nayi niyyar taimaka maka,kuma bai kamata mutane masu amana da rike mutuncin alƙawari su ƙare ba,kayimin abinda bazan mantaba nima,inshaallahu dama ina da niyyar buɗe shago toh zan baka ka riƙemin nan gaba,amma a halin yanzu wannna shine kaɗai hanyar dazan tsimaka maka" Farin cikine haɗi da jin daɗi suka kamani har na rasama da wanne irin baki zan gode mata irin kyautar da tyimin haka. Itama ganin na diriricene yasakata saurin barin falon tana murmushi,da alamun bata son godiyar tawa kenan. Nikuwa hakan bai wuceba dan dana koma ma na faɗawa hajara tun kafin na rufe baki tace zatayi mata godiyah tsakanin itah da itah. Tun daga fita godiyah ba itah hajara ta,dawoba sai wajen karfe tara ba dare,abinne ya ɗauremin kai inda na tamabayeta mai yah faru,nan take cemin wai hira suke tayi irinna mata ,musammaan ma akan ciki da kuladashi,da kuma tsabtar jiki da tah muhalli. Sannan tace mata idan cikin yakai wata biyar zasu dunga zuwa awo tare. Tun daga lokacin daga na fita sai hajara ta tafi sashen hajiyah maryam tanan tayata ɗan ayyuka ita kuma tana koyamata abubuwa,musamman da yake karatun nursing tayi saidai bata aiki a kan hakan. Nima bana hanata zuwa tunda ina ganin sanji a abubuwa da dama a game da zamanta da hajiyah maryam ɗin,kuma bata zama cikin kaɗaici sai ma wani haske da ta ƙara saboda kyakykyawar kulawa da take samu a wajen hajiyah maryam ɗin,matar da ba abinda zan iyah saka mata dashi sai alkhairi. Wani muhimmin shirye shiye aka fara a gidan na tarbar dawowar mai gidan wanda yake aiki a kasar India,mukan mu ganin hajiya mairo tana murnar tarar masoyinta yasa muma muka fara tayata murnat duk da bamusan shiba bare jin labarinsa,hajara kamma a can ta yini suna ta aiki. Can wajen la'asar misalin karfe uku ji karar shigowar motoci,tab nan fah abin yazama abun kallo,dan kuwa inaga duk girma da faɗi irinna farfajiyar gidan saida suka cika da motoci kaff,babu koh masakar tsinke. Mudai muna tsaye daga bakin ɗakinmu wanda yake ɗan gefe da inda motocin suke fakawa ,mun zubawa sarautar allah ido. Can bayan sun gama shigowane kuma sai dukkan sauran motocin suka baɗe suka fito. Samarine da mata farare kall ba irin na kasar nan ba,duk da akwai masu surkin bakin fata a cikinsu,sanye suke kkwannensu da kaya baƙiƙƙirin kaman zunubi. Dukkan layi sukayi a jikin jar motar da take tsakiyah wanda itah ce kaɗai mai banbancin kala a cikinsu,dan duk sauran baƙaƙene. Na gaban motarne yah fito kafin yazo yah buɗe bayan motar. A ɗan jima kafin mamallakin motar yah jefo ƙafarsa waje,kafin yah fito da dukkan sauran jikinnasa. Kyakykyawane na fitar hankali,dan koni dana ke na miji naga kyawunsa bare kuma mace,. Kayane a jikinsa farar shadda ƙal,da kuma baƙar hula da takalmi shima baƙi siɗik, taku yake cikin kwanciyar hankali har yazo yah wuce falon hajiya mairon,yayinda sukuma sauran naga duk sun koma motarsu sun bar gidan,sai jar motarce kawai take nan da kuma wanda yah tuƙota. Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎5~6💎 Tun lokacin daya dawo aka ɗauko wasu masu aikin daban ana biyansu ,saboda abincin da'ke dorawa gidan yah fi na mutum ɗari ƙartin samari,duk kuma na sadaka ne,da farko hajara taso tashiga cikin masu girkin ta tayasu amma hajiyah maryam ta hanata,a son ranta tah huta ba'ason mace mai ciki tanayin aikin wahala mai tsanani. Har aka shafe kwana uku da zuwan alhaji ABDULWAHAB kullum gidannan a cike yake da mutane masu neman taimako,kuma duk wanda yah shigo toh baya fita hannu rabbaan saida kayan abinci koh na sutura,gwargwadon abinda yazo nema dai. Masu karbar abinci kuwa har dare ake kaiwa ana karbar abinci a kofar gida,dan masu rabawa da ban masu dafawa daban haka masu sakawa a cikin robobi. Muma kanmu kayan da hajiyah maryam ta bani har kuka nayi saboda ganin yawansa. Tunda muka kalli alhaji abdulwahab lokacin da yah zo gidan zuwan farko bamu sake sakashi a idonmu ba saboda yawan zirga zirga dayake tayi na,meeting halarta wurare da sauransu. A kwana na huɗu kuwa yah koma inda yah fito wato ƙasar India da sassafe ma yata fi koh tashi bamuyi daga bacciba. Shima saida rana nakejin zancen a wajen hajara ta dawo daga wajen hajiyah maryam,wai ƙiran gaggawane yah sameshi daga can akwai abinda zayyi. Kwanci tashi har muka shafe wata guda ciff a garin bauchi gidan alhaji abdul wahab,shahararren mai kuɗi da duniyah take damawa dashi. Zuwa sannan hajara tah daina wani laulayi saboda cikinta yayi wata biyar,duk bayan sati biyu yanzu suke zuwa awu ita da hajiyah maryam,inda direba yake kaisu yah ɗakkosu. Kowa yah kalli hajara sayya yayi mamakin canjawarta tayi luwai da itah. Nikuwa a cikin wata biyunnan zuwana gida uku,kuma kowanne sainayi sati guda nake dawowa,hankalin ramatu bai zo kaina ba saboda tah samu sana'a tanayi ,gashi kuɗi yana shiga mata,idan nace tazo mutafima nasan bazata biniba tunda bata san wainar da ake toyawa a canɗin ba. Da haka rayuwa ta cigaba da garamana har watan haihuwar hajara yakama. Naƙuda tah fara gadandan inda hajiyah maryam ta zauna a wajenta tana taimakata,amma ganin abin yana son yah fi ƙarfin saninta gashi itama da tsohon ciki,sai ta ɗakko mota domin mu tafi asibiti,musamman dana faɗamata yanda tayi a cikin fari,da kuma matsalar da mahaifarta take dashi. Can asibitinma saida muka kwana tukunnan a washagarine tah samu damar haihuwa. Munyi farin cikin samun kanta duk da tah galabaita amma saidai yarinyar tana jin jiki ga kuma tare ta fito duk da mahaifar gabaɗaya,wannan labarin yaui mana babu daɗi amma babu yadda zamuyi sai rungumar ƙaddara. Kasancewar yarinyar bata da lafiyah saida muka zauna a asibitin na tsawon kwana biyu tana karbar magani,ga tsada amma hajiyha maryam tace koh godiya kar muyi mata,itace da godiyah ma zaman da muke da itah,saboda bata da kowa a garin bauchi aurene kawai yakawotah. Ranar suna iyah yan uwan hajara ne guda dayah tazo,wanda itah ma shekararta biyune da aure dama tana da niyyar zuwa,wato inna rabi. Yarinya taci sunan hajiyah MARYAM,ana kiranta da sunan tah,kar kuga murna a wajen hajiyah maryam kaman ta cinye yarinyar dan murna,dan ma bata da lafiyah ko yaushe tana ɗaki,ba a fiye futowa da itah ba,saboda cutar sanyi da take ɗauke da shi. Bayan sati biyu da haihuwar hajara itama hajiyah maryam tah haihu,inda tasamu ƴa mace,saidai ita a gida ta haihu,kawai ma'ikaciyar lafiyar aka turomata domin tah taimaka mata. Cikin koshin kafiyah kuwa suka samu kansu daga itah har y'arta ba'a samu wata matalaba,itah ce ma aka ɗan yi mata ɗinki saboda ɗan ƙaruwa da tayi. Tun kafin suna mutane suka fara cika da mutane,mutanen arziƙi da kuma ƴan uwa wanda dama haihuwarta suke jira. Lallai munga mutane kam kuma manyan mutane ba mutane haka ba. Duk da haihuwa tah farko da alhaji abdul wahab yasamu amma bai zo ƙasar nigeria ba,hakan yabawa mutane da dama mamaki kan cewa wane irin aikine ya riƙeshi haka,dan tun farkon samun cikinma bai wani murna ba,saidai tambayar lafiyar uwar kawai yakeyi,ga shi shekararsu huɗu da aure sai yanzu allah yabasu arziƙin samun haihuwa. Da sati yah zagayone yarinyah taci suna SAMEEMAH,suna kawai taci,kasancewar hajiyah maryam tanason sunan. Biki akayi a lokacin sunan kaman na yin auren wata mace,saboda dumbin mutane da taro yah tara, banda abin duniyah a da akayi ta rabawa. Tun daga sannan hajiyah maryam ta cigaba da rainon ƴar ta ciki kwanciyar hankali. Maryam kuwa tun bayan haihuwarta kowane sati sai ankaita asibiti domin gwajij numfashinta,amma koda da sau ɗayah hajiyah maryam bata taba gajiyawa ba akan hakan,mukan ma har mun fara cire rai da rayuwarta,musamman ma mahaifiyarta wanda cikin dare idan na farka saina ganta tana zaune tah zuba mata ido,soyayyar ɗa da mahaifi duk sainaji nima wani iri. Dahaka muna cikin yanayinnan har maryam tayi wata huɗu,amma kaman ƴar wata biyu haka take. Wata ranane jikinnata yayi tsanani muka tafi asibiti kwananmu biyar acan tace ga garinku nan. Ko mukanmu iyayenta bamu yi damuwar da hajiyah mairo tayiba,dan saida nazo ina basu baki itah da hajara. Dawowa gida mukayi gida saboda ayi mata sallah da kuma kaita gidanta na gaskiyah,inda kowa zaman jiran nasa yake yi. Bayan sadakar uku har mun fara manatawa da itah,dan dama itah ba lafiyayya bace. Zuwa yanzu sameemah tayi wayo dan kullum nan muke yini da itah,saboda hajiyah mairo tah koma aikinta na asibiti,duk da alhaji Abdul wahab baya so amma haka ta lallameshi ta,koma aikinta a cewarta taimakon mutanene zai kaita ba neman kuɗiba. Shaƙuwa sosai tah shiga tsakaninmu da sameemah,dan wani lokacin da ƙyar mamarta take ɗaukarta idan tah dawo daga aiki,dayake akwai abincinta na yara shi ake bata. Itah ma hajara daga bayah aiki hajiyah maryam ta,sama mata a asibitin suke na shara da gogen daƙin masu jinyah,sai yazamana tare suke tafiya a motarta,idan hajiyah maryam ta shiga aiki sai hajara tah riƙeta,kusan ko yaushema tana wajen hajaran idan dai ba dutynta bane. Haka har muka samu shekara biyu kyawawa a gidan,yamzu ansaba kowa yasan da wa yake zaune,dagani har hajara munyi sabo da mutanen wajen sosai da sosai. Sameemah kyakykyawar yarinyahce dan kallo ɗaya mutum zai tabbatar da hakan,saidai bata da son mutane irin na uwarta,dan idan ka ɗauke mu da mahaifiyarta toh babu wanda take sakewa dashi,da farko hakan kaman abin ƙiwa ne yarinta sai kuma hakan yajuye kaman halinta ne,amma duk da haka yarinyah ce mai shiga rai da kuma farin jini a wajen mutane. Kwatsam da tsakar rana saiga alhaji abudul wahab yadawo saidai wannan zuwam babu manyan motoci kaman na farko,ita kanta hajiyah maryam tayi mamakin rashin zuwannasa da kuma zuwan bazatan dayayyi,dan daga kallon irin kallon da take jifansa dashi mutum yasan tana jin haushin rashin zuwannasa. Sameemah da take hannunta yah miƙo hanu zai karba,aikuwa dama badai kiwuyah ba,da sauri tah maida hannun gefe tareda juya kai. "Kagani koh,ko ƴar ka ma tana ƙin zuwa wajenka tunda bata sanka ba" Dariyah kawai yayi tareda karbar yarinyar duk da bata so yayi hanyar kofar tasu. Itah binsa tayi a baya,ni ma kuma muka bar wajen har sannan muna mamakin irin zuwan bazatan da babban mutum kaman alhaji abdul wahab yayi. Lokacin da kwana uku yah cika munyi zaton zai koma,sai muka ga har anyi sati guda bai tafiba,hakan yasa mukayi tunanin koh hutu yah samu a wajen aiki yasa yazo domin yayi su da iyalansa,kuma ya kyauta hakan,dan itah kanta hajiyah maryam taji daɗin hakan. Sannan sameemah har ta fara sabawa dashi dan koyaushe yana tare da itah,kuma duk sanda yah fita sai yah siyo mata abin wasa da kayan ciye ciye,wani abin ma bata iyah amfani da shi,kawai siyah yake irinna iyaye masu ɗokin irin na ƴaƴan fari. Mukuma a namu bangaren muna tah shirye shiyen tafiyah zuwa gida,saboda iyayen hajara suna so taje ganin dangi,nima kuma inason zuwa ganin yah yanayin gidan yake tafiyah. Mun yanke shawarar nan da sati ɗaya zamu tafi,kuma zamu kai wata guda bamu dawoba. A ranar da daddare kowa yayi bacci kasancewar daren yayi sosai,ba abinda mutum yakeji sai shirun duniyah kawai,kowa yan kwance yana hutawa. Ban daɗe da zagawa bayi ba naji bugun ƙofar ɗakinmu,saida na kalli hajara wanda take kwance kafin na isa bakin kofar ina wasiwasin na buɗe ko kuma na barta,ina cikin hakane naji muryar hajiyah maryam da alamun tashin hankali a cikin muryarta tana cewa, "Malam umaru kabuɗe ni ce,kayi sauri banida lokaci sosai" Cikin sauri har jikina yana rawa na zare sakatar dakin da sauri. Haɗa ido mukayi da itah jikinta sai rawa yakeyi lokaci zuwa lokaci tana waigawa baya kozata ga wani yana biyota. Sameemah ce a hannunta wacce take ta bacci abinta,saurin mikomin itah tayi da sauri,zuwa lokacin hajara tah tashi,sai na miƙa mata yarinyar,tun kafim na tambayeta ta fara magana cikim sauri muryar tana rawa, "Na roƙeku dan darajar allah,ku fitah daga gidannan a yanzu basai gari yah waye ba ku bar gariannan ma idan san samu ne,bazan iya yimuku bayanim abinda yake faruwa ba,saidai inaso ku riƙemin ƴata da amana a wajen ku,duk da nasan zakuyi hakan tunda nafi kkwa sanin halinku na mutunci,sannan ku kumin alkawari zaku riƙeta a matsayin ƴar da kuka haifa a cikinku,kar wani yasan gaskiyar iyayenta,na baku itah halak malak burina kawai tasamu gata da kuma rayuwa mai kyau koda bana cikin rayuwarta,kartayi maraicina ko kuma rashina", Tana gama faɗan hakan tah ciro wani ƙullin kuɗi a jikin rigarta ta miƙamin kafin ta cigaba da cewa, "Ga wannan kuɗin,na aikina ne danayi na tsawon shekara kuda,wannan zai isheku hawa motah,wannan katin kuma na asusun bankine mabuɗin cirewar sunan sameemah ne,nabaku zaku iyha amfani dashi wajen inganta rayuwarta,amma idan kunga bazaku iyah amfani dashi ba saboda nasan halinku toh,ku ajiyemata idan ta girma ku bata a matsayin kyautata tace a gareta kuma ina rokonta,da tayi muku biyayya tamkar mahaifanta" "Kuyi sauri ku fito yanzu nan kafin lokaci yah kure mana,kuma dan allah karku bari sameemah tah tako garin bauchi lo da wass" Tana gama faɗan hakan tah fara haɗamana kayanmu da sauri,akwati ɗayah muka ɗauka ta rako mu bakin get ɗin gidan,hajara tana rungume da sameema a jikinta,duk da bamusan menene ba amma munsan abinda zai raba ɗiya da mahaifiyarta na kaɗan bane ba. Hajara ce tayi karfin halin cewa ,"amma hajiyah maryam bazaki iyah guduwa keda itah ba ko kuma boye ta?" "Dazan iyah hakan danayi tuntuni,ku tafi kawai wannan shine iyah abinda zan iyah,zanyi mata alkhairi daga inda nake ma" Tana gama faɗamana hakan tah juya cikin gidan da sauri,hawaye yana zuba a idonta amma sai ƙoƙarin hanasu zuba takeyi,saidai ko daga ganinta tah ɗan aamu nutsuwa data raba ƴarta da koma menene yake tunkarowa. A daren muka fara tafiyah har da gudu gudu,domin muma babu abinda yake cikin ranmu sai ƙoƙarin ƙubutar da rayuwar baiwar allah da take bacci a bayan hajara,batasan ma me akeyi a duniyarba. Kafin gari yah waye har mun kai wani kauye dayake kusa da bauchin a hanyar gidanmu,tsaywa mukayi domin hajara ta huta saboda gajiya ga kuma goyon yarinyah ƴar shekara biyu. Anan muka tsaya muka sayi ƙosai muka ci,kafin muka tsaya jiran motar garinmu a wajen. Cikin sa'a kuwa saiga mota bata cikaba muka shiga sai gida. Da tsakar rana sai gsnimmu akayi babu tsammani,sai tambaya suke mai yasa muka taho yau bayan sai wani satin,cawa muka kamawa takeyi kawai,sauran mutan gida sai tambayar hajara suke akan suga ƴartata,ba musu kuwa ta sakko da sameemmah wanda take tah bacci abinta,jin hayaniyane yasata farkawa,aikuwa tana ganin inna Hauwa matar mumkaila wanda amaryace a lokacin zata ɗauketa tayi saurin maƙalrewa a jikin hajara,tana kukan rikici. Kowa mamaki yakeyi da kyau irin na sameemah har ma kyau na kayan jikinta,marasa haƙuri kam ma har saida suka yi magana irin su inna ramatu. Nidai daga ni har hajara babu wanda yace wani abu,sai sunane muka ce musu an samu sabani ne sunan ta sameema ba maryam ba kaman yamda aka faɗamusu,dan haka bamu sha wahala ba wajen boye ainihin tarihin sameemah a wajensu. Tun daga lokacin sameemah ta ware tamkar ƴar gida,dan dama ta saba damu sosai musamman ma hajara. Shekarar sameemah huɗu hajara tah dara ciwon ƙafa,wasa wasa ana tah magani amma ciwo sai gaba yake yi,sannan nikuma kulawar danake bawa sameema sai yah fara zuwa idon mutanen gida,hakan yasa dana ga za'a samu matsala na fara ja baya da lamarinta ba kaman da farko ba. Haka na shigaba da kulada itah,har zuwa wasu shekaru inda tace itama ga garinmu. Wannan shine iyah abinda nasani a game da abinda yake faruwa, Ina mahaifin sameemah bansaniba kawai nasan yana aiki a india sannan kuma mahaifiyarta bansan koh tana rayeba,dan maganar da take yi mana kaman wasiyyah haka take yinta. In kuma tana raye bansaniba,dan nasan danginta amma ban san a wane gari suke ba,abinda nasani shine itah ba ƴar garin bauchi bace kawai. Amma tabbas tah kargaɗeni akan kar na sake na barki kije garin bauchi. 💎~~~💎 Yana kawo nan a labarin sa saida kowa ya zubar da kwallah na tausayin hajiyah maryam da kuma tunowa da mutuwar inna hajara musamman ma inna rabi an taso mata da tsohon mikin mutuwar ƴar uwarta mai sonta,banda sameemah wanda fuskarta babu alamar rauni a cikinta,saima kallon gefe da tayi kawai. Tashi baba umaru yayi ya ɗauko wani ɗan akwati ƙarami ja. Buɗeshi yayi da wasu lambobi yah ciro wani kati a ciki,na shaidar sumun asusu a banki. Miƙawa sameemah yayi tareda cewa, "Wannan shine abinda mahaifiyar ki ta bamu akan cewa mu baki idan kin girma ko kuma muyi amfani dashi,saidai bamu taba ba dan aduniya babu abinda bazamu yiwa jinin hajiyah maryam ba,dan tayi mana abinda bazamu taba mantawa dashiba. Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎7~8💎 💎*Sameemah a madubin Gani*💎 Duk abinda yake faɗa ina sauraronsa,har yah ɗauko wani akwati yah miƙomin wani kati wai inji mahaifiyata,dan kuwa wai ne,dan jin zancennasa nake kaman a mafarki,kar ba nayi ina kallon katin batareda nace komai ba,sukuwa sai kallona suke dan ganin mai zance,inna rabi kuwa idonta yayi luhu luhu na munafurci,saika ce addu'a take wa ƴar uwar tata idan ka tsareta,kowa sai munafurci na iyah shege. Tsallakewa nayi na fita a ɗakin na barsu sai ta'ajjabinsa sukeyi wanda bashida dalili,babu yanda za ayi na tsaya wannan abu tunda na samu abinda nake buƙata shikenan kawai. Kayan aikin na cire badan na soba,duk da ina da taurin kai amma idan na ɗau alkawari nakan iyah ƙoƙarina dan naga na cikashi. Ninke kayana nayi na adana dan ban cire ran cigaba da,aikina ba koda nan gabane kuwa. Inna rabice tah shigo ɗakin har sannan idon ta bai washeba da kukan munafurcin,dan haka sukayi a mutuwar ummah ɗin,duk wanda yagansu sai yayi zaton idan dare yayi kwana zasuyi suna yi mata addu'a,amma kowa ana yin sallar isha ta sau baki tayi bacci. "Yamzu kam tunda kinji mai akace sai kizo kuka ki tsefe wanan kan kuma da kuma lalle saboda yin kwallliyar amare kaman kowacce amarya idan za'a kaita ɗakinta." Kallonta nake ina mamakin katsalandan irin na wannan matar,itah ko gajiyah batayi da shiga rayuwar mutum,narasa ma mai zan mata ta rabu dani,dan nakula koh zuciya batayi koh wacce irin magana mutum yafaɗa mata. Ko magana banyi mata ba na jawo system ɗin na fara wani aikin,dan shiru ma amsa ce idan tana da hankalin hakan. Aikuwa haka tah fita,nayi zaton tah haƙura ashe nacinta yah wuce hakan ashe,dan kuwa dawowa sukayi da baba umaru, "Meyasa kika kasance mai taurin kai ne sameemah,kince idan aka faɗamiki mai yake faruwa zaki amince kibi mijinki gashi yanzu kuma an faɗamiki amma har yanzu abu bai sanja zani ba" Toh tanan suka bullo kuma,mai yasa akeson takurani ne haka,kullum hankakin kowa yana kaina dole sainayi abinda yake so,wai baza'a barni na yi abinda nakeso bane?,ɗago kai nayi na kalli baba umaru tareda cewa "Toh shikenan naji zanje wajen kitson amma daga nan bazan karbi koh komaiba,sannan bayan shi babu abinda zan sake yi,koda kuwa me zakuyi kuwa" Dan nasan idan ba haka nayi musu ba zancen bazai wucewa,jijjiga kai kawai baba umaru yayi kafin yabat ɗakin yah barni daga ni sai inna rabi,wanda duk tabi ta takurawa rayuwata. Haka babu yanda zanyi na ɗaga wayah nakira burgu sabon ango,shima saida yayimin tsiyah tukunna abinda banaso kafinnan na faɗa masa saƙona kan ya turomin mai kitso da fulawa,amma kar ta daɗe,dan idan yakai yamma na fasa. Saida yah sheƙe da dariyah kafin yace, "Amaryah amarya ranki yahdaɗe amaryah,da girman kujerarki amaryah a wajen ogah sameer gashi..........." Ban gama jin abinda yake faɗaba ba kashe wayar dan ba abinda nakeson ji ba kenan. 💎* Sameer a mdubin gani*💎 Lokacin da baba umaru ya,gama bada labarin abin yayi matuƙar ɗauremin kai sosai,dan tsawon wannan shekarun kallon sameemah nake a matsayin ƴar uwata ashe ba haka bane,dan yanzu gashi lamarin yayi zuwa yanda bana tsammani na samu kaina da zama mijin aure a wajentah,tabbas ina cikin cakwakiyah na wanne irin zama zamuyi da itah a can tukunna,danni shaidane bata tankwasuwa gata da ɗan banzan rashin mutunci na bugawa a jarida. Duk labarin da aka bayar kamata yayi tafi kowa shiga cikin damuwa amma koh a jikinta saboda gasheshshiyar zuciyah ce da itah,sam baka sanin mai yake cikin ranta,nine zan zama shugaba aknata ko itah ce shugabar,saidai kowa yayi rayuwarsa dan allah yagani bazan takurawa kaina ba. Ganin wani karbar katin da tayi a hannun baba umarune tareda ficewa a ɗakin yasa kowa yah bita da kallo,nima ganin hakane yasa na tashi domin shirina dan yau zan koma gida,dan na samu abinda zan saita kafin zuwanta nan da kwana uku. Ɗakin da kayana yake na nufah,duk lakar da take jikina ta shika,banda faɗuwar gaba ba abinda kirjina yake yi,danni kaɗai nasan irin matsalar dazana fuskanta. A katifar ɗakin na zauna,nafi awa guda kafin na fito da jakata a hannuna na nufi ɗakin ƴanmatan gidan inda sameemah take,yau ne karon farko da shigata ɗakin tun bayan raauwar ummah a ciki. Tsayawa nayi ina kallon cikin ɗakin bayan nayi sallama. Saidai ko sallamar bata amsaba bare tah ɗaga kai ta kallleni,uhmmm nafaɗa a raina. "Ina sallama keba musulma bace bazaki amsaba,koh nima tsiyar taki zakimin dan kin rainani" Nan ma bata kalleshiba sai amsa sallamar da tayi kawai,katin cire kuɗi na fitar a aljihuna na miƙa mata tareda cewa, "Gashi wannan ki sayi duk abinda kike buƙata,saidai karki sayi sutura koh kuma abin amfani dukka akwai acan,idam ma da wani abun ki kiranj ki faɗamin" "Bana bukatar kuɗinka saboda ina dashi basai ka baniba,kuma duk abinda nakeso zanyi ba wanda wani yakasaniba tunda babu wanda na dogara sashi bare yayi min yadda yaga dama" "Dama badan kina dashi na bakiba,na bakine saboda kina da hakki a kaina na hakan,sannan karkiga dan zakizo gidana kinemi yimin tashin hankali ina gargaɗinki da ki shiga hankalinki" Sabanin abinda na tsammata tayi,dan iyah murmushi tayi na gefen baki wanda sai mutum yah kula kafin yagane shi. Nima juyawa nayi na fitah daga gidan zuwa cikin motata,baba umaru dama munyi sallama dashi ɗazu,bazan iyah sake tsyawa ba kuma,dan anyimin abinda kwata kwata naji babu abinda nakeso sama da bawa garin baya kk zanji sanyi a raina. Tun a hanya kiran saleema yake ta shigowa,ina gani naƙi ɗauka dan tun ranar ɗaurin auren take ta ƙirana tun ina amsawa har na daina. Kafin na isa gida saida tayimin ƙira ya kusa goma ina katsewa,dan idan na ɗauka bansan mai zan ce mata ba,dan haka kawai na barta idan na ja koma menene zanji daga gareta. Banfi shafe wasu awanni masu yawa ba na isah garin porthacourt sakamakon gudun danakeyi yah wuce na hankali,burina na isa kawai domim nasan mai zanyi. Ina shiga sojojin da suke bakin kofar suka buɗemin na wuce,tun daga bakin falon na tabbatar cewa na daeo gida,hakanma farfajiyar hajiyah saleema,dan komai da gindinsa yake zaune a falon,duk da babu datti amma fah babu tsari ko kaɗan irinna na ɗakin ƴa mace. Fitowa tayi daga ɗaki muna haɗa ido da itah,babu sannu da dawowa bare yah hanya sai ƙorafi dayah min sallama,na kashe mata wayah danayi. Dan takaici ba tsaya yi mata wani bayani ba nayi hanyar ɗakina,ina jinta tana biye dani har sannan bata daina ƙananan maganganu ba,jin abin zai min yawa goma da ashirin yasani dakatar da itah,tareda cewa, "Dan allah saleema ki barni na huta tukunna koma menene sai tambayeni ,amma yanzu bakya ganin daga hanya na dawo,babu sannu da dawowa bare ruwan sanyi sai aukin ƙorafi,wai yaushe zaki sanja ne?" Jumbura daki tayi irinna sakalai kafin tace cikin muryar shagwaba, "Haba honnnney,yanzu hakama zaka ce dan gaka ina damuwa da kai,fisabilillahi tun yaushe ka bar garinnan,sannan tun kwana uku da suka wuce yakamata ace ka dawo,amma baka dawoba sai ma kashemin waya dakayi bayan na ƙiraka,wai meyasa kake min hakane " "Ni babu abinda nayi miki saleemah,kawai akwai abinda yasa na tsaya ne,kuma idan kikayi haƙuri inna zauna zan sanar dake,domin kema yah shafeki" Daga haka na juyah na wuce ɗakina ina riƙe goshina,wanda nakejij kaman zai iyah darewa a kowanne lokaci. Wanka na shiga naji ɗan dama dama,ina fitowa na samu saleema a bakim gado tana jirana,ban yi mata magana ba sai da na shiryah kafin nazo na zauna,anan na kula ashe abinci ta taho dashi,ta wannan bangarenne kawai take burgeni,dan idan na faɗamata abu tanayi,sannan kuma bata fiye yimim musuba,barta dai a shagwaba kam har da ta siyarwa. Jawo kwanon abincin tayi tah juba,duk raina bayaso saboda na ƴan aikine,ita kuma babu dama tah dafa abinci da kanta,wannan sam ya zama abinda tah maidashi haramun a gareta. Kaɗan naci kafin na ajiye cokalin ina kallonta,wanda tunda nafara cin abincin ta tsura min ido tana kallona, "Uhm ......dama saleema akwai abinda nakeson baɗamiki,kar lokaci yaƙure ban faɗamikiba kice ban kyautaba" "Uhm ina jinka honey mai yah faru ne?" "Da farko kinsan ni mijine ke mace sannan kuma an halattamin auren mata guda huɗu idan ina da dama koh?" "Tsaya tsaya haka,banason jin wanann bayanin gaskiyah,dan wallahi babu kishiyar dazaka yimin ana zaune kalau,nasan ma bazaka yi ba ai,dan haka a bar wannan zancen" "Amma yah kamata ki dunga tsayawa kina jin karshe magana,dan aure ba zancen za'ayi bane an riga anyi ne,dan yanzu haka ma amaryar jibi za tare kuma samee.............." "Karka cigaba da faɗin abinda kunnuwana bazasu iyah ciggaba da jiba sameer,me kake nufi,aure!!!,kuma ma har an daura,nan da wasu kwanaki matar zata zo ta zauna a gidana,kuma itama tah mallakeka kaman yanda nakeyi,inaaaaaa hakan bazai taba yiyuwa ba kama canja zance amma ba wannan ba ............kasan mai kake faɗa kuwa??" "Nasan mai nake faɗa mana salee............" Tun kafin nagama magana ta watsamim wani kallo wanda tunda nake bansan ta dashi ba ta bar ɗakin da sauri tana bugomim ƙofar ɗakim kaman zai karye. "Yah salam" Shine kawai abinda na faɗa,dannasan shikaɗai zai kawo min mafita akan abinda yake shirin tunkaroni. 💎*Sameemah a madubin gani*💎 Lokacin da mai lallen ta zo ma kaman bazan tashiba,da jinake wani baƙin ciki yana taruwa a cikin kirjin lokaci zuwa lokaci,samun waje tayi tah zauna ba kin katifar sameerah ta da,tana sunkuyar da kai kaman mai tsoron haɗa ido dani,ƙoƙarin katse shirun ɗakin nayi tah hanyar cewa, "Miye sunanki?" "Hamiddah" "Karki yimin mai yawa,shima dan babu yanda zanyine kawai shiyasa zanyi" Tasowa tayi tah fara haɗa kayan yin lallen,har tah gama. Wata shawara ce tah kawo kaina cikin ƙanƙanin lokaci,aikuwa nayi shu'umin murmushi. Bamu daɗe da farawa ba muka gama,dan cewa nayi tayimin zanen da tasan ba'ayi a lalle kaman zanen kwari da na su ƙadangare,kallona take da mamaki kafin tah fara abinda nacemata,dayake ta iyah zane kuwa,sosai hotunan ƙwarin suka fito kaman suyi magana harda kala ta saka musu,ɗaga hannun nayi ina kallon zanen yamda yah fito raɗau a hannuna,dan duk mai tsoro ƙadangare da kuma su dandoriyah to yana gani nhannu na zai fita da gudu,daɗi ne yah isheni koba komai zuciyahta tayi ɗan sanyi danayi tsiyah. Tana gama lallen koh nace zanen tayi shiru tareda ɗan matsawa gefe,sai kallon abinda yake hannuna da kuma ƙafata takeyi. "Ai baki gama ba,ina so kiyimin zanen maciji ya nannaɗe wuyana,ina zaki iyah?" "Eh zan iyah anty" "Yawwa toh yimin yayi biƙi sosaifah" "Toh anty" Ina gama faɗan hakan na cire rigata nabar iyah zani ɗaurin kirji,lallen da sake haɗawa kafin ta fara zanen Wanann sai da ya ɗaukemu lokaci domin so nake ya fito kaman na gaske,aikuwa nima kaina sai da naga kyau na macijin,rai na fari tass yayi ganim abinda nake shirin aikatawa yah fara tafiyah yanda nake so. Kuɗin aikinta na bata ta tafi,kitso kuma shagon gyara nake son zuwa saboda kawai abinda nake son aiwatarwa. 💎*Saleema a madubin gani*💎 Tun naji furucin daya fito daga bakin sameer mai kama da dafin maciji na tashi na tsaya,ji nake duniyar tana juyamin duk illahirin jikina rawa yakeyi ga kuma wani tashin hankali da baƙin ciki da suka taru a ƙirjina,numashina har sama sama yakeyi. Ɗakina na nufah ina haɗa hanya dan ko hanyar idanuwana basa gani sosai,babu abinda yake amsa kuwwa a cikin kai na kalmar da sameer yah faɗa ta,aure aure kishiyah kishiyah. Da ƙyar nasamu damar sakawa Zuhra riga(mai sunan mahifiyar saleemah,hajiyah Fatima)na sunkuceta sai bakin motata,shikuwa farouq bai dawo daga makaranta ba ta isilamiyya,idan yah dawo ubannasa yasan yanda zayyi dashi. Ikon allah ne kawai yah kaini gida,sa'a ta ɗayah babu nisa duk a cikin barikin sojojinne,saboda girmansane yasaka ni ɗaukar motar dan idan na ce zanje a ƙafa toh zam iyah yin kusan wata a ganina ban ƙarisaba. Ina kashe motar na fitah daga motar da gudu zuwa cikin gidanmu,har na kai bakin ƙofah na tuna nabar ƴata a cikin motah,da gudu na koma na ɗaukotah kafin na shiga cikin gidan. Akan kujerar falo na dire zuhra dan ita haushinta nakeji ubanta yah shafamata,mai aikin gidan nagani zata wuce madafar abinci. "Ke zo ki ɗauki yarinyar nan ki kula da itah sannan ki bata madara" Zuwa tayi tah ɗauketa ni kuma na yi ɗakim mommy da gudu har ina tuntube,babu abinda nake buri sai,wanda zan samu na faɗawa mai yake faruwa,sannan kuma da wanda zai rarrasheni. Ina shiga na faɗa kan mommy wacca take naɗe kayan ta ƙanana akan gado,kuka na rushe dashi wanda dama na daɗe ina riƙeshi,sai yamzu yah samu damar kwacewa yah fita.cikin shshshekar kuka nafaɗamata abinda yah faru. Tana gamajin labarin tah tureni daga jikinta tareda cewa, "Dallah ni matsa kiban waje,dan mijinki zai ƙara aurenne kike wannan kukan kaman wata sakaryah,ke kuwa kina hankali kuwa?,kai kai wallahi alhaji yajiƙa aiki daya shagwabaki,ya maida ke bakisan kinemi abu ki rasa ba,sanann ya maidake bakisan kiyi haɗaka da wani ba akan abin duniyah,saidai yanzu alhamdulillahi gwanda da yayi auren koba komai zaki koyi darasin haɗa abu da wata,kuma zaki san duniyah ba kullum abinda kake so kake samuba koh ake yi maka ba" Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎9~10💎 Matsawa nayi daga jikinta na bar ɗakin,da wanne zanji da kishiyar da akayimin koh kuma da faɗan da takemin,idan tana wani abun saikace ba itah ta haifeniba matar ubace,nidama nasan batasona kaman yanda abba yekiyimin,kullum cikin yin faɗa take da hantarata. Kuma wallahi ban haƙuraba daddy yana dawowa zan faɗamasa,bazan bar gidan bama anan zan zauna har sai ya saketa tukunna kaman yamda ya aureta. Ɗakina na gidan na nufah,ina kuma danna ƙiran wayar SUHAILAH,tsuka naja ganin tana ta ringing amma bata ɗaga ba sai daga baya kafin ta ƙirani. "Sully kina ina ne wai,ina ta kiranki baki ɗauka ba,akwai matsala fah" "Matsala kuma wace iri,banganeba mrs major,fayyacemin naji mai ake ciki" "Hmmm ke miyema bai faruba aikawai sai kinzo,dan zancen baxai yiyuba a waya" "Toh shikenan gani nan zuwa,dama yamzu na dawo daga makaranta,cin abincina kenan,bari nayi wanka nazo naji mai yake faruwa" Ajiye wayar nayi bayan nagama wayah da suhaila,nasan ana jimawa zan ganta,safa da marwa na fara a ɗakin tsakanin kujerar madubi da kuma bakin gado,duk abin duniyah yah isheni,lokaci ɗaya har na rame na fitah hayyacina,dama haka mata suke ji idan za'ayimusu kishiyah?,tabbb gaskiyah abin babu daɗi,dole ne muyitah,koh ni koh itah,duk da bansan ma wacece ba. Sai kusan magriba kafin suhaila tazo,ita kanta nasan a lokacin uzuri takemim saboda babu laifi tasha madifa tafi cikim kwando. Itama bata wani bani shawara gamshashshiyah bah,duk daga nayi kwalliyah,na dunga jan ajina,sai kuma kar na bari tah rainani,kallon suhaila nake lokacin da take faɗan hakan,lallai bata san me ake jiba idan akayi maka kishiyah,dan taga batada mijinne bare kuma zancen yimata kishiyah,toh yaushe ma zan zauna da itah har nafara wannan shirmen na jan aji da kuma kwalliyah. Ita kanta surayyah ganin nayi mata shiru yasa itama ta kama tura saƙonta a wayah,ni hakan ma yafimin da wanann zance nata. Daddy yana shigowa tun kafin yah zauna na fito daga ɗakim ina haɗe fuska,kallona yayi da alamar damuwa a fuskarsa ganin yanayin dana ke ciki. "Ƴar daddy mai yasameki haka?" Kallon mommy nake wanda take zabgamin harara kaman idonta zai fito,hakan bai dameni ba saima ɗauke kaina danayi ina kallon inda mai sona yake wato daddy, "Daddy inadai wai sameer ne yaƙara aure....." Ina gama faɗin hakan hawaye ya fara zuba a idona,daman yau kam ai idon cike yake da hawaye. Cikin razana da kaɗuwa daddy yafara magana ransa a bace, "Aure kuma,daga aura masa ke kawai sai yahsake aure,ni naga ga mahaifiyarki nan ban sake mata abokiyar zama ba,sai shi ne zai wani yi miki kishiyah da yarintarki kawai dan ya bata miki rai" Ina jin haka na sake rushewa da wani kukan ina ɗora kaina a kafaɗarsa. Dan tsabar takaici dayah shaƙi mommy buɗe baki kawai tayi tana zubawa sarautar allah ido,dan kam abin yah fara bata mamaki. "Kutt yanzu alhaji abinda zaka ce kenan,kana ganin tah baro gidanta ta dawo gida sai tijara takeyi da girmanta ,ba ƴar yayeba harda ƴaƴa biyu,da a ƙauyene ma tah kusa auren ƴarta shine kake wani rarrashinta harda ɗaure mata gindi dan kawai mijinta yah ƙara aure?,toh wallahi bazan yarda da hakanba,yau ɗinnan basai gobeba zata koma ɗakinta,idan kuwa tah kwana a gidannan akan wannan abin,toh kuwa zanyi fushi da itah" Binta mukayi da kallo nida abban,wanda shima bai ji daɗin mommyn tace ba,saidai babu yanda zayyi tunda ta faɗi hakan toh bazata sanjaba tana nan akan bakanta. Dadare na fara da kafafuna ina kiran daddyn,ganin hakanne yasashi ɗaga wayah ya ƙira sameer akan yazo yana son ganinsa,nikuma yah lallabani na tafi ɗaki kafin sameer ɗin yah ƙariso. 💎*Sameer a madubin gani*💎 Tun lokacin da saleemah tah bugamin ƙofar ta fitah ina jinta har tashin ƙarar motarta,wanda dama nasan sai hakan tah faru,abu ƙaramima take kaiwa ƙararsa bare kuma al'amari irin wannan. Baccine ya ɗaukeni na wahala a wajen,dan kaina ji nake kaman zai sare gida biyu. Sai can wajen magribane naji ƙarar buɗewar ƙofar dakinnawa,farouq ne ya shigo da kayan islamiyyah a jikinsa,kaina yah ɗale da sauri yana dariyah,nima wani sanyi naji yah jiyarci zuciyata,dan rabona da ɗannawa nayi ɗan kwana biyu,muna nan zaune sai kuma na tashi nayi masa wanka kafin najashi muka shiga madafar abinci. Taliyar yara na yimasa,dan dama kowane yaro yana sonta,da farinciki kuwa yah karba ya nufi falo da gudu. Nima bin bayansa nayi ina murmushi,sai surutu yakemin maganar bata fitah,wani nagane na bashi amsa wani kuma saidai kawai na kalleshi,*yara manyan gobe* Waya tace tayi ƙara ina dubawa naga abban saleemah ne,nasan *za'a rina wai an saci zanin mahaukaciyah* Ɗauka nayi tareda yin sallama cikin girmamawa,cewa yayi na sameshi idan anyi isha a falon sa,amsawa nayi da toh kafin na kashe wayar. Wajen anty talatu (nanny ɗin farouq)nakaishi bayan yagama cin abincin nikuma na wuce masallaci. Lokacin dana dawo anyi isha,farouq na dauka a motah muka nufi gidan su saleemah. A falo nasameshi a zaune,saleemah tana gefensa idonta yayi luhu luhu,na ɗan ji tausayinta a raina amma kuma ta wani bangaren dama inaso tayi hankali,tasan ba kullum ake kwana a gadoba. Zama nayi akan daddumar da take kasan falon tareda gaishe da alhajin. Dadai lokacinne itama hajiyah Fatima ta shigo fuskarta ɗauke da murmushi,daga gani alhaji Musa bai so shigowar ta ɗakinba saidai baice komaiba. "Yawwa sameer ina jinka,yarinyah tah daho tana kuka wai tacemim ka ƙara aure,ɗazu ka faɗamata sannan kuma amaryar jibi zata taro,wani abu saleemah tayi maka ne" "Babu abinda tayimin,sannan abinda tah faɗa gaskiyahne,nayi aure kwana uku da suka wuce,jibi za'a kawota m" Ina gama faɗan hakan na basu labarin nima jinayi kawai an ɗaura auren bayan an gama ɗaura na ƙannena wanda naje nasu ɗaurin auren. Jinjina kai alhaji musa yayi kafin yace, "Yanzu yah ake ciki kenan,gida ɗayah zaka haɗasu?" "Eh hakan nake da niyyar yi,dan a tsarina banason yin gida biyu gaskiyah" "Ammma.........." Hajiyah fatima ce tayi saurin katse alhaji musa daga maganar dayake son yi tace, "Shikenan sameer munji duk abinda kace,munayi maka fatan alkhairi allah ya tayaka riƙo ya kuma baka ikon yin adalci a tsakaninsu,yanzu kaje ka jira ta,nasaka ta ɗakko zuhrah da kuma jakarta yanzu zata fito ku koma". Har a raina naji daɗin yanda hajiyah fatima ta taƙaita maganar,dan har raina nake yaba irin halin dattako da sanin yakamata irin na hajiyah fatima,matar ta kwanta min a rai,ganinta nake tamkar mahaifiyata. A hanyar mu tah dawowa gida kuwa babu wanda yayi wa wani magana tsakanin nida saleemah,dan ko kalllona batayiba,idonta yana kan titi,farouq kuwa yana kulata zata zabga masa harara shima dayaga hakak sai ya cigaba da wasansa a gefe ,ni dariyah ma tabani. 💎*Sameemah a madubin gani*💎 Mutane sai taruwa akeyi ƴan ina da biki,zuwa yanzu kowa yasan alaƙata da sameer,cewa ni ba ƴar inna hajara bace riƙeni tayi,saidai babu wanda yafaɗawa kowa su waye iyayena,kowa idan yagam kwakkwafin yaga bai gano komai na sai ya haƙura. Ina jinsu suna tah hidimarsu da mutane a cikin gida saidai koh inda nake babu wanda yake zuwa barekuma ayimin tsokana irin tah amare. Kaman yanda na faɗa nabada ɗinki kuwa haka akayimin,wannan duk hidimar surayyah ce,dan itah kadaice take shigowa ɗakin tah gama yimin tsiyah ta fice,tun da safe burgu yah kawota akan idan aka yini tah kwana washagari a tafi kaiwani da itah,hmmm lallai aure manya,zasu san sun sakani cikin masu aure kuwa. Riga ce jah ta yadi mai tsada,saidai anyi mata ɗikin buɗaɗɗen wuyah,sai kuma tah matse kunkumi tah zuba a kasa ,lokacin dana faɗamata yanda za'ayi rigar bata so a yi irinta ba,amma yanda na bayar dole haka za'yi ina haka na kuma na fitah da kaina na kai ɗinkin. ~~keee mai taurin kai,koyaushe kina cikin karya mana doka koh,mun ce kinuna ƙin amincewar ki akan aurennana amma kikayi biris da zancen,idan san samune ki kawo mana jinin mijinnaki ana kaiki gidan,sauranki jinin guda uku ki hau kan karagar mulkinki,wanda dama lokaci yake jira,idan kuma kika ƙi aikatawa ............ Bazan aikata ba daman,karku bata lokacinku,koh kasheni zakuyi bazanyi abinda kuke so ba sai abinda nayi niyyah,tsarinku daban nawa na daban,sannan sau nawa nake faɗa muku banason kiran ruhina da kuke batareda ixinina ba zuwa duniyar mafarki,idan har kuka cigaba da aikata hakan,toh zan samo hanyar yin abinda bakwaso kodah kuwa yah zama koni koh ku ne.~~~~~ Tashi nayi daga kan gadon ina kallom rufin ɗakin wanda nagama kwanan na na ƙarshe a cikinsa,tareda tunanin mutanen mafarkinnawa,ruwa na ɗauko a gefena na fara sha saida na shanye shi tass,natsani ƙishirwar dasuke sakani ina ji,wayonsu shine su ɗaɗe dani a duniyar mafarkin har sai na buƙaci shan jini a wajensu idan inaso naji dadai,saidai sun makaro,domin na koyi fitowa daga wajennasu koda suna so koba su so,nasan hakan bai yi musu daɗiba saidan babu yanda zasuyi ne. Bankoma bacciba sai ƙoƙarin hada canjin wajen aiki da nakeyi,dan burina shine ina zuwa can na nemi aikina na cigaba dayi. Washagari tun da hantsi motoci guda uku suka tsaya a ƙofar gida,ina jin dirinsu na tuno da motar alhaji bala dana ɗauko,wanda jiyah nasa burgu ya mayar masa kayarsa,dan dama banida niyyar riƙeta din din,saboda bana ra'ayin mallake abinda ba nawaba,dama na taho da itah ne dan yaji haushi. Wanka na shiga nayi,kowa idan zan wu ce sai bina yake da kallo,kome suke kallo oho. Saida nagama shiryawa na saka rigar dana bayar akayimin,surayyah ce ta nace sai tayimim kwalliyah,hakanne yasa na barta tayimin amma kuma baƙi yafi yawa a kwalliyar,dan jam bakimma baƙiƙƙirin aka saka hakama gira da kwalli,bataso yamda na bata kwalliyar ba saidai yazatayi dani. Muna cikin yine saƙo yah taddani cewar baba umaru yana ƙirana, Abinda ya tsana kenan wannan wa'azinnasu na munafurci,banda munafurci sun san fah mutum ba sajawa zayyi a sakanniba imdai har girmansa bai canja ba,kawai a damu mutum da iyayi kawai. Lifayar kayan da ɗauka na yane jikina dashi kafin na fito zuwa dakim baba umarun,a zaune yake akam dadduma yana jan carbi,sallama nayi ciki ciki tah dole,shima murmushi kawai yasan dan dole nayi sallamr ba da san raiba. "Toh sameemah allah ya kawoki lokaci kema zaki ɗakinki kaman sauran ƴan uwanki,ina miki fatan alkhairi allah ya zaunar daku lafiyah ya baku zuri'a dayyaba,ina yimiki nasiha da ki bi mijinki sau da kafa,sannan yi nayi bari na bari,banda musu da kuma tairin kai,dan nasanki sosai,saidai naga kaman kwannan kinyi hankali kaman ba lokacin baya ba,dan haka a zauna lafiyah ........" Surutunsa yake tayi ina jinsa,da ni mai saurin dariya ce ma dana tuntsure da dariyah,saidai kasshh ba komai bane yake sakani dariyah,yasakani a gaba yama wani surutu kaman ya samu yar shekara biyu,hmmmm. Tun yana maganar a marmari har yafara gajiyah,rufewa yayi da addu'a,yana ƙara cewa na zauna lafiyah,inna rabice dake gefe take ɗan matse wata ƴar ƙwallah,tabbb lalllai mutanennan nifah suna bani mamaki,tashi nayi ganin innna rabi batada niyyar tashi nayi hanyar fita daga ɗakim ina yiwa baba umaru sallama,toh mezan tsaya nayi bayan yagama surutun. A hanyah inna rabi ta isoni da ɗan sauri,batacemim komai ba dan itah yamzu abin yah fara daina bata mamaki. Motar da aka kawo muka nufah,sauran motocin duk an cika su sai wanda zamu shiga nida inna rabi ce tah saurah. A gidan baya muka zauna ina tsaƙiyarta itah da wata mata,wai naji suna kanwar iyah mai kalwace. Maganganun da baba umaru yayi minne suke dawowa cikin kwanyah tah. Me baba yake nufi ma tukunna,ai shikenan nayi hankali saina zauna a gidan sameer lafiyah? Inaaaa hakan bazai taba yiyuwa ba,waisu nan a barikin sojoji,ai shiyasa aka haɗani dashi ana ganin babu abinda zan iyah,sai kuwa san ya kaini cikin gidansa,dan sai yah gagareshi samun kwanciyar hankali,ballanta kuma matarsa,dama naga rainine da itah,dan haka itah zan fara gyarawa zama tukunna,sai azo ta kan mazauannan gidan,duk wanda ya taboni koh bindiga ce shi ba sojaba saina saita shi. Natsani zama da wasu,a gida ma zaman dole nakey ,shine harda suka min aure koh,hmmm bazance yasakeni na amma zanyi masa abinda dakansa zai gaji da zama dani. Lallai basu san wacece sameemah ba,wasan yan zu za'a fara bugawa kawai. Ina cikin tunani na saƙar zuci bansan lokacin da muka shiga garin porthacourt ba sai gani nayi mun doshi babban barkin sojojin mai kama da gari guda a girma,ko kalle kalle banyiba saboda wanann ba shine karona na farko a ganin barinkin sojojiba,naga wanda suka fi wannan ma girma da komai, sabani sauram mutanen ƴan tafiyar musamman ma wanda dama basu taba zuwa birni kaman hakaba. Ba laifi yana da girma sosai dan saida muka ɗanyi tafiyah kafin muka zo bangaren gidajen manyan ma'aikatan. Buɗe murfin motah kowa yayi yah fito yana tah wawware ido dan bawa idonnasa abinci. Wani sojane ya taho yana wani taƙama da ƙasaitah,uniform ɗinsa na kalla kawai nasan wane muƙami ne dashi. Murmushi nayi tareda cewa,lallai akwai aiki anan wajen sosai. Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎11~12💎 Wuceshi nayi nice ma ta farkon shiga cikin gidan,saboda su sun tsayah ɗari ɗari da kuma bashi amsa,hannu yaɗaga mim akan meyasa na wuce,kallo ɗaya nayi masa dana juya kafin na wuce ciki. Da sauri inna rabi tah taho ta riƙe hannuna tareda yimin kallon tah gaji da halina,ko a jikina sai ma ɗauke kai danayi. Babban falone yayimana salllama yasha kayan alatu irinna ƙyalelen duniyah. Wasu manyan matane masu kama da hajiyoyi a zaune akan kujerun ɗaya bangaren,mukuma muka zauna a wanda suke kallonsu. Dayake kafin mu shigo inna rabi ta sakamim baƙin ƙyalle a fuskata dan haka bana ganin fuskarsu saidai maganar su kawai,tsinkayo maganar wata daga cikinsu nayi wanda take cike da gadara da kuma isa. "Toh da farko masu kawowa amarya barkanku da zuwa,saidai ina son sanar daku cewa nan gidan saleemah ne dan ita aka zo aka samu,karkuga cewa wai dan itah tana ƴar uwar miji ta nemi yi mata iko koh gadara,toh hakan bazai faruba,dan itah kanta dukiyar da sameer yake da itah da kuma ɗaukakar da kuka ganshi da itah har kuka laƙaba masa ƴar ku,duk mallakin mahaifin saleema ne,yanzu amarya zata buɗe mana kanta mugani kafin kuma mununa mata ɗakinta,kafin sannan kuma........." Jin maganar nayi tah isheni haka zuciyata da kunnuwana baza su iyah cigaba da jin irin wannan kalar rainin hankalin. Saurin yaye alkyabbar nayi ina kallonta ido cikin ido,ganin ɗan razanar da tayi ne tanan kallon lallen dayake hannuna na hotunan ƙwari da majicai na baƙin lalle anyi musu ado da jan lallene yasata zare idanu,su kansu wanda suka taho tareda dani basusan mai yake jikinba sai yanzu,surayyah ce kawai ta sani,ɗauke alkyabbar nayi daga jikina gabaɗaya nayi wurgi da itah a ƙasa,hoton macijin dayake wuyanane yah fito fili,zanen kansa yana kwance akan kinrjina wanda akayiwa ɗinkin mai buɗaɗɗen wuyah. Tun daga kan kwalliyar da take fuskata da kuma irin nau'ina lallen dayake jikina mutum zai ɗauka daga cikin duniyar ifiritai na bayyano. Kallon saleema nakeyi wanda tayi suman tsaye,da alamun bata san waye a cikin gyalenba sai yanzu ta tabbatar da wa zatayi zaman wani abu wai shi kishi. Mayar da kallona nayi kan wacce take feso magana sakkanni kaɗan da suka wuce,ganin kallon bazai isheta bane yasa na matsa har inda take ina ɗora ƙafa ta ɗayah mai tsinin takalmi a kan hannun kujerar da take kai,dan dama ni ban cire takalmina ba daza mu shigo. Fuskata nakai har wajen fuskarta,dan baifi tazarar yatsa ba na bari a tsalaninmu,ɗaga girar hagun nayi tareda kanne ido ɗaya sannan nace , "Ke....mekika ce maimaita naji,bazanyi taƙama da abin gidannan ba?,ke wacecs toh a gidan?da har kika samu ƙwarin gwiwar fadamin hakan,toh bari kiji na faɗamiki,tun daga kan itah matar tasa da kuma shi babu wanda ya isah yah takani,barekuma wani can banzar bazara baƙo a gidannan,itah kanta wacce kikeyiwa wannan aikin wato matar gidam ta fiki sanin wacece ni,ke bakisan komai ba a kaina,dan haka ina jan kunneneki da idan goda wasa watarana kikazo gidannan kikayi zancena ,sai na cire harshe fiyattttt ma kuwa,.............dan haka yanzu zaki iyah nunamin ɗakin dazan zauna ɗinne koh kuma har yanzu baki shiryah faɗan suanan ɗakin ba?" Tsayawa nayi na bata ɗan lokaci saboda ta samu damar jan numfashin da ta riƙe shi tun ɗazu,ga kuma gumi dayake keto mata,duk da sanyin Ac din ɗakin. Da hannu ta ɗaga tah nunamin ɗakim da takasa cewa komai da bakinta. Matsawa nayi daga kanta domin tasamu ta sha iska,murmushi nayi mata tareda miƙe hannuna nayi wata miƙa kaman hannuna zai balle gida biyu,juyawa nayi na kalli mutanen da muka zo dasu wanda suma sukayi tsitt suna bina da ido. "Kuje su nuna muku ɗakin dazaku zauna dan wancan nawane,kuma bacci zanyi na huta dannagaji,idan kuma wata tazo tah tasheni hmmmm" Jiyawa nayi nasake kallon matan da suke gefen saleema, "Sauran kuma na tashi naji kun cigaba da watsawa wanda muka zo tare magana,wallahi ko mai gidan bai isa kwatarku a hukuncina ba,zai fi mukuma na tashi na samu kun bar gudan" Saida na zare ido tareda haɗe fuska kafin na faɗi hakan,har na fara tafiyah na juyo na kalli surayyah wanda itama mamakinnawa takeyi,duk da tasan hakan kadanne daga halina. "Ke kuma zo mutafi dakinnawa akwai abinda zan faɗamiki" Da sauri tah tashi zata biyoni,inna rabi tagumi kawai tayi,ba ko gigin biyoni ba,dan yamzu itama tasan halina. Muna shiga ta maida ƙofar ɗakin tareda cewa, "Yanzu anty sameemah me kikayi haka kenan?ƴan uwan ogan mijinki ne fah,amma kika yi musu haka daga zuwamki" "Toh yan uwansa ƴan uwanane,kema ba surutu na ƙiraki kiyimin na,yanzu dai ciro mun kaya a cikin wajen kayannan tukunna,sannan idan kin ciro ki je ki dubamin matannan,duk abinda suakyi kizo ki fadamin,dan ba yarda dasu nayiba,ƴan tuƙa tuƙa kawai" Surayyan ta buɗe baki zata sake cewa wani abu nayi saurin shigewa banɗakin. Dan banson yawan surutun yanzu,ina jin dariyarta a ɗakin har kuma tayi shiru. Cika bahon wanka nayi na shiga na kwanta,gaskiyah nayi kewar ƙasar palastine dan rabona da danayi wanka na cikin baho tun ina can. Saida na kusa awa guda kafin na fito daga bandakim,shima ina fitowa na samu surayyah ta fitomin da kayan,dan haka ina sakawa nabi lafiyar gado. Bangaren masu aikin gidan aka kaisu dan shima wajene mai zaman kansa,sun mafi sakewa a canɗin akan dakina,dan wallahi babu da matar da zan kwana tunda bani na gayyatosu ba ai. 💎*sameer a madubin gani*💎 Tun dazu nake zaune ina aiki amma nagaza tabuka wani abin kirki,daga na fara tubutun da shigar bayanai sai na ajiye,ni kadai na jera tsuka tafi cikin kwando ina zaune. Na rasa ma abin da yake min daɗi,ni kaɗai nasan irin ƙalubalen dana ke shirin fuskanta na rayuwa da sameemah a cikin gida guda,kirjina sai bugawa yake yi lokaci bayan lokaci. Ga saleema tun lokacin dana daukota daga gidansu tah daina yimin magana,ko na kulata ma saidai ta bar wajen,abin duniyah duk yah isheni. Sallama akayi tareda bugo ƙofar office ɗinnawa,ina ɗaga kai mukayi arba da Ahmad babban abokina wanda tare muka yi karatu da kuma tafiyah service a Russia. Miƙomin hannu yayi muka tafa kafin yace,haba mutumina kana ango wanda za'a kawo masa amaryah yau amma kuma kake aiki,wai yama naganka da damuwa a fuskarka,kamata yayi yau ka yini cikin fatin ciki ai" Hmmmm kawai nace,dannasan idan nayi masa magana ma bazai fahimta na sam,dan haka babu ma wani zancen tsayawa bata lokaci akan maganar. Wasu abokan aikimmune suka sake shigowa,sai tsiyah suke min,dole babu yanda zanyi na ajiye aikin tareda ta fiya gida. Gidan su Ahmad muka wuce,dan shine zai auri suhaila ƙawar saleema watan jibi. A dakinnasa yada zango,akan zasu rakani zuwa dare,saboda nace bazan yi komaiba dan haka dole suka ƙyakeni tunda basu san dalilina ba na ƙin yin komai ɗin. Wajen ƙarfe goma na dare muka shigo cikin gannawa kowa a cikin motarsa,nidai binsu kawai nake duk abinda suka ce,dan karsu gane halin da ake ciki. Falon babu kowa kaman ba bu mutane a gidan,ɗakin saleemah muka fara nufa wanda yake bangaren dama yana kallon wanda sameema take ciki. Nufar ɗakin saleema muka farayi tukunna amma ƙofar ta ƙi buɗuwa tah kulleta,ɗan jimm nayi kaman mai tunani kafin na koma inda su ahmad suke,ɗan yaƙe nayi wanda yah fi kowa ciwo. "Ina ga tayi bacci kaman" Ɗaga kai sukayi alamar sun fahimta duk da basu yarda da abinda nace ba,ƙarbar ledar dayake hannun ahmad nayi ina yi musu murmushi. Fatan alkhairi sukayimin kafin kowa yah shiga motarsa yah nufi gidansa. Ajiyar zuciyah nasake ganin yanzu niƙadaine a cikin cakwakiyar nan babu kuma mai tayani yinta. Ɗakin sameema na tura na shiga,a zaune na sameta ta saka kayan bacci gefe kuma tana ƙurbar tea a kofi,duk wanda ya kalle ta sai yayi zaton dama gidantane kuma ta daɗe a ciki,dan batayi kama da maryar da aka kawo yau ba. Daga kai tayi ta saman system ɗin datake gabanta ta kalleni kafin na ɗauke kanta,daga nan bata sake cewa komaiba sai ma cigaba da aikinta da ta cigaba dayi. Nima banyi mata magana ba,sai ajiye ledar nayi a kan drawar gadon da nake kusa da itah,juyawa nayi na fita daga ɗakin,har na fita naji muryarta tana cewa, "Baka rufemin ɗakina ba,sannan kayi na farkone amma daga yanzu in wani abune ka fada nazo na ƙarba,banson a dunga shigomim ɗaki babu izini" Jijjiga kai kawai nayi na koma falo na zauna,yazanyi allah ya hadani da mata,mabanabanta,daga wacce sakalcinta yayi yawa sai wacce sakalcin matan ma bata iyaba kaiiiii. Ina nan zaune na kunna kallo amma hankalina kwata kwata baya kan kallon,yana kan yanda zamyi na magance abunda yake shirin faruwa a gidana. Alamun wulagawar mutum nagani yah shiga kicin,wanda ban ma kula sanda ya wuce ba,saida tah fitone na kula a she sameemah ce ta ɗauko plate daga kitchen ɗin. 💎*sameerah a madubin gani*💎 Har dare yayi amma na gagara bacci saboda halayyar umaruje tun ba a je ko ina ba ta fara canjamin,dan yanzu nakula akwai wacce yake so,suke wayah kullum,idan na tambayeshi ne kawai gani gashi Bayamin musu,amma idan abu a wayane cewa yake cewa bai sani ba ɗin,danaga hakanne na fara lallabashinsa dan a zauna lafiyah,saidai naga abin kaman gaba yakeyi ba baya ba, Yanzu ma zaman jiransa nakeyi tun safe bai shigo gidan ba har yanzu,gashi gobene tafiyar sa Dubai,abin takaicin waccen shegiyar uwartasa. Ina cikin safa da marwan na juyo kenan muka haɗa ido dashi sai layi yakeyi na maye,ga kuma zagi dayake da ɗurawa,takaicine yah kamani ga warin giyah,na rasa ma da wanne zanji,ni gsni nakeyi gwada ma salma koba komai alhaji bala baya shan giyah,sannan ba itah mijinta zai tafi yah bari ba,dui da itam da itah da babu duk ɗayah ne a cikin gidan,dan hajiyah mairo tafi ƙarfin tunanin mutum. Tallafoshi nayi tareda tsinke tunanin danakeyi ganin yana ƙoƙarin hawamin gado a haka,tureni yakeyi yana maganar da ni kaina banajin mai yake faɗa. Daƙyar allah yabani iko na cire masa rigar jinsa da takalmimsa kafin ya kwanta. Bakajin komai sai minsharinsa kawai,dan baccinsa yafara hankali kwance,hmmm ga kuɗi da jin daɗi amma babu kwanciyar hankali kwata kwata. Da safe da wuri na tashi nayi abinda zanyi na tafi madafar abinci,dan yanzu duk mune muke komai na gidan kaman yamda hajiyah mairo ta faɗa. Har nagama abinda zanyi na fita umaruje bai tashiba,nima ban tasheshi ba na bar ɗakin zuwa aikin dazanyi. A wajen nasamu salma wanda tarigani zuwa yau ba kaman kullum ba,kallonta nayi ban cemata komaiba,itama bata kulaniba da babu wanda yake yiwa wani magana kaman bamu san junaba,kowa tasa ta fishshsheshi. Kayan abincin muka fara haɗawa,dan ma yanzu aikin yaragu saboda babu na ƴan sadaka,mu kaɗaine kawai. Bamu kai minti ashirin ba a wajen muka kammala tsaff,nice na wanke kwanukan da mukayi aikin yayinda ita kuma salma ta kai abincin wajen cin abinci. Saida muka gama kafin muka jiyo hayaniyar hajiyah mairo itah da alhajin suna saƙƙowa,gaishesu mukayi kafin muka ja kujera kowa ya zauna. Har an fara zuba abinci hajiyah mairo tah kalli kujerar umaruje babu kowa akai,wani kallo ta watsamin kafin tace, "Ke ina mjinki ban ganshi a wajen cin abinci ba?" "Uhmm dama mommy yana baccine,tunjiyah daya dawo yana maye na giya bai tashiba" "Mtsww baki san yanayin kulada mijiba bare kuma sirrinsa" Tashi nayi nayi hanyar sashenmu domim tashinsa,dama da gangan na faɗi har da giyar dayasha dan taji haushi,duk da nasan ba komai zasuyi mar ba daga itah har ubannasa. Lokacin danaje tashinsa har yah tashi ya shiga banɗaki sai ƙarar ruwa dana ji kawai. 💎*sameemah a madubin gani*💎 Lokacin dana buɗe idona daga bacci samun kaina nayi kwance a kan sabon gadon da aka mallakamin a matsayin nawa. Hasken rana ne yake shigowa ta windon ɗakin da alama hantsi yayi duk ina bacci,dama kuma ban kwanta a da wuriba ina tah shirye shiyen yanda zan kai takardar neman aikina a nan garin,wanda jira nake ayi kwana uku na fita neman aiki kar lokaci ya ƙure. Surayyah ce ta shigo ta tiren abinci a hannunta,a jiyewa tayi tana murmushi,wani lokacim har mamaki take ban,bata fushi abinda koyaushe tana cikin murmushi. Gashi tayi haske abinta saboda ƙaramin cikin da take dashi,kallonta nake yanda take zuba shayi akofi tana kuma gulmar su inna rabi sun cinye abinci mai yawa kuma basu ƙoshiba,saikace masu cikin rumbu kalan su jawo mana magana a wajen mutaneen gidan. Bance mata komai ba akan zancennata dan ba abin mamaki bane zasu aikata,musamman ƴan ƙauyen da baba umaru yah nace sai an taho dasu. Bayan mungama karyawa nne na shiga wanka,dan yamzu wankana zai dawo saboda ga ruwa ko wanne lokaci,dama na saba da wanka akai akai,rashin sa ne a gida yasa nake yin guda ɗayah. Wasu fararen kaya nasaka acikin kayam da aka sakamin a cikin ɗakin,dogon wandone da riga iyah gwiwa sai kuma ɗan mayafi. Lokacin dana fito zanje sashen da su inna rabi suke ma'aikatan gidan sai kallona sukeyi har na isa wajen. Banyi sallama na shiga kawai nayi,gabadayah a iyah kwana ɗaya duk sun birkice falon,kallon wajen nakeyi da mamaki,da guntun biredi ruwan shayi akan kujera harda yaro mai fitsari. Dan takaici koh magana banyiba,inna rabice da kwarin gwiwarta tace, "Amarya bakya laifi,yah kwanan baƙunta kuma,ya mijinnaki da abokiyar zaman,ɗazu yazo nan muka gaisa ai zai fita aiki,yace ma mushiryah motoci su mayar da mu" "Toh ashe kin ganshima kuma kike tambayata ya yake,ni babu wanda na haɗu dashi dan tashina kennan,itama da kike tambayata itah ban ganta ba,yanzu dan tsabar nuna hali kuga yanda kukayimusu da muhalli,kaman awaki sunyi kalacen safe?" Wata ce daga can gefe da kofi a hannunta tace, "Lahh wai waje,bamu kohiii ba ma,gahii masu aikin sunƙi karo mana,dan sunga muna ƴan uwan amaryah,hiiine nace tunda kinzo me zai hana ki ƙaro mana,wajene ina ba ta ziri ba bazaka ƙara dawowao ba bare kaci mai daɗi aradun allah" Kallonta nake kaman na shaƙetah. "Baku kohii ba,toh karku kohiiin ƴan kohin uwa kai,nabi kohin da gudu,wallahi banga laifinta ba taƙekin kuzo mata gida,ku kalli yanda kuka maiida wajennan,kallai uban kulolin da aka ciko da abinci kaman na mutum hamsin,amma ku iyah goma kun tashi dashi,toh wallahi naji wacce tace bata koshinba,kuma kuna gamawa babu mai barin gidannan saikuna gyara wajennan tassd,bari ma ku gani na karbo muku tsintsiyah" Tashi nayi na daure fuska,saida na surfesu tass,kowa tayi tsuru tsuru taan jina,haba mutum bai san komaiba sai ci kawai,kaman jaki. Fita nayi zuwa ɗakko musu tsintsiyah kowa saitattare na gabanta takeyi,mai ɗan ta kuma da yayi fitsari ta tafi nemo ruwa. Hmmm karutai kawai aka ce basaji....... Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎13~14💎 Komawa ɗakina nayi nikaɗai ina tsuka,haba irin wannan halin ai dole komai ma a fada muku. Bayan sun kammala inna rabi ce kawai tazo mukayi sallama,sauran wai haushina sukeji,itama ciki ciki mukayi magana,a raina nace ai sai kuyi babu dama mutane basason gaskiyah kwata kwata. Ina jin ƙarar tashin motar tasu,dan daga window na ma ina ganin kokuwar da sukeyi akan shiga motar. Yau kwana na uku a gidan sameer,rabona da ganinsa tun lokacin da yakawomin kazar amarci,ko nace kazar al'ada,matar gidan kuwa rabona da ita tun a falo sanda aka kawoni,ina jin motsinta a falo da kicin,duk da yawancin muryar wata nakeji a ketchen ɗin daban. Ganin zaman ɗakin ya isheni ne kwana uku yasa na saka wata doguwar riga bayan na fito daga wanka,babu abinda na saka a fuskata haka na fita zuwa falon. Babu wanda na samu sai kallo shikaɗai yanayi,wajen abincin na wuce na zubo masa da miyah taji hanta na dawo falon wajen da kallon yakeyi. Ina jiyo hayaniyar saleema ita da wani,da alama mijinnatane yake nan. Can wajen kamar minti uku naga sun fito daga ɗakinnasa,sai shagwaba take yimasa shikuma yana biyeta kaman wata yarinyah,ta wani lafe a ƙirjinsa tana bubbuga ƙafa, "Uhm uhm honey wallahi nikam zan bika mutafi,kayimin akawarin waccar tafiyarfah amma shine zaka cemin wai bazanje wannan ba" "Kai saleemah da rigima kike,da da yanzu ba ɗaya bane,lokacin baya ke kadaice amma yanzu kinga ku biyune koh" "Ahah ni bazan yaddaba,naga ita ba sonta kake ba auren dolene kawai da cika wasiyyah,dan haka nikam muyi tafiyarmu kawai" Shiru yayi na ɗan wasu lokaci da alamun bai so ta faɗi hakanba saboda sun san ina jinsu,ita kuma da gangan ta faɗa dannaji haushi,kuma take mammanne masa dan ta nunamin ita kaɗaice a wajensa. Kallonta yakeyi da alamar meta aikata haka,ita kuwa harda wani murguɗa baki alamar tayi ɗin. Duk abinda suke ba iyah jinsu nakeba harda kallonsu,saidai ba kowane zai kula ina kallonsu,saboda na kware a wajen satar kallo da kuma ɗauke magana. Ƙarasowa sukayi cikin falon har sannan tana maƙale dashi,wanda duk da ba damuwata bin ka idaba amma nasan ka idar amarya itace da miji,amma daga dukkan alamu a ɗakinta na kwana,kuma ma dannasam hakanne yasa ta shigaba da faɗar. "Honeey jiya fah muna kwance da daddare na fada maka cewa,ni bazan yi sharing falo da wata ba,kuma baka ce komai ba,gaskiyah saidai tah koma ɗayah bangaren kawai" Kallon fuskarsa nayi wanda yake min wani kallo da niyyar yana jiran yaga mai zanyi,bai san koda za'ayi shekara suna zancensu bazan yi magana ba saidai idan sakani sukayi a ciki. Tashi nayi na nufi kitchen domin kaiwa plate ɗin danaci a binci a ciki. Lokacin dana dawo suna dinning wajen cin abinci,cigaba nayi da kallon labaran da akeyi a ƙasar iraq cikin harshen larabci na ƴan ta'adda da suka kai hari. Hankalina ya tafi gabaɗaya wajen labaran da ake yi,banzata ba sai gani nayi an sanja tasha zuwa ta zee world. Kallon mai wannan aikin nayi,saleema ce a ɗaya kujerar da take gefena ta saka idonta akan tv,ga kuma remote a hannunta tana jijjiga ƙafa wanda tasa ɗaya kan ɗaya. Dan takaici ma bansan abinda zance ba,dan ko kaɗan banida ra'ayin yi mata magana a lokacin bare kuma faɗa. Shima kansa sameer yana kallon abinda yake faruwa,amma ko ƙala bai ceba.rintse idona kawai nayi domin tunano mai ma zan mata wanda zan huce. Sauke idon nayi a kanta wanda nasan koba madubi a gabana nasan sun sanja kala daga yamda suke. "Ko ki mayar da tashar da takeyi ɗazu ko kuma nayimiki abinda ba kya tsammani,sannan idan na ƙirga goma baki mayar ba,shikansa tv to daga yau yah tashi a aiki bazai ƙarayiba,sannan duk wanda yaje gidannan abinda zai biyo baya bazai yimasa daɗiba. Sanann abu na ƙarshe ina baso kike na karya ki karal ki tashi daga aikiba toh karki kuskura a zantukanki kisake sakoni a ciki,dan abin bazai yi miki kyauba" "Heee me kike tunanin zaki iyah yimin,toh dama jira nake ki tanka dannaji ɗazu kinyi shiru,toh idan baki saniba ba'a shigo sansanin zaki a taba ɗansa a fita lafiyah,dan haka ke ba komai bace a cikin garinnan ma bare kuma gidannan,dan duk abinda yake gidannan toh ki sani mallakina ne nikaɗai,komai kika taba alfarma aka yimiki,dan haka dole nayi yanda naga dama,babu abinda zaki iyah,idan ba hakaba kuma nasa a hukuntaki kuma babu mai ƙarbar ki a hannuna koda kuma mutum zai saida gidan gandu" Zuwa yanzu maganar na kula bada iyah ni kaɗai take ba harda shikansa uban gayyar,dan taga kissar bazata kaitaba sai ta koma gargaɗi kawai. Murmushin gefen baki nayi,ita ana ta tunanin ƙananan sojijin da ubanta yasa suyi gadinta,wasuma a cikinsu koh training cikkeke basuda shi sune zasu iyah yimin wani abu,saidai nayi mata uxuri ai zaman yamzu aka fara zata yi abinda bazan ƙyaletan ba. Kallon agogon falon nayi wanda yah nuna goma dadai,mayafin kai na na gyara kafin na koma ɗakina domin ɗauko takardun aikina,akwai abinda nakeson yi banida lokacinta. Lokacin dana fito daga ɗaki na fita waje sameer yana ƙoƙarin tayar da motarsa zai fita. Kallon kallon muka sake yi,sannan ma bai yimin magana ba,nima kuma banyi alamar zanyi masanba,yana fita da motarsa nima na fita daga gidan zuwa office ɗin ƴan vigilantee na garim porthacourt. 💎*zainnb a madubin gani*💎 Kallon zanin dayake jikina nayi wanda yayi duƙun duƙun dashi kaman an tono ni a cikin toka,dam takaici ta kuma wuyah inaga nayi kuka yafi cikin kwando daga kawoni gidan yunusa,wanda koh wata ɗayah banyiba,gashi jiyane tun waccan satin yakamata naga al'adata inaga ma cikine dani,wayyo allah na da wanne zanji haka. Wallahi ji nakeyi kaman na gudu a rasani gabaɗaya ma. Muryar inna laraba naji daga cikin gida kaman goge tana ƙirana,tun safe nake gindin murhu har gashi la'asar tayi amman koh gyaran ɗaki banyiba,gashi miji na maidashi sabatoto,naje anyi masa asiri bashida aiki sai cemin toh duk abinda nace kuwa. Amsawa nayi a ƙasan maƙoshi kafin na gita dan jin menene dalilin ƙiran. "Wai a Ina kika makalene tun d'azu nake kiranki kaman an aiki bawa garinsu" Shiru nayi ban bata amsaba,toh mai zance bayan tagama fadanta kuma. "Kowa yunwa yake ji kizo ki raba abincinnan mana,ko so kike ki kashemu da yunwa dama kin washemu,ga altine ma yar mijinki tazo,ƴaƴanta sai yunwa suke ji,kizo kobasu abinci dan basu saba da yunwa ba" Takaicine ya isheni,mai take nufi kenan,ni na saba zama da yunwar ne aka fadamata kome? Dan babu yamda na iyha haka na je gaban ƙatuwar tunkuyar na fara zuba shinkafar,jajir da itah bata da maraba da dawa,daɗinta daya ma banice da tuwon dareba,zan samu na nakwanta na huta kafin wani jiƙon kuma. Ina gama rabon na ɗebi nawa na tafi ƙofata,dan dama nikaɗaice a ƙofar yunusa yah tafi aikin ƴan sanda an turasu garin darazo a jihar bauchi. Burina bai wuce yah samu sugama training ɗinba yasamu aiki a wani garin na bishi,ko na huta da wannan uƙubar da ko yanzu aka barni da itah na azabtu yanda yah kamata kuwa. Tsabar gajiyar danayi koh abincin dana shigo dashi banciba,ina kwance ina ta tunani har bacci yah ɗaukeni bansaniba. 💎*sameemah a madubin gani*💎 Ina fita bakin titi na samu mai adaidaita sahu nayi masa kwatancen office ɗin ƴan vigilantee,mun dan dade muna tafiyah kafin muka iso wajen,a bakin wajen na sauƙa na bashi ƙudinsa kafin na wuce zuwa cikin wajen. Bansamu wani wahala ba na ganin shigaban kasancewar babu layi kaman office ɗin dana je a baya. Wani na samu aciki ana sallamarsa da alama aikin yazo nema shima,dan ƙaramin matashine mai jini a jika,bai dade da shigaba sai gashi yah fito yana murmushi da alamun yayi nasara,nima shiga nayi na zauna a kujerar da take kallon shugaban. Karim farko takarduna ya ƙarba,ya dade yana dubawa kafin ya dauko wata takardar a gefen sa ita ma yah duba,ɗagi kai yayi yana kallona kafin yace, "Sameemah umar koh?" Daga masa kai nayi alammar ehh,zare glass ɗin dayake fuskarsa yayi kafin yace, "Saidai kiyi haƙuri,amma ma'aikata sun cika a nan bazai yiyu mu baki aikiba" "Hmmm yallabai kenan,waye ya hana a bani aiki anan wajen,sannan menene dalilinsa" Tun kafin yabani amsa na tafi wani tunani,irin kallon da sameer yakemin lokacin dana zo fitowa daga gidan,sannan shekaran jiyah naji kamshin wani turare a dakina wanda ba nawa bane,tabbacin wani yah shiga ɗakina kenan,wato yah plan ɗina na cigaba da aikina shiyasa ya min haka. Dakatar da shugaban nayi tareda cemasa, "Karka bata bakinka,nariga nasan wanene yasaka ka hanani aiki anan wajen,na gode da bani aron lokacinka" Takarduna na ɗauka na fice daga office ɗin. Tun daga bakin titin na danna ƙiran burgu a wayah. Ringing biyu tayi yah amsa,duk hayaniya ma da alaamun yana kan hanyah,saidai tunda yana jina shikenan. "Kai burgu" "Na'am shugaba jar wuyah amarya a wajen major yah akayi ne" "Ba surutu na ƙiraka kayimin ba,ina so kaje anguwarmu inda na bada ajiyar su bingo,kasaka minsu a manyan motoci su kawomim su garinnan,yau ba sai gobeba,so nake zuwa gobe sun iso wajena" "Amma shu......." Kittt nayi saurin katse wayar dan banason wani dogon surutu kuma. Alllah allah nake gobe tayi su bingo su kariso,so nake na koma ainihin sameemah da kowa ya sani,banason hakurinnan danakeyi da kuma yin shiru akan abu,zuciyata batajin daɗin hakan,saboda bada wannan sameemah na daceba sam. Shikuka sameer zai san yahana a bani aiki,badai zaman gidansa yakeson nayiba ,zai san yah sakani zaman gida kuwa. Wani mashin ɗin na hau zuwa gidan,tun daga bakin ƙofar shiga falon nakejin murayar wata a falon,koh sallama banyiba na shiga. Haɗa ido mukayi da wata wacce bazata wuce sa'a taba,daga yanda suke zance mutum zai san abokiyarta ce. Har nakai bakin ƙofar ɗakina naji tayimin magana,hakanne yasa nadawo daga shiga ɗakin, "Amaryar bakyaa laifi,babu maganane,sunana suhaila budurwar Ahmad abokin mijinki,koba komai zaki zo mugaisa koh" "Toh koh shi Wanda kika ƙira da sunan saurayinnaki ban sanshiba,ko na sanshi ma ba tsayawa zanyu mu gaisa ɗinba,bare kuma ke da kike matsayin budurwarsa" Ƙarisa maganar nayi ina kallon cikin idonta tareda da ɗaga girata kuda ɗaya dan tasan ma da gaske nakeyi,sakin baki tayi tana kallona da mamaki,bantsaya jin mai zata sake cewa ba nayi cikin ɗakina. 💎*saleema a madubin gani*💎 Tunda aka kawo sameema cikin gidana akayi kwana uku naga babu abinda yake shiga tsakanin sameer da sameema sai hankalina yah kwanta,sai kuma nafara ɗaura ɗamrar mallakewa mijina niƙaɗai ,dan na nuna mata ita bata isa ta ƙwacemin shi ba. A falo ma duk abinda mukayi nayi zaton zata tabani ko kuma tayimin wani abu,dama na shiryah ɗaureta zan sa ayi a ɗakin horo har sai kammanninta sun canja,sai kuma ta shafawa kanta ruwan sanyi batayi komaiba,sai ma ficewa da tayi daga gidan. Ina zaune niƙaɗai a ina bawa zuhra nono,ina kuma chatting a whatsapp sai ga suhaila tah shigo,da tayi nayi niyyar mushige daki amma sai muka yada zango a falon kawai. Tafawa mukayi bayan na faɗa mata abinda na aikata da safen. Muna cikin hakanne sai gata ta shigo,da alama wani waje ta je,signa suhaila tayimin nima nayi mata lokacin da sameemah ta kusa shiga ɗakinta. Ina jin duk maganar da,sukayi da kuma amsar da sameemah ta bata,nidai bance komaiba sai gyara ƴa ta danakeyi wacce take bacci a cinyata. Kama baki suhaila tayi tana kallona jin irin amsar da sameema ta bata. "Ke kiji wannan matar,wannan magana haka,kaman ana bata action,uhmmm gaskiyah kin gamu da aiki daga gani,sai fah kin dage,dan ma kincemin baya kulata,amma duk da haka saifah kin dage,ba a shaidar ɗan kuturu sai yah shekara da ya tsunsa tukunna" Murmushi nayi kawai,danni kaɗai nasan irin abinda na shuka zam aiwatar a gidannan,duk abinda zanyi na kori sameemah a gidana to zanyi,domin itah ɗin hatsarine zaman ta cikin gidan. Hirar mu muka cigaba da suhaila kuma duk bata wuce akan sameemah bane. Sai wajen magriba kafin suhaila ta tafi gida,lokacin sameer ya dawo daga aiki suka gaisa ma a waje. Tare muka shigo dashi,ina kalllonsa yama kallon gefen ɗakin sameema,haushine yakamani duk da nasan ba komai ne a tsakaninsu ba,jakar hannunsa na karba tareda kamo hannunsa cikin tattausan hannuna duk dan na ɗauke hankalinsa daga tunanin ta,kallona yakeyi da idonsa da sukayi ɗan ja saboda yawan aiki. Nima sansanyan kallo nake aika masa wanda nasan yana narkar da zuciyarsa a duk lokacin danayi masa,musamman idan yana a yanayi na buƙata. Ɗakinsa muka shiga yah rage kayansa yah shiga banɗaki,nikuma na ajiye jakar tareda zuwa ɗauko abincin da kareematu mai abincina tayi. Lokacin dana shigo ɗakin har yah fito daga banɗakin yah saka ƙananan kaya marasa nauyi,hada ido mukayi dashi,lokaci ɗaya na karanci duk abijda yake kwance a cikin idonsa,kirjina yabada ƙarar bugawa fatt,saboda nasan in yana wannan yanayin bana karewa da ɗadin jiki,dan sai nayi gashin jiki tukunna. Kawar da tunanin hakan nayi a raina na cigaba da zuba masa abimcin,saƙƙowa yayi inda nake zaune daff da dani,ɗan matsawa nayi kaɗan domin bashi damar cin abincin,saidai daga fuskarsa nagane bahakanne a gabansa ba. Ko kuma mai yah tuna sai kuma naga ya jawo plate ɗin abinci yah fara ci. Lokacin dayah gama an ƙira sallahr magriba,dan haka alwala yayi yah tafi masallaci,yayinda nima nayi nawa ɗakin. Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎15~16💎 💎*sameer a madubin gani*💎 Har na isa masallaci babu abinda nake sai tunanin yanayin gidannawa,a yanda halitta ta take nasan nayi ma saleema karfi saboda yanayin jiinta,idan har nace zan tursasa mata toh zan iyah shiga rayuwarta. Bangaren sameema kuwa banajin koda mun shryah zan iyah zaman aure da ita,saboda har yanzu idanuna sun kasa ganinta a matsayin matata sai ƙanwata. Zaman damuke yi da itah a gidan ma ya isheni bare kuma zancen wani abu daban. Da ƙyar na samu na yage tunani a cikin raina nayi sallah. Bayan an gama sallah ma ban koma gida ba sai addu'o'i da nakeyi dan samun kusancin ubangiji da kuma neman sauƙi akan abinda yake shirin faruwa. Sannan ya,zabamin abinda yake mafi alkhairi a game da mafarkin danakeyi na sameema da kuma dukkan ayalina a cikin wani yanayi marar daɗin gani. Lokacin dana ɗauko hanyar gida goma ta kusa,sojojin da suke patrol ɗin dare har sun fara,ɗaga min hannu sukayi tareda buɗemin kofar gidan na shige. Har nayi niyyar wucewa sai kuma na shiga ɗakin sameema,duk da nasan bata son ana shigemata ɗaki,saidai ba ra'ayinta nake biba nice da iko da itah ba itace take da iko dani ba. Murda ƙofar danayi a hankali ko a rufw yake,saidai cikin sa'a naji kofar tah buɗe. Ina gama shiga ɗakin ita kuma ta fito daga banɗaki ta towel a hannunta ɗaya kuma tana goge ruwan daya taba gashin kanta. Tun daga ƙasa idona yafara yawo a jikinta,yah wuce dogayen kafafunta farare masu matsakaicin ƙiba,har zuwa laffaffen cijinta da ko kaɗan bai ɗago towel ɗinba,saukewa nayi akan fuskarta wanda ita ma ni take kallo,saidai muna haɗa ido da itah ta ɗauke kanta tareda zefar towel ɗin dake hannunta ta nufi gaban madubi. Yanda take yin kowane motsinta sia yake nuna kaman dani takeyi,amma itah a nata bangaren yi kawai take. Lotion ta ɗauko ta ɗage towel ɗin har zuwa kusan kunkuminta kafin ta fara shafa man. Babu abinda nake ayyanawa a raina sai yin salati da kuma yiwa zuciyata gargaɗin kan cewa,abinda take gani fa miliyoyin mutanene suka gani kuma suka taba,dan haka babu abin zan hankali akan abinda ya riga yagama zaga duniyah. "Wai binciken kazo sake yimin koh kuma yau turoka akayi ka tsareni da ido duk abinda nakeyi" Duk da abinda ta faɗa gaskiyane ita nake kallo,amma yanda ta faɗi ina kallonnata sai abin yah bani haushi. "Mai zan kallah akan abinda yah riga yagama zaga duniyah,kowa yah gama kwasar romonsa yah bari" Murmushi tayi saidai har yanzu bata ɗago tah kalleni ba,saima tashi da tayi ta nufi wajen kayanta na bacci,ɗauko wasu pink tayi masu kyau ta ajiye akan gado kafin ta juyo ta kalleni, "Toh zan iyah sanin mai yah kawoka ɗakin wannan karuwar da karfe sha ɗaya na dare har kakemin wannan kallon ,bayan kana da mata,ko ta kasa kashe maka kishirwarka ne kazo muyi cinnki. Saidai kasani farashina yana da tsada sosai,amma karka damu nasan zaka iyah biyah ai,yanzu sai muyi ciniki,dama kuwa na dade ban sayarda hajata ba gashi na samu costomer da wannan daren,kuma kaima ka taki sa'a da bakayi booking ba bare kuma bin layi kawai ka samu a kyauta" Duk baƙincikin danake ciki a yinin ranar nan baikai kwantan kwacin maganar da sameema ta faɗa min ba,wannakuwa anya mutunce,abinda nah fada a ransa kenan. Ganin koda nayi niyyar faɗar wata kalmar bazata samu damar fitowa ba,juyawa nayi kafafuna suna rawa ga raina yana tafarfasa. Ɗakina na nufa dan ban ra'ayin ganin itah kanta saleema ma a lokacin,tambaya nayiwa kaina ,meyasa nake jin haushi dan ta faɗi hakan,meyasa nekjin maganar tayimin zafi?,nidai ba kishinta nake jiba koh?. Kodah yake dole nayi kishinta ai ƙanwata ce. Da wannan amsar zuciyata ta yada har na kwsnta bacci bansan sanda barawon baccin ya ɗaukeni ba. 💎*sameemah a madubin gani*💎 Ina jin sanda yah bugomin kofar da ƙarfi bayan ya fishe,ko ba a faɗaminba nasan yah ji zafin maganar danayi masa,hakan yanamin daɗi idan mutane suka ɗaukeni a wata siga da zuciyarsu ta raya musu ba tareda sunyi bincike akai ba. Kayan baccina na saka tareda bin lafiyar gado,har sannan ban daina murmushiba da kuma tuno yanda yake bin jikina da kallo,wanda kuma hakan zai ganshi yah bari,dan bana kowa bane na wane ni ka kadai. Washagari da safe ina tashi da feɗuwa na sauƙo daga kan gado,dan yau kam nakoma sameemah tah kuma,na gaji da waccar wacce bata yin abinda taga dama,kokuma ta dunga barin abu idan anyi mata. A wajen saka kaya dama wani wando na samu jean irin mai ɗamewar nan,sai wata me ɗan tsayi,itah ɗinma saboda rashin mutunci ban barta hakaba saida na ɗaureta ta koma dadai inda wandon zai fara,facing cap na ɗauko irin rigar na nasaka sannan na sneaker suma masu adon pink. A taƙaice dai na fito kaman wata mawaƙiyah a ƙasar turai dama kuma ga farina mai harkene sosai. Fitowa nayi falon dadai su saleema suna karya wa ita da sameer a table,farouq ma yana gefensu yana cin taliyar yara. Ɗago min hannu yayi tareda cewa, "Hi anty" "Ya kke ka tashi lafiyah" Dariyah yamin irin ta yara yana ɗaga kai,kallon iyayennasa nayi tareda ɗaure fuska kaman banice nayi wa yaron murmushi ba. "Ku kuma na tafi juggling na exercise kwana biyu ina zaune har na fara tara cholestrol. Sameer ne dayakai shayi bakinsa yayi saurin zubarwa har yana ƙwaruwa kafin yace, "Me......menaji kince,excercise?" "Ashe kaji mai nace ɗin kake neman na maimaita" "Toh bazakije da wannan kayan ba kam" "Saikuma kayi ai wai karuwa taga mai wa'azi" Juyawa nayi na fita hankalina kwance,dan tundaga cikin falon na fara juggling ɗin ban fitaba. Hanyar dazai kaini jejin cikin wajen na nufah,dan daman dan yaganine nace masa cikin wajen zan shiga,amma dayasan yanda banason cikin mutane daya sau ransa a inuwa. Bani na dawoba sai can wajen tara da rabi,dayake tun bakwai na fita. Wanka nayi tukunna na fito falon. Wayata ca tayi ringing ina ɗauka naga baƙuwar lamba,saidai nasaka a kunnena naji ashe wanda aka bawa saƙon kawomin karnuka nane yazo yana bakin barinki sojojin an hanashi shigowa. Fita nayi zuwa bakin wajen,dayake akwai tazara na jima ina tafiyah kafin na iso bakin wajen,su bingo suna kallona suka fara ƙoƙarin ƙwacewa a hannunsa. Alama nayi masa da ya sakesu,dan daga gani a tsorace yake dasu sosai. Aikuwa kaman jira suke suka rufo da gudu kaman sunga nama,tsugunnawa nayi na taresu,sai kaɗamin jela sukeyi. Maganar wani soja ce tah ɗago dani wanda yakeyi kaman mai koyon hausa. "Hajiyah zakina biyamu kuɗin ƙarba saƙo fah" ”kudin me kuma ana zaune kalau,ba abinda zan baku idan kunga kuma zaku iyah toh ku biyoni gidanan ku karba" Har zai sake magana wani a cikinsu yah raɗa masa abu a kunne,yana jin hakan yah yi shiru yana juyah fuska. A hanyane muna tahowa na kulada yanda raze taƙi sauri shikuma bingo yaƙiyin gaba ya barta kaman yanda suke wani lokacin,tsayawa nayi ina ƙaremusu kallo,sai a sannan na kula da yanda cikinta yayi faɗi yai ƙasa,kallon bingo nayi mai kama da harara,saurin juyawa yayi yana shinshina bushasshiyar ciyawar da take wajen,shafa kanta nayi kawai kafin na ce, "Allah ya sauƙeki lafiyah" Da haka muna tafiyah har muka iso kofar gidannamu,wannan wanda yayi mana tambayoyine lokacin farkon zuwana gidannan,dan na kula a duk cikin sojojin da suke gadi yah fi kowa iyayi da taƙaama. Kabani wajen na wuce,kafin na maimaita sau biyu,idan kuma ba haka ba wallahi zan iyah shiga na fita aikin soja sai yah gagareka a rayuwarka. "Ina zakije a da wannan dabbobin,ko karnukan sojoji baza'a basu damar wucewa ta nan ba,bare kuma wannan" Tahowa nayi zan wuce sai ya tare kofar dan yaga mai zanyi,tafiyah nake zuwa wajen get din,nima ban fasaba,har saida nazo gaf dashi amma yana tsaye bai ko motsa ba. "Nayi maka last warning ka bani waje na wuce tun kafin raina ya baci" "Bazan ........" Tun kafin ya karisa maganar nayi masa wani naushi a hanci,taga taga yayi yai baya zai fadi,amma duk da kokarinsa saida yah daku da kasa,ta gefensa na tsallaka na wuce koh kallonsa banyiba,injinsa yana rike da hancin yana face majinar dole. Direct cikin falon na shiga suna biye dani har dakina,saleemah tana zaune a falo sai ganinmu tayi mun shiga,tashi tayi tana kallona har na wuce dakina. Gyalen dayake wuyana na cire kafin na jawosu muka fito zuwa kicin,robobi guda biyu na ɗauka a wajen set ɗin robobi,ja da kuma koriyah. Abinci na diba na cika kowacce roba kafin na fita,suna biye dani kaman jela har garden din cikin gidan. Ajiyewa nayi tareda komawa debo ruwa,a hanyar komawar ne mukayi karo da sameer wanda dawowar sa kenan da key din mota a hannunsa, "Meyasa kikawo karnukanki gidannan batareda izinina ba,bayan kisan koh sanda muka je gida ma ba sonsu nakeba,kina mace mai zakiyi da karnuka hakan ma a kina mayar aure,abimda kike yakamata ke a ganinki" "Kai wanda kakeyi na ya kamata ne,karnuka kuma nawane ni naga damar zama dasu shiyasa na taho dasu,kuma babu mai fitar dasu a gidannan,dan zamana sukeyi,idan zasu var gidannan saidai mu tafi tare" Kedai kika sani,amma koda wasa karna kuskura naji akan wasu wata maganar ta fito,idan kuwa ba hakaba zasu bar gidannan koh kinaso ko ba kyaso" Kafi kowa sanin halina akan hakan,amma idan aka daboni bana shiru saidai koh maima yah faru" Daga haka yah juya yabar wajen zuwa cikin gida,saida na tsaya na tabbatar suna cin abinci kafin na shige cikin gidan. Hayaniyah na ji a falon inda na tsinkayo muyar saleema tana faɗin bazata zauna da karnuka a gida d'aya ba,harara ta bini dashi dana shigo da alama bataso zaman karnukan ba,nikuwa babu yanda zatayi dani nan gani nan bari ɗumamen mayyah. Satin su bingo ɗayah a gidan har sun washe da gajiyar mota,babu inda basa shiga a cikin gidan,ɗakina kuwa saidai idan gari bai wayeba,duk da reza bata fiye zuwa wajena ba saidai idan na je inda suke,kasancewar cikine da itah. Sojan dana bigewa hanci kuwa,wanda naji sunansa wai samuel,kullum muka haɗu sai yah harareni da alamun zamu hadu,ni har dariyah ma yake bani. Fita exercise yanzu da bingo nake zuwa,tun sameer yana masifah,har kusan marina yayi amma ban fasaba,kwata kwata banajin daɗin zaamn gidan,bayyi kama da inda zan zauna ba a yanayina,dan ma nakan je cikin maakrantar koyar da ƙananan sojoji da akeyi wani lokacin ina kallonsu,hakan yakan dan debemin kewa,sannan kuma mukan fita yin training nida bingo,dan ɗan barshi danayi a gida har yayi laushi wajen gudu. Tun da safe naji motsi a ɗakina amma bana su bingo bane ,ƙin juyowa nayi saboda nasan waye a wajen, "Nasan ba bacci kike ba,nazo na fada miki cewa ki shiryah zan kaiku gidan su saleema ku yini,saboda tunda kikazo basu gankiba,yakamata kije su ganki" "Bazan jeba mai zasu min idan sun ganni din" "Kinba ba gardamarki nazo jiba,magana ce na fadamiki kishiryah nan da karfe goma zan kaiku,saura kuma naji wata maganar ta fito kuma" Lokacin dana jiyo wayam naga wajen babu kowa da alamar har yah fita bayam yayi maganarsa ta karshe. Tsuka nayi na juya na cigaba da baccina saboda safiyah bata wayeba sosai,dan dai yah ci sa'a bana rude kofa ne shiyasa yake shigowa yanda yaga dama. Jeans da t-shirt nasaka sai kuma kimono dana ɗaura akai baƙi da mayafinsa. Lokacin dana fito saleema tana gaba da zuhrah a akan cinyarta faruoq kuma yana gidan baya,sameer ne daya taho daga bayana yake magana. "Ke wannan wane irin kayane,koh gidan kawarki bazaki je dasuba bare kuma wanda suke kaman a matsayin surukanki,dan su tamkar iyayena ne a garinnan". "Kai suke matsayin iyayenka amma ba niba,ni bani da wasu surukai kuma ban shiryah yin wasuba,idan kuwa dole saina canja kayannan,toh wallahi bazanje na saidai na zauna,na gaji da wannan juyin,saikace zanje ganin Annabi." Jijjiga kai yayi alamun na isheshi,hakan nakeso,wayace da aka daura masa ni baice ba zai iya ba,buɗe gidan bayan nayi inda farouq yake na shiga. Yaron ne ya ɗago ya kallaeni fuskarsa dauke da murmushi yaca, "Morning aunty" Tun kafin nace wani abu,saleema tace, "Idan kasake gaisheta sai na cire ma harshe,mai shegen surutu kawai,wanda yake gaisuwa ake gaisarwa,ba wanda bai san darajarta ba" Sameer ne ya katseta daga maganar da takeyi, "Ke saleemah bana son irin wannna halin,bai kamata ki dunga nunawa yaro hakaba,karna sake ji" Maganar su suke tayi har muka zo gidan banyi saka musu bakiba. Shiga mukayi cikin gidan,babbane sosai dan yah fi wanda muke ciki girma,dan jikin bangon gidanma abin kallone ga wanda bai taba ganin irinsa ba Zama mukayi a kujerun gidan dukkanmu,saidai jin alamar sakkowa mutum daga daga samane naga sameer ya sauka daga kan kujerar a yah zauna a kasa,kallona yake da alamar nima nayi,a raina nace kana ruwa kenan,idan ni zan yi yanda kace. Kara bude kimonon dayake jikina nayi tareda sake gyara zamana a kan kujerar yanda jeans din jikina zai dan fito waje. Cize baki sameer yayi yana kallona cike da daya sanin tahowa dani,hmm wayace yah taho dani. Dattijuwar matarce ta zauna a akan kujera fuskarta cike da fara'a,. Muna hada ido da ita naji matar ta kwantamin arai duk da bansan mai yasaba,jinai bakina yah bude ina gaisheta bayan banyi niyyar hakanba. Nikaina nayi mamakin hakan bare kuma mutanen da muka taho da su. Yar magana kadan muka yi da ita sameer yah tafi,da niyyar zai zo daga baya yah daukemu,nidan shiru nayi in kallonsu,duk da banajin gidan ya isheni kaman yanda nakeyi idan naje wani gidan,abin yabani mamaki sosai,dan matar har ɗakinta ta jani,akan nayi sallah. Kallonta nakeyi dan bansan mai zance ba,itama kallon nawa takeyi bayan ta shimfidamin sallayah,ita kuwa saleema tunda taga mahaifiyarta ta kukani,tayi fishi da mamar tata ta fi dakinta,da ubanta yadawo kuwa wajensa ta nufah. Tun daga nan na kula ubantane ya sakaltata ba mahaifiyarta ba,dan daga idon mahaifiyatata ina ganin rashin jin dadinta game da halin y'ar tata. "Uhm dama hajiyah ina period ne" "Period kuma,amma bakiyi kama da mai period bah,danna karanci likitan matane,babu abimda bansaniba akan mata sai abinda baza'a rasaba. Saidai ban saniba koh bakya son yi ina nan ne" Tana gama fadar hakan cikin murmushi ta fice daga dakin,bandakin cikin dakin na shiga jikina a sanyaye,dan babbban abinda duk duniyah bazan iyaba shine sallah,koda na nayi niyyar aikatawa nasan bazan iyaba. Alwala nayi na fito zuwa inda sallayar take,kallonta nake kaman mai nazari kafin na dorah ƙafata akai. Runtse ido nayi saboda jin wani abu kaman allaura ya huda kafata har zuwa cikin kaina,idona yana rufe nasake ɗaga ɗaya kafar nasake ɗorawa akan sallayar. Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎17~18💎 Cikin dauriyah dakuma san gwadawa nafara tada sallar,saidai bankai gayin ruku'u ba nayi saurin zama a wajen ina rike kaina,dan nasan yau kam bazanyu bacciba koda naso hakan,nasamu najima da fitinar boyayyun mutanen can. Ina zaune a wajen mahaifiyar saleemah tah shigo dauke da wani kwano a hannunta,miƙomin tayi tareda cewa, "Ƴata maza shanye wannan zai miki amfani kinji" Girgiza mata kai nayi alamun banaso,mamaki hakan yabata "Meyasa bakyaso,karki damu bamai cutarwane ba nice nake hadawa da kaina,sannan karkiyi tunanin zan cutar dake,dan wallahi har cikin rai na nakejinki tun lokacin da na hada ido dake" "Nasan bazaki cutar dani ba,sannan nasan ba abun cutarwa bane,hasalima nasan menene kawai dai bana bukatar sa rayuwata ne,shiyasa" "Kamanyah kenan,kina mace amma bakya gyara kuma" "Ina gyara mana irinna wanka da wanki,saidai irin wannan gyaran dakike nufi nasan bazanyi shi a rsyuwar data ragemin sauraba,saboda wanda akeyi dan shi wato miji bana bukatarsa a rayuwata sam" Zata sake wata maganar ne nayi saurin katseta ta hanyar cewa, "Babu abinda yake hadamu dashi shiyasa" Saurin daure fuska tayi lokaci daya kafin tace, "Me saleemah tah aikata da har hakan ta faru" ,ƙoƙarin tashi take na dakatar da itah ta hanyar cewa, "Babu hannun ƴar ki akan hankan,wanna zabina ne bana kowaba,kuma kiyi hakuri bazan iyah fadamiki daliliba,kawai ki dauka haka nake,sannan ki gargadi yar ki ta rage shiga harka ta idan tana son lafiyar ta a jikinta" Daga haka na fito na bar dakin na zauna falo,dan hakan shine mafi saukina,narasa miyasa na yarda da matar har nake fadamata irin wannan sirrin,inaga idan muka dade zan iyah fadamata komai bansaniba,daga bay nazo ina nadamar hakan. Ina nan zaune har sameer yadawo daga aiki yazo ɗakarmu,sallama nayi mata saidai yanzu babu murmushi akan fuskar matar,sai kallon tausayi da take bina dashi,shareta nayi tareda cewa ke ta shafa kuma,bazan sake dawowa gidannan ba gaskiya,duk da zuciyah ta tana son dawowa gidan koda kuwa a gobene. Kwanaki sunja da tafiyah ta garin porthacourt ko kuma nace da zamaan a can,har surayyah ta haihu mace sun saka mata sunana,nidai da sun nemk shawarata da basu saka mata suna na ba,saboda ina tsoron kar wani abun yasameta ,sannan wane abin kirkin na ajiye da har na cancanci hakan, bayan suna da mukayi waya da burgu yake cewa yaji labarin zainab ma ta kusa haihuwa,toh kawai nace dan banga ta inda hakan yah shafeniba,ni har na manta dasu ma saida yah fadi hakan tukunna. 💎*sameer a madubin gani*💎 A hanyar dawowa ta daga wani wajene na tsaya nayi nama ɗauri guda biyu,duk da nasan cewar akwai a gida amma ihsani yana da dadi. Lokacin dana shigo har zan wuce dakin saleema sai kuma naga danaje dakinta na sake dawowa na sameema wanda yake farko gwara na mikawa sameema inyaso sai na kaimata nata,gashi na gaji daga wajen aikin da muka tafi,dan kwannan kullum cikin harim yah ta'adda da yan boko haram muke. Ban kwarkwasa kofar ba shige wa kawai nayi danna san a bude yake dama. Duhune dakin hakan yasa na kunna wutar dakin tun daga bakin kofah,saurin runtse idona nayi saboda ganin irin kayan dayake jikinta. Daga ita sai pant da breezier a jijinta baƙaƙe,duk da cewa ana zafi amma ai zata iyah kunna AC idan tana bukata. Ido daya ta bude kaman wata munafuka kafin ta mayar dashi ta rufe tareda juya bayanta. Hakan da tayine yasake dukan kirjina kaman ana sokamim wani abu,dan yarinyar babu karyah akwai zubin halitta mashaallah,dakyar na samu na tattaro wasu yan guntayen kalmomi nayi amfani dasu wajen cewa, "Wannan wace irin kwanciya kikayi sameemah,sannan wannan kayan kuma fah" "Ina ruwanka da kayana,kwanciya kuma wacce naga dama zanyi,tunda dakinane,kona kiraka dakinne bare kayimin kutse cikin rayuwata" Duk maganar da takeyi ta dayah bangaren takeyi,dan tajuyah bayanta can,murmushi nayi dan dama nasan hakan zata faru,domin kwata kwata batada burki a bakinta wajen yin maganar da ranta yakeso,kaman wata GOYON GWAURO,batasan tauna magana ba kwata kwata. Ficewa nayi daga dakin tareda kashe mata wutar bayan na ajiye mata hakkinta. Dakin saleema na nufah ,saidai ina zuwa na jishi a rude kirib,nasan ba bacci tayi ba duk da kwankwasawar danayi amma bata budeba,kome nayi mata itakuma oho,....kai mata! Na fada a raina. Da safe da wuri na shiga dakin saleema,a zaune na sameta a tsakiyar gado,zuhra kuma ta kama bakin gadon tana ta zuwa tana dawowa irin na yara masu koyon tafiyah. Duk sallamar danayi mata bata amsaba,haka maganar danyi mata, "Ina miki magana kinyimin shiru wai me yafarune haka,nace miki kishiryah zamuje bikin samun matsayi na abokina a katsina koh" "Bazan jeba,ka dauketa ku tafi ,kodan kana tsoronta,saika nunamin fada kukeyi a haka itama,amma daga dare yayi saika shige dakinta kuyi ta soyayyarku,wato kun maidani shashasha,toh allah ya toni asirinku,da idona naga shigarka dakinta kuna magana,dan haka ka dauketa ku tafi amma ba niba kam" "Mai kike nufi,wai daman dan kina ganine nake kin shiga dakin sameemah?,toh tun wuri kisanja tunani,babu abinda zaki hana a alakata da itah haka rabuwarmu,batun abinda yakaini dakinta kuma bakya bukatar sani tunda kin baiwa kanki amsa,batun zuwa da ita kuma zanje da itah dunta kin ce hakan" Fita nayi daga dakinnata daga haka,dan gsskiyah ta fara bani haushi,mutum bashida aiki said kishi kuma akan abinda ba hakaba. Dakin sameemah na nufah lokacin tah fito a wanka,fuskata babu alamar wasa bare tayimin taurin kannata daya zame mata jiki. Ina Mamakin yanda duk daure fuskata amma koda wasa tayimin kallon ta ga kwarjinina batayi,abinda koh maza ma sai na maji tukunna yake kawomin wargi. "Ina so ki shiryah bamu je wani waje yan zunnan" "Wai nikam mai ........." "Sameemah banason jin dogon surutunki a halin yamzu,kedai kawai ki shiryah mu tafi,ba dadewa zamuyi ba" Na boye matane saboda nasan idan ta san inda zamuje koh tsafi nake da baƙar zaba bazatajeba. Da haka allah yabani sa'a ta shiryah dim. Sauke ajiyar zuciya nayi ganin ta fito da wani material a jinkinta purple,yayi mata kyau kuwa sosai,baƙin gyale ta yafa irinna adon kayan. Mota muka shiga babu wanda yake cewa wani abu har muka dau hanyar barin gari. Kallonta nayi tah gefen ido dan naji mai zatace,amma bata ce komaiba saima danna waya da takeyi lokaci zuwa lokaci takan daga ido ta kalli titi. Tabb wannan wace irin mutum ce haka,na faɗa a raina. 💎*sameemah a madubin gani*💎 Ina kallonsa yana min kallon gefen ido lokacin da yah kama hanyar barin cikin gari,nasan dan yaga mai zancene koh yah fuskata zata nuna. Bai san duk maganar da suke shida saleemah ina jinsu ba,dan tundaga dakina ina jin duk abinda suke fada,saidai idan ban ga damar jin abinda za'a ce ba,ta wannan ma nasan nisan jin maganata yah fi na sauran mutane duk da bansan su ya suke jiba. Lokacin dana ji mai yaca nayi niyyar idan yazo nace bazanjeba,amma kuma ta wani bangarena na zuciyata yace na bishi mutafi dannaga mai ita saleemah zatayi. Har muka isa garin bayan azahar babu wanda yayi magana nidashi,a bakin wani katafaren gida yah tsaya,wanda tundaga bakin kofar gidan mutum yasan nairah tana kuka a ciki. Harabar gidan an kawatashi lokacin da muka shiga,da alamun a wajen za'ayi walimar da mukazo dominta,lallai mutane ma,yanzu haka kawai na bata lokacina tundaga wani gari nazo waje dan walima,kawai dan ace nazo?. D'aki guda aka kaini domin na huta na kuma yi sallah na ci abinci,saidai iyah cin abincin nayi da kuma hutawar. A wajen taronma bamu wani dade ba muka juyo da niyyar komowa gida,saboda tafiyar hanya,babu yanda abokinnasa bayyi dashi mu kwana ba amma yace yanada aikin da zayyi washagari. Lokacin da muka dawo gidan yayi tsitt kowa yayi bacci,muna zuwa yah shige dainsa koh magana bayyiminba,nima na wuce nawa dakin,dan daga ganin yanayinsa ba karamin gajiyah yayi ba,saidai dauriyah kawai. Sanda na shiga daki ban yi niyyar kwanciya ba,dan ko alamun wata gajiyah banjiba saboda nasan jikinnawa yasha banban dana sauran bil'adama. Har nayi shirin zuwa dubo su bingo amma kuma dana leka window sai naga dare yayi sosai. Dole na ha kura badan nasoba,saboda tunda muka shigo nakejin kaman wani abu yasamesu,da kyar na daure na kwanta akan zuwa gobe naga yamda suka yini. Da safe kuwa tun kafin nayi komai na fita wajen su,da kayan baccima a jikina gyale kawai na yafa. Ina zuwa wajen naga reza a kwance,yayinda shikuma bingo yake kwance a gabanta yah tsura mata ido. Karisawa nayi inda suke,mai zan gani........! A kwance take tana nishi,duk jikinta zanen bulala ne raɗa raɗa,sai jini yakeyi. Tabdijan,lallai an tabo rina a kaba,tambayar bingo nayi akan wanene yayi mata haka?. Jan rigata yakeyi yana tafiya har zuwa inda Samuel yake zaune yana jiran kofah,haushi ya fara a gabansa ,shikuma dayaga haka sai dauki dutsi ya zefeshi dashi. Duk abinda suke na ina kallonsu daga nesa,dana cije fatar bakina saida tah fashe dan bakin ciki,babi abinda ake fada a cikin kaina sai irin kalar hukuncin dazan yiwa Samuel ko zan huce haushin danake ji. Bingone yadawo inda nake said kuma yayi cikin gidan yana min alamar na biyoshi. Ina cikin hakane Yaseer yazo wucewa,wani sojane sabon zuwa wanda nake haduwa dashi a wajen training can Bori camp Idan Naje kallonsa. Bayan mun gaisane na tambayeshi tareda cewa, "Yaseer Akwai abinda zakayi ne?" "Ahah aunty,Akwai matsala ne?" "Eh toh zaka dan kulamin da wata karyane anyi mata duka kuma tana da ciki,akwai abinda zanyi kafin na dawo" Muna magana har mukaje inda reza take,shima kansa saida ya tausaya mata,amma ina famasa wanda yayi yace zai aikata,dan suma mugunta yake musu sosai,a raina naji dadin wannan labarin,koba komai zan samu damar hukun tashi da dalili mai karfi. Komawa nayi inda bingo yake,muna tafe har bakin dakin saleema,karkada mun jela yayi a bakin kofar dakin kafin yah juya yah fita. Kama Baki nayi ina jijjiga kai,wato harda itah a wannan aikin kenan dan taga jiyah bana nan nabi sameer koh,sai yanzu na tabbatar babu abinda suka mata kawai zallan mugunta ce,zakuwa taga yanda ake mugunta akanta. Komawa nayi inda yaseer yake na aikeshi ya siyomim magani,nikuma nasaka musu abinci suka,duk da yanda take ciki amma hakan bai hanata cin abinci dayawaba abinka da dabba. Lokacin dana koma falon saleema ta fito,hankalinta kwance kaman babu abinda tah aikata,dan ko wanka daga gani batayiba daga ita said kayan bacci,cuna min baki tayi da muka hada ido,nikuwa Murmushin gefen baki nayimata,da tasanni sosai da zata gano mai Murmushin yake nufi,saidai kash bata masaniyah akan hakan. Lokacin da ta koma dakintane naji alamar sallamar yaseer a waje,fita nayi na karbi sakona,maganin kam karba yayi yace zai bata,sannan zai dunga kulada ita,godiya nayi masa bayan na bashi maganin. Komawa dakina nayi tukun kafin na fito na nufi dakin saleeman. Babu kowa a dakin sai karar ruwa a bandaki,hakan ya tabbatarmin da cewa tana wanka,zama nayi a hankali kwance na jirata har ta fito. Lokacin data fito turus tayi a bakin kofar bandakin ganina a cikin dakinnata,abinda bata taba tsammata,shiru tayi kaman mai nazari kafim kuma ta matso zuwa ainihin cikin dakin. Ta shi nay I daga bakin gadon tareda nufar inda take,duk da akwai tsoro cikin idonta amma hakan bai hanata tattaro jarumta ta yafawa kanta ba ta hanyar cewa, "Me kike min a dakina kuma da wannan lokacin,akwai abinda kike bukata ne" "Ba abinda nake bukata,kawai dai nazo yimiki tambaya ne,shin mai reza tayi miki kikayi mata wannan dukan lokacin da bananan jiyah" "Au hhhhhh dama akan wannan dabbar ne kike wannan tambayar,ai said ki fadamin tun wuri,baki sakani tunanin wani abu ne ya kawoki ba" "Duka na daketa kuma ko gaban waye zance na daketa,dama ina jin haushinta kuma tashigo har cikin falona,dan rashin mutunci,ko kuliya bazan yadda da zamanta cikin gidana ba bare kuma kare kazami,dan haka shiyasa na kamata nasa Samuel ya rike min itah na dakata,idan da abinda zaki iyah yi kiyi akan hakan" "Oh haka kikace a ko gaban waye zakice ke kika daketa kuma ayi duk abinda za'ayi?,zakuwa kiga abinda mai itah zatayi yanzunnan,dan ko kasa da sama zata a hade a lokacinnan said nayi miki ninkin abinda kikayi mata,dama ina taraki da rainin dakike min,ko kina tunanin dan nazo garin da ubanki yake shikennan bazan iyah miki komaiba koh?" Ina gama fadar hakan na bita da kyawawan maruka har gida biyu a ta kowanne kumatunta,fadawa kan gadonta tayi tanna ihu,hakan bai dameni ba sai ma komawa danayu nasaka key a kofar sannan na dauko bulalata dana ajiye a wajen. Jijjiga ta nayi kafin na fincike towel din dayake jikinta na zuba mata itah gadon bayanta iyah karfina,murmushi nayi danaga ta shigeta sosai, ɗagawa na sake yi na zuba mata,a na ukunne naji bugun kofar tata da alamar sameer ne dannaji muryarsa........ Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎19~20💎 Duk da bugun kofar dayake yi kaman zai balle kofar hakan bai hanani cigaba da zambada mata ba,har saida naga bata motsi sosai,fatar jikinta kuwa duk ta yi ja sai zubar da jini takeyi abinka da Wanda hutu yah ratsashi sosai. Shima bani na bude kofarba kallonsa kawai nayi a gabana ya fizge bulalar da take hannuna kafin yah wanka min mari. KO kusa banji zafin marinba saima murmushi danayi masa ganin aika aikar danaso yi ta tabbata raina yayi fari tass kaman farin dutsi. Karisawa inda take yayi da sauri yana dagata a hannunsa,wata harara ya aikamin kafin yah fice zuwa wajen da motarsa take. Nikuwa ɗaga kafaɗata nayi ko a jikina,na rama abinda naga bazan iya bariba yah tafi a banza. 💎*sameer a madubin gani*💎 Lokacin dana dauki saleema a hannu na na nufi motata ko motsi bata yi,lokaci zuwa lokaci nake leka ta a bayan mota inda na ajiyeta, amma koh motsi batayiba har muka isa asibiti. A hanya na kira hajiya fatima nake fadaamta,dan bazan fara kiran alhaji musa a lokacin ba,nasan abin bazai tafi da kyau ba. Kusan tare muka isa da itah dayake dama ta fita anguwa tana kusa da asibitin. Har nursing suka karbeta suka turata a keken asibitin bata tambayeni mai yah faruba,saida muka ga anshiga da itah an fara magance ciwukan jikinta sannan an saka mata ruwa tukunna muka zauna,kallona tayi cikin kwanciyar hankali kafin tace, "Menene yah faru haka sameer?" Bata labarin abinda yah faru kawai nayi mata,shima wanda nasani kadai,na manta key din drawer tah ta office,ina dawowa naji kukan saleemah a dakinta,dana buga kofar kuma najita a rufe,jijjiga wa na cigaba dayi,amma ganin bazata budeba ne yasa na tafi dakina na nemo spare key na bude dakin. Nan nasamu sameemah a tsaye a bakin gadon tana ta dukanta kaman an aikota. Numfasawa tayi bayan taji abinda yake faruwa,saidai abinda yafito daga bakin hajiyah fatima ne ya bani mamaki inda tace, "Amma yakamata a bincika dan aji mai tayi mata,idam babu toh inaga ita ma tana da matsala yakamata a binciki lafiyarta,dan abinda takeyi bana mai lafiyah bane,dannaso gano hakan lokacin da muke magana da itah a dakina,sannan kaman tana cikin kadaici sosai" Kallonta nake da alamar mamaki,anyah kuwa ana samun irin wannan matan,wata tayiwa ƴarki irin wannan dukan amma kina kokarin sanin ko tana da lafiyah,ba ta ma yattaki kike ba. Muna cikin hakanne alhaji musa yah iso wajen cikin rawar jiki dan yaji ance tana asibiti. Tambayar abinda yah fari yafarsyi cikin daga murya,hajiyah fatima ce ta kamo hannunsa tareda bashi labarin abinda yah faru cikin kwanciyar hankali,saidai bata kai ga gama fada masa ba ya tashi da sauri yana danna waya yana fadin. "Ina baza'a yiyu ba,ni dama tundaga farko banso zaman wanna matar kusa da ƴataba,kece kika nace sai an bi ta mijinta ,toh gashi nan tana neman kashe mana yarinya a aikim banza,kuma billahillazi babu mai hanani hukuntata a cikin garinnan . Kai kuma ka shiryah zan yimana booking jirgi in anjima duk zamu tafi mu uku harda itah muje ayi jinyarta dan nan ba abinda suka iyah,awa guda amma har yanzu bata koh farfaɗoba" Yana gama faɗan hakan yah amsa kiran daya shigo cikin wayar,dsyake a handsfree take kana jin irin girmamawar da na ɗayah gefen yakeyiwa alhaji musan. "Kai ba wata doguwar magana nakeson muyi ba,inaso ka tura sojoji suje gidan sameer su ɗauko wata mai laifi,kuma so nake ku kaita ɗakin horo dayake a bakin daki" Daga can mutumin ya amsa da cewa an gama ranka yah dade. Duk da cewar abinda sameemah tah aikata bai daceba,saidai hukuncin akamota har cikin gidana kuma ɗakin dayake nata na aurena sainaji abin bayyimin daɗiba,koba komai yakamata a barni naji abinda yake faruwa,ba kawai akama matata a saka cikim cell,kuma sannan a saka gardawa suyi tah dukanta. Sannan wani abunma wai saina ajiye aikina na bisu wajen jinyarta a wata ƙasa daban. Haka muka cigaba da zama amma shiru babu alamar zata farka,anan muka kwana har washagsri kafin na tafi gida zuwa dauko kayana wanda zamu tafi can kasar Germany inda za'ayi mata maganin. Banda kudi baya yiwa wasu wahalar cirewa menene abin tafiyah wata kasar,ita wacce aka kai wajen horo na kasa (dungeon)ai saita fita shan wahala ba kadan ba. Ina isowa da mota naga nashiga cikin gidan,fayau naga falon bakowa sannan kuma babu alamar motsin mutum,dan farouq yana wajen nanny sa ita kuma zuhra tana wajen hajiyah fatima. Dakin sameemah na leka,ina tuna yanda nake ganinta idan na shigo dakin,duk da wsni lokacin bata kulani har na fita. Dakina na nufah na hada kayana,har na zo shiga mota sai kuma na nufi hanyar garden dannaga wulgawar mutum,yaseer nasamu sabon sojan da bai dade da zuwaba,abinne yabani mamaki mai yake a wannan yankin shida yake zaune a cikin bori camp. Turus mukayi dashi yana shirin fitowa,dauke kansa yayi yana kkkarin wucewa,hannunsa dauke da karyar sameemah wanda take ta numfashi dakyar,jikinta duk zanen bulala. Tambayarsa nayi menene yasameta,kallonta yayi tana hannunsa kafin yace, "Nima ban Sabina,kawai jiya naga anty sameemah tana dubata ganin irin abinda akayi mata,daga nan ta ce nasayo mata maganin dazai warkar ciwon sannan na sayo mata bulala dorina mai kai biyu. Jiya kuma da azahar tacemin idan naji lbarin an kamata to na kulu mata da karnukanta kafin ta fito" Hanya nabashi ya wuce da itah dayan ma yana biye dashi har suk bar wajen. Shiru nayi ina tunani har na isa inda cell din da samemah take,wato karenta ta,ramawa dukan da saleemah tayi masa,kuma tasan za'a daure ta amma tsyi hakan,wannan wace irin macece ne?. Da kyar mai kulada wajen yabarni na shiga wajen dan nafishi matsayine da nasan bazan samu kallonta ba. A zaune na sameta an daure hannun ta baya,rigarta ta wani wajen duk ta yage saboda duka,hakika na tausaya mata ganin akan ceton kare ta saka rayuwarta a haka. Karisawa nayi har inda take na tsugunna,dago kai tayi tah kalleni kafin ta kawar da kanta. "Yanzu abinda kikaga yafi kenan,kisaka rayuwarki a haka saboda karya?" "Hakan jai shafeka na ni kadai ya shafa,sannan bannemi taimakonka akan hakan ba,naga zan iyah shiyasa na yi,kuma da kake zancen na saka rayuwata a haka dan kare,ta cancantane wani ko da kudi yasakani bazanyiba,saboda suma zasuyi min abinda yafi haka idan ina bukata. Karka damu dani ka tafi jinyar matarka yafi ka tsaya kana bata lokacinka annan" Rasa ma abinda zance nayi lokacin da ta gama maganarta,tashi kawai nayi na fita ina fadin allah yah kyauta a raina. Lokacin dana je har an gama sakata a jirgi dan haka shiga mukayi kawai muka tafi,nidai da da yadda zanyi da bazan bisu ba,saidai ko mai zanyi nasan alhaji Musa bazai fahimtaba,illah ma yace da saka hannuna akan hakan. 💎*sameemah a madubin gani*💎 Ina kallonsa lokacin daya fita,haka kawai na tsinci kaina dajin haushin yanda bai tambayi dalili ba saima kokarin gani laifina dayake yi,nasan a halin danake ciki da zuciyar mace ce dani da saina rushe da kuka,saidai babu yamda zanyi saidai na hadiye bakincikina kawai. Bai dade da fita ba wani yah shigo da abinci a hannunsa a wani kwano irinna bawa dabbobi abinci. Ina kallonsa har yah ajiye abincin,maimakon yah fita sai yah matso kusa dani yana tanɗe baki,hmmm maza wani lokacin suna bani mamaki dole sai mutum yasakawa ransa taba abinda ba nasa ba. Hannunsa yah miko har yakusa taba cinyah ta na kalleshi. "Karka kuskura wannan kazamin hannunaka ya taba cinyata in kanason zama da lafiyarka,idan kuma ba haka na ka gwada" Baiji gargadin danayi masa ba sai ma kara matso da hannunsa dayake kokarin yi. Shiru nayi masa har yakai hannunsa yagama shafa cinyata kafin yah dauke, "Yanzu kaji dadi daka taba cinyata koh?,saidai inaso na sanar maka cewa,bazaka kara yin komai da hannunba,domin babu abinda zaiso hannunka yah karisa kusa da shi ko kuma abinsa " Ina gama fadin hakan na kalli hannunsa wanda shima hannun yake kallo. Wasu kurajene suke bullowa daga hannunnasa cikin kankanin lokaci,ihu yafara yana jijjiga hannun,yayinda nikuma nake Murmushi da ganinsa cikin yanayin hakan. Fita yayi da sauri yana ihu,saidai bashida ikon fadan abinda na aikata masa,sannan duk maganin da zayyi bazai warke ba. A haka na cigaba da zama a cikin wajwn badan bazan iyah fitaba sai dan ban ra'ayin hakan,masu yimin bulala goma kuwa kullum sai sunzo sun yimin da safe kafin su tafi. Yanayin halittar da jikina yake nunawa kullum kara gaba yakeyi,dan yanzu ina iya control din warkewar da ciwon dayake jikina zayyi,sai sun gama yimin dukan da ransu yakeso,nikuma sai na bari idan sun fita saina sake jikina wajen ya koma yamda yake,sannan nakan jiyo hayaninyar mutane daga nesa,sannan kullum inajin muryoyin wasu halittu suna kara yawa a cikin kokon raina. Yaseer kuwa ko yaushe yakan zo yah fadamin halin da karnukana suke cikin,watarana yacemin reza ta haifi ƴaƴa guda hudu,biyu sun mutu saura biyu,sannan itama ta mutu,tabbas naji haushin hakan amma raina bai baciba kaman yamda akayi mata wannan duian,saboda yanzu zuciyata ta saba da rashin wanda ta fiso,tunda ummah ta ta rasu na rayu to zan iyah rasa kowama a duniya ta. Duk da bandamu da mutuwarta ba saidai kuma wata zuciyar tana cin na fita kodan na yiwa ƴaƴan ta rainbow da duk cikin barrack dinnan babu wani kare da akayiwa irin horon. Can cikin darene na fara jin karar mota tun daga get dinner farko na shigowa wajen,daga yanda motar take tafiyah,sannan kuma da karar bindiga danaji yatabbatarmin da koma wanene bada zaman lafiyah ya zoba. Waigawa gefena nayi naga babu kowa,shikansa mai gadin bakin kofar bacci yake irin mai nauyinnan,dan yacika wajen da minshari shi kadai. Duba sarkar dake hannuna nayi domin gano inda zan cinke ta,zuwa yanzu na fara jin hayaniyar mutane da kuma harbin bindiga,duk mutanen da zasu shigo har cikin barrack su kawo hari gaskiyah abin ba karami bane dan harda kukan yara da mata nakeji. Zan salary hannuna nayi saida ta cinke da karfin gaske,nufar bakin kofar nayi na balle ta,ban damu da tashin mai gadinba kawai bindigar da take gefensa na dauka,sai a sannan yatashi yana dawurwuri cikin yanayin gaga'a. Kasan bindigar na kwada masa a Kansas yah koma baccin dole wato suma,saboda idan na tsaya batamin lokaci zayyi. Gyara zaman bindigar nayi na fita da sauri,babu kowa a hanyar danake da alamar duk duna gidansu,tafiya nake cikin sanda har nashiga ainihin cikin bori camp inda yawancin gidajen ƙanannan sojoji yake,da kuma ɗaliban da suka karatu a army acadamy . Hasken fitilar mutanen na fara gani daga dan nesa kadan,har nayi niyyar karisawa saikuma na koma zuwa gidan major Nazeer wanda shine akabawa oder kamani kuma shine babba a yanzu tunda sauran basanan duka. Kallon rigar jikina nayi wanda bazata yimin dadin tafiya ba a haka,domin riga tace ta bacci tun wanda aka kaini cikin cell din da ita. Kamata nayi na yage kasan ta ya zamo bata gi iyah gwiwa ta ba,sauran kuma na daure a kunkumina,gyara zaman bindigar nayi na nufi hanyar headquarter inda gidan mu muma yake,tum daha bakin kofar na gano wani mutum sanye da bakin kaya rike da bindiga a hannunsa,hakanne ya tabbatarmin da cewa suna cikin wajen basu fita ba. Tafiyar nake a jikin inuwar dare cikin kwarewata a fannin sanɗa,har na kariso inda yake bai saniba,sai jin dukan bindiga da yayi a kansa,saurin murde masa wuyah irin wanda bazai mutuba amma kuma zai iya yin sati a kwance bai tashi ba. Shiga nayi cikin harabar wajen babu alamar tsoro a tattare dani,dannasan duk cikinsu babu mai iya ja dani,saidai idan da ayar Qur'an yake tafe,amma bada bingida ba kam. A hangar shigata cikin gidan ma saida na hadu da wani a bakin kofa,shikam ya kulada zuwana saboda babu damar na bi ta bayansa a yamda yake tsaye,kokuwa muka fara na bugashi da jikin tiles din wajen, haka na barshi dan baya bukatar karya wuya tunda kashin bayansa yah karye. Sashen gidanmu babu haske ko kadan saboda ba kowa a ciki,iyah sashen major nazeer ne kawai da wuta,itama ba sosai ba dan daki dayane kawai yake da wutar. Hanyar gidan na nufah cikin tafiyah na mai yin fako,ban hadu da kowa ba tun daga wancan guda biyun har na je kusa da gidannasa. Wani window nasamu mai matsakaicin girma,a fuska bazai isa na wiceba,amma tunda nayi kaurin suna wajen iyah shiga gidan mutane na yashe kudi a baya wanann bazai bani wahala ba. Ina dira cikin wajen naga ashe kitchen ne inda na shigo.ƙoƙarin bude ƙofar na fara cikin dabara yamda baza'a gane ba ko jin motsin hakan. Cikin sa'a kuwa ƙofar bata da kara,har na fito daga kitchen din babu wanda ya ji,wani corridor na bi wanda zai kaini inda nakejin hayaniyar,dan sake dukkma karfin ji na kunnena nayi domim gano ta ina numfashi yake fitowa da kuma motsi ko bugun zuciyah,dan a cikin satinnan kunne yafara daukomin sautin bugun zuciyar duk wani abu mai rai dayazo wucewa ta kusa dani. Dakin da na hango da haske a cikin sa lokacin ina waje,ta nan nake jiyo alamun rayukan mutane a ciki. Window dakin na fara lekawa dan ganin mai yake faruwa a ciki,yara ne mata guda biyu bazasu wuce shekara sha biyu zuwa sha biyarba,dukkan su wasu mutane sun saka musu bindiga a kunne,da alamun wani abu suke nema,sannan kuma da yaran sukeyiwa major nazeer barazana,dan yana gefe yayi kneel down idonsa yayi jawur,matarsa kuma tana gefensa said sheshshekar kuka takeyi. Kofar wajen na nufah ina gyara rikon bindigar dake hannuna. Saida na saita tukunna kafin na afka cikin dakin da karfi cikin zafin nama wanda na dade banyi aiki da shiba. Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎21~22💎 Ina Shiga ban Bata lokaci ba na saita bindigata a kan ogannasu wanda yake zaune a bakin gado yah rude fuskarsa da wani bakin kyalle,kallonsu nayi ina cewa, "Koh Ku dauke bindigarku daga kan yarannan ko kuma yamzu ku debi kwakwalwarsa a kasa" Har sunyi niyyar ajiye bindigarsu naji yah buge bindigar dake hannuna da karfi yah rike wuyana tareda manna ni da bangon dakin dayake kusanmu,matsewar dayayimin nasan da ni mutumce kaman saura da idan ban mutuba toh zan shiga coma, "Ke yar gida uban waye da namiji bazai iyah tunkara ta ba bare ke figyagygyiya dake?" Muryarsa kadai ta isa ta bawa mutum tsoro yanda take fidda amo,murmushi nayi masa kafin nace, "niba yar uban kowa bace saboda ba da matsayin uban kowa nake taka rawata ba,sannan babu mai sakani koh hanani sai na ga dama" Nima nasa wuyan narike kaman yanda na rike nawa,wani yunkuri nayi muka juyah yazamo shine a jikin bangon ina rike da wuyansa sabanin da shine yake rike da nawa wuyan. Kakarin amai yake yanda na rike masa maƙogaro a hannuna gam,kallon idonsa nake wanda yayi ja saboda rikona, "Yanzu waye figyagygye tsakanin ni dakai,*bar raina allura karfece*" Saida na tabbatar yayi laushi kafin na jefar dashi a tsakar dakin,kallon wanda suka dora bindiga akan yaran nayi amma sai suka kara manna bindigar jikinsu yah fara karkarwa,barazana suke min amma ban fasa isa inda sukeba,har saida dayah yah fara nuna ni da bindigar,banyi tunanin zai harba ba amma saijin karar shigar bullet nayi a kafada ta ta hagun. Karar iskar shigarsa ce tasa na fada can gefe sannna na bugu da gado,gsnin hakanne yasa ogan yayi saurin tashi yana rike da makogaransa suka fice da sauri tareda sauran yarannsa,matarce tayi saurin matsowa kusadani amma na dakatar da itah,tareda cewa, "Ki dauke yaranki tukunna,sune suke da bukatarki bani ba a halin yanzu" Tashi nayi na fita daga dakin ina rike da inda aka harbenin,saidai ina fita waje na jefar da bullet din nayi hanyar gidanmu. Shikuwa dama major nazeer tun sanda suka fita ya bi bayansu da guda lokacin da ya dauki bindigar dana shiga da itah. Ina Shiga Gidan ban same KO inaba sai dakin sameer,dayake dama akwai key din kowanne daki a jikin na kofar shiga gidan ,wanda aka bawa kows idan ya dawo gida zai shiga. Kunna wutar dakim nayi kafin na bude drawer kayansa,cikin sa'a kuwa na samu abinda nake nema wato kayan aikinsa,dauka nayi nasaka cikin sauri sauri,duba gefen kayannayi na dauko bindgarsa ita ma a wajen kayan amma a kasansu. Gyara zaman bullet dinnayi,harda Murmushina danajita a cike da bullet gata kuma dama favorite ɗina kenan. Kallon kaina nayi a madubinsa nayi murmushi danna fito sak raudah abdulsalma dina,saiya tuna min abu dayawa. Fitowa nayi ina rataye da bindigar har haraba headquarter,anan na samu su major nazeer suna ta magana,tsitt sukayi dasuka ganni na iso wajen,musamman yanda nake tafiya kaman mamallakin kayan,tun kafin major nazeer yayi magana nace, "Mai ake baza'abi bayansu ba har yanzu karfe hudu na asuba yah kusa" Wani ne daga cikin sojojin yace, "Eh wato ranki yadade ogah ne yace bazaiyiyu a bisu yanzuba saboda ba'asan mai suke dauke dashiba" "Dole sai an bisu kuma yanzunnan,natsani naga mata suna tsoro bare maza,saboda shi iyalansa sunanan kalau ko?,na wasu ko oho,yamzu za'a bi bayansu kuma babu dawowa sai an karbo matan dasuka dauka,su basu ji tsoron zuwa daukar abinka ba sai kaine zakaji kunyar zuwa karbo naka abin" Ina gama fadan hakan na nemi a kirawomin hackers da kuma tracker,suma zuwa sukayi gaba,hadasu nayi a mota dayah nikuma na shiga tsakiyarsu,saboda akwai wani abu danakeson yi a game da wanda suka tafin,shima major nazeer dayaga mun shiga mota mun fara tafiya sai yah hau mota suka biyimu a baya. Wani abu na hada a system din da sauri sai ga hoton inda za'a saka yatsu yah fito. Nawa hannun na dora sannan nayi search dinsa a area inda muka tafiya,cikin sa'a kuwa saiga hoton yatsan yah fito wanda yake wuyan shugabannasu a area wajen. Kara gudu mukayi su major nazeer suna bin mu a baya har muka fita daga ainihin cikin mutane,wani jeji muka shiga inda hoton yake nunawa,har muka,zo inda mota bazata wuceba dole saidai mu tsaya a mushiga da kafa. Ana zuwa wajen major nazeer yah daga hannu akan nida wanda suke tracking mu tsayah a wajen,harda ajiye mana soja guda dayah yah kulada mu,tunda nake na dade banyi dariyah ba sai a wannan lokacin,tashi daya kuma na murtuke fuska.kallona yake cike da mamaki ganin a halin da ake ciki hakan ma ina mace amma kuma bai girgijani ba. Gyara zaman bindigar sameer nayi a hannuna kafin na wuce gaba,har shidin ma na barshi a baya na fara kutsawa cikin jejin,har yah bude baki zayyi magana nayi masa alama da yatsana akan yayi shiru kawai ya biyoni,bai yi musuba yah biyoni a baya tareda sauran sojojin, muna tafiyah muna duba inda zanen hannuna yake har muka zo bakin wani gida wanda akayi shi da ya jingar ciyawa. A Hankali muka cigaba da sanda har muka iso bakin kofar gidan. Wasu nayiwa alama da hannuna akan su zagaya,wasu kuma su saita taryar wanda zai fito,wasu kuma su yi shirin afakawa,a masu afakawar harda ni da kuma major nazeer,ina kallonsa yana min kallon mamaki ganin yanda nake bada umarni cikin kwarewa. Kirga numbobi mukayi zuwa biyar kafin muka shiga da sauri. Wayam muka gani babu kowa da alamun ansan da zuwammu. Kara naji tana tahowar makami hakan yasa nayi saurin jan su major nazeer muka fadi a kasa,kifiyoyin kuma suka wuce a iska,kallona yake da taya akayi na sani,saidai ba lokacin tambaya bane yanzu,alamar karar mutane naji wanda idan an rufe bakin mutum take fita,nuna musu nayi tareda cewa, "A can hanyar suke kuma ba a cikim gidannan bane saidai babu damar mu tashi tsaye saidai muyi rarrafe" Basuyumim musuba haka muka fara rarrafawa har muka fita ta wata kofa a cikin gidan,wani jejin ne yayimana salamma irin na farko,kafin mu mike daga rarrafen muka ji karar wani abu a kawunan mu giffff,ina kallon sanda suka suma nima sai nayi suman karya domin na samu damar yin plan. Suna ganin mun suma suka fara fitowa daga inda suke boye,ina kallon su ta gefen ido har suka kaimu wani waje inda sauran yara da matan suke. Suna fita na bude idona, tashi nayi hannuna a daure har na isa wajen wata mace,wanda da alama tafi sauran jarumta dan ita bata kuka kaman yanda sukeyi,sunkuyawa nayi har zuwa inda igiyar dake hannunta take,wata karamar reza na fitar daga bakina na fara yanke igiyar a hankali har na yi nasarar hakan,tana ganin na kunceta ta daga hannun tana kallo,suma sauram mutanen kallon suke da mamaki. Juya mata baya nayi da niyyar ta kwance min,cikin sauri hannunta yana rawa ta gama ciremin kafin tafara cirewa sauran mutanen da suke wajen, Nikuwa ban dauki bindiga ba wani kulke na dauka mai fadi na nufi wajen da barayin suke. Duk wanda muka hadu dashi saina saita murfin keyarsa nake sauke masa har muka zo inda ogan yake kwance a kan gadon kara an nannaɗe masa kai inda na bugashi a gidan major nazeer. Kallonsa nake shima ni yake kallo da alama yagane ni,jefar da kulkennayi wanda yayi ja saboda jinin dayake jikinsa,tsalle nayi na hau kansa tareda kafa masa hakorana a wuyansa,saida na dade kafin na daga. Murya na fara ji a cikim kaina ana shewa tareda cewa saura daya takk. Kwata kwata na manta sai a sannnan na tuna saurana kaiwa biyu na kasance ɗaya daga cikinsu,kuma konaso zama da mutane a lokacin bazan iyaba,nadama ce ta zomin dan yanzu nasan control din danke kokarin yi zayyimin wuyah a yanzu dan a kowanne lokaci dada zama hatsari nake ga mutanen da suke kewaye dani. Ina cikin tunaninne naji sautin tafiyar mutane,saurin goge bakina nayi tareda ture gawar mutumin daga kan gadon dan kar aga hoton hakorana a kan wuyansa. Motocin da muka zo dasu har da na barayin muka hau domin komawa gida,kowa sai murna yake,nidai jinsu nake kawai dan na auka cikin kogon tunanin wannan juyayyar rayuwartawa. Har muka isa na wuce gida babu wanda nakula a cikin masu yimin magana da tambayoyi dan bata su nakeba a lokacin. Burina nayi wanka na kwanta sannan kuma nayi tunanin a wane mataki nake na rsyuwa a kusa da mutane. Washagari da safe ko nace da hantsi dan sannan na nayi wanka na karyah saiga yaseer ya kawomin kwikwiyon da reza ta haifa,bakakene wuluk babu fari a jiknsu kuma gasu bulbul sunyi wayo,godiyah nayi masa na karbesu na kaisu garden inda iyayensu suke tun farko,dama bingone shikuwa yanzu ba zama yaje ba tunda yake zuwa wajen karen sojoji. Muna zaune a garden din wani soja yazo wajen,saida yah saramim alamar jinjina kafin yah faɗi abimda yake tafe dashi. "Ran shugaba yah dade,major nazeer yana son ganinki a office dinsa dake can headquarter idan kina da lokacin hakan" Jim ina Tunani kafin nace masa yaje ina zuwa,juyawa yayi yah tafi tunda yah isar da sakon dayake dauke dashi. Kallon yaseer nayi wanda shima ni yake kallo,dan murmushi yayi kafin yace, "Kin cancanci fiyeda jinjina a wajen sojojin gidannan anty,domin kin saka kanki a kasada a cikin dare guda kika ceto musu da iyalansu,abinda su kansu basuda kwarin gwiwar hakan saida kika nufar dasu tukunna" Uhm kawai nace kafin na koma dakina domin shiryawa zuwa kiran. Riga da wando nasaka amma rigar zuwa gwiwa sai gyalen dana yane kaina dashi. Duk kayan baƙaƙene sai hakan yah fito da farin fatata a cikin kayan. Lokacin dana isa office din da sauri sojojin dake tsaron kofar suka bani hanya na wuce,kafin ma nayi magana. A zaune na sameshi akan kujerarsa,yana kallona yah tashi tsaye tareda nunamin kujera yana murmushi,ƙara murtuke fuska nayi saboda kar ya kawomin wargi ma idan yaga nayi murmushi. "Barkanki da zuwa,gaskiyah naji dadin amsa gayyata ta da kikayi,ba komaine yasa na kiraki ba saidan inaso naji shin a ina kika koyi salon fada da kuma aiki irinna sojoji haka,bayan a yamda muka san tarihi baki taba zuwa wajen sojojiba" "A inda ake koya mana na koya,ko iya nan ake koyon aikin sojoji kawai,a ganina banyi laifiba bare a tsaya ana tuhumata koh" Shiru yayi dajin amsata cikin izzah,can kuma sai yace, "Banyi niyyar tuhumar ki ba sameemah,kawai abinne yabani mamaki,sannan kuma abinda kikayi kowa yagani ,toh idan aka tambayeni mai kikeso nace,yanayin aikine yazo da hakan,idam ma bakyaso a sani zamu iya boye hakan" Tashi nayi na tsaya tareda zefa masa takardun shedata ta brazil wanda na karba a matsayin Raudah Abdulsalam. Kallona yake baki buɗe kafin shima yah tashi tsaye yana kallona, " mai kuma takardun wannan jarumar yake a wajen ki,ina dai wacce tah lashe gasar harbi da kuma hacking a akayi a kasar Brazil" "Mtsww to mai zayyyi a wajena idan ba nawa bane,haka kawai zata dauki takardu ta banine,idonka baiga hoton da kyau bane,kawai badda fuska nayi ɗan kaɗan, sannan karka tambayeni ya akayi naje ko taya naje,dan ba faɗamaka zanyi ba,wannan ma dan nasan zaka dameni ne da surutu" Takarduna nayi na fice daga office dinnasa. Yau anyi sati da harin da aka kawo barrack din,kowa yah ɗan fara mantawa,saidai ganin girmana a idon mutane kullum kara hau hawa yakeyi,dan yanzu har matan sojojin zuwa suke har gidana su gaisheni,duk da ba magana nake yi musu sosai ba amma hakan bai damesu ba,dan sun kula halina ne hakan. Karnukan da reza ta mutu ta bari kuwa,wanda nayi musu suna Blacky da kuma Darky,sun tashi cikin girma na musamman,kasancewar ubansu dama ba breed karnukan kasarnan bane, Training nake yi musu na musamman,tun suna shan wahala su kasa motsi har suka saba yazamana yah bi jikinsu. A cikin Satinne major nazeer yah turo request daga office dinsa kan cewar na dunga bawa dalibansu train din harbin bindiga sannan na yi masu koyon na'ura ma,kin amincewa nayi daga farko,dan har saida turo kusan sau uku kafin na karba,shima sai da naga dama tukunna,ranar asabar na tura masa da sign din na yadda,sannan kuma ran monday zan fara zuwa. Ran lahadi major nazeer yah aikomin da kayan mai horo,saidai daga gani dinkasu akayi dan kayan irinna matane,sannan kuma da karamin hijabi a ciki. Tun karfe bakwai na tashi nayi break fast naci na koshi,dan yanzu nikadai ce a cikin gidan,sai nanny din farouq wanda na aika ta dawo,saboda tun lokacin daya zo gidan yaki komawa gidan hajiyah fatima gun mai aikinta,ganin hakanne yasa nace su dawo nan shida itah su zauna,tunda a kwai wani dakin a wajen. A kitchen din nasmaeshi yana tsaye,har na wuceshi sai kuma nadawo na ce, "Menene naganka a nan wajen da wannan lokacin,akwai abinda kake bukata ne?" "Eh aunty,uncle have muje makaranta da wuri yau akwai abinda za'ayi,kuma naga lokaci ya kusa gashin anty nanny bata tashiba" Kama hannunsa nayi muka shiga dakina nayi masa wanka da brush kafin na aikeshi yah dakko kayan uniform din,da sauri yah tafi yana murna. Kayan na saka masa kafin na zuba masa abinci yaci,na saka masa wani a cikin basket dinsa. Tunda nafara sakawa yake tah murmushi ,lokacin dana bashi ma har yah tafi saida ya dawo da gudu yah rungumeni kafin yah juya da gudu yah fita wajen drivernsa. Yau daya a rayuwata naji wani shauki wanda ban taba jiba yah soki cikin kirjina,saurin rike wajen nayi ina dan sunkuyawa,tambayar kaina nayi mai hakan yake nufi?......... Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎23~24💎 Fitar da tunanin nayi a raina na wuce dakina damin nima nayi nawa shirin. Kayan sunyimin kyau sosai a raina naji dadi sosai,ganin nasake samun wani aikin a karo na biyu. Lokacin dan isa wajen da masu training din suke duk ansaka su cikin sahu na layi. Dama daga gani suna jiran isowata ne dan idon su duk akaina lokacin da major nazeer yah ke gabatar dani,shima ina kallon dan alamun girmamawa dayake min,wannan al'adar sojane nuna girma ga wanda yafika matsayi. Babu Bata lokaci muka fara abinda yah taramu wanda muka aiwatar dashi a wani fili na koyon harbin,dukkansu kowa ka ganshi yayi laushi kaman an yimasa duka,saboda aiki dani ba sassauci,kallon mugunta nayi musu kafin nace kadan ma kuka gani indai nice mai koya muku abu. Direct wajen masu koyon tracking da hacking na wuce bayan na gama da masu harbin,zasuje wani ma yah cigaba daga inda na tsaya . Sai wajen la'asar sukam muka tashi,domin aikin dana basu ba karami bane,kuma da gangan nayi musu hakan dan su san ba wasa ne yah kawosu ba. Ina is a gida na hada gumi shirkiff ,wanka nayi nasaka kananan kaya kafin dare kuma yayi nafara nasu blacky dan zuwa yanzu suma sunyiwa sauran karnukan barrack zaryah tun daga yanzu suna kanana,dan jikinsu haryah fara murdewa irin na karnukan manyan yan daba. Idan muka gama training kuma na barsu a jije su kwana suna maimaici,wanda bayyi ba kuma yakarbi hukunci mai tsanani,sannan bana barsu su saba da kowane mutum,daga ni sai yaseer,sannan abinci su koyaushe nama ne saidai a sarrafashi tah hanya daban yanda zai kara karfafa jikinsu. Fitowa nayi daga dakin na wuce kitchen na hado custard,dan bana bukatar abinci a lokacin,farouq ne yah ganni kasan cewar babu islamiya yau yana gida,mikamin kofi yayi yana min kallon dolly irinna yara idan suna son abu,karba nayi na zuba masa dam ba lallai na shanye shiba. Komawa falon mukayi muna kallo,wanda ni hankalina ma baya kai saboda duk cartoon ne,sai anyi abune yake taboni ya nuna min,ko banganeba to nake cemasa kawai. Muna nan zaune har aka kira magriba,kallonsa nayi nace, "Farouq tashi ka tafi masallaci an kira sallah maza" Cuna baki yayi bayason zuwa,amma yana kallon fuskata yah tashi da gudu yah fita zuwa masallacin. Jijjiga kaina nayi kawai bayan na kashe kallon,dan idan ban kasheba yazo yah gani bazai je lessons din dare ba yau. Kuruciyah da daɗi. Lokacin daya shigo gidan dakina ya shigo da gudu har yana tuntube,kallonsa nayi da takaici,badama baya son zama waje daya kullum cikin rigima yake. "Yanzu farouq bazaka tafi a hankaliba kaman ana binka a baya?" "Aunty yi hakuri,dama sauri nake karki tafi wajen su blacky kibarni tunda kince yau kam zanje koh?" Shiru kawai nayi ina tunani,kusantuwa ta da yaron kullum kara yin gaba yake,ina tsoron kar hakan yajawo matsala idan iyayensa suka dawo. Sai nayi niyyar yimasa fada sosai ko nesan tashi daga saikuma na kasa,saboda kama da yakemin da sameer haka ummah tah,sannan bayan wannan inajin yaron a cikin jikina sosai. Dan sunkuyawa nayi na kama kafadunsa kafin nace, "Suna cizo sosai sannan kaga dare yayi ka bari gobe sai muje da yamma idan ka dawo daga makaranta koh" Daga kai yayi alamar yah amince,sai kuma yayi murmushi,gyara masa gadon nayi yah kwanta bayan na bashi chocolate din dare,duk dan kar yah biyoni,dan nanny dinnasa wani lokacin ba gidan take kwana ba tana wajen mazan sojoji,kuma wai ita suka bawa tarbiyyar yaronsu,dan sati guda kenan bata gidan. Zuwa yayi yah fadamin akan yana tsoron kwana shikadai kullum,wanda nima na kula da hakan. Tun daga lokacin na dawo da duk kayansa zuwa dakinnawa,shima dayaga hakan murna yayi tayi,ko yaushe sai yah shiga yah fita,wai yah zama dan dakina. Tun daga lokacin idan na tashi nayi abin karyawa sai na tasheshi na shiryashi nima na shiryah,idan muka gama komai saina fito na kulle gidan shikuma na kaishi wajen mai kaishi makaranta. Idan ya dawo kuma sai yaje inda nake bada horo mutaho gidan tare,idan nayi mana abinci muka ci,saina shiryashi cikin kayan islamiyyah bayan yayi sallah,duk da bana takurashi amma yah sani idan yah yi ba daidaiba ina horashi yanda yakamata,dan banason sakalci ko kiyuwa ko kuma raini ga wanda suka fishi. Shi ma daya ga haka yana kokarin kiyayewa,koda ya manta yayi da sauri yake bada hakuri idan yah tuno mai zai biyo baya. Yanzu nakan barshi yaje wajen su blacky shikadai bayan na tabbatar sun dan saba dashi bazasu cutar dashi ba,dan karnukan sun sanja kama zuwa wani abu mai hatsari ga duk wanda yah gansu,saboda zaman cikin jeji da kuma bada horo mai tsanani. ***** Zuwa yanzu nasamu wata guda uku kennan da karbar matsayin mai bada horo a cikin bori camp dake cikin porthacourt barrack. Na sauya abubuwa da dama a cikin haron daliban,ciki harda kara tsawon lokacin yin train,sannan banda wasa ko shiririta,yanzu na zamo kusan duk taro da za'ayi a cikin wajen toh sai an turomin takardar gayyata,wani nakanje wani kuma nace bazanjeba,dan haka suke hakuri dani,bana nuna respect ga kowa,dan wannan dabi'ar ita kadai na rasa a cikin aikin sojan,wato respect ga na gaba dasu. Watarana ne ina zaune major nazeer yah kirani,nayi mamaki daya nunamin wani office an kawatashi wai nawane,sun bani alhakin kulada horon sabin sojoji,sanann kuma ga kudi da,suka bani mai yawa,wanda kuma zasu cigaba da biyana wata wata,kallon office din nake har da motar da take bakin wajen mai paint din sojoji,kuma wai tawa ce. Biki akayimin na hakan ,wasu manyan sojojin daga wasu jahar ma saida suka hallara,musamman dasuka ga irin aikin danayi da kuma sabon salon horo dana kawowa barrack din. Gaskiya nayi mamakin abinda sukayimin ban zata zai kai har haka ba,sai ganina nayi na daukaka lokaci guda an bani matsayin mai bada horo da kuma saka hannu cikin tsaron wajen,zan iya gyara duk abinda naga dama a kuma lokacin danake so. Yanzu daliban dana yaye a cikin wata hudu gwarazan da suke cikin su sune suke gudanar da wasu ayyukan,ni yanzu banida time sosai,koyaushe ina office. Farouq ne yah shigo office din da sauri yana narai narai da ido,kallonsa nayi naga har hawaye yakeyi. "Menene yah faru ka dawo da wuri haka" "Ba .....ba cikina ne yake ciwo ba" "Wani Abu kaci ko,bayan na hanaka" "Ahah anty" Ajiye aikinnayi na kira yaseer ya karisa dan yanzu shine mataimakina,kuma nina bukaci hakan,mahaifiyarsa takanas tazo tayimin godiya. Daukarsa nayi dannaga harda sakalci yau yake ji daga gani. Gida muke je na ajiyeshi a bakin gado,bandaki na shig na hada masa ruwan wanka,lokacin dana fito har yah cire kayan makarantar,koh magana banyimasa ba yah shige bandakin,dan zuwa yanzu babu abinda bai saniba na dokokina basai na fada da bakiba. Fita nayi na hada masa abinci. Kallonsa nayi lokacin daya fito daga dakin sanye da gajeren wando irinna sojoji da kuma farar T-shirt. Mika masa abincin nayi,yana karba yace, "Nagode ummah" Saurin kallonsa nayi jin sunan daya kirani dashi,daga haka bai sake cewa komaiba har muka gama cin abincin yah fita zuwa gidan major nazeer wasa,dan tanada son yara. Har sannan kalmar mommy bata daina yawo a cikin kaina ba. A satinne na kira meeting kan cewar bai dace ace an saka kaso na sojoji a bakin wani gida kawai dan tsaro ba,sannan kuma kamata yayi ace sojoji guda biyu a kowanne gida,shima kuma za'a dunga sanjawa wasu su tafi training wasu kuma suje wajen iyalansu. Cikin saurin bukatata ta karbu dan hakan shine yah fi,a kofar gidanmu kam,duk sallamar su nayi nasaka iyah guda biyu da rana,idan dare kuma yah yi su blacky ne suke tsaron bakin kofar,ko kafi uwarka kokari baka isa ka wuceba sai sun baka dama,shima sai na yadda tukunna,ta hanyar ganin hotonka a camera kofar gidan,idan na yadda zan kunna green idan ban yadda ba sai na danna red,toh dole ka juya badan kanaso ba. Tun daga wannan lokacin farouq yakoma kirana da mommy,dan a cewarsa yanzu babu wanda yake kuladashi saini,nima banyi kokarin hanashiba dan yanzu yaron ya shiga raina sosai. Washagari da safe aka bada sananrwar dawowar general musa daga jinyar yarsa daya tafi yi a kasar Germany,hmm abin ma ba tsari ko kadan,tun wata biyu da zuwansu ta warke amma tace baza ta dawoba sai anyi mata aikin fata an cire duk tabon zanen bulalar dayake jikinta,wannan ne ya daukesu har tsawon wata hudu acan. Nikuwa naji labarin dawowar tasu amma babu abinda nayi a ciki,tashi nayi kamar kullum na shirya farouq zuwa makaranta,nima na fita nawa aikin,a hanya duk sojoji sai sara min sukeyi,dayake yawancin dalibaina ne dana yaye wata uku da suka wuce,sannan su san bana wasa sanann bana mugunta ko zaluntar wani,da haka na kankaro mutuncina a wajensu. Yau ban tashi da wuri ba,dan farouq ma daya dawo daga makarantar safe anan na bashi abinci yaci yah kawanta,sai la'asar tukunna na sabashi a wuyana zuwa gidannamu. Dan zuwa lokacin nasan su yah sameer sun dawo,kuma da gangan na ki dawowa da wuri duk da nasan tahowar wajen azahar zasuyi. 💎*sameer a madubin gani*💎 Tun jiya da akacemin zamu taho nakejin kamar nayi tsuntsuwa,babu yanda nayi haka na zauna a kasar badan komaiba sai dan kar na taho ace matata ce tayi mata illah amma na barta na tafi,haka badan nasoba mukayi tsawon wata hudu acan. Kusan karfe daya dadai muka iso Nigeria,itah dama direct wucewa sukayi gidansu,nikuwa wani sojane ya dawo dani gida,tun karfe biyu nake tsaye a bakin kofar gidana amma bahu sameemah ba alamunta,ina taje oho bansaniba. Har naje sallahr la'asar nadawo ina tsaye kenan na hango wata mace ta dosoni da kayan coach a jikinta,abinne yaban mamaki yau she aka samu mace mai bada horo kuma,ni kadai na tambayi kaina. Ga kuma duk Wanda tayi karo dashi sai yah bata girma kaman wata general. Saida tazo tab dani naga ashe sameemah ce,dan tsabar mamaki kasa cewa komai nayi,ga kuma farouq a wuyanta yana bacci. Wuceni tayi ko magana bata minba ta bude gidan,danji komaiba dan dama ban yi tunanin sun gaisuwarba ko kuma maganar. Bin ta nayi a baya bayan ta bude gidan,sai kuma naga ta nufi dakinta da farouq din a wuyanta,nima binsu nayi dannsan nawa dakin bazai shiga ba saboda kura. Sanda nashiga dakin har farouq ya tashi ita kuma ban sameta ba tana bandaki,kallona yayi da mamaki sai kuma ya rungemeni da karfi yana dariyah. Karar budewar kofar bandakice tasa shi sakina da sauri yana ja dab baya,sai kuma ya dan sunkuya tareda cewa, "Barka da hanyah daddy ka dawo lafiyah?" Dan Mamakin Sabin halin dana ganshi dashi ma kasa magana nayi,bai jira amsata ba yah juya wajen sameemah wanda take rike da hannun kofar bandakin. "Kiyi hakuri mommy bazan kara haka ba" "Apology accepted" Tana fadan hakan ya tafi da gudu yah wuce bandakin ta hanyar data bashi a kusa da itah. Wajen kaya ta bude a kusa da nata inda naga kayan farouq a ciki an gogesu. Wasu riga da wando ta fitar marasa nauyi sai kuma tah fesa musu turare kadan ta ajiye akan gadon. Fita tayi zuwa kitchen inda nima na bita a baya,amma ko kulani bata yi ba. "Yanzu sameemah ko ba magana babu bare sannu da dawowa" "To mai kakeso nace maka,tunda gaka kadawo ai na ganka ko tunda ba makahuwa bace ni" Hmm kawai nace kafin na dawo falo na zauna ni kadai ina tunani amam narasa na menene. Can Bayan wani lokaci farouq yah fito da sauri bayan yah saka kayan da ta fitar masa dazu,a hankali ya shigo falon kafin yah samu waje a kusa dani yah zauna sai murmushi yakeyi idan muka hada ido. Nima Murmushin nay masa kafin nace, "Yaushe yaron daddy yayi hankaline haka uhm?" Bayyi magana ba sai murmushi kawai dayake yi,muryar sameemah ce daga cikin kitchen tana kiran farouq. Da sauri yah tashi yana cewa ganinann mommy. Plate ne a hannunsa na abinci yana zuwa yah ajiye min a gabana,sannan yah koma kitchen din da sauri yah kawomin ruwa a jug da kuma cokali. Wannan karon tare suka fito shida ita tana rike da wani plate din a Han nun ta. A jiyewa tayi a kasan carpet din da cokali biyu a ciki sannan kuma da kofin ruwa guda biyu. Har yah zauna a daya gefen tace, "Jeka canja tashar nan zuwa taka" "Toh" Remote ya dauka ya maya zuwa tashar yara mbc 3,daga wrestling din dana kunna. Ɗaukar abincin nayi ina ci,saidai rabin hankalina yana kansu sameemah yanda suke cin abinci,da kuma yanda yake diban abinci a gabansa a hankali yana kaiwa bakinsa,yaushe ya,sauya daga yanda yake zuwa haka oho,sannan ina nannyn sa take shima oho. Mai aiki na kira daga bangarensu dan su sharemin dakina ,ita kanta dana kirata saida tayi mamaki,daga gani sun dade basu shiga sashenba. Har na saleemah ta gyara tsaf kafin tazo ta fita,zuwa lokacin ana magriba. Kama hannun farouq nayi nace, "Abban zo mu tafi masallaci tacan muje dauko mommynka" Saurin zame hannunsa yayi yana kallon sameemah. "Zaka iya tafiya amma iya yau kawai,hakan ma kuje da abbannaka ka fada masa yau ba karatu" Muna fita na tambayeshi menene, "Uhm uncle ne mai yimin lesson,amma sabone dan ummah tah kori wancan din tun ranar data ga yah kun na min waka muna ji,yanzu uncle yaseer ne yakemin,ummah take biyansa,tace idan ban jeba yah zaneni,sannan kuma tace idan an ce nayi abu banyiba ya fada mata" Muna cikin tafiya a hanyar mu ta zuwa gidan su saleemah yana tamin tadin abinda yake faruwa ,jijjiga kai kawai nayi tareda Mamakin hali irinna sameemah,yamzu a yanda take zata iya bawa wani tarbiyya amma kuma idan ita ce bazatayi ba koh?. Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎25~26💎 Lokacin da muka shiga cikin gidan ma suna zaune a falo har da abokananta,sakin hannuna yayi yah tafi wajen hajiya fatima da gudu,dan ko ta kan saleema bai biba,ita ma bata wani kulaba sosai. Gaishe da hajiyah fatima yayi kafin yah je wajen saleema ya gaisheta da kuma yimata yah hanya,har da abokannata,dukkansu tsayawa sukayi suna kallonsa da mamaki kaman yanda nayi a baya. Wata ce daga cikin matan ta fito da chocolate ta bashi,bai mika hannu ba said jijjiga kai da yayi. "Ummah ta hanani shan chocolate,da tana siyamin amma daya sakani ciwon ciki shikenan sai ta daina bani saboda da muka wsjen likita cewa yayi ta daina bani chocolate,kuma tace ko an bani kar na sha" "Wacece ummah taka wacce bansan ta ba" "Anty sameemah nake cemata amma yanzu nakoma cemata ummah" Wani ashar saleema ta ruga tareda mikewa tsaye ta kamo farouq a hannunta, "Dan ubanka ita ta haifamin kai tayi zafin nakudarka da zaka cemata wata ummah ina raye da raina,iyee wato ta lahantani ta turani neman magani kai kuma ta mallakeka ko saboda taga bazata haifi nata ba " Hajiyah fatima ce tayi saurin fincike yaron a hannunta har yah fara kuka,sannan ta fara mata fada,saidai babu alamar fadan yana shiga kunnenta. Share masa hawayen take tareda tambayar sa meya faru,cikin kuka yafara cewa, "Ammee ba ita tace na dunga cemata ummah ba nine na fadamata,saboda lokacin da nanny take barni nikadai na kwana a daki da daddare sai da safe ta dawo itace ta maidani dakinta take kwana dani,kuma kullum take shiryani zuwa makaranta da wuri,idan na dawo ta bani abinci sannan ta kori mai yimin lesson saboda baya min karatu ta daukomim wani,idan banida lafiya ta kaini asibiti,har kudin makaranta ta da aka ce na kai ina gani da kudinta ta bayar na albashinta,dan a gabana tayi waya tace su biyata kudin zata yi wani abu dashi,da muka je makarantar tabiyamun sannan ta tari mai mashin ta dawo gida. Koyaushe ita take kuladani tunda kuka tafi,da nanny ta dawoma korarta tayi da daddare,banyi bacci ba ina ji tana ce mata wai,ta sallameta bazata bari ta bata tarbiyyata ba ta tafi can wajen sojojin da take zuwa wajensu,kuma ammee...." Yah isa haka farouq duk munji mai kace sannan nasan da gaske kakeyi,shin kanason cigaba da zama a wajen ta?" "Eh ammee zan zauna a wajenta mommy kuma ta rike zuhrah" "Toh shikenan a wajenta zaka cigaba da zama idam har abbanka ya yarda" Jiyowa yayi yah kalleni na daga masa kai da sauri,har saleema zatayi magana hajiya fatima ta zefa mata wata harara,da sauri tayi shiru. Da muka tashi dawowa harda hajiyah fatima muka dawo wanda alhaji musa yah tursasa mata akan sai taje tayiwa sameemah gargadi. Bayan mun shigo hanyar gidan muna zuwa saitin gidannawa gurnanin wasu abubuwa suka doki dodon kunnenmu,kallon saleemah nayi wanda itama ni take kallo lokacin da wasu hallotu masu kaman zakuna suka bayyana a gaban mu. Farouq ne dayake gidan baya yah bude yah fita da sauri lokacin da muka tsaya a gabansu a bakin kofar gidan. Nima fita nayi da sauri domin taro shi kafin suyi masa illah,saidai ban karisa fito da kafata ba naga yah tsugunna a gabansu sukuma suna shinshina shi. Ina karisawa kusa da su daya yah boyeshi a bayansa dayan kuma yana min gurnani na alamar karna kariso. Dariyah farouq yah tuncire dashi kafin yace, "Daddy barin naje gida na danna muku alamar bada damar shigowa" Daga haka yah shige gidan da gudu,muna nan tsaye saida wata koriyar danja ta haska kofar gidan kafin kkwannensu yayi nasa wajen,jikinsu har wasu juyawa yake saboda tsabar murdewa.ga kuma rigar bullet da aka saka musu,tunda nake banda ba kallon karen farauta haka ba. Karisawa mukayi cikin gidan babu wanda yace wani abu har muka isa falon. Sameemah muka samu farouq ya dora kansa akan cinyarta sai surutu yakeyi itakuwa ko magana batayiba. Daga kanta tayi ta gaisheda hajiyah fatima wacce muka shigo tareda ita,daga ni har saleema kuwa ko kallon inda muke batayiba. Hajiyah fatima ce tafara magana cikim dattako kaman yanda ta saba. "Da farko ina baku hakuri dukka sannan zamantare dole saida hakuri musammman kai sameer wanda suke karkashinka. Duk da bansan mai yah hadaku ba a baya amma ke sameemah ga saleema nan ta dawo dakinta bayan lokaci da bata nan sai kuyi hakuri a cigaba daga inda aka tsaya. Idan wani abune ku sanar da mijinku ba kudau hukunci a hannu ba" Saleemah ce tayi saurin cewa, "Kuma a ja mata kunne kar ta kara gigin aikata min wani abun dan hukuncin dazai biyo baya bazaiyi mata dadiba.sannan kuma ta bani hakuri akan abinda tayimin kafin zance yah wuce" "Ke Wacce kika aikatawa kin bata hakurine har ta mutu?" Hajiyah fahima ce tace, "Wacece ta mutu kuma?" "Ita tasani ai ki tambayeta kiji" Kallon tane yakoma kan saleemah wanda cikin borin kunya tace, "Danna yiwa karyah hukunci manene,da har zaki hadani da itah a daraja" Shiru kowa yayi nan na zayyanewa hajiyah fatima abinda saleemah tayi da kuma,amma bansan karyar ta mutuba saida ta fada yanzu. Ran hajiyah fatima in yayi dubu yah baci,bata san lokacin data zabgawa saleemah mari ba, "Yanzu duk wahalar dakika saka mutane a she kece ummul aba isin faruwar komai,wai kishi haukane harda zaki kama dabab ba abinda tayimiki kiyi mata duka da tsofon ciki har ta mutu ita da wssu daga cikin yan cikinta,wannan wane irin zaluncin ne haka,nidai bansan halin wa kika daukoba dan duk dangina babu wanda yake da wannan halin" Kuka saleema ta rushe kafin tayi hanyar dakinta tana cewa, "Wallahi saina fadawa mommy maryam duk abinda akemin nasan ai zata bi bayana idan taji abinda kae min." Babu wanda yah kulata bare yasake bi takanta,itama hajiya fatima tashi tayi domin tafiyah,anan take fadawa sameemah ta,bata farouq halak malak idan tana da bukatar rikeshi,godiyah kawai tayi kafin tayi Murmushin da bakai yi nisa sosaiba. Da safe da,wuri na tashi domin akwai meeting da major nazeer yah bukaci ayi. Na shiga kitchen din da niyyar dan hada wsni abu naci naga sameemah ta,juya baya tana wsni abun,mantawa da abinda ya kawoni nayi na tsaya ina kallon bayan ta yanda yake murzawa da kuma juyi. Lallai allah yayi halitta anan,shine abinda nafada,dan kunkuminta ma kadai abin kallone bare kuma duk jikinta,ganin kallon bazai kaini bane yasa na karisa tareda sakala hannuna a kunkuminta,saurin jiyowa tayi muka hada ido har numfashinmu yana haduwa dana juna. Juyawa tayi ta cigaba da abinda take amma ta saka daya hannunta ta ture hannuna daga kan kunkuminta batareda tace komaiba,nima banyi kokarin maida hannunba sai cewa danayi. "Ina kwana maman farouq,idan abin karyawa ake hadaamsa a danyi dani please ina bukata" Bata cemin komai ba saidai daga yanyin kallon nasan maganar bata bata mata raiba ko kadan. Daga haka na juyah na koma dakina domin na shiryah. Lokacin dana fito shima farouq yah fito da jakarsa a bayansa shida sameemah,da alama ita ta shiryashi. Abincin ta zuba masa nima ta zubamin kafin ta,ajiye masa wanda zai tafi dashi makaranta. Wucewa tayi dakinta kaman mai saurin yin wani abu. Nidai dana ga cikina ya dauka fita nayi zuwa wajen motata domin zuwa headquarter. Kowa yah hallara ana zaune amma wasu har sannan basu zoba,mutsutsuka idona nayi domin ganin wacce ta shigo cikin hall din kuma ana fadin wai mai kulada tsaron duk camp din ce dakuma kulada harkar horo. Bakina saki ina kallonta musamman yanda tasha kaya ga kuma hade fuska da tayi kaman wanda take fagen daga. Nima dauke kaina nayi daga kanta ganin ko inda nake bata kallaba. Shugabane ya shigo tareda masu tsaronsa aka fara meeting,shima daga gani kallom mamaki yake yiwa sameemah kaman yanda nayi mata. Major nazeer ne ya tashi yafara zayyana irin gwagwarmayar da sameemah tayi a cikin barracks din da kuma irin nasarorin data kawo harma da daliban data yaye da kuma jajircewarta a wajen aiki. Duk wannan bai basu mamaki ba sai da suka ji cewa nice Raudah abdulsalam wanda suke jin labarinta. Da haka aka gama meeting din kowa yah koma bakin aikinsa,nima office dina na shige daga nan,dayake nawa a wani branch din ne daban ba ainihin cikin barrack ba saida nayi tafiya zuwa cikin gari tukunna. Bani na dawo gidan ba sai wajen magriba hakam badan nagama aikinba sai dan kawai na hakura sai gobe na cigaba. Tun daga shigowa nake jin kamshin abinci a kitchen,ko ba tantama nasan ba saleemah bace a ciki,aikuwa hasashena ya zama gaskiyah domin sameemah ce daga itah sai boxer na mata iyah gwiwa,sauran fararen cinyinnan duk a wake,wayyo matar nan zata kasheni ina ga. Mtswww naji tsuka a bayana,ina juyawa naga saleema ta cika tayi fam,muna hada ido da ita ta juya ta bar wajen tana cewa, "Aikin karuwamci kawai" D'aki na shiga na canja kaya kafin na fito zuwa masallaci. Lokacin dana dawo gidan tsitt dashi kaman ba mutane kowa yana dakinsa. Leka dakin samemah nayi farouq yana zaune a tsakar daki yana assignment,ita kuma tana nade masa kayansa na makaranta. Zama nayi a gaban gadon ina kallon yamda yakeyi,lallabashi nayi yah fita falo domin yah cigaba da yin assignment din. Ta shi nayi na nufi inda sameemah take tsaye,hannuna na sakala a kunkuminta na jawota zuwa jikina,shiru mukayi daga ni har ita ba wanda yace komai,wani irin yanayi nafara jina a ciki sanadiyyar yanda dumin jikinta yake shiga cikin jikina. Bakina na kai wajen kunnenta cikin muryar dani kaina bansan inada itah ba na fara yimata magana. "Menene yah faru lokacin da bana nan,yah akayi kika hau matsayi kuma baki taba fadamin nabaki umarnin yin hakanba,amma kinsan ke mallakinace koh?,sannan ya akayi kika zama Raudah abdulsalam,please ki fadamin,duk da nasan kina da taurin kai amma bana son kiyimim gardama kinji" Shiru nayi daga hakan ina hura iska cikin kunnenta a hankali yayinda hannuna kuma yake yawo a cikin ta da kuma kan kunkuminta. "Baka bukatar sanin amsar hakan,idan ma kana bukatar sani toh kaje ka tambaya mana,amma bani zaka tsare domin samun amsarka ba. Juyo da fuskarta nayi izuwa kan tata fuskar ina fesamata kallon da yake dauke da ma'anoni dayawa ,mun dade muna kallon juna kafin ta dauke idonta daga kaina,banso hakanba saboda hada ido kadai da mukayi ba karamin kawo wani shauki cikin zuciyata yayi ba. Kara dago da fuskarta nayi nasake hade kallon da muka fara a baya,dan murmushi nayina dan gefen baki kafin nasake cewa, "Please kanwata kidaina amsa magana a haka idan na tambayeki,banajin dadin hakan,idan ina yimiki wani abu wanda bakyaso ki fadamin,nayi alkawarin dai nawa inshaallah,amma kallonki kina abu cikin kadaici kaman bakya da kowa hakan yana damuna" Ture hannuna tayi cikin zafin rai wanda bahaka takeba lokacin dana fara maganar,da alama na tabo mata wani tabo a cikin ranta wanda yake mata kaikayi. Yin gaba tayi kadan yanda bana ganin fuskarta kafin tace, "Sai a yanzu dana girma tukunna kadaicina yake damunka,lokacin danake tsaka da bukatar lokacinka ka tsallake ka barni a garin da babu wanda yake bukatar yaganni na kwana na tashi a raye baka ji zafin hakan ba sai yanzu da jikina yah fara daukan hankalinka tukunna ka tabbatar da cewar ni matarkace a yamzu ba kanwarka ba koh? ........kaine sanadiyyar daka sa na kulle zuciyata sannan nadaina yarda da kowa a cikin duniyaranan,na yarda kunci yacigaba da lullubeni har lokacin suka sauramin na bar cikin duniyarku suzo" Saurin jawota nasake yi jikina a karo na biyu wannan lokacin zuciyata tayi nauyi dajin kalmar da take fitowa daga cikin bakinta. "Mai kike fada haka sameemah ,ki fayyacemin komai naji daga bakinki,duk abinda kika san zakiyi mim wanda zai dauke wannan kadaicin a rayuwarki na yarda kiyi,ko horo kike bukata kiyimin na barin ki lokacin da bakida yawo naji na dauka zan karba duk da bayin kaina bane hakan." Kallona take da alamar bata fahimceni ba,nima daga mata kai nayi alamar haka ne, "Tun bayan rasuwar ummah da kwana uku komai yah sauya daga cikin rayuwata,ba abinda na tsana kona budi ido na gani kaman ke da kuma yan uwan ummah,abin yana damuna kuma nasan akwai abinda yake damuna,a duk lokacin da kika matso kusa dani ji nake kaman na shakeki har sai kin daina numfashi,domin duk wani laifi da akayimin sai na ji kece kikayi sanadiyyar yinsu. Ana nan bayan kwanaki sai ya zamana garin ma yah fara fita a cikin raina,kullum da kyar nake kwana nake tashi har yah zamo nafara aman jini musamamn idan ina cikin gida,wata rana ne da muka fita daga garin nida abokina sai naji babu ciwon danakeji yah tafi kaman an zare shi. Hakan yasa na tatttara kayana nabi wani soja a anguwarmu saboda na samu abinda zan dogara da kaina,sannan na nemi magani na dawo domin kulada ke. Lokacin dana samun gidan dazan zauna nayi murna sosai,hakan yasa na shiryah naje har gidan gandu domin daukoki,saboda ina tsoron abinds yah cutar dani kema zai iyah cutar dake,saidai mai zam tarar wai bakyanan kin shiga duniyya haka aka fadamin. Nayi bakin ciki har kuka nayi,shin mai zam je duniya na fadawa umma akanki da wane ido kema zan kalleki idan mun hadu. Ban sake haduwa dakeba sai lokacin dana ganki kin fito daga mota lokacin nayi aure naje da saleemah,tambayar danayi miki amsar farko danaji shine budurcin ki kika bayar aka baki itah. Bayan tsawon lokaci dana dauka ina nemanki gari yah gari amma sai na karbi wannan amsar........rudu fargaba da tashin hankali gameda bakin ciki su suka tattaru a cikin zuciyata lokaci guda. Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎27~28💎 Hakanne yasa na cika da bakinciki har na fara miki fada,banida niyyar sakaki cikin kadaici sameemah duk abinda yah faru yah fi karfina ne sannan ina baki hakuri akan rashin fahimatar dake tun daga farko" Duk da bana kallonta amma nasan maganganuna suna shiga cikin kunnenta,samun waje ta samu ta zauna a bakin gado,yayinda nima na bita na zauna a gefen ta tareda jawota zuwa cikin jikina sanann na cigaba da maganar danake yi. "Bazan tursasaki ki yarda da abinda nake fadaba,saidai ko wata rana zaki iyah bincike akan hakan,ki yafemin da barki cikin wannan halin,bazan gazaba waj en baki hakuri a koyaus Koyaushe ,idan bazaki damuba inaso naji mai yah faru dake har kikabar gida sannan a ina kika tsinci kanki" 💎*Sameemah a madubin gani*💎 Shiru mukayi daga ni harshi,ina jin yadda zafin jikinmu yana gauraya zuwa guda d'aya, Wani irin yanayi nakeji yana shiga cikin jikina wanda na ji a duk lokacin da farouq ya matso kusa dani,duk da banason yanayin saboda yanda yake saka zuciyata yin rauni a lokaci da ya,amma kuma bazanyi karyaba yana sakawa najini kaman ina raye nima kaman sauran mutane,duk da cewa zuciyata bugawa take saboda ina tsoron kar na cutar dasu acikin kowanne irin lokaci. Musamman danaji dalilin tafiyar yah sameer daga gida sai na tsinici kaina da son kai saboda kullum tawa matsalar nake gani ba matsalar wasu ba,hakan yasa nake kara ganin laifin mutane fiyeda abinda sukayimin. Dago da fuskata nayi ina kallon fuskarsa wanda yasake matse jikina acikin nasa kaman zai maidani cikin nasa. Haka kawai bansan mai nene yasami shiga cikin kaina ba na tsinci kaina da bashi labarin yanda nayi kokarin tafiyah birni aiki da yanda yan fashi suka taremu na cececi sauran yaran ta hanyar mika kaina garesu har zuwa yanda nayi rayuwata a kasar palastine da kuma kasar Brazil. Abu daya na boyemasa shine yanayi halittata da kuma dafin dayake kwance a cikin jikina harda kuma shaidanun danake magana dasu. Wanda kuma nayi hakanne saboda lafiyarsa,dannasan idan suka tabbatar yasani to zasuyi kokarin hallakar dashine wanda hakan shine abinda har karshen rayuwata bazan yafewa kainaba. Dora habar sa yayi akaina kafin yace, "Kiyi hakuri da rayuwa sameemah hakika munga jarabawa kuma muna kan gani,saidai ko kusa ban fada rayuwar da kika shigaba,ke jarumace nasake fada ke jarumace sameemah,wanda ko cikin maza ba kowane zai jure abinda kika jureba,saidai ina fatan wahalar rayuwa yah tsaya miki iya haka,sannan kuma yah baki ikon karbar hakan a matsayin kaddararki,ina fatan nacigaba da zama dam uwa a gareki mai sharemiki kuka,sannan ina saka ran kasancewa miji nagari agareki idan kin bani damar hakan,sannan kuma uban y'ay'anki" Gabana ne yah buga rigifff,saboda nasan abinda yake hasashe ba abune mai yiwuwa ba koda kuwa mun so hakan a tsakaninmu,yau daya a rayuwata naji babu dad'i kasancewata daban da irin rayuwar mutane,saidai cikin sauri na katse tunanin hakan daga cikin raina tareda cire jikina daga na yah sameer ta hanyar matsawa gefe. Shima dayaga hakan light kiss yayimin a kumatu tareda da cewa "saida safe" 💎*salma a madubin gani*💎 Tun da nazo gidannan ko na muka zo nida sameerah babu wanda yaji dadin gidan. Ni kullum a gaban mijina da akwai da babu duk dayane,ita kuwa sameerah mijin ma bata ganshi ba,dan yanzu an shiga wata na hudu kenan da barin daga kasar,yah tafi can wai an turashi da sunan karatu yana ta sharholancinsa. Tun daga yanzu banyi shekara da aureba amma danasanin auren nakeyi ,kullum cikin aiki mukeyi,idam kuma kasamu ka kwsnts baka da aiki sai tunanin yanda rayuwarka zata kaya washagari. Nida sameerah sai murna muke hajiya mairo zasuyi tafiyah itah da alhaji bala zuwa kasar india,zataje a duba mata kafarta. Dan yanzu mun hade kanmu nida itah,dan dolen uwarmu,koba komai naka nakane,da muka uwar bari sai muka hade kanmu,amma hajiyah mairo batada masaniyar hakan. Muna gani suka shiryah suka tafi sai rankwada kai takeyi,shikuwa duk yanda tayi sai ya yi mata sannu,bakinciki kaman zai kasheni danna tsani hakiyha mairo kaman na kasheta nakeji ,shegiyah tsinannaniyah. Ita kam zainab taji dadi yamzu,duk da a baya itama tasha wuya,yanzu suna can ita da mijinta da kuma yar ta. Waya san halinda sameemah kuma take ciki oho. Da haka dai muka rakasu sai hararar mu takeyi,nidai dauke kaina nayi a raina nace zaki san kin gasamu aradu,wallahi duk saina juye tijarar daki yi mana a kanki. Zamuyi shiri muna nan zuwa kanki muma. Aikuwa hakanne ta faru,dama munyi shirin idan sun tafi muyiwa alhajin kira,dole yah barta ya dawo koyana so ko bayaso,daga nan zanyi duk dabarun dazanyi na naja hankalinsa izuwa gareni,idan ta dawo bata da ikon yin komai sai abunda muka yi. Ni da sameerah kullum muna kulla yanda komai zai kasance cikin sauki ba tareda a ansha wahala ba,maida hankalina kan sameerah nayi kafin nace, "Nikam inaga sameerah idan har alhaji yha dawo da hankalinsa toh bazan yi masa asiriba zan jawo hankalin sa ne da duk dabarun danake dasu,saboda nagane duk mallakar asirinnan aikin banzane idan ya karye shikenan ya barka a tutar babu" "Kuma fah hakane salma yamzu kina ganin umaruje da bani yake soba,duk lokacin da asirin yah fara karyewa sai na rasa kansa bare gindinsa fah. Gaskiya nima na gane,idan har zan iya shawo kansa zuwa kaina da karfin kissa irin ta mata to ina ga hakan za'ayi,muje kawai na biki muyi musu kiran a tare,idan mukayi sa'a kafin ta dawo mun shawo kansu sai muga ya zatayi kuma" Hakan kuwa akayi mukaje wajen malami mukayi masa bayani sanann muka bashi suanan alhaji bala da dansa,da niyyar idan sun dawo tamu basirar zamu hada muyi amfani da itah a kansu. Washagarin ranar da muka je wajen malamim kwatsam muna zaune sao ga alhaji bala ya shigo gidan,bamuyi masa maganar ina hajiyah ba sai sannu da dawowa da mukayi musu,sameerah ce tayimim signa akan ma dam gwada action,aikuwa cikin dakewa na matsa kusada shi dama nayi kwalliya nasha turare. Karbar jakar hannunsa nayi niyyar yi,abin mamaki kuwa sai ya sakemin ita dukka kafin yayi hanyar dakinsa,shewa mukayi nida sameerah marar sauti kafin na bi bayansa da Sauri. Bai koreni ba haka bai yimin magana ba har na hada masa ruwan wanka ya,shiga sannan na kaimasa abinci. Har yagama cin abincin ina zaune a gafensa amma bayyi magana ba,hada kayan abincin nayi da niyyar fita zuwa kaiwa kitchen sai naji ya zawo hannuna tareda cewa, "Salma Idan kin kai abincin ki dawo,inajin kaman jikina babu dadine shiyasa na kasa yimiki magana,daga gani dai kaman ba yau aka kawoki gidannan ba amma kuma sai naga kaman ni yau na fara ganinki a gidan kai na ya daure sosai" Saurin saka hannuna nayi a bakinsa kafin nace, Shshh alhaji komai ya wuce yanzu,bari nakai na dawo" Gyada min kai kawai yayi,ina fita muka tafa nida sameerah wanda muna cikin hakan mukaji alamar jefar da jaka a kasa,dukknamu bakin kofa muka kalla inda umaruje yake tsaye,kallon sameerah yayi cikin takaici kafin yace, "Mtsww ni wallahi narasa ma maiyasa ma dawo akanki,kwata kwata ma ya akayi na aureki oho,aikin banza kawai,dallah kawomin abinci ni" Jikinta yana rawa ta gyda masa kai,nidai wucewa nayi na ajiye kayan kafin na zo na wuce wajen alhajin,dan dama ba magana nake da umaruje ba. Yamzu zamanmu da alhaji bala ba yabo babu fallasa,saidai abin farincikin shine kullum kara sakewa muke dashi,sannan mukan zauna muyi hira dashi ta fahimtar juna,har sameerah wani lokacin ma da ita ake hirar,kasancewar umaruje har yanzu tsakininsu abin yaci tura,dan dama ba da soyayya sukayi aurenba,yah aureta ne ba a cikin hakalinsa ba,shiyasa abin duk yaki daidai tuwa. Muna nan nafara jin kaman banida lafiya,nice ba nice ba kullum cikin kawanciyah da kuma amai,alhaji na samu na fadawa halin danake ciki. Nan da nan kuwa muka tafi asibiti,gwajin farko aka tabbatar da cewa cikine dani,koni kaina banyi farincikin da alhaji bala yayiba,kaman shine haihuwarsa ta farko. Dawowa gida mukayi bayan sun damin bincike akan komai lafiyya,sameerh ma ta tayani murna sosai,dan ma sa'a ta daya cikin baya bani wahala sosai kaman yanda yah fara a farko kafin naje gwaji,kaman dama jira yake musan yana nan. Soyayya Mike zubwa nida alhaji bala kaman wasu yara,komai nayi biyeni yake babu ruwansa,danshi kansa naga yayi laushi dayaga hanyar dayake a baya bamai dorewa bace. Cikin yana da wata hudu wanda yakama hajjyha mairo tayi wata hudu kenan a kasar india,dan duk a zatonta alhaji bala yana Egypt wajen wani program yanda ya fada mata. Rana tsaka ta tashi dawowa hakn ma dan sunyi waya da yusrah ne ta fadamata cewa alhaji bala yana Nigeria duk tsawon watannin nan,aikuwa kaman iska haka hajiyah mairo ta tayar,ko gama zamn batayiba ta kamo hanya ta dawo. Muna kitchen nida sameerah muna abinci,na dawo falo kenan na zauna saboda sameerah tace na huta kawai,ina zama saiga hajiyah mairo ta shigo,idonta dama a kaina yake kaman zai fado kasa,musamman da taga abinda yake gabana wato ciki. Tun daga cikin idonta kana ganin kalar bakin cikin da ya kunsa,dan nasan tayi datasanin zuwa neman maganin,da ta bar kafar kawai ta rube. Kaina tayi da niyyar turmusheni akan kujerar daidai kuma da fitowar alhaji bala daga cikin dakinsa,saurin dakatar da hakiyah mairo yayi Yana cewa. "Baki da hankaline da girmanki da komai kike kokarin cutar da ita,bayan kuma ga ciki a jikinta,idna wani yayiwa yarki haka zakiji dadine iyee,to wallahi karanaji na gani mairo,idan kuwa kika kuskura naga kin sake cutar da wannan mutanen a cikin gidamnan kaman yanda kikayi a baya,toh a bakin aurenki,ke sai kibar gidan in yaso kawai,tun da ba zaman lafiyay kike so ba" Yana maganar cikin daga murya,daga gani ransa yah baci sosai. Daga haka yah juya ya fita daga gidan,nikuwa kallon zakisan dawa kike nayiwa hajiyah mairo wanda dan takaici har kwalla idonta yakeyi. "Yaushe haka ta faru,wane asirin kika yiwa mijina dan ubanki" "Wane asirin na karya dai,babu boka ko malam sai zalllan kissa,idna kema kika cigaba zaki samu naki rabon fiyeda nawa ma tunda kin fini saninsa" Shiru tayi kaman ta dauki magana ta sai kuma tayi dakinta da sauri kaman ana jefata,dukkuwa da kiba irin ta jikinta. Haka zaman ya cigaba da kasancewa tsakanimmu dani da hajiyah mairo babu wanda yake shiga harkar kowa,saidai sameerah kam tana shan wahala a hannunsu,musamman da suka ga tana kula dani. Karyah babu irin wacce hajiyah mairo batayiwa umaruje akan sameerah,a dole sai ta saka yah musguna mata. Zancen da tayi na auren yar kawarta kuwa yana nan babu fashi sai shirye shirye sukeyi. Duk wanda yaga sameerha sai yau tausaya mata,don ta rame ta fige kullum tana cikin tagumi,gashi wani irin so take yiwa umaruje kamar ta ci babu. Dan yanzu karatun ta nutsu tayi sallah bata wuceta,har makarantar dare ta shiga saboda rage zama a Gidan ma Yana rage mata kewa. Domin kusam kullum Mufeedah tana gidan wai tazo gaishe da hajiya mairo,shikuwa umaruje sai rawar kafa ta tashi,koda idon sameerah baya sa ya dauke idonsa,saidai ita ta bar musu wajen. Takaicin hakan nake gani gashi banida ikon yin komai akai,koba komai sameerah yar uwata ce,ganinta cikin hakan yana tabani sosai zanyi,dan nima ta kaina nake,ni kadai nasan wahalar danake sha a cikinnan. Shirye shiyen auren ake dan har an kusa saka rana biki ya fara kan kama,a zaune muke a dakina sameerah ta kawomim shayi na dare wanda yazam kaman jiki kullum sai nasha. Kallonta nake da mamaki sanann da tausayinta ganin yamda ta tsurawa waje daya kallo ko kyaftawa batayi,danni kaina sshaida ce a irin soyayyar da take nunawa umaruje. "Sameerah ki dunga hakuri,idan kika biye hakan zai iya kaiki yah baroki sannan kuma dolene a jarrabi bawa,amma idan kinga zaamn yana cutar dake yakamata kiyi wani abun. Dannaga wani abun da gangam sukeyi dan suga iyay gudun ruwanki akai" "Nasani salma nasan duk abinda yake faruwa,saidai na ma gode allaah da abin da na shuka nake girba dun daga nan duniyah,ba a barmin shi sai naje lahiraba,dan salma wallahi sai yanzu nake nadamar rayuwar danayi a baya,musamman idan malamin mu na makaranta yana fadan wani abun,sai naji ashe mu duniya kawai zuwa mukayi bamu karu da komai ba. Inaji a jikina abinda nayine ake nunamim a gidannan,idna na tsalleke na tafi kaman na bar baya da kurane,dan haka zan cigaba da zurewa salma har zuwa inda zuciyata bazata iya daukaba,alkawari na daukawa raina bazan taba cewa umaruje ya sakeni ba saidia idna shine yaga yana bukatar hakan. Nagode salma sosai da nuna kulawarki dan a wajwnki ne kawai nake samun nuna kulawa mai kyau,dan ummah kan idan naje bata da magana sai ta na koma wajen boka a sake min aiki. Gaskiya nikuma naga ba abinda boka yake yiwa rsyuwar mutum banda kara masa wahala da kuma zefashi cikin hallaka,wanda nayi a baya ma ina neman yafiyar allah,dan haka bana bukatar sake dorawa kaina wani laifin wanda bansan iya kacin masifarsa ba" Tana gama fada hakan ta dauki tiren shayin cikin sanyini jiki tayi hanyar kofa tareda yimin saida safe. Lokacin data jamin kofar bansan sanda na fashe da kuka ba mai cin zuciyya,lallai munyi rayuwar dana sanj a baya kam. Istigifari nake tsyi ina maida zuciyau har bacci ya daukeni. Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎29~30💎 💎*Sameemah a madubin gani*💎 Tun da muka yi maganar nan da yah sameer nakeji wani irin yanayi yana jiyartar cikin jikina yana taruwa a cikin kirjina,tun yana min ina iyya daurewa har yah zamo na farajin zafi a cikin kirjina,"mai hakan yake nufi?" Shine tambayar danayi wa kaina amma banada amsar hakan. Da haka bacci yah daukeni,saidai bankai ga jina cikin duniyar baccin tsulum ba mutanena suka bayyana cikin siffa ta bacin rai. ~~~me like nu fine Wai,kina nufin zaki bar soyayya ta huda cikin zuciyarki wacce take haramun ce ga kowanne namiji yha shigeta,to hakan bazai taba yuyuwa ba dole ki tashi daha yaudararren maganar daya miki matukar kina so ki karisa guntun rayuwar da ta sauramiki a cikin su lafiya" Kowanne lokaci cikin kwarin gwiwata nake tsayawa a gabansu,saidai yanzu ma nemi wanann kwarin gwiwar narasa shi,sai ma sunkuyar da kaina danayi kawai ina jinsu har suka gama masifarsu mai hade da gargadi suka bacewa ganina. Tambaya daya anan shine"shin zan iya abinda suka umarceni da yi,wato cire ɗigon soyayyar yah sameer data darsu a cikin raina a daren??". Da safe dana tashi kokari nayi na katse duk wani tunani daya shafi abinda yah faru a daren jiyan daga cikin raina,saboda halina ne banason duk abinda zai dunga tsayawa a cikin raina yah dunga yawo lokaci zuwa lokaci. Ina Bude kofar tawa idona ya sauka akan fuskar sameer wanda ya dam jingina a jikin tasa kofar yana kallona,Murmushin dayake aikomin daga wajen dayake tsayene yasa na saduda na mika dukkan ragamar danayi niyyar rikewa daga farko,"wayyo allah yazanyi da wannan halittar da take kokarin keta rayuwata ta,shiga" Takowa yake a hankali har yah iso inda nake tsaye,hannunsa yasaka mai laushi sosai kaman ba na namijiba yah dago fuskata izuwa ga tasa. Kallon kallo muke yi a haka kowa yana enjoying yanda zuciyarsa take shigomasa da shauki. "Dafatan wannan kyakykyawar kanwartawa kuma matartawa tanajin abinda nake ji a cikin raina,sannnan kuma da yanda na kwana cikin begenta da kuma son kasancewa a kusa da itah" Har zuciyata tana kokarin sallamasa kaman yanda take da burin na barta tayi abinda take some tun lokacin dana hada idona dashi. Saidai kuma abinda zai biyi baya nake tunanin,ni ba kowacce sauran yam adam ce mai yanci ba,kowa yana da ikon yin abinda yaga dama,amma ni bana da wannan ikon koda nayi niyyar yin hakan. Jan numfashi nayi mai karfi kafin na sauke hannunsa dayake kan fuskata nayi saurin shigewa kitchen,nasan abinda nayi ban kyautaba kuma bazai ji dadin hakanba,saidai hakan shine yafi masa kuma yafimin,yaj kamata nayi nesa dashi tun ina da damar hakan. Shiryawa nayi kana na shiryah farouq muka bar gidan,saleemah kuwa tun lokacin da aka dawo da ita ba wani haduwa muke sosai ba. Duk hanyar dazan bi dan naga na gujewa haduwata da yah sameer abin yaci tura,dan koyaushe yana mkaale dani yana min murmushi ko kuma bani hakuri wanda nikaina bansan mai yayimin ba. Yauma ina cikin aiki a office naga yah shigo yah samu kujera yah zauna,dago idona nayi na kalleshi kafin na cigaba da yin abinda yake gabana. Gyara kwamciyarsa yayi akan kujerar dan dama bansa a raina zai fita lokacinba,har nagama aikina na tattara kayana yana zaune yana danna waya,wucewa nazoyi ta wajen dayaje zaune aikuwa karaf naji ya zawoni zuwa kan cinyarsa,zuya idona nayi zanyi magana yayi saurin nunamin bakinsa nayi shiru. Hakan kuwa na tsinci kaina dayi wato bin umarnin daya bani. Tashi yayi daga kwancen dayake yah hada kirjina da nasa ya rungemeni sosai,banyi kokarin raba jikinnamu ba dan bazanyi karyah ba ina tsintar kaina cikin farinciki idan hakan ta kasance. "Meyasa sameemah kike guduna a kkda yaushe,sau nawa zan fadamiki nesanta ni da kike daga kusadani Yana cutardani,sau nawa bakina zai cigana da furtamiki cewa Yana sonki sanann Yana kaunarki,kece mahadin rayuwarsa,sameemah babu karyah a cikin maganar daake miki. Dagoni yayi domin naga hakikanin gaskiyar a cikin idonsa wanda ko ban ganiba nasan abin hakane,cigaba yayi da furta kalmomin da suke sakani jin ina raye,ta wani bangaren kuma suke kasheni sannan suke kara nisantani daga gareshi,yaushe bakina zai iyha buduwa yah sanar dashi halin danake ciki,anyah kuwa zan iyya zure wannan rayuwar da muke ciki. A duk lokacin dana kwanta na tashi sai shedanun sunyi kokarin mallake jikina da kuma ruhina,wanda dama hakan shine burinsu kuma sun fara samun nasara. Hannuna na saka a bakinsa domin banason cigaba da jin wanann kalmomin da dama nariga nasan suna cikin ruhinsa, "Yah sameer kayi shiru da fadin wannan kalmomin nasan dama Akwai su a cikin zuciyarka kuma da gaske kake duk abinda ka fada" "Idan Har kinsan da gaskene meyasa kika kasa bani dama sameemah akan mu koma zaman da kowanne ma'aurata suke,ko baki da lafiyane,idna akwai wata matsala ki fadamin" Saurin kallon idonsa nayi tareda jijjiga masa kai da sauri,da hankalin sa yana kaina sosai da zai gano shock din dana shiga a lokaci guda. Ta shi nayi daga kan cinyasa nayi waje,shima dayaga hakan biyoni yayi muka tafi gida,a hanyama babu wanda yace wa kowa komai. Magana muke jiyowa daga dakin Saleemah lokacin da muka shigo gidan,muryar ta babbar matace da alama kuma sameer yasan wacece,dan hannuna yasake da sauri ya nufi dakin saleemah din,nima nawa dakin na wuce domin canja nawa kayan. Ina jin lokacin da Saleemah ta rako matar tana ta yimata shagwaba amma ban fitoba dan bana son shishshigi a lamurana sosai. Can wajen magribane sameer yashigo dakinnawa yake cemin doctor maryam ce kanwar hajiyya fatima tazo,bata kasarnan taje karo karatu jiya ta dawo,zata fara aiki a sibitin cikin barrack dim,toh kawai nace masa dan yamzu yawancin lokuta yakanzo dakina yayi ta min hira koda bazan amsaba,nima har na saba da zamansa a kusadani yanzu shida farouq,idan babu daya sai na yi ta jina cikin kadaici. Kiran sallane yasa ya tashi ya tafi masallaci,nikuwa da ba yi nake ba ina zaune ina cigaba da aikina. Sake shigowa yayi a karo na biyu saikuma naga ya tsaya daga bakin kofar kamar mai nazari. "Sameemah kinyi sallah kuwa fitata daga dakinnan?" Tambayar ce tayimin wani giff a cikin kirjina har tasa nayi shiru narasa wace irin amsa zan bashi. Shiru nayi ban ce komaiba sannan ban tashi daga inda nake zaune ba,har nabude baki zan cemasa bana sallah sai kuma naji yace, "Shin mai yake damunki sameemah,tunda nake dake ban taba ganin kinyi sallah ba,nasan yanzuma cewa zakice bakya sallah amma kuma bahaka bane,saboda tun sanda nake zuwa office dinki ban taba ganin kin tashi kinyi sallah ba,wane irin al'ada ne zayyi wata guda yana zuba uhm?" Gumine ya fara karyomin ta ko ina a cikin jikina,shin mai zancene ma tukunna. "Ba wasa da sallah kike ba sameemah,kwata kwata ma batada lokacinki mai yasa haka,kuma ina kukada dake zaki saka farouq yaje masallaci amma ke bakya zuwa yij sallah,dan muyi bauta aka turomu duniyayr nan sannan wajibice akan kkwa babu wanda aka daukewa,Allah yana cewa a cikin alqur'ani : Wama kalaqtul insi wal jinni illah .........." "Liya'abudun" Nayi saurin karisamasa numfashina yana cikowa,yah sameer naji kuma zanyi yanzunnan. Kallona yake da mamaki saidai shima tasa fuskar babu alamar wasa a cikinta. Bandaki na shiga na dauro alwala jina ke kaman na junduma ihu saboda tunowa irin azabar da zan fuskanta. Lokacin dana fito baya cikin dakin,hakan yasa nayi ajiyar zuciya tareda komawa na cigaba da abinda nakeyi.wayata naga tana haske,ina dubawa naga sunan husband,yaushe kuma haka ta faru,kenan shine yamin saving number sa. Ɗauka nayi na kara a kunnena domin jin mai zaice, "Kinyi sallahr ne?" Uhm kawai nace masa a taikace kafin ya kuma cewa, "Kizo dakina yanzu ina son ganinki to" Daga haka ya kashe wayar,nima ajiyewa nayi ina tunani,mai zai cemin wanda ba zai fada a dakina ba. Kawar da tunanin hakan nayi kafin na dauki gyalena na nufi hanyar dakinnasa,dadai nazo shiga dakinnasa na hadu da saleemah saidai banda harara babu abinda ta iya yi dan shakka ta takeji ba kadan ba kuwa. Tura kofar nayi nashiga batareda nayi sallama ba,a kan kujera naganshi yana wani rubutu. "Zaki shigo dakin mutum amma babu sallama,sannan idan anyimiki ma bazaki amsa ba koh" Duk da hakan halina ne amma saina tsinci kaina da jin babu dadin yanda yake fadar hakan,bakina nabude kaman wanda yake ciwo na ce, "Salamu alaikuma" Amsawa yauyi tareda tahowa inda nake,kama hannuna yayi ya zaunar dani a bakin gadon shikuma ya zauna a kasa na, "Barka da zuwa dakin mijinki karon farko tun aurenki,nayi farinciki sosai da kika amsa gayyata ta seemah" Seemah!! Shine abinda na fada a cikin raina,yau kuma lallai kam. Kama hannuna yayi yasaka a cikin nasa kafin yace, "Ina matukar son rayuwa tareda ke seemah amma kinki amincemin muzama abu daya cikin inuwa daya,duk da nasan kema kina da bukatar hakan,ina sonki sosai sameemah amma naga alama kinfi son ki ganni kullum cikin kewarki da son kasancewa tareda ke koh" Maganganunsa kashemin zuciya suke ba kadan ba,ko kadan banason ganinsa cikin wanann halin,hakan yana cutar dani,musamman da nasan cewar nice silar hakan,yah aureni yah fara sona nima ina sonsa amma kuma na kasa yimasa abinda kowacce mace zatayimasa,duk da zuciyata tana kin yarda amma nasan saleemah tafini a wajensa,tunda zata iya yimasa abinda ni bazan iya yimsaba,kaitona da zamtowa wani bangare na rayuwarsa wanda zai zame masa ciwo ba maganiba wayyo allah nah!. Rintse idona nayi tareda saurin kawar da bakina daga nasa bakin wanda yake kokarin hadawa da nawa,bazanyi wanann gangancinba ban shirya ganin gawarsa a gabana ba tukunna,ina cewa zan iya rasa komai bayan ummah tah sai yanzu nagano duk zancene,rasa wannan ruhin da baisan komai ba sai soyyayyata abune da bazan iyah zurewa na sam,dan haka bazan iya yin abinda zamyi danasani ba koda kuwa zuciyata hakan take matukar bukata. Kamo fuskata yayi yana kallona ko akwai abinda yake damuna,saidai ko kusa naki bude idona wanda nasan zuwa yanzu sun tashi daga kalar irinna bil'adama,kamani yayi yah rungumeni a jikinsa yana magana cikin sanyin rai. "Seemah narasa gane mai yake damunki,nace miki idan bakya da lafiya ki sanar dani bazan iya zurewa zamanmu a haka ba sameemah,ni namijine mai matukar bukata,na fadamiki idan wani abune nayi miki ki fadamin zan gyara,amma idan kika hanani kanki abin zaimin yawa seemah,bazan iya dauka ba sam,ina kaunarki sosai fiye da yanda bazan iya misaltawaba kiyimin afuwa da kuma uzuri dannima haka na tsinci kaina ciki. Horonki yana gasanj ba kadan ba,bansan har zuwa yaushe zancigaba da jiranki ba,koda babu ke dole zan kara aure saboda bazan iyah zama da mace daya ba,amma yanzu tunda na aureki banda burin sake Lauren wata macen kece dama zabina na dade ina jin wani abu a game dake tun kina karama sameemah,nasha kuka daki ina tambayar kaina mai yasameni nake sha'awarki bayan kin kasance muharrama a gareni,saidai daga baya ganin abin ba zai wuceba yasa na yanke hukuncin nesanta ki daga inda nake tun lokacin da ummah tana da rai. Amma yanzu ke halaliya tace sameemah karki bari wani abu a cikin ranki ya dakushemana farin cikinmu,inason yin rayuwa dake har zuwa lokacin da numfashina na karshe zai fita" Saurin zare jikina nayi daga nasa ina matsawa can gefen gadonnasa,wani abu naji yazo ya tokaremun makogaro,ganin banida ikon yin abinda mijina yake bukata daga gareni,duk ina bukatar sallma masa kaina amma bazan iya ba domin gangar jijin ba mallakina bace,an riga an gama iko da ita. Wani irin kuka na fashe da shi karon farko kenan bayan ummah ta ta rasu sai yamzu na samu ikon yin kuka. Wani irin zafi da tafarfar fasa zuciyata takeyi yayinda nake jin wani zafi yana tsaga sassan jikina,duk da haka ban sareba saida na tattaro sauran kalomomin dake bakina nafara cewa, "Kayi hakuri yah sameer! Kayi hakuri mijina ! Kayi hakuri masoyina. Hakika da ina da ikon aikata abinda kake bukata dana aikata,koda kuwa hakanne zai kawo karshen wanann wahalelliyar rayuwartawa,banida ikon yin nesa dakai ko kuma yi maka musu saidai hakan baya cikin abinda zan iya aikatawa. Barinka kana isowa har kusan jikina ma ka tabani ba karamin kokari nayi ba akan hakan yah sameer,inajin kunyar kaina a halin yanzu,ban taba jin banason yanayin halittata ba sai yanzu,amma babu yanda zanyi hakan shine kaddarata dama tun farko banida ikon hanawa barekuma canjawa. Ni wata irin matace sannan kuma wata irin masoyiyace wanda bazata karu da mijinta da komai ba sai kawo masa damuwa da kuma hatsari,zan kasance mai son kai idan nace kacigaba da nuna min so ko kuma tunawa dani,dan haka kayiwa allah badanniba sai dan allah yah sameer ka koma rayuwarka da kakeyi a baya kaman kk wanne mutum mai farin ciki,ka barni nacigaba da rayuwata kaman yanda nakeyi wacce banajin tausayi banajin shauki sanann banjin dadi,ta hakane kowa zai zauna cikin farin ciki nima kuma na rayu ina kallonku kusa dani " Shiru nayi da magana ina cigaba da rusa kuka mai tsima duk zuciyar wanda yake saurarona,kirjina na rike gam wanda yake barazanar fashewa da hannuna,shima sameer dayaga haka rarrafowa inda nake yayi idonsa yana zubar da kwallah,wamda nasan ganin halin danake cikine yah saka shi. Rike dukkan hannayena yayi da nasa hannun kafin yace cikin karfin hali. "Menene yake faruwa da rayuwarki sameemah,kiyimin magana naji kinji ki daina rike abu ke kadai haka" Bude bakina nayi zance masa wani abu sai kuma naji bakina yah cika da wani abu mai dandanon gishiri,zubar dashi nayi da sauri,anan naga ashe jinin ne har da guda guda,wani tarin ne yasake sarkeni da karfi mai matsanancin ciwo. Jinine yake ta zuba daga bakina kaman famfo wanda da kadan kadan naji jikina yana shikawa har saida yah zamo dishi dishi nake ganin komai,bude idona nayu dukka akan fuskar masoyinna wa kafin namayar na rufe da sauri wani duhu ya lullubeni. Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎31~32💎 💎*sameer a madubin gani*💎 Duk maganar dake fita daga bakinta ban saka su cikin madubin fahimta ba saida naga lagababbben jikinta yayi kaca kaca da jini akan kirjina,babu abinda nake maimaitawa a cikin raian sai innalillahi wa innna ilaihi rajiun,dan na rasa mai zanyi,babu abinda kwakwalwata take haskomin sai kokarin rasata da nakeyi bayan nayi kuma rashin ummah ta a baya. Mika hannuna dayake rawa nayi na dauki waya ta,da kyar ma na samo number dake farkon call log dina na danna kira,saleemah ce ta daga tareda cewa lafiyay?. Cikin magana a rarrabe nacemata, "Salee......mah ddddakina.... Samee. ....mah ce" Da sauri ta kashe wayar ta shigo dakin,yamda muke zaune ta rankwafo akan kirjina haka saleemah ta samemu ko motsawa na kasa yi. Jinin da taga yana zuba a bakin sameemah ne ya razana hakan yasa ta koma da sauri dakinta ta dauko waya tareda danna number doctor maryam. Ina nan zaune har suka shigo suka dagata daga jikina ita da doctor maryam din zuwa cikin mota. Bayan sun tafi da wasu mintuna ne na tashi na bi bayansu,ko tunanin sanja kayan dake jikina banyiba,burina kawai bai wuce naga halin da take cikiba. Tun daga bakin kofar shiga wajen doctor maryam ta kama hannuna ta zaunar dani tareda yin magana cikin kwanciyar hankali. "Ahah bai kamata kashiga a haka na hakanma da wannan daren sameer,matarka tana da rai yanzu hakama mun saka mata karin ruwa saboda anyi sa'a jininta bai kai a kara mata ba,saidai akwai bukatar ta ringa cin abinci mai saka kujari. Yanzu kai kuma kaje ka cire kayannan kasaka wasu in san samune ma sai gobe ka dawo,domin zamu kulada ita sosai. Haka badan nasoba na juyo da baya zuwa gida amma hankalina gabadaya yana kan sameemah da kuma wane hali take ciki. Haka na kwana banyi bacci ba ina kai kukana ga allah,da safe kuwa tun kafin garin ya waye sosai kama hanyar asibitin. Murmushi doctor maryam tayi data ganni a wannan lokacin. Dakin da sameemah take kwance ta rakani,a kwance take tana kallon silin kamar mai tunani,lokaci daya tausayinta ne yakamanni lokaci guda ,abin tashin hankain ma shine bansan mai yake damunta ba. Karisawa inda take kwance nayi a hankali kaman mai sanda,juyo da idanuwanta tayi kana ta saukesu a kaina,kara mayar dasu tayi zuwa inda take kallon tun farko kafin shigowata dakin. Hannu nakai zan rike nata wanda baya dauke da karin ruwan a jikinsa,amma sai tayi saurin janye hannun tanamun gargadi da idonta akan kar na tabata,banyi yunkurin sake tabata a karo na biyuba saima tambayar ta danayi yha jikinta. Motsa baki kawai tayi kaman zatace wani abu amma batace komai ba. Doctor maryam ce ta shigo dakim da tire a hannunta,ajiyewa tayi a gefen tiren tana cewa, "Patient a ta shi a ci abinci ko tunda jiki yayi sauki" Dago da idonta tayi ta zubasu a cikin na doctor maryam din,wanda hakan yasa ta dan ja da baya tana karewa sameemah kallo kaman mai nazarin wani abu,can kuma ko mai ta tuna sai kawai ta kawar da tunanin tareda mika hannun ta domim taimaka mata ta tashi. Hannun doctor maryam din ta kama ta tashi,maimakon ta saki hannun sai ta,rikeshi gam kaman wani yana son kwance hannun doctor maryama din daga nata. Matsawa kusada ita nayi domin rikota amma sai ta matsa jikin doctor maryam kaman zata koma cikinta,magana tayi cikin dashshshiyar murya irinta marar lafiyah. "Yah sameer bawai ina gudunka bane amma dan allah ka bani lokaci tukunna matsowarka kusadani akwai matsala a halin yanzu" Ina jin hakan na daga mata kai alamar na fahimta saidai hakan bai yimin dadiba ,itama ta fahimci hakan sannan nasan kaman yanda nake bukatar ta a kusadami koyaushe nasan itama tanajin hakan. Alama doctor maryam tayimin akan na bata lokacin. Cire karin ruwan dayake hannunta tayi kafin ta jata zuwa bandaki domim ta gyara bakinta,basu dadeba suka fito har sannan sameemah tana jikinta kamar wata karamar yarinya,abinne yaban mamaki domin nasan halin sameemah sarai,bata nuna ita yarinya ce sai a gaban ummah kadai,tunda ta rasu kuwa tafison komai tayi da kanta basai an taimaka mata ba. Abincin ta saka a plate ta fara bata tana ci har taci da dan yawa,komawa tayi ta kwanta kaman yanda take a farko. Fita doctor maryam tayi sannan tayimim alamar na biyota zuwa office dinta. Muna fita wata nurse kuma taje domin kula da itah. Saida ta zauna akan kujerarta kafin ta nuna min waje akan na zauna. Min dan samu sakanni a haka kafin ta fara yimin magana. "Hakikanin gaskiya sameer bamuga komai ba gameda abinda yake damu matarka,da farko nayi mata gwajin ciwon zuciya amma sai na samu kalau babu wata matsala,sannan abin mamakin shine yanayin yanda ta zubda jini bakai ace ma zata iya rayuwa ba amma kuma da muka gwada sai mukaga jininta normal ne bayyi wani low sosaiba. Komadai menene yasameta yanzu komai normal ne babu abinda yake damunta saidai dan gajiya kawai da tayi amma babu wata matsala,zuwa nan da yamma zamu iya sallmar ta. Godiya nayi mata bisa kokarin da tayimana kafin na koma wajen sameemah,dan yau kam babu batun aiki. Nursing din data ga shigowa ta fita tayi ta bamu waje nikuma na zauna akan kujerar da ta tashi din. Banyi zaton zatayi magana ba amma kuma sai na ji tace, "Yah sameer kayi hakuri da abinda yah faru sannan ina mai baka hakuri a gameda halina,saidai alfarma guda daya zan nema a wajenka ita ce dan allah karka tambayeni abinda yake damuna" "Shikenan zan yi kokarin yin hakan tunda shine burinki amma ki sani badan nasoba zanyi kuma bazanyi miki karya ba hakan zai dameni matuka" 💎*sameerah a madubin gani*💎 Tunda mukayi wanann zancen da salma ta daina tambayata akan wane hali nake,saidai kuma koyaushe idan muka hada ido ina kallon yamda take bina da kallon tausayi. Hakan na cigaba da zama da umatuje cikin halin bakinciki da rashin walwala,bai san ya na tashiba ina lafiya,mai nake bukata ko kuma mai nake so daga gareshi,duk yah tsallake wanann abubuwan. Kullum cikin sakani ayyuka yake nayi masa kaza nayi masa kaza,duk da nace naji nagani zai jure amma nasan hakan da matukar wuyah,kawai namika lammurana ne ga mai duka,da burin watarana zai iya kawomin dauki a rayuwata. Zancen aurensa da mufeedah kuwa kullum dada hau hawa yakeyi,wani lokacin ma akan gadona a cikin dakina zai tsiri waya da ita dan kawai naji haushin hakan,haka zan juya masa baya nayi ta kukan zuci har bacci yah daukeni a haka. Da safe dana tashi kitchen nashiga domin yin abinci karyawa,yanzu nikadai ce nakeyi kasancewar na hana salma shiga kitchen din,saboda cikinta yana bata wuya tun sanda yah shiga wata na biyar,kullum cikin zuwa asiniti sukeyi ita da alhaji bala,wannan abinba yakara wutar tsana tsakanina da hajiya mairo domin na daukewa salma girki ni nakeyi ni kadai. Wani lokacin da gangan zata tsiri yin abincin sadaka badan allah ba sai dan nasha wahala,duk abinda takeyi na tura mata aniyarta nasan idan ma bata daina ba dole ai akwai mutuwa,idan na mutu shikenan ai. Yamzu bikin umaruje da Mufeedah yakama saura sati daya,saboda tsabar samun gindin zama a cikin gidamnmu ake hidimar bikin harda na dangin amaryar,dan hajiya mairo ce ma ta dauki nauyin gyaran amare da kuma kwalliya. Tun safe nida masu aiki muke kwabin fukawar cincin har kusan magriba muna aikinnan,duk wanda yaganmu sai ya tausaya mana saboda yanda muka kode kamar tsohon kaya. Salma ce ta shigo kitchen din wai zata tayamu suyah,hannunta na rike na karbi matsmin kafin nafito domin rakata dakinta,a falon muka hadu da hajiya mairo ita da hajiya zulai mahaifiyar Mufeedah. "Ke ya naga kin fito daga wajen aikin,kun gamane iye" "Bamu gamaba barin na raka salma dakinta tukunna zanje mu karisa" "Ita batada kafa ne da bazata iya tafiya dakin dakanta ba,ko munafurcin za'a gwadamin,hmmm ke wai mai yar uwa ko,shine kika hanata aikin komai a gidannan kika karba kikeyi,zubamiki ido nayi zanga lokacin dazaki kasa ko kuma kikasa zaman cikin gidannan ki karbi takardarki,dan wallahi dama banda aikin asiri ai dana yafi karfinki guzuma kawai. Yanzuma ina samun suruka zaki tattara naki ya naki ki bar gidannan" Wannan kalmomi na hajiyah mairo sun dade da haddatuwa a cikin kunnena saidai duk da haka ko yaushe idan na jiSu komawa suke tamkar sabi dall a zuciyata. Salmace ta rike hannuna tareda yimin murmushi karfin hali kafin tace, "Bantaba sanin duk zamana danayi dake a gida kina da irin wanann halinba,zuriyah da kuma tawakkali wanda ba kowace macece zata iya ba,inshaallah zakiga haske a cikin rayuwarki anty sameerah,ina alfahari dake sosai" Kwallah ce ta zubomin wanda nake ta kokarin mayar da itah lokacin da salma ta sau hannuna ta shige cikin dakinta da sauri. Share hawayen nayi na koma wajen aikin da mukeyi na cigaba . Sai wajen isha kafin muka gama wannan aikin,ko ina a cikin jikina ciwo yakeyi kaman an sassaramin shi. Dakyar cikin dauriya naja jikina na shige nawa dakin,bandaki na shiga da sauri na tari ruwan dumi mai zafi na fara gasa kowacce gaba ta jikina,na dade inayi kafin na dawo na haye gadona,dan dama nayi sallahr isha tun sanda muke aikin,batun yin hadda kuwa wanda zan kai wa malaminmu babu zancenta dan bazan iyaba koda naso yin hakan. Da haka ina nan kwance bacci yah fara daukata,gashi nasan zamana acikin gidan yakusa karewa,saboda gobene za'a daura auren Mufeedah da mijina kuma ko naki ko naso nasan ban isa nayi kishi da ita ba,dolene na bar gidannan na basu waje su yi rayuwarsu,dan duk wanda yaga kallon da umaruje yake yiwa Mufeedah yasan ita ce zabinsa kuma muradinsa. Can cikin dare wajen goshin asuba naji hayaniya taki karewa a cikin gidan,lalumar zanina nayi na dora akan rigar baccina na nufi kofa domin naga mai yake faruwa,nikadai ce kuwa a dakin umaruje baya nan ya tafi wajen abokinsa a Sokoto,ko yana nan ma dama baza'a sameshi a dakina ba,dan mun daina hada daki dashi tun waccen satin,a cewarsa shi ya gaji da hada daki dani ma. Murda kofar nayi a hankali na fito zuwa falo,hajiya mairoce a tsaye sai karkarwa jikinta yajeyi,itama hajiya zulai din haka na fanta,ganin salma a zaune a gefensu ne daya gefen kuma Mufeedah ce da kawayenta a zaune. Matsawa nayi gefen salma tareda tsugunawa na tambayeta mai yake faruwa cikin murya kasa kasa. Kallona tayi kaman bazata ce komai ba sai kuma tace, "Anty sameerah umaruje ne yayi hatsari a hanyarsa ta dawowa daga sokoto dazu,wai tafiyar dare suka dauko sai babbar mota tabi ta kansu,shi dayan ya rasu amma umaruje baijj ciwo sosai bama sai kunkumin sa daya bugu yanzu haka an taho dashi asibitin garinann suna hanya" Jin maganar nake tana yawo a cikin dodon kunnena,hatsari umaruje yayi hatsari,mjina fah kenan. Saurin tashi nayi daga tsugunnen danake ina kokarin saita numfashina dayake barazanar daina shiga cikin huhuna. Inna lillahi kawai bakina yake furtawa babu adadi,ganin zaman ma bazai kaini bane yasa na koma dakina da sauri na dakko kayana nasaka sannan na dauko karamar wayata da nokia na dawo falon ,sannan har an fara shiga mota domin tafiya asibitin saboda an iso dashi. Nima kama gidan baya nayi na mota nashi ga da sauri,ina ji hajjya mairo tana zagina amma bata ita nakeba a halin yanzu. Muna isa asibitin kowa yah fito daga motar muka tafi ruuu harda mamar Mufeedah da ita kanta Mufeedah da kuma wasu kawayeta. Wata nurse ce tayi saurin taremu tareda cewa bazai yiyu mushiga sanann ba. Komawa mukayi wajen jira dukka muka zauna,bakina banda motsi wajen kiran sunan allah ba abinda nakeyi,duk lokacin da muka hada ido da hajiya mairo sai ta watsamin harara. A raina nace keda danki yake kwance a sibiti kiyi ta kanki mana. Muna nan zaune har akayi kiran sallah nafarko,tashi nayi na tambayi wata mai gogegoge inda zam sami ruwan alwala,nayi sa'a kuwa ta bani ruwan. Ina jin hajiyah mairo tana cewa, "Dama ai munafurcine yasa ta biyomu dan taga mai ya sameshi ta dora a gaba,dangin tsiya kawai" Ina jinta banyi magana ba har na tada sallah nayi raka'atainul fajari. Sannan nacigaba da addu'o'i dakuma domin nemawa umaruje lafiya. Har na idar sallah likitan bai fito daga dakin ba sai can wajen rana ta kusa fitowa kafin ya fito daga dakin. Dukkan su tashi sukayi domin nufar inda yake,nima tashi nayi daga kan dan kwalina nayi wajen sa da sauri. Kallonmu yakeyi kaman ba zaije wani abu ba sai kuma yace, "Idan Yana da mata to ta sameni a office dina ita da matarsa" "Eh likita yana da mata amma kuma akwai wacce za'a dauramusu aure yau dan haka itace zata zo taji mai yake faruwa" "To shikenan itama wacce zai aura din zata iya zuwa taji mai yake faruwa dashi,amma matar tasa ma tajo" Haka ba yanda hajiya mairo zatayi na bisu a baya zuwa office din likitan domin jin mai yake faruwa. Lokacin da muka shiga a bakin kofa natsay amma ina jin duk abinda likitan yake cewa. "Toh hakikanin gaskiya hajiya d'an ku bai samun raunika sosai ba a jikinsa amma yasamu wata matsala sakamakon buguwar da kunkuminsa yayi yah taba mazakutar sa,wanda ina mai baku hakuri akan abinda zakuji amma gaskiya bazai iya haihuwa ba a halin yanzu .........toh fah Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎33~34💎 Shiru dakin yayi babu wanda yace wani abu jin abinda likitan yah fada,sai shine yasamu kwarin gwiwar cigaba da cewa. "Sannan kuma koda mun sallmaeshi zai iya samun wata guda kafin yah fara tafiya saboda yanayin buguwar da yayi,wannan shine sakona a gareku ina fatan ku kasance masu tawakkali da kuma karbar kaddara a duk yanda tazo muku" Dukkanmu juyowa mukayi domin fitowa daga office din,a bakin kofar muka hadu da alhaji bala shima dawowar sa kenan daga tafiyar dayayi yaji abinda yah faru,rabewa yayi ta gefenmu yah shiga office din zuwa wsjen likitan. Mukuwa hanyar dakin da umaruje yake muka nufa dukkanmu. A kwance yake yana kallon sama,an saka mayafi irin na asibitin a kunkuminsa zuwa kasa,in ba kaji abinda yake faruwa dashi ba bazaka ce baida lafiya ba. Samun waje hajiya mairo tayi ta zauna kusada shi tareda yi masa sannu cikin murya mai dauke da damuwa. Kallon hajiya zulai tayi kafin tace, "Ina hajiyah zulai zancen daurin aurennan saidai a daga sai yah warke koh?" "Wane daga auren kike magana akai hajiya mairo,kunnenki bai jj abinda yake damun danki bane,amma duk da haka kike kokarin hadashi da dana,toh wannan zancen babu shi kwata kwata,dan ina ji ina gani bazan hada Y'a ta da juyaba wanda bazai haihuba" Itama Mufeedah share hawayen dayake idonta tayi kafin tace, "Gaskiyar ummah ne bazan iyah aurensa bayan nasan bashida lafiya,koda an daura auren ma dole za'a warwareshi bare allah yah taimakeni ba a dauraba dama,dan haka sali alin babu abinda ya hada" Baki hajiya mairo tasaki tareda cewa, "Hajiyah zulai kinsan abinda kike fada kuwa keda yarki,kanmu a hade zamu hada wannan auren amma dan kawai wani abu yah faru shine zaku watsamin kasa a ido?" "Kai kaji hajiya mairo dan allah,banda kina so ki cutar da Y'a ta dan kinga ba y'ar ki bace naki yarda shine laifina,wannan ai son kaine,ina ganin fah yanda kike zaluntar y'ar wata dan kawai tana auren danki" Har hajiya mairo zatace wani abu alhaji bala yayi saurin katseta ta hanyar cewa, "Hajiyah mairo ya isa haka,gaskiyar tane abune na kowa yana da hakki dan haka tunda bazata iya aurensa ba shikenan,kuma koda anyi auren tace bazata zauna dashiba dole a raba auren haka shari'a tace" Kuka hajiya mairo ta fara ganin abin yama neman fin karfinta,babu wanda yah kulada ni a cikin dakin sai lokacin da alhaji baka yamin magana,dukkansu harda hajjya zulai da suke shirin fita daga dakin kallonsu ne ya dawo kaina. "Kema kina da zabi sameerah akan zama da umaruje,kindai ji mai likita yace kan cewa bazai kara haihuwa ba,shin zaki zauna dashi ko kuma kina neman takardar ki a wajensa na ya sawwakemiki?" Saurin jijjiga kaina nayi tareda cewa, "Zan Zauna dashi abba" Kowa kallona yayi da mamaki harda hajiya mairo da take share majina,magana alhaji bala yasake yi a karo na biyu cikin tabbatarwa, "Shin kin yarda da zabin da kikayi,idan harkin amince ki zauna dashi akwai sharadin banason kuma wata maganar ta fito daga baya,idan ma lokaci kike so a baki na tunani duk za'a baki amma kiyi tunani" "Bana bukatar lokaci nayi tunani,dan dama hakan shine zabina tun kafin hakan ta faru,nayi wa zuciyata alkawarin cigaba da zama dashi cikin kowanne yanayi da kuma hali har karshen rayuwata,saidai idan shine yayi ra'ayin sawwakemin saboda yagaji da zama dani,toh yanzuma hakanne idan yaga bazai iya zama daniba xai iyha sawwakemiin ,kuma ina mai sake bashi hakuri bisa hanyar damabi na aureshi ba tareda yardarsaba,dan haka duk abinda zaimin bazanga laifinsa ba ko kadan kuma zan cigaba da zama dashi har karshen rayuwata ......saboda ina son..sa sosai har zuciyata,haihuwa kuma dama allah ne me bawa mutum kuma zai dauke a duk lokacin dayaga dama,dan haka banida matsala da rashin haihuwarasa a gameda zamana da shi,ina fatan allah ya bashi lafiya yah tashi kafadunsa" Ina gama fadan hakan na rushe da kuka wanda dama yake cina kwana da kwanaki,ganin abin zai min yawane yasa na bar dakin da sauri nayi waje domin na samu zuciyata ta yi sanyi koda kuwa dan kadanne. Na dade a zaune a waje ina ta tunani sai wajen azahar tukunna na raba na shiga dakin,babu kowa sai hajiyah mairo itada yusrah,shikuma umaruje akan gadon ,babu wanda yake cewa komai a cikinsu,nima daga sallma ban sake cewa komai ba na shige bandakin kaman wata munafuka. Fitowa nayi na shimfida dan kwalina a gefensu na tada sallah,lokacin dana idar na dade ina addu'a kafin na shafa na koma gefe na Zauna. Dire bane ya shigo dauke da kula a hannunsa inji salma wai,karba hajiya mairo tayi ta bude,shikaface da miya sai kuma farfesun hanta a daya kular na marar lafiya. Had'a ido mukayi da ita nayi saurin dauke nawa idon zuwa gefe,zuba abincin tayi a plate ta mikawa yusrah sannan ta zuba farfesun a plate daga gani umarujen zata bawa,tashi nayi da sauri na karbi nasan daga hannun sa akan zan bashi,xuciyata tana dardar dan banyi tunanin zata sakemin plate din ba sai kuma naga tasake min. Plate din abincin yusra ta dauka tareda cewa, "Ummah inaga muje waje mudin ko" Batace komai ba amma kuma tabi bayan yusrah suka barmu mu kadai a dakin. Hannuna nakai a hankali na taimaka masa yah tashi kadan kafin nasaka masa filo a bayan kansa,nishi yayi irin na maijinya idan ya motsa inda yake masa ciwo. Sannu na fara jera masa har bansan iyah yawan yanda na fada ba,kallona yake kaman mai son cewa wani abu sai kuma yayi shiru,abincin na diba kadan a cokali na fara bashi,da haka har yaci da dan yawa kafin ya matsar da kansa,ruwa na debo hade da maganin da zai sha a lokacin na bashi. Saida naga yasha tukunna na juya domin barin wajen gadonnasa,kamo hannuna naji yayi tareda jawoni zuwa kusa da shi. "Sameerah" "Na'am. .....Akwai abinda kake bukata ne" "Ahah hankalin ki kawai nake bukata ki bani" Juyawa nayi muna kallon juna idona har yakawo hawaye, "Meyasa kika amince da zama dani duk da kinsan abinda yasameni?" "Karima miyasa kacigaba da zama dani duk da kasan cewa cutar dakai nayi ta hanyar aurenka a da yaddarka ba?" "Saboda ina jiran wani lokaci dazan sallameki amma kafin sannan saina hukuntaki a gameda abinda kikayimin" "Nikuma na amince da zama dakaine saboda ina sonka sannan nayi alkawarin zan zauna dakai a duk halin dakake ciki,domin kaine mutumin da a dalilinsa nasan wace irin rayuwa nake ciki kuma harna fito daga duhu nagane gaskiya" "Banbancinmu dake kenan sameerah ke macece da duk wanda yagane yanda kike to yayi dace,ina rokon da ki yafemin abinda nayimiki sannan ki bani damar farantamiki idan har nasamu ikon hakan" "Nima ina rokon ka yafemin sannan kuma kabani damar shiga zuciyarka da gaskiya da amana bada guru ko laya ba" "Ina farin cikin karbarki cikin zuciyata sameerah daga wannnan ranar ,ina fatan allah yah bamu zaman lafiya mai dorewa" Murmushi nayi shima ya mayarmin da kwatankwacinsa,daga haka muka fara hira muna dariya kaman ba jinya yake ba. Satinmu guda aka sallamomu daga asibiti saidai an hadomu da wheelchair saboda har yanzu baya tafiya da kansa sosai. 💎*sameemah a madubin gani*💎 Kwana na daya a asibitin doctor maryam ta sallameni saidai har na tafi gida bansan mai yake damuna ba kuma ban tambayi sameer akan hakan dannasan zancen gizo baya wuce na koki,bazai wuce shedanuna bane suka yin hukunci saboda ina shirin ketare iyakarsu. Kwana daya kenan da zamana a wajen amma har cikin zuciyata bana son barin wajen saboda doctor maryam,domin wani abu naji a yana tsargamin cikin jikina fiyeda yanda nakeji a gameda hajiya fatima. Haka badan nasoba na bi sameer muka tafi dama nima inada aikin dazanyi a office dina. Washagari tun da safe na shiryah na bar gidan,dan kwata kwata banason wani abu ya hadani da mutanen gidan,saboda baraxanar cutar dasu da akemin a kowanne lokaci idan na kusancesu. Ina dawowa na samu doctor maryam a falon suna magana da saleemah sai shagwaba takemata. Har zan wuce sai kuma naji zuciyata ta kasa aminta da hakan,dawowa nayi zuwa cikin falon na zauna a kujerar datake facing dinta. "Ina wuni doctor yah aiki" Murmushin nan tayimin wanda yake sakani sukuni kafin ta ce, "Lafiya kalau amma ban san sunanki ba gashi ninan fa dubaki nazoyi naga ya jikinnaki amma saleemah takecemin kin fita aiki" Sunkuyar da kaina nayi kafin nace, "Sunana sameemah" Jin tayi shirune yasa na dago kaina dan ganin lafiya,amma sainaga tana ta maimaita sunan a bakinta kaaman mai son tuna wani abu. "Ayyah to yah jikinnaki da fatan da sauki ko,amma da kin dan huta a gida ki na kwana biyune kafin ki fara yin wani abu mai bukatar motsa jiki sosai" "Ahah ba komai naji sauki sosai ai babu matsala" "Toh shikenan haka akeso ,ni bari natafi gida dama na tashi a aikin,saidai ina saka ran ganin ziyararki zuwa wajena kinji" Daga mata kai nayi ina murmushi,dan harga allah inason na zauna da matar bansan mai yasaba. Da zata tafi ma har waje muka raka ta nida saleemah tana kara tunamin na kawo mata ziyara. Motarta tana kulewa a wajen saleemah taja tsuka tareda cewa. "Aikin banza mutum yayi ta kalan dangi,an mallakemin uwa kanwar mahaifiyar tawama so suke a mallaketa" "Ke saleemah ya isheki haka idan ba so kike kisake cin na jaki ba kumadu,dan wallahi rashin mutuncinki yafara isata,kibarni naji da halin danake cikima ya isheni" Saurin wucewa dakinta tayi tana magana dan bata yi shiruba duk da tsorone kwance a kan fuskarta. Ina shiga daki na cire kayana nayi wanka kafin na fito domin neman abinda zan saka a cikina,jinayi an rungemeni ta baya ina dubawa naga farouq ne . "I miss you ummah,yajikinki daddy ne yace bakida lafiya dana tashi da safe ina neman ki zan tafi makaranta,yau ma kuma daddy yace karna dameki kina bacci" "Uhm bana da lafiya amma naji sauki,nima ina kewarka farouq" Murmushi yasakeyi na jin dadi,jin nace ina kewarsa nima,kitchen din muka shigs tare yana ta min surutu,duk da ban kulashiba amma ina sauraronsa,kuma nayi kewarsa sosai yini daya kawai. Tare muka ci abinci kaman yamda muka saba,kana muka cigaba da kallo. Bayan isha ina zaune farouq kuma yayi bacci a gefena sai ga sameer ya turo kofar ya shigo,zama yayi a drawer dake gefena ta gadon kafin yace cikin muryah mai dan kauri. "Ya jikinnaki sameemah" "Da sauki sosai" "Aha mashaallah,abinda yake damunki yana damuna kasancewar bansan menebe ba,ita kanta doctor maryam tacemin batasan me yake damunkiba,ina sonki sosai shiyasa nakasa kauda maganar a cikin raina" "Kayi hakuri" "Bazancen hakuri bane saboda ba abinda kikayimin,kuma a yanda nake gani wani abune yake damunki wanda bazaki iya fadaba,kuma hakan yana damunki sosai,nikuma inshaallah sai nagano ko mai nene" Saurin kallon sa nayi jin lafazin daya fito daga bakinsa,shima kallonnawa yake kafin ya tashi ya bar dakin,hannu na mika da niyyar kiransa sai kuma na fasa yin hakan,domin maganar tawa ba abinda zata rage tunda yai wannan kudirin a ransa. Da tunanin hakan na gama aikin danakeyi na kwanta. Yau nayi sa'a mutanennawa basuzo magana dani ba amma kuma wani abin da shima tashin hakalinne yah bayyano a daren,muryar wasu mutane da ba ta yan gidan bace ta doki dodon kunnena da tsakar daren. Saurin tashi nayi na nufi hanyar fita daga dakin,ina bude kofar naji wani abu kaina dimmm,rike wajen nayi ina kallon mai aikata hakan,kafin nayi yunkuri naji wani yah fisgo gashina zuwa cikin falon,dayanne yafito da farouq a hannunsa sai kuka yake. Raina ne yabaci ganin yaro bai musu komaiba amma suka yi masa wannan rikon. Gefena na kalla inda sukayiwa sameer duka jikinsa yana zubar da jini amma hakan bai sa yah kwanta ba,saleemah kuwa sai kuka take ta rungume zuhra a kirjinta. Kallonsu nayi cikin bacin rai nace, "Me kuke bukata kukayi musu irin wannan dukan" "Hhhhhhh lallai bakida kunya,har zaki tambati mai ya muke bukata,toh matsayinsa muke son yah rasa ta hanyar kawar dashi daga duniyar nan,sai musamu biyan bukata" Wanda yake rike da farouq ne ya wanka masa mari saboda ya damesu da kuka,saurin tashi na yi na fizge daga wanda ya rike min gashi na daga shi na bugashi da akan tikes din,saida kansa yah tsage,jini na ne nakejin yana kara gudu acikin jikina da alamun karfina ma yafi na dadai mutane. Kama wuyan wanda ya rike farouq din nayi na dagashi sama ina kallon cikin idonsa,jikinsa ne yafara karkarwa ga dukkna alamu yah kalli abinda yake cikin kwayar idona,jefar dashi nayi da karfi a kasa ko motsi bayyiba yah suma. Wanda yake bayan saleemah ne yah kwada mata bindigar dake hannunsa dayaga ina nufo inda yake,riko wuyansa nayi ina magana cikin bacin rai da muryar da tasha banban da tawa. "Mai ta aikata maka ka cutar da ita,mai yasa kuka kasance masu cutarwa iyee" Matse makogarsnsa nayi da karfi,saida naga yadaina motsi kafin na zefar dashi,idona ne ya sauka akan wanda yake rike da sameer,da alama kuma shine shugabansu. Tunkarar inda yake nayi,duk ya saitani da bindiga da kuma yimin alamar kar na kariso hakaan baiyyi tasiri a zuciyata,dan a lokacin kallonsa nake a matsayin wanda zai hallaka masoyina,kuma zan iya yin komai domin cetarsa saidai idan na gaza. Maida bindigar yayi kan wuyan sameer din ganin ni bandamu da nawa rayuwarba,ya kuwa yi sa'a domin tsayawa nayi cak ina kollonsa da jajayen idanuwana, "Koda ka kasheshi baxaka fita daga gidannan da numfashinka ba dan haka ka mika wuya tun ina cikin yanayin yi maka afuwa" Daga gani gargadina bai shiga cikin kunnensa saima kokarin sai ta bindigar da yayi a wuyan sameer din,.........,karar bindiga ce ta amsa kuwwa adakin tassssssss. Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎35~36💎 Firgicine ya cikani da tunanin kar ya kashemin yah sameer shikenan,saidai dana daga idona sainaga razanar da take kan idon sameer bata halin ciwo bace,da alamun ni yake kallo. Inda yake kallon nima na bi da nawa idon,sai a lokacin naga ashe kan kirjina bullet din ya Saita na dama. Mayar da kallona nayi kansa cikin ajiyar zuciya ganin a kaina abin ya sauka,saidai hakan dayayi yah nuna baya son nayi masa afuwar kenan. Zefar da bindigar hannunsa yayi yana zagayani yana cewa, "Well well ki sumar min da yara kina tunanin zan barki haka,da alamun dai soja yaje yah auro mai kamar maza,ga shikuma ita mutuwar tsaye take yi,gaskiya ta cika sojan" Lokacin daya gama juyawar ya dawo dabana ne na damki wuyansa ina murmushi kafin nace, "Ba suman tsaye ba dai fakon tsaye nakeyi,da alamun kaine zakayi mutuwar tsayen," Har nayi niyyar kafa masa hakorina sai kuma na matsar da bakina,amma duk da haka dai na yakeshi da farcena akan wuyansa,danaga jini ya fito da alamun farcena ya garwaya da jininsa sai kawai na wanka masa mari shima yah fadi. Duk abinda ya faru akan idon sameer wanda shikadaine kawai bai suma ba a falon,farouq na dauka da zuhra a kafadata nayi dakina da sauri jin karar shigowar sojoji,da alamun karar bindigar ne yajawo hankalin su. Bansan ya aka kareba ina jin dai sanda aka suka shigo suna ta magana,nikuma na kwantar da zuhra kenan,sameer ne ya shigo cikin dakinnawa da sauri muna kallon juna,karisowa yayi har inda nake ya kama kafaduna tareda yage rigar wajen da mutumin yah harbeni,wajen ya koma ya hade amma ba sosai ba saboda bullet din yana ciki,dole saina nutsu kafin na cire. "Miye hakan yake nufi iyee,yakamata kizo mu tafi asibiti" "Ahah niba asibitin da zanje kuma ina rokonka karka fadawa kowa ni aka harba,hakan ba komai zai haifarba sai matsala na rokeka" "Yanzu kina nufin nayi shiru kenan duk da abinda nagani?,shikuma wannan ciwon ki kwana dashi a haka,kuma kina tunanin sai nayi yanda kikace" "Ciwona ba matsala bace zuwa gobema bazaka ganshi ba amma idan ka fadamusu abin bazai tsaya iyah gobeba,mutumin daya harbeni kuwa ku barshi yah tafi kawai ,da kansa ma zai mutu nan da kwana uku,idan kuma baka yadda ba ka biyoni bandaki ka gani" Babu yanda na iya haka na jashi badakin domin nuna masa hujja,saboda nasan taurin kansa zai iya zuwa yah fada,dan haka na kwammaci shikadai yasan ya nake da duk mutanen barrack dinnan su sani. Almakashi na dakko na saka a wajen ciwon yana kallo na burkulo bullet din kafin na saka hannuna na fitar dashi na ajiye,ina gama fitarwa na ajiyeshi a sink din da ruwa yake fita. Wajen kuwa kaman jira yake yafara hadewa da kansa. Dakko bullet din nayi daya wanke da ruwa tasss na mikawa sameer tareda cewa, "Nasan zasu bukaci ganin bullet din koda kuwa kacemusu a jikin bango yake,dan haka gashi,yanzu ka gane mai nake nufi,idan kacemusu a jikina yake zasuce ina ciwon yake sannan a wane asibitin nake,toh banida wannan amsar shiyasa na bukaci kayi shiru please" Hannunsa yakai inda na cire bullet din yana dannawa maimakon ya karbi bullet din a Hannun a DA nake mika masa, "Har yanzu bazaki fadamin komai akan abinda yake damunkiba duk da wanda idona yaganemin,saima kokarin rufe bakina da kikeyi,ina kallon yanda idonki yasanja kala,sanann kuma kinyi kokarin cizonsa a wuyah sai kuma kika fasa kika yankeshi da farce mai hakan yake nufi?" "Nayi niyyar zuke jininsane amma kuma Akwai dalilin dayasa na fasa kawai na saka masa guba a cikin jininsa kawai,duk da haka kuma banason ka tambayeni mai yah faru dan bazan iyah fadamaka ba,sannan kuma ka dunga nesan kanka daga gareni tunda kaga illar danake dashi ga rayuwarka,komai dazai fito daga jikina hatsarine yayi gauraya da jikin mutum har ma da sauran halittu,please kadunga yin nesa dani sameer idan kana so ka rayu ko domin yayanka ma" Daga haka na barshi a bandakin na dawo dakin bayan na damka masa bullet din a hannunsa,shima fitowa yayi yah fice ya bar dakin zuwa waje. Da safe danaje dakin saleemah bacci na sameta tanayi haikan. Kwantar da zuhrah nayi a gefenta naje wajen kayanta domin na saka mata,tunda banida kayanta a wajena kaman farouq. Ina cikin saka mata wando saleemah ta tashi,kalonmu take dason tunowa mai ya faru,daga gani ta tuna abinda yah faru daren jiyan daga yanda ta razana,karisowa wajen danake tayi da sauri ta dauki zuhra ta kankame a jikinta,nima ganin hakanne yasa na juya domin fita daga dakin. Can kasan makoshinta tace,"nagode sosai ta kulamin da y'ay'a na da kikeyi" "Basai kin him in godiya ba hakkina nne nima na kare iyalina indai ina da damar hakan,allah ya tsare gaba" "Ameen ya Allah " Daga haka nabar dakin na nufi nawa domin shirya farouq zuwa makaranta,saidai yanda jikinsa yake rawane yasa na cire masa kayan inyaso gobe sai yaje idan hankalinsa yadawo jikinsa. Zaman gidanne ya isheni saboda yanzu na saba da zuwa aiki,saidai gidan dole yana bukatar mai dan lafiya,saboda saleemah tana daki yini tayi jikinta yana rawa,ga zazzabin da takeyi kumadu. Can wajen rana ina kitchen sameer ya shigo da alama har sannan a wajen caae din suke,kitchen din yah shi go tareda kama hannuna yana kallon farcena,nima kallon sa nake da alamar mai ya faru,saida yagama kallon dan kansa kafin yah dago ya kalli idanuwana. "Menene a jikin farcenki sameemah,jiya da daddare ina kallon lokacin da kika yanki mutuminnan a wuyansa,yanzu muna masa bincike mukaji yana ihu amma ba na horon da muke masaba sai dan abinda yake wuyansa. Mun kaishi wajen likitoci sun ce cell din cikin jijiyoyinsa ne suke mutuwa a kowanne bayan sakanni,wajen yayi baki kuma tafiya yake yama mamaye dukkan ilahirin jikinsa" Sunkuyar da kaina nayi dan bansan mai zance masa ba,gashi nasan idan ba fada masa nayi ba zai barni ba. "Nima bans an mai yake damuna ba haka na tashi na ganni,ummah ma tasani kafin ta rasu ita ce ta nunamin yanda zan boye halittata daga idon mutane ,duk abinda ya cijeni ko kuma ni na cijeshi ko kuma wani bangare na jikina yah shafi cikin jininsa to zai rasa ransa,sannnan duk ciwon danaji baya minti daya yake warkewa" Zare ido sameer yayi shikadai yana nazarin wani abu wanda banida masaniya akai,dan murmushi nayi kafin nace, "Yah sameer kana tsoro kar na halaka ku ko,wannan abin shikadai nake gudu a rayuwata sannna shine abinda yakasance tamkar bakar razana a gareni wanda nake kwana kuma nake tashi da shi.ko yaushe tunanina shine taya zan nesanta masoyana daga sharrina,a kokarin hakan dole sai na zamo Wacce suka fi tsana saboda munanan halinta,ta hakane kawai zasu kauracemin koh ban umarcesu da hakan ba. Burina shine kayi nesa dani yah sameer abinda kake tunanin bazai taba yiyuwa,bazan iya soyayya dakai ba mu yi rayuwar aure har mu haifi yara. Haka nake kuma bazan iya sanja hakanba koda ina da ra'ayin hakan,saidai ina so kasani bazan iya cutar da ahalinka ba koda inada bukatar hakan,akan haka na kwammaci na kasance cikin azabtarwarsu ko kuma su daukeni daga rayuwarnan kaman yamda suke da bukata" Hawayene yake zuba daga idanuwana wanda kwannan nakasa gane kaina,abu kadan sai nayi kuka inda ina gaban yah sameer sai naji ina rauni. Abinda banyi tsammani bane ya faru,wato rumgumeni ya sameer yayi sosai a jikinsa kaman zai maidani cikinsa,nima hannuna na saka a bayansa na jagayeshi a jikinnawa kaman wata zata kwacemin shi. Cigaba nayi da kukana a hankali ina jin yar nutsuwa tana shiga cikin zuciyata,shidin haskene a gareni da banaso nayi nesa dashi sai dai haakan ya zamemin dole. Cikin muryar damuwa yacemin, "Suwaye suke da niyyar daukeki daga gareni sameemah,kin kasa bani wannan amsar meysa haka?" "Bazan iya baka amsar ba koda ina da bukata nima kayi hakuri" Cireni yayi daga jikinsa zai share hawayen dayake fuskata,saurin rike hannunsa nayi danaga ciwo a hannun wanda mutanen suka ji masa,jijjiga kai nayi , "Ahah karka kai hannunka fuskata ,duk da ban taba gwadawa ba ina tsoron hawayena yayi maka illah yah sameer,bazan iya yafewa kaina hakanba idan ya faru" Murmushin ya fahimta yayi min kafin yace, "Yanzu kenan idan kikaji ciwo komawa yake ya dinke da kansa? " Murmushi nayi masa kafin na dauki wukar na yanka a tafin hannuna,har yakai hannunsa zai rike sai kuma wajen ya koma yanda yake tamkar ban yanka ba. Daga haka muka cigaba da hira ,duk da kowa zukatansu a cunkune yake da zullumi iri iri amma hakan bai hana mun turasu kasan zuciyoyinmu ba mun rungumi kaddara. Kwana biyu dayin hakan saleemah ta warware saidai duk da haka bata wani sake wa mu zauna amma bata min kallon tsangwama kaman lokacin baya,saima kallon jin kunya da takeyi a ganinta na ceci yaranta harda ita ga barayin,gashi na hanata tayimin Godiya,sai hakan yakara sakata jin nauyina. Komai yakoma normal nima na koma bakin aikina,yayinda sirrina kuma muka binne nida sameer,abinda yakfaru nayi zato zai nisanta kaina dashi saidai hakan bai faruba sai ma kara shigowa rayuwata da yakeyi lokacin cikin lokaci. Nima tun ina kin amincewa da yanayin dayake jiyartata har ya zamo nakarbeshi hannu bibbiyu sannan na amince da tunkarar duj abinda zai biyi baya. Yamzu kusan kullum da kyar nake bacci kowane dare saboda matsanancin ciwon kirji danake yi harda jini nake amarwa,nasan bai wuce saboda ketare dokar danake ba,nikuwa bazan iya hakan ba zan cigaba da karbar kulawar yah sameer a daga gareshi kafin lokacina yakare,bazan kara yarda na koma rayuwar kadaici danake a baya ba wannan lokacin. Duk nasan idan yagane halin danake ciki zai shiga damuwa,shiyasa nake toshe duk wata hanya dana san zai gano wane hali na ke ciki. Madubi na kalla inda naga bakin abu kaman jijiya yana bin wuyana,zaro ido nayi dan ban taba kulada shi ba sai yanzu,hoda na dauko mai kalar jikina na shafa a wajen,domin boyewa kar wani yagani,kawar da damuwar data shiga cikin zuciyata nayi kafin na fito zuwa office. Har nayi hanyar zuwa asibiti wajen doctor maryam ta dubani sai kuma wani tunani yazomin,ida naje mai zance mata,sannan idan ta duba bata komai ba nan ma mai zance?,da haka na juya cikin sanyin jiki na wuce wajen aikina. Dakyar na bari lokacin tashi yayi na koma gida,saboda haka kawai banason naga mutane suna matsowa inda nake,gani nake kaman sudin ba jinsi na bane,kuma wannan yanayin ya farune saboda shigowar sabon wani shedani zuwa jikina a daren jiya da daddare. Ina shigowa gidan na samu saleemah a zaune,sannu da dawowa tacemin cikin magana kasa kasa,duk da najita amma ban kula ta ba,ina shiga daki nayi wurgi da jakar hannuna ina huci ni kadai,nasan wannna abu danake ji kuma nake aikatawa bani bace,amma babu yanda zanyi inaji ana iko da jikina. Washagari ban je aikiba saboda munyi da yah sameer zai kaimu wajen doctor maryam mu yini,haka kawai na tsinci kaina da jin dadin maganarsa,dan ba kadan ba matar take birgeni sosai. Tun safe mukayi shiri nida saleemah,dan ina kulada itah bata so aka ce da ni za'ajeba,duk da wani abu baya hadamu na kiyyaya haka ma babu Abu na so dayake hadani da ita. Lace na saka milk mai adon chocolate,sai kuma nasaka gyale kalar adon lace din,dan a rayuwata banason saka hijabi duk da a ina da bukatar yin hakan,da gangan wasu kuraje suke fitomin wanda nasan ba na allah bane. Sai da mukayi dan tafiya kafin muka isa,kasancewar gidanta yana da dan nisa da inda muke ,duk da tana da gida da aka bata a barrack din amma tafison zama a nata gidan. Shiru gidan babu motsi kaman babu mutum a gidan ,shiga mukayi da sallama cikin gidan,wata yarinyace bazata wuce shekara sha biyar ba a falon tana rubutu,da alama assignment takeyi. Dagowa tayi ta kallemu tanayi wa farouq murmushi,shima sunkuyar da kai yake da alama yasanta . Gaishemu tayi a hankali said kuma tashiga cikin daki domin kiran doctor maryam din,itama saleemah bin yarinyar tayi zuwa cikin gidan. Nikuwa ganin nikadai ce a tsaye yasa na koma kan kujera na zauna,shima yah sameer din zama yayi kaman da alama zuwansa na farko gidan kenan . Idon nane yakai kan wani hato dayake rataye a falon,kallon yah sameer nayi da sauri wanda shima idon sa yake kan hoton,da alama yaga abinda nagani. Tashi nayi zuwa gaban hoton kafin na maida kallona zuwa kan sameer wanda shima ya zare ido cikin mamaki. Muna cikin hakane doctor maryam tashigo falon hannunta rike da na farouq,kallon mu take da mamaki ganin munyi cirko cirko bama cewa komai . Nice hannuna yana rawa na nuna hoton ina kallonta amma kuma na gagara furta ko kalma daya daga bakina. Murmushi tayi irinna manya kafin tace, "Lah wannnan hoton mai kuma yah faru naga kina mamaki wasu masu aikina ne wanda nake jinsu kaman yan uwana wani abune yah faru" "Ahah kawai dai nasan na jikin hotonne amma bansan ya akayi hotonsu yazo nan wajen ba" Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎37~38💎 "Hmm dolene hotunansu yazo nan wajen,kuma duk inda nake ma hotunansu zai zo wajen. Sudin mutanene da bazan manta dasu ba a tsawon rayuwata,saidai bansan a ina zan sake ganin su ba,hakan yasa na dauki hotonsu da muhimmanci har nake tunawa dasu a rayuwata,amma naji kince wai kinsansu a ina kenan?" Sunkuyar da kaina nayi a raina ina cewa,kar ko abinda nake Tunani yakasance gaskiya,kallon yah sameer nayi wanda shima idonsa ya nuna alamar hakan. "Su din iyayenmune nida yah sameer,ummah hajara ta rasu inada shekara goma a duniya,baba umaru kuma yana gida" Tashi tayi tsaye tana kallona,kafin kuma tace, "Inalillahi was inna ilaihi raji'un, Hajara ta rasu?kincemin ke yar tace shin ta kara haihuwa ne bayan mun rabu,kuma baga sameer ina mijinkine" Yah sameer ne yakatse maganar mu nida doctor maryam ta hanyar cewa, "Shin kece hajiya maryam da baba umaru ya bamu labarin yayi aiki a gidanki a garin bauchi shekarun baya da suka wuce?" Daga kai tayi da sauri kafin tace, "Eh tabbas nice wanda muka zauna da su a gidana dake garin bauchi" Dan tsabar kaduwa bansan lokacin da na zauna a wajenba,kenan doctor maryam mahaifiyatace ,kuma nida saleemah yan uwa ne kenan,mahaifiyarta yayar mahaifiya tace,wannan wane irin al'amarine haka. Dago da kaina nayi ina kallon doctor maryam wanda itama take bina da kallo,sameer ne yasamu damar cewa wani abu bayan dukkanmu munyi shiru. "Indai da gaske kece wacce baba umaru ya bamu labari to ya tabbata kece mahaifiyar sameemah wanda take zaune a gabanki a halin yanzu" Sakkowa tayi daga kan kujerar da take ta matso zuwa kusa dani,har numfashinmu yana bugar na juna,hannunta tasaka ta rungumoni zuwa jikinta wanda yake rawa kar kar, "Kece sameemah meyasa ban dago sunan ba bayan nasan sunane da ba'a cika jinsa a gun wasu ba,tabbbas kece kam babu tamtama,allah sarki kawata ta kaina hajara itadin mutumce mai wuyar samu,hakika ba karamin babbar ni'imace ba dana hadu da ita,nasan ko ban tambaya ba tayi miki rikon da koni iyakaci kenan" Dagowa nayi daga jikinta duk da ban ki mu shekara a haka ba saboda wata sabuwar nutsuwar da take shigamin,saidai dolene na yi mata tambayoyi na dalilin bayar dani ga ummah hajara da tayi, bakina yana rawa kaman bazai budeba na ce, "Amma in da gaske kece mahaifiyata kuma kina sona kaman yanda na gani a cikin idanunki, mai yasa kika rabu dani kika raba rayuwata da taki a lokacin danake tsaka da bukatar kulawarki" Lokaci daya daga gama jin tambayartawa yanayin ta ya sauya gabadaya,hawaye yana zubowa daga idanunta kuma tana jijjiga kai. "Ban rabu dake dan son raina ba,sai dan tseratar da rayuwarki sameemah,kuma har yau bana nadamar yin hakan,amma kiyi hakuri bazan iya fadamiki dalilin ba,banida ikon yin hakan" Kallon ta koma kan sameer wanda yake goge hawayen tausayinmu nkda ita, "Tabbas kam kai dan kawata hajarane dan ga kamar tanan a fuskarka,duk da ban taba ganinka ba amma nashajin labarinka sosai a wajen ta,fatana allah ya jikinta da rahama,sannan allah yasa halinta ya bita,yanzu kutashi mutafi wajen yaya fatima tukunna" Daga haka ta mike daga tsugunnen da take kafin ta kama hannun sameemah wanda har sannan kanta yake sunkuye. Dukkan mu gidan hajiya fatima muka tafi,cikin motar babu wanda yake cewa komai,saidai lokaci zuwa lokaci muke hada ido da saleemah,wanda said ta kawar da kanta kaman mai kunyar wani abu. A falon muka sameta tana kallon news hankalin ta gaba d'aya yana kai,dan ko sallamar ma bataji sosai ba. Kallonmu take da mamaki ganin mu har da doctor maryam sannna kowa fuskarsa tana dauke da wani abu daban. Hannuna ta kama zuwa gaban hajiya fatima kafin ta kama nata ita ma ta rike, "Yaya fatima kinga sameemah na ganta,saidai mahaifiyar tata wanda na bata ita ta rasu ,bansamu damar ganinta a karo na biyu ba,saidai nayi ta mata addu'a a kullum,dan ta nunamin kauna haka ma ta nun aw a jikina tsakininta da allah,tunda har ta raineta sannan kuma ta hada ta d'anta aure,babu abinda zan iya saka mata dashi yaya fatima" Kuka take sosai wanda nake jinsa har cikin raina,ban san meyasa ba amma kukan sosai yake taba cikin zuciyata,hannuna na kai zuwa bayanta na dafa duk da bakina yagaza cewa komai. Its kanta hajiya fatima bata ce komai ba sai tsshi da tayi ta nufi dakin ta tana cewa, "Bari na Kira alhaji tukunna,dan maganar ba tawa bace ni kadai,yazo ga y'ar amininsa a raye bata mutuba kaman yamda muke zato" Bayan kamar awa d'aya kowa yah hallara a falon,har da matan da nayi musu gargadi farkon zuwa na gidan sameer,ashe suma kannen mahaifiyata ne wanda suka uba daya,kallona suke da alamar sun ganeni,yayinda nima din nake kallon su din. Alhaji musa ne yafara gyaran murya kafin yace,, Toh hakika wannan abin mamakine,ashe muna zaune da y'ar mu har tana kishi da tamu y'ar amma bamu saniba said yanzu,babu abinda zumuce said yiwa allah godiya. Sannna kuma zamuso jin ya hakan ta kansace kafin asan yanda za'ayi" Nidai banyi magana ba har yah sameer yagama basu labarin rayuwata a gidan gandu tundaga farko har karshe,kama daga labarin zamana a palastine da kuma zamana a kasar Brazil,har da yanda aka sha fama dani a akan aurensa na ki amincewa,siada aka cemin wasiyyar mahaifiyata ne tukunna. Abu d'aya ne naji dadinsa daya boye sirrina na halittata bai gada ba,hakan yayimin dadi sosai,kuma yasa nakara yarda da sameer fiyeda yarda da nayi masa a baya. Lokacin daya gama bada labarina babu wanda bai yi ta'ajjubiba,hajiya maryam kam harda kukanta wiwi wai ta tausayamin,nidai ban dau tausayin a matsayi sosai ba tunda ta barni ta tafi. "Hakika gaskiya munyi mamakin yanda ta sameemah ta rayu a wajenku,sannan kuma bamu da bakin godiya akan hakan,dolema said munyi shiri munje har wajen Malam umaru munyi masa godiya bisa namijjn kokarin dayayi akan rayuwar ita sameemah. Duk nan mu yan uwantane ga hajiya fatima mamar saleemah,itance yayar mahaifiyar ta wanda suke uwa daya uba daya,sai hakiya delu kanwarsu ce itama ,saikuma hajiya bebi itakuma kanwar mahaifinki ce wanda shikuma amininnane da muka tashi tareda har girma,zamane ya kaishi garin baushi a lokacin baya. Toh haka kaima sameer dama kai dan gidane sannan faruwar hakaan tasa munakara yarda dakuma son jawoka cikin danginmu,kuma gashi kana auren wa da kanwa. Dama saleemah tun suna yara ta girmi sameemah da shekara hudu,dan haka dama yayrtace,to a yanayin zamansu cikin gidanka ma tarigata shiga,dan haka idan wata matsala ta faru kar wani yaji kunyar zuwa yah tunkatemu a cikinku. Abinda akayi a baya kuma a sai a yayyafe,musamman ke sameemah da na nuna sonkai akan lamuranki har hajiya fatima tana nusar dani,ashe bansaniba kedin Y'a tace kema,wanda zan iya komai dan samun farin cikin ki. Dan lokacin da maryam ta zo gida duk jikinta faca faca babu wanda baiji tsoroba ,mun tambayeta tace ta bada ke ga wasu Wanda ta yarda dasu,tun daga wannnan duk tambayar da mukayi mata bata bada amsa,idan muka takurata ma said ta birkice sai an dade ta dawo hayyacinta. Tun daga wannan yanayinta ya sauya,kullum tana zaune ita kadai,bayan an debi shekarune ta ce zata koma karo karatu India,ban hanataba saboda a ganina zata samu nutsuwa,daga haka ta tafi karo karatu,da ta gama ma tayi zmanta a can tana aiki,sai yanzu allah yayi dawowarta da rabon zata gamu da y'ar ne ashe. Daga haka aka fara hira kowa yana fadin albakrkacin bakinsa,nidai shiru nayi amma a labarin da aka baya akwai abinda babu shi a ciki,tambaya nayi wa akaina cewa,toh ina mahaifina,me mahaifiyata ta gani da har ta zabi a rabuwa dani a lokacin danake da kananan shekaru,sanann me yasa take shiga firgicin idan anyi mata maganar meya faru? Ko ita ma bazata iya bada labarin halin da take cikiba kaman yanda nima bazan iya bayarda labarin ba,kenan haka take yamda nake nima?,kai anya kuwa?. Wannan amsoshin banida su sanann bansan waye zai bani amsoshinsu ba a halin yanzu,kuma koma menene ba shakka suna da alaka da yanyin halittata danake ganin ta sha banban da ta sauran bil'adama. Sallah aka fara kira ta azahar inda kowa yah tashi domin yin sallah,bin hajiya maryam nayi a baya wanda take a matsayin umma ta yanzu,domin naga shin itama bata iya sallah kamanni ko kuma ita tanayi. Dakin babu kowa sai motsin ruwa da alama alwala takeyi,zama nayi a kan gado har ta fito murmushi kawai tayi min da muka hada ido nima na mayar mata. Hijabinta ta gyara ta tada sallah har ta gama ta fara addu'a ina zaune,mamaki abin yaban ganin tana sallah ta normal babu abinda ya sameta,nikuma bana iyaww,to ni da ita ba iri daya bane,wa na iyo kenan idan ba ita bace. Juyawa tayi ta kalleni,saida tayi magana kafin hankalina ya koma kanta. "Ina sallah zakiyi,kije kiyi alwalar mana ai na idar" Uhm kawai nace nasake zamana, "Period kike kenan?" "Uhm " Ina jin dar dar na fada mata hakan,saboda kar naje ta ganoni kaman yanda hajiyah fatima tayimin. Daga haka dagani har ita babu wanda yasake cewa komai har lokacin tafiya gida yayi. Yah sameer ne yazo daukarmu amma sai alhaji musa ya dagatar dashi ta hanyar cewa, "Major in a ga da ka barta taje gidan ummah koda sati d'aya tayi kafin ta dawo dakinta,hakan ina ga zaisa su fahimci junansu koda kadanne" Jijjiga kai yayi alamar ya yarda da maganar alhaji musan,amma nikam ban so hakan ba saboda banason zama sa mutumin da zai dunga ganin mai nakeyi,shiyasa naji dadi da dakina nikadai nasan mai nake aikatawa a gidan sameer. Murmushi hajiya maryam tayi alama taji dadin hakan sosai,dan daga gani tana so na dunga zama kusada ita. Hakan kuwa akayi ina zuwa gida na hada kayana da safe yah sameer ya ajiyeni a kofar gidan hajiya maryam,farouq kuka ya dunga yi akam sai mun tafi tareda shi,hakan kuwa akayi inyaso sai driver ya dunga zuwa yana daukarsa a can,nima dama bazan ji dadin barshi din ba,saboda mun saba kwana tare. Lokacin danazo fitowa ciki ciki Saleemah tayumin a dawo lafiya tareda cewa na gaida hajiya maryam,nima daga mata kai kawai nayi. Ina Shiga Gidan na samesu a zaune,yarinyar da muka samu a gidanne rannan tazo da gudu ta karbi akwatin hannuna tareda cewa, "Aunty Sannu da zuwa dama ummee tace zakizo ki zauna damu" Murmushi nayi mata tareda cewa, "Eh hakane amma sati d'aya zanyi kawai" "Ayyah duk da haka naji dadi Sosai" "Toh humairah kai mata akwatin mana sai ki dawo ko" Saurin jan akwatin tayi farouq yana binta a baya. "Ina kwana ummee" Nafada domin kama sunan da yarinyar da ta kira da humaira take fada mata. "Lafiya kalau sameemah,ya mijinki da kuma yar uwarki" "Duk lafiyar su kalau" "Mashaallah barkan ki da zuwa to,bari na gama kawo abincin dama yanzu na gama" Binta nayi kitchen din domin dakkowa abincin,hira muka dan farayi saidai duk akan zaman da tayi dasu baba umaru take fadamin,wani lokacin idan ta tambayeni na bata amsa,wani kuma na daga kai kawai,dan harga allah nakasa sakewa da itah duk da ina da bukatar hakan. Hakadai zamannamu ya cigaba da tafiya,har nayi kwana uku a gidan,zuwa yanzu nafara sakewa da ita muyi hira,saidai har yanzu bata fadi abinda nakeson tayi magana akaiba shine mahaifina,nikuma na kasa tambayarta hakan, duk da shine abinda ya tsaya min a raina. Ranar ta hudu danayi a gidan muna zaune muna kallo ,duk saina jini wani iri saboda bana zuwa wajen aiki,kiran sallah ne ya doki cikin kunnena,humairah ce ta shiga dakinta domin yin sallah,ummee ce take kallona taga ko zan tashi amma babu alamar yin hakan, "Sameemah har yanzu kina period ne?" "Eh ina yi" "Bakiyi Kama da mai period ba sameemah,dan tun a farko na gano hakan amma na zubamiki ido kawai,meyake faruwa da bakya sallah kina matsayin musulma kuma hakan bai dameki ba,kina tunanin hakan zayyi miki kyau barekuma wanda kike tareda su,meyasa bakya sallah sameemah,sannan kuma bakiyu kama da wanda bata da ilimi ba,menene yake faruwa?" "Akwai abinda yake faruwa ummee,saidai idan har zaki iyah fadamin ina mahaifina yake,sannan kuma manene yasa kika badani ga ummah,kuma meyasa kike firgicewa idan aka tambayeki mai yake faruwa,to nima zan iya fadamiki dalilin dayasa banayin sallah" Lokacin danayi maganar mun kai wani lokaci amma babu wanda yayi magana a cikinmu,kowa yana zullumin abinda ke cikin zuciyarsa. Tashi tayi cike da damuwa ta wuce dakinta,ina nan zaune humaira ta zo falon tana cemin naje ummeee tana kirana. Ina Shiga na same ta a zaune da carbi a hannunta,gabana ne ya buga dan ba abinda nake tsoro ya carbi,tun horon da mu'allim yayimin dashi,tambaya nayiwa kaina cewa mai take shirin yimin dashi to. Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎39~40💎 Hannu ta dagamin alamar na zo,cikin sanda na kaman wanda kwai ya fashemin a ciki na isa wajenta na durkusa. Hannuna ta kama dukka biyun kafin tace, "Duk da bansan wane hali kike cikiba amma nasan abin akwai wahala,saidai ina so ki sani duk da halin dakike ciki kar ki bari wuya ko kuma wani yanayi ya hana ki kusanci zuwa ga ubangijinki,tabbas nasan akwai abinda yah faru a daren dana badake ga ummanki hajara,amma nakasa koda abinda nayi lokacin barekuma mai ya faru,abinda nasani kawai shine idan nayi kokarin tuna mai yah faru nakan ji duk kaina ya juye ina kokarin fita daga cikin hayyacina,bansna mai ya faruba kwata kwata,har shikansa Abdulwahab bansan mai ya faru dashiba. Sameemah muna cikin jarabawa dagani harke amma karki yanke kanki daga neman sauki a wajen allah ko kuma neman agajinsa,a duk inda kika samu kanki ki kasance mai mika lamarinki ga allah,a cikin dad'i harma da cikin wahala" Wani irin rauni nakeji zuciyata tanayi lokacin da nake sauraron abinda yake fitowa daga bakinta,hawayen danaga yana zuba a cikin idonta ne yasani rungumeta a jikina kaman kar mu rabu. "Nagode ummee inshaallah zanyi kokarin yin amfani da abinda kika fada min" "Kici gaba da addu'a komai zaizo da sauki watarana sai labari inshaallah" Daga haka tacigaba da yin lazimi ina zaune a gefenta,zaman wajen kadai tayarmin da hankali yakeyi amma haka dole na daure saboda naga farincikin a kan fuskarta. Ranar na biyar da zuwana gidanne da rana ina kwance a kan gado naji ana kiran sallah,abinda ummee ta fadaminne yadawo min cikin kaina,saidai duk da haka ban taba gwada yin sallahr ba koda wasa,kenan ban dauki maganarta da kima ba koh,kuma ban kasance Y'a tagariba,bar batun wannan ya tsakanina da mahaliccina to,wanda shiya halicceni amma kuma nakasa bautamasa tsawon shekara da shekaru saboda bin umarnin wasu shedanu can,yanzu idan na mutu mai zancewa ubangijina,shin hujjar danake da ita na sun hanani yin ibada nikuma ban yi wani kokariba ta isa kareni daga ranar karshe??. Wani saurin tashi nayi daga kan gadon hawaye na zuba a cikin idona,yayinda jikina yake rawa kaman an jonamin spring,tabbas akwai kalubale a gabana ba kadanba. Hangar vandakin na nufa,duk da baraxanar bugawa da zuciyata takeyi amma haka nayi biris da ita na fara alwalar,yau na dauki alwashin gwada yaki da duk abinda yake cikin jikina. Fitowa nayi na dauki hijabi a kan gadon ummee wanda take sallah dashi na saka,kafin na shimfida sallaya. Tun daga hawa sallayar nakejin kaman nadora kafa akan wani abu mai zafi,amma haka na jure ina runtse ido. Kabbara na tayar wanda ina ga ban tabsyin guda uku ba tsawon rayuwata,abinda yasa ban mantaba saboda anayinta a masallatai ne kullum. Suratul maryam bakina yakama nafara karantawa,daga iyah aya biyu na yanke nayi ruku'u,ina jin kaina yana barazanar fashewa amma ban fasa abinda nakeyi ba,lokacin danakai sujjadane naji wata murya tansmin magana cewa, ~~Hakika kin Kaimu bango a yau,kina tunanin zamu sallamar da ruhin da anriga an yi mana kyautarsa,to hakan bazai yiyuba,daga yau zamu kasance mune zamu tinga control din gangar jikinki har zuwa nan da wata uku lokacin da zamu mallakeki ki rike matsayin dayake jiranki,idan kuma ba haka ba dole mu hallakar dake,yanzu ma dolene ki karbi hukunci~~ An gama fadar hakan naji wani zafi da kuma kara ya ratsa cikin kaina,hakanne yasa nima na zunduma tawa karar danima bazan iya zure azabarba. 💎*Sameer a madubin gani*💎 Yau kwanan sameemah biyar a gidan mahaifiyar ta, ko waya bamu tabayi ba duk kewarata ta isheni,duk da ba komai ne yake shiga tsakanimu ba amma ganinta kawai a cikin gidan yakan sa naji nutsuwa a tareda ni. Hakanne yasa na yanke shawarar dama zanje wajensu ita da farouq sannan na gaishe da hajiyah maryam. Hanyar gidannasu na nufa har na isa gidan,a falon na samu hajiyah maryam tana aiki a system tasaka glass,Murmushi tayi da taga nine, "Lahhh ango ya biyo sawun amarya kennan,da alama kana kewar iyalanka,ya d'aya y'ar tawa take ita da mai sunan yaya ta" "Lafiyansu kalau hajiya" "Mutuniyar taka tana ciki bari na kira maka ita ko" Dan sosa keya nayi dan dama hakan nakeso naji tace. Ta ta shi kenan da niyyar shiga ciki,mukaji karar sameemah daga cikin daki,da alama wani abune yake faruwa da ita,da sauri dukkan mu mukayi dakin da muryar take fitowa. Akan sallaya muka sameta duk gaban hijabinta ya baci da jini gashi dama mai haskene,saurin tallafarta mukayi nida hajiyah maryam muka nufi hanyar kofar gida wajen mota. Da sauri muka turata zuwa dakin taimakon gaggawa,inda ummee tayi saurin sanja kayanta a office dinta ta shiga wajenta. Muna nan tsaye zuwa lokacin kowa yazo yan uwa domin labari yah isa garesu. Ummee ce ta fito daga dakin amma babu alamar nasara a fuskarta,alhaji musa ne yayi saurin tambayar mai yake faruwa,amma cewa tace bata farfadoba cikin karamar magana. A zaune muke dukkanmu a office dinnata, Dagowa tayi ta kallemu fuskarta dauke da damuwar halin da y'ar ta take ciki, "To yanzudai bamusan mai yake faruwa ba,dan duk wani gwaji munyi amma babu abinda muka gani,gashi har yanzu bata farfado ba tukunna,saidai mu tsaya mujira mai zai faru. Wasu sun tafi gida amma ni da hajiyah Fatima da kuma ummee a anan muja zauna domin ganin mai zai kasance,baba umaru ma an aika masa suna zuwa shida inna ramatu wanda tace zata zo ta gani saboda munafurci. Ni kadaine xaune a gefenta akan kujera na kifa kaina akan gadon,can wajen misalin karfe dayan dare naji kaman hannunta dana rike yana motsi kamar a mafarki. Saurin bude idona nayi na ga dukkan jikinta yana jijjiga,tashi nayi na tsaya akanta,a lokacinne naga idonta ya bude wanda babu alamar farar kwayar ido bakine sidik. Wani mungun murmushi tayimin kafin tayi saurin tashi ta kama wuyana da wani irin karfi ta mannani a jikin bangon dakin,dariya taci gaba dayi da bakinta wanda yake bakikkirin,wuyana ta saita tana niyyar cizona ,har na lumshe idona na saddakar,saboda duk karfin mutum bazai iya kwacewa da wannan rikon ba,can kuma sai naji ta tsaya cak kuma tana huramin numfashi a wuyana,kaman wanda take yaki da wani abu a cikin ranta. Karar budewar kofa naji dama na danna alarm danaga tana jijjiga. Ummee ce ta shigo dakin wata nurse tana biye da ita a baya, Jefar dani tayi a kasa kamar shamfora tayi kan ummee da wani sauri wanda ba nata ba,tsaywa tayi a gaban ummee tanayi mata kallon kaman yaro yana son gane mahaifiyarsa,har ta kama ummee sai kuma ta saketa da sauri ta kama wuyan wacce suka shigo da ita ta gatsa da karfi,ihuu ta saka na azaba kafin ta durkushe akan gwiwoyinta,daga baya kuma ta fadi summamiya. Hanyar waje tayi tana nufin fita nayi sauri na tashi da dan karfin dayayi saura ajikina naje bakin kofar na tsaya inda zata wuce, Wani kallo takemin na ranta ya baci amma ban matsa daga kofar ba,saima wayata dana ciro a cikin aljihuna na kira alhaji musa na fada masa ya taho da malami. Tanajin abinda nafada tayi kukan kura da sauri ta nufi inda nake da niyyar bigeni ta wuce,saurin rike kunkuminta nayi tareda yi mata magana a kunne. "Ki tsaya sameemah ki saurareni,karki bari koma menene yayi iko dake,kiyi kokarin yin abinda ya dace,ke jarumace sameemah kiyi amfani da jarumtarki,nasan kina jina kiyi kokarin saita kanki,nasan zaki iyah,kidaina cutar da wanda basu da laifi karki zama wacce zata kasance abar tsoro a cikin mutane" "Ni ba mutum bace ni nakasance wata halittace daban,sannan zanyi abinda irina sukeyi,kadaina kusanto inda nake,inaso idan ka ganni ka gudu saboda ni dododanniya ce abar gudu ga kowa" "Keba dododanniya bace,ke matata ce kuma masoyiyata abar sona,bazan taba daina sonkiba,sannan idan kina son ki fita ki cutar da mutanen to ki fara taina sameemah,niya kamata ki fara hallakawa saboda nine na bar rayuwarki lokacin da kike bukatar wani a kusa dake,sannan na kasa bincikar halin da kike ciki har sai da abin yafi karfinki,dan haka ki fara ta kaina" Duk da har yanzu yanayinta na wani abune daban amma hakan bai hana na gano alamar sararawa ba a jikinta,zuyawa tayi ta kalli ummee wanda tayi suman tsaye tana kallon nurse din ta take kwance kaman gawa jini yana fita daga wuyanta. Dago da idonta tayi ta dorasu akan y'ar tata wanda idonta yayi baki,hakoranta sukayi tsayi har da gashinta. Baya ta fara ja da kadan kadan tana kiran sunan allah,wanda hakan yasa sameemah yin gurnani irin na namun daji tana rike da kunnuwanta. Ganin ummee bata daina salati bane yasa sameemah tayi kanta da niyyar shaketa,saurin riketa nayi ta baya dakyar, "Dan kinga y'ar ki tana nuna tirjiya akan karmu tabaki shine har kika samu ikon fadamana wannan kalmar?,kece sanadiyyar sakata yin abinda mukafi tsana wato sallah,shine kike cigaba yanzu ma dan kinga mun kyaleki?" Tana cikin maganar ne mukaji alamar tahowar wani,daga bakin kofa,hankalin ta ne yayi wajen da sauri,saidai tana isa wajen ta dawo da sauri tana buya a bayana,wani malamine da hiraminsa sai kuma alhaji musa shida baba umaru. Karatu malamin yah fara tun daga shigowarsa,wanda hakan yasa sameemah ta zube a kasa tana wani irin karaji,itama ummee zubewa tayi tareda fasa kara mai karfi. Dukkan mu abinne ya kidima mu muka fara kallon kallo. Cigaba yayi da karanta wasu ayoyi da kuma addu'a harna tsawon lokaci kafin sameemah tai shiru kaman ta sankame. Cikin sauri yace a daukesu a biyoshi yanzunnan. Nine na ciccibi sameemah yayinda wasu nurse suka fita da wacce sameemah tayiwa rauni,wasu kuma suka sauki ummee zuwa cikin mota. A hanya alhaji musa yayiwa hajiyah fatima waya ta samemu a gidan malamin. Muna zuwa gidan ya bude wani daki mai dogon lungu,saida mukayi tafiya kafin muka zo wani daki,shiga mukayi ina dauke da sameemah a hannuna. Wata igiya ya dauko siririya doguwa daga cikin wata kwarya mai ruwa ya daura a hannun sameemah kafin ya daura a jikin wani karfe dayake wajen. Ajiyeta nayi a kasan wajen ya karisa daureta a wsjen,tausayinta ne yakamani sosai,hakika taga jarabawa dayawa,yanzu kuma wannan halin zata kuma shiga. Kallon malamin nayi kafin nace. "Malam wannan igiyar zata iya tiketa kuwa,tana da karfi fa sosai" "Hmm nasan karfinta,amma kai baka san karfin wanna igiyar a gun shedanu ba,duk da bansan wane irin shedanu ne a jikinta na haka ma bansan iya karfinsu ba,amma nasan bazata iya tsinka igiyar nan ba,yanzu dai muje tukunna sai anyi binciken wane irine kafin a fara magani,saidai naga kaman kuruwarta bata jikinta na tsawon shekaru,da wata kuruwar daban take rayuwa,dan haka dawo da tata kuruwar zai bada matukar wuyah". Daga haka inaji ina gani babu yadda zanyi muka tafi muka bar sameemah a wajen,wanda tayi summ kaman sankararriyar gawa. Komawa mukayi daki inda hajiya fatima take yiwa ummee fifita,itama a kwance take kaman gawa. Wucewa malamin yayi zuwa wani daki ya dakko wani kokon ruwa yah fesa mata,ajiyar zuciya ta sake kaman wanda aka sakawa sabuwar rayuwa. Tashi tayi zaune kaman mai cutar mantau said kallon mu take,kokon hannunsa yah mika mata ,hannu tasa ta karba kaman mai karbar umarni tackai bakin ta,kurba biyu tayi mika masa abinsa,saboda wata atishawa da ta turnuketa. Kallon muyayi kafin yace, "Da alama an goge mata wani bangarene na tunanin ta a shekarun baya,kuma yana da alaka da abinda yaje jikin yarinyar" Aikuwa bai gama rufe bakiba ummee ta fashe da kuka kafin takama rigar hajiya fatima ta tike gam tana cewa, "Yaya fatima na tuna abinda yafaru,wallahi na tuna,yaya fatima Abdulwahab ya cuceni yah yaudareni ya zalunceni nida Y'a ta yasakamu cikin tsaka mai wuyah,bazan taba yafemasa ba har numfashi na na karshe ya fita daga jikina. Bazan yafe masaba sai anyi masa hisabi nida shi,uwa uba kuma sameemah ya cuceta fiyeda abinda baki zai yah fada yayi mata abinda ko a tarihi said an tona kafin a samu. "Meyafaru maryam ki sanar damu,ko yamzumma baza ki iya fadaba kaman sauran lokuta a baya" "Yanzu zan iYa fada,natunna komai duk abinda yah faru babu wanda ban tuno ba yanzu zan fadawa kowa mai yah faru,koda kuwa abinda yah fada gaskiyane cewar idan nafada abakin raina,to saidai na mutun amma sai na fada kowa yah ji.......toh fah🤭 Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎41~42💎 💎*Hajiya maryam a madubin gani*💎 Auren soyayya mukayi da Abdul wahab ina sonsa yana sona,saidai abu dayane yake hadamu dashi shine kullum zancensa akam yanda zayyi kudi a dunga kwatancensa,ni kuma duk sands zai fadi haka sai na yi masa wa'azin akan yanemi zabin alkhairi,ban dauki abin amatsayin wani abuba saoboda a ganina idan har ya girma ko kuma allah ya xaunar masa da sana'arsa ta Engeneer to zai bari. Saidai ashe abin ba haka yake ba. Muna nan zaune yah samu nasara sa'anarsa ta bunkasa yazamana sai a tsallake manyan Engeneer azo wajensa neman wani abu ko aiki,abin yabani Mamaki da farko amma sai na dauka cewa iko ne na allah. Kwanci tashi bayan shekarar uku da aure sai wasu kamfani suka kirashi aiki zuwa kasar india. Da farko nayi zaton tare zamu tafi saboda naga aikin yana kawo masa kudi amma sai yace zamu koma garin bauchine da zama saboda zai saka kasuwamci ne a can. Kasan cewar nasan aikinnasa tun daga farko sai vandamu sai nasan mai yake gudana a can kasar india ba. Haka muka zauan yana zuwa akai akai amma daga baya sai zuwansa ya ragu.idan ban mantaba nayi barin ciki har sau biyu a can,kafin na samu cikin sameemah,amma kwata kawata bana tuna nayi barin sai yamzu,kumma dukkansu sai yazo nake barin kafin ya tafi,cikin sameemah ne har aka goyashi na haifeta bai saniba,lokacin dayazo tana da shekara kusan biyu sannan,dan har na yayeta ma. Nayi farincikin zuwansa sannan nayi bakin cikin rashin zuwa wajena akan lokaci,koda badanni ba yakamata yazo yaga y'ar sa wadda yake da ita kwal a duniya. Lokacin daya dawo sameemah kin amincewa tayi dashi saboda bata son mutane sosai inba wanda ta saba da suba,amma dayake yana zanta a jiki da kuma siya mata kayan wasa sai ta sake dashi a kwana uku,naji dadin hakan sosai ganin yanda yake janta ajiki kuma yake nuna mata so matuka. A tsakanin zuwansa na sati biyu kusan kullum sai sun fita shida sameemah idan zasu dawo sai na gansu da kayan wasa ko kuma su minti da biscuit. Abinda yasakani shiga firgici kuma bazan taba mantawa dashi ba matukar ina cikin hayyacina shine: Wata rana muna zaune dashi sameemah na cinyata shikuma yana zaune a bakin gado muna hira,sai nace masa bari naje wajen hajara hira,tunda shi yacemin magana zayyi mai muhimmanci shida abokan business dinsa. Daukar sameemah nayi muka fito,har munzo bakin kofar fita daga falonnawa naga tayimin fitsari duk da wayonta amma ta iya wannan tsiyar idan taso,dungerata nayi kafin na koma dakin domin dauko mata pant,abinda naji ne yasaka ni cikin firgici da tunanin anya kuwa ba mafarki nake ba , "Eh duk yanda muka tsara ya tafi,kuma munyi nasara jininnata yayi daidai da wadda kujerar mulkin take bukata,nidai burina shine idan kun karbeta ni kubarni na dawo kasata da zama,tunda na baku wacce zata maye gurbina,yakamata nadawo gida kar a fara zargina da aikin danakeyi,inason zaman aure kuma da matata da kuma rike kamfanina,y'ay'a ne nasan zan samu wasu nan gaba,tunda nabaku wata daga jinina wacce zata maye gurbina shikennan............eh na bata abun ta cinye na tsawon kwana ukune sannan nakaita wajen da kukace din ma,abinda ya saura shine gobe zan bawa su muhiddeen ita su taho da ita,kuma ina so ku kuyi wani abu ta yanda za'a manta da ita a rayuwa,ya zama tamkar ba a haifeta ba kwata kwata......." Numfashina ne yake hawa sama sama har bansan lokacin dana kankame sameemah a jikina ba wacce nakejin za'a rabani da ita,rababwar da bata da maraba da kashe rayuwarta,dabara ce ta fadomin da sauri nayi hanyar dakin su hajara ina bugamusu kofa. A lokacinne na basu sameemah halak malak kuma nace kar suyi abinda zai kawota garin baushi koda wasa. Sunyi dani nazo mutafi saidai kuma a sanann bata rayuwata nake ba sai ta Y'a ta wacce nake da ita d'aya. Ina Shiga dakin naji an shake wuyana da wani abu,maganar Abdulwahab nani yana cewa, "Ina Kika kaimin Y'a ta,sannan miyasa kikaji abinda bai kamata kijiba a rayuwarki" Fazge wuyana nayi na kalleshi cike da tsana nace, "Natsaneka Abdulwahab,ka cutar dani sanann ka cutar da Y'a ta kwaya d'aya danan mallaka,saidai kasani burinka bazai cika akan taba,dan bazaka sake kallonta ba har abada,na kwammaci naga gawarta dana baka ita ka hallakar da ita kaman yanda kake akan hallakar" Wata fizgowara yasake yimin,zuwa wannan lokacin yafita a cikin hayyacinsa,dan ina ganin sanda jini yake fita daga hancinsa da bakinsa,amma ko digon tausayinsa banjiba dan a lokacin babu abinda nake buri daya wuce naga gawarsa a kwance a gabana. Shakeni yayi yana magana amma banajin abinda yake fada,da haka har jijinsa ya shika na samu na kwance,ina gani yana wani abu yana fita daga bakinsa baki marar dadin gani har ya mutu,wani irin kara naji a cikin kaina wadda tasani shiga firgici har na tsinci kaina a garinnan wajen yaya fatima bansan ya akayi ba,amma na kasa furta koda kalma daya data shafi Abdulwahab. A tunanina na tsetar da sameemah daga sharrinsa ashe van saniba suntiga sun hada ruhinta da nasu,sun cigaba da cutar da ita a tsawon lokacinnna ba tareda sanin kowaba,allah sarki baiwar allah,sun zalunceta da yawa,allah ne kadai zai saka mata abinda ubanta yayimata............." 💎*sameer a madubin gani*💎 Kuka ummeee take kaman ranta zai fita,duk dakin babu wanda baiyi kuka ba haka ya girgiza da al'amarinba,tabbas babu abinda ya gagari allah,kuma duk mai imani yaji labatin sai ya tausayawa rayuwar sameemah. Hajiyah Fatima ce ta jawo ummee jikinta ita ma tana share nata hawayen a kan fuskarta. Malaminne ya numfasa kafin yace, "To yanzu tunda munji abinda yake faruwa aikin bazai dade ba za'a fara,saidai amma zai bada matujar wahala da kuma daukar lokaci,saboda sun riga da sun cakuda da jikinta da kuma gangar jikinta na tsawon lokaci,dan haka zamu dauki lokaci kafin mu rabata da abinda yake jikinta,idan aikin yayimin karfima sai munkaita wajen malamina tukunna,amma kafin sannan zamu fara dadai kokarinmu. Daga haka ya sallami ummee tunda ta samu lafiya,baba umaru da alhaji musa kam basuce komai ba sai jinjina lamarin da sukeyi. Komawa gida malamin yace muyi saidai mu dunga zuwa muna kallonta,duk lokacin da muka zo sanda yake tsaka dayimata magani haka zamu dunga jiyo ihunta da kuma karar wata irin dabba da takeyi. Yau kimanin tsawon wata biyi kenan da kulle sameemah a gidan malamin,kullum sai na je dubota amma daga waje yake bada damar hangota kawai,saboda shiga wajen hatsarine sosai,koyaushe cikin saka magani ake,saboda hana wasu shedanun shiga jikinta,dan idan abin yayi yawa bazata iya daukaba. Duk da munsan malamin yana kokari saidai kuma kunsan dan adam dason cigaba da gwada wani salon musamman idan wannan din babu cigaba. Yauma hanyar gidan malamin na nufa,dan hanyar ta kasance ta bina ce a kkwace rana,a bakin gidan nayi parking na shiga,sallama nayi masa amma kuma babu alamar mutum a ciki,hanyar dakin sameemah na kalla wata zuciyar tana cemin naje wata kuma tana cemin na bari sai ya dawo. Bin ra'ayin zuciyata nayi wanda ta mato akan san ganin masoyiyarta,a hankali nake tafiya zuciyata tana bugawa kadan kadan har na wuce inda muke tsayawa idan mun zo ganinta. Kofar na tura na sameta a daure kaman ko yaushe,kayan jikinta da aka daureta dashi har ya sanza kala,ita kanta yanayinta harda fatar jikinta ya sauya,ta fita akan halittar jikin dan adam. Duk da haka ban yi alamar zan tsaya daga karisawa izuwa gareta ba,dan hakan shine abinda zuciyata take ra'ayi . 💎*sameemah a madubin gani*💎 Tun ranar dana gwada yin sallah na suma,dana tashi naji ni a wani yanayi daban,babu abinda zuciyata take buri sai cutar da duk wanda idona ya sauka akansa,kullum zugani ake akan na bar wajen mutane na tafi inda nafi dacewa dashi. Lokacin da wani mutumi ya zubamin wani abu naji wani duhu ya lullubeni dan dama yaushe nasaba da kasancewa cikin duhun. Ta shi nayi na samu jikina daure da wani abu kaman zare,amma duk yunkurin dazan yi nayi amma na kasa tsinkewa daga zaren,sai kuma na kula da yanayin siffata yana sauyawa zuwa wata kala daban irin ta mutanen danake gani a cikin mafarkina. Duk da bansan wane lokaci nake wajenba amma nasan na dad'e a jikin wannan zaren danan tsana a rayuwata,da kuma mutumin dayake zuwa yama konamin jikina da wani ruwa. Ina jin Karar bugawar zuciyoyi suna zuwa kusada inda nake,amma duk sanda wannan zuciyar tazo ina jin kalar nata sautin yasha banban dana sauran,duk da cewa suma sauran zuciyoyin inaso naga sun matso kusada ni amma nafi burin wannan zuciyar ta matso kusadani,kodan na fita daga kangin abinda suka zagayeni. Shikadaine idan yazo nakan samu kaina da dagawa yana kallonsa,saidsi babu yanda na iya haka nake ganinsa ya juya ya tafi,duk da inason yah matso inda nake amma nafisan yakasance a nesa saboda kar na cutar dashi. A inda nake ɗaure ina jin karar takun sawun wani ruhi yana tunkarowa inda nake,dan tun daga nesa nake iyah jiyo karnin jininsa yana dukan hancina. Tun daga bugawar zuciyarsa na tabbatar wannan ruhinne wanda yake tamkar haske a baƙar duniyata,ba abinda zuciyata take muradi sai kasancewa dashi a kowanne lokaci. Duk da nisanta dashi yana cutar dani amma babu yanda zanyi,domin idan na kasance mai yi wa ruhin soyayyar gaskiya,toh bazan so ifiritan ta suje jikina su cutar dashi ba. Hannuna na kalla wanda farcen yayi tsawo yana zubar da jini,ga kuma gashin kaina dayayyi wani tsayi kaman na sabuwar fatalwa,ɗaga idona nayi na kalli ruhin daya shigo ɗakin,tun daga idonsa ya nuna bayason kallona a wannan halin,saidai babu yanda zayyi,domin hakan shine ƙaddarata,wanda bana tunanin zai iyah cika alƙwarin daya ɗauka na fiddani a cikin wannan halin. Saboda duk maganar da suke ina jinsu,yanda yake fadar zai iya komai duk wahalar sa idan har zan samu lafiya matukar bai sabawa mahaliccinsaba. Dawowa nayi daga tunanin dana tafi ganin ya wuce wani layi a gabana yana shirin karisowa daf da inda nake,kallonsa nake da alamar gargadi wanda nasan ya fahimci mai nake nufi,amma kuma bashida niyyar juyawa da baya. Hannunsa yasaka a kunkumina tareda jawoni zuwa jikinsa ya kankameni,a duj tsawon zamana a wsjen yau ne kadai najj wani abu wai ita nutsuwa ta jiyarci jikina,sannan bakin dana dulmiye a ciki yafara wsshewa ina kallon hasken daya zomin dashi a gabana,har na samu kaina dason yi masa magana saboda abinda naji yana cewa, "Kiyafemin sameemah,koda kowa zai ji tsoron zuwa inda kike ni bai kamata na yi hakanba,ko umma idan tana kallo bazata yafeminba saboda nima na taak rawa wajen zamowarki haka dana kasa rike ragamar kulada ke wsnda aka bani. Sameemah inasonki sosai,har yanzu ban fidda ran zaki dawo gareni muyi rayuwar da muke da burin yi ba,kiyi yaki da abinda yake jikin ki sameemah,karki bari suyi galaba akanki,ke jarumace nikaina nasani matata jarumace,zaki iya sameemah kituna muna jiranki zamu iya komai dan gsnin kin fita a wannan kangin da izinin allah,amma zaman ki a wajennan yana cin zuciyata,komai nafara idan na tuno inda kike bana iyawa ..............." "Yyyyyyaa.....sssammmeerrr". Saurin dagowa yayi ya kalleni dayaga nayi magana,abinda bai taba tsammaniba,duk da maganar bata fita sosai ba kasancewar na dade banyi ba amma nasan yagane abinda na fada ,nima naji dadin hakan dana ga yaji sunansa dana ambata. Hawaye naga ya ciko a idonsa sai kuma naga yana murmushi,kai na yarike yasake rungumeni a jikinsa yana fashewa da kuka,dago kai na nayi kafin na dage nace, "Wanke jiki datti banaso sune suke so ni banaso,ka wankemin datti banaso ba dadi datti jikina da jini" Saurin kallon jikina yayi da alamun ya gane abinda nace,tsugunnawa yayi wajen kafafuna inda jinin daya fito daga jikina ya daskare babu dadin gani,duk da banajin komai sai karnin jinin mutane amma nasan akwai wari a tattare dani. Sautin wata zuciyar naji tana matsowa inda nake,wacce take saka firgici a cikin rai na,gurgana nin danayi ne yasaka sameer dagowa ya kalli bakin kofar,tashi yayi tareda tsayawa a gabana yana kallon malamin. "Meyasa kashigo har nan wajen sameer,bakasan hadarin hakan ba ko?" "Ba abinda zai faru malam,saida ina ga yakamata a tsaftace mata jikinta,dan tace dattin yana damunta,ga kuma al'ada da tayi a jikinta" "Yaushe tayi maka magana da har ta fadi hakan,idan magana zata fito daga bakinta to ba yaren dazaka gane takeba,sunayine dan a kuncesu" "Amma malam da hausa tayi magana,kuma tace wai kazanta suke so ita bata so,kuma suna kara karfi a hakan" Shiru malamin yayi kaman mai zullumi,nikuwa fargabata kar ya kori sameer daga inda nake ,ajiyar zuciya nayi danaji yace bari ya nuna mana bandaki,amma sai an zagaye dakin tukunna da tsari. Juyowa sameer yayi tareda since igiyar datake hannuna,yi nayi kaman zan fadi naji ya rike ni gam a kirjinsa ko kyankyamin bayaji. Irin daukar amarya yayimin tareda nufar dakin da aka nuna masa,a jiyeni yayi a gaban wani baban baho wanda yake cike da ruwa. Kayan jikina yafara cirewa a hankali,har yagama rabasu da jikina. Wani cup ya dauka a gefe yana debo ruwan yana wanke abinda yayi cinyoyina zuwa kasa. Lumshe idona nayi ina jin azabar da ruwan yakeyi akan fatata saboda na hadashi da wani abin,da kuma sanyin da hannunsa yake haifarwa akan fata ta yana maye gurbin zafin. Bayan yagama wanke dattinne ya daukeni zai sakani a cikin ruwan,hannunsa na rike ina rokonsa da idanuwana,murmushi yayi kafin yace, "Kiyi hakuri kinji,babu abinda zai faru kisaka hakan a cikin ranki,komai zai zo da sauki,ina tareda ke kinji" Sauke ajiyar zuciya nayi kamin yasakani a cikin ruwan,ina kallon yanda yake kallon jikina amma haka ya kawar da duk abinda yake cikin ransa ya wanke ni tass. Wani kaya ya dauKa masu duhu ya sakamin.doguwar rigace amma tana da laushi sosai. Motsin shigowar wani naji hakan yasa na matsa jikinsa da sauri ,shima ya rungumeni yayi sosai wanda hakan yasa naji nutsuwa a cikin raina. Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎43~44💎 💎*sameer a madubin gani*💎 Tun lokacin da sameemah ta fada cikin hali na rashin lafiya ban taba jin tsoronta koda da na minti daya bane,saidai zamanta a wajen babu mutane a kusada ita yana cimin tuwo a kwarya,musamman kazantar wajen. Bayan na gama yi mata wankan na saka mata kaya kamanta har ya fara dan dawowa duk da kowaye ya kalleta yasan ba lafiyar ta kalau ba,ita ma kanta naga taji dadin tsaftace jikin. Karar shigowar mutunne yasa ta manne a jikina kaman wanda za'a yankata,har yaron malam din ya kawo ruwan magani ya ajiye amma bata dago idonta ba. Kawowa nayi kusan fuskarta amma ta hade rai tareda kawar da baki,nima bata fuskar nayi tareda nuna mata da gaske nakeyi,saida taga ina kokarin cireta daga jikina kafin tayi saurin kaiwa ruwan maganin bakinta,shima tana hawaye da kuma cuno baki. Kurba biyu tayi ta mayar da kanta kan kirjina tayi shiru. Lokacin danazo tafiya rikeni tayi tana gunzin kuka kamar ana zare ranta,kallon malamin nayi nima zuciyata a karye,dan har ga allah banason barinta nima,sunkuyar da kai yayi kafin yace, "To gaskiya sameer ban san ya zacayi ba amma fitarta waje a kwai hadari sosai,baga iyah mutane ba harda ita kanta,saboda zamanta ananne yasa har take iya control din kanta wani lokacin,amma idan ta fita gaskiya rabata dasu ba abune mai sauki ba" Nima kaina na fahimceshi,haka duk da zuciyata tana so amma na cireta daga jikina na fita da sauri,dan banason jin ihunta kuma tanayine danni ba dan kowaba. Haka Har rayuwa ta sake daukar mu zuwa sati biyu,amma babu wani cigaba sosai,kullum ina zuwa na dubata nayi mata wanka sannan na bata magani saboda ni kaidaine take karba tasha a wajena batare da anyi mata dole ba. Idan ka ganta fes da ita amma wani lokacin sai fatar jikinta tayi duhu gashinta ya tashi,to a lokqcin ne muke gane cewa ba ita bace. Kowa hankalin sa a tashe yake,saboda yanayin da sameemah take ciki,har saleemah ma takan damu tazo ta ganta,idan tazo tayi da kuka kenan tana lekata,ummee kuwa ba'a magana,dan in ka ganta ta bar kan sallaya to wani uzurin zatayi. Ranar ina office malam ya kirani akan wata magana,da sauri nabar abinda nake nayi hanyar gidansa. Ina zuwa na tarar su baba umaru da su ummee a zaune da alama kowa yana wajen ni ake jira. Kallona yayi tareda cewa, "Wato abinda yake faruwa sameer shine,malamina ya dawo daga sudan jiya,wanda nake da niyyar turaku wajensa,saidai ba anan yake zaune ba yana cikin kauyene,sannan fita da ita zuwa can akawai hadari sosai,zakuyi matukar kokarinku wajen ganin kuna tareda ita kafin a isa can din,kar ku bari ta bace muku ku rasata a jejin zuwa wajensa. Idan kukaje kuce nina turoku munyi magana dashi akan matsalar,inshaallah za 'a samu dacewa da izinin allah,amma fah saikun kula sosai,karku bari a samu matsala idan ba hakaba kuma bazata taba warkewa ba sai wani tsananin ikon Allah" Tunda mukaji yana wannan gargadin munsan ba abune mai saukiba,saidai munji mun gani inshaallah zamuyi da izinin allah. Shirye shiryen tafiya wajen maganin muka fara,dani da ummee da alhaji musa da kuma baba umaru. Muna shirin tafiyar ne wani labarin daban shima yazo mana wanda yasa muka daga tafiyar zuwa bayan kwana uku. 💎*Sameerah a madubin gani*💎 Yanzu zaman mu da ummaruje babu yabo babu fallasa,an cire masa karfen dake kunkumin sa yanzu yana tafiya da kansa,ba said da wheelchair ba,saidai har yanzu wani abun sai a hankali tunda dama ba sona yake da farkoba duk da yanzu naga zuciyarsa tana karkatowa wajena. Hajiyah mairo ma ta daina abinda take,dan idan na tura umaruje muka je falonnata hira har sai mukai sha dayan dare,wani lokacin harda salma ake idan jinyar cikinta ya daga mata. Dan ba karamin wahala take sha ba,koyaushe cikin zuwa asibiti akeyi,wani lokacin ma hajiya mairo ce take kaita idan alhaji bayanan,yanzu ba karamin tausayinta takeji ba,dan dui mai guntun imani idan ya ganta zai tausaya mata matuka. Ranar da umaruje ya fara tafiya har yar walima hajiya mairo da hada saboda murna da farinciki. Gaskiya kam munyi murna sosai ganin cigaban da ake samu,musamman ma shikansa uban gayyar,yagaji da zaman gidan ba wajen zuwa,a ranar ne kuma alhaji bala yabashi takardar aikin daya sama masa wanda zai fara zuwa wani satin. A zaune muke da daddare ina gyara kaya shikuma yana kan gado,hankalina ya tafi wani daban ban kulaba said jin hannunsa nayi a bayana,juyawa nayi ina kallon idanuwansa wanda suke dauke da yanayi kala Kala. "Kiyafemin abinda nayimiki sameerah,tabbas ba shedar mutum daga farkonsa ko kuma daga waje said na zauna dashi,sannan baka gane mai sonka sai ka shiga wani hali,nikaina shaidane akan son dakikemin sameerah,fatana allah yabani iko nima na soki na baki farinciki kaman yanda kika sadaukar da farincikinki domin zama dani duk da kinsan bazan baki abinda kowane miji yake bawa matarsa ba na d'a" Saurin saka hannuna nayi a bakin sa tareda cewa, "Wayace naka baka bani farincikiba ,kaine ka bani farinciki tunda har ka yarda na zauna tareda kai,duk da kana da damar nesantani da inda kake,ba abinda nake bukata daya wuce muyi rayuwar farinciki kaman yanda kowane ma'aurata sukeyi,y'ay'a bayarwace ta allah ba akanmu aka fara hana haihwa ba kuma ba a kanmu za'a kareba" Runugmeni yayi kaman zai maidani cikinsa yayinda nima nayi yanda yayi din. Hayaniya mukaji a sashen su salma hakan yasa nasaka hijabina akan kayan baccina muka fito nida umaruje. Hajiyah mairo ce rike da salma alhaji bala kuma yana binsu a baya. Asibiti muka nufa inda akayi dakin haihuwa da ita da sauri. Muna nan zaune har akayi sallah gari ya waye amma babu alamar sauki a lamarin,sai ihunta damuke ji kawai da nishi. Zuwa rana su inna karima sunzo harda inna larai,dukkanmu kowa jikinsa yayi sanyi ganin halin da take ciki. Ganin ana shirin kwana biyu amma babu alamar haihwar ne yasa likita ya nemi alhaji bala yasaka hannu ayi mata aiki kawai. Hakan kuwa akayi muna gani aka wuce da ita dakin tiyatar ko motsin kirki batayi sosai,fargaba bazata fassaruba a wajenmu kowa yayi kozai kozai. Muna nan zaune nurse ta fito da yarinya a hannunta an nannadeta a towel,katuwa da ita cikin koshin lafiya. Karbarta nayi da sauri saboda nice a bakin kofar,kallon yarinyar nake wanda take kama da umaruje sak,mamakin hakan nayi saidai dana tuna kaman alhaji bala suke sai koma tunanin wani abu daban na ya halin da uwar y'ar kuma take ciki. Tun kafin nayi magana nurse din tace, "Wacece sameerah,mai haihwar tana nemanki keda mijinta da kuma mahifiyarta" Da sauri nabi bayan nurse din gabana yana bugawq saidai bansan mai yake faruwa ba. A kwance take akan gado da kayan marasa lafiya a jikinta,karisawa wajenta nayi ina rike hannunta,murmushi tayimin na dauriya kafin tace, "Anty sameerah kinga yarki dana haifamiki koh?,ban taba tunanin a duniya zaki kasance yaya a gareni mai son farincikina ba saida na samu kaina a inda ke kadai nake da ita,ina alfahari dake,to nasan Y'a ta ma idan yakasance tana karkashin kulawarki bazaki bari wani ya lahanta rayuwarta ba sai inda karfinki ya kare,dan haka ni salma nabaki Y'a ta dana haifa halak malak kece mahaifiyarta ban yadda ta nemi wata uwaba bayan ke.ki yafemin abinda nayi miki sannan ki taimaka wajen nema min gafara a wake duk wanda na zalunta" Kuka nake son yi ko kuma zuciyata ce takeson tsayawa na kasa tantancewa,mai salma take nufi ai wasiyya takemin yamzu haka,ina kallom sanda ta daga kanta tana kallom mijinta da kuma mahaifiyarta wanda suma sun so daurewa amma sun kasa yin hakan. Kai na narike wanda yake barazanar fashewa saidai babu yanda zamuyi muna kallon sanda numfashi na karshe ya fita daga cikin huhun salma,ta mutu kenan ta bar duniyar kamar bata taba wanzuwa a cikinta,saidai hotunan ta dakuma tunanin ta acikin zukatan mutanen da tayi rayuwa dasu. Hannunta data rikeni ne ya shika yayi samyi kalau kaman ba nata ba. Innalillahi wa inna ilaihi rajiun Kullu nafsin za ikatul maut Haka Muka fito daga dakin da take kwance babu mai cewa wani abu a cikinmu. Gawar muka karba muka nufin gidan mijinta domin ayi mata sutura a can,kowa ka gani mutuwar ta bugeshi ba kadan ba ,musamamn mu da muke zaune da ita. Ina runtime da yarinyr a kirjina ,duk duniya ji nake babu wanda zaizo yarabani da ita,idan kuwa yace dole sai yayi hakan to saidai yafara ta kaina tukunna. Kwananmu uku muna karbar makoki amma sameemah bata zoba,iya yah sameer ne ya taho da kuma anty saleemah,sai wata mata itama mai kama da sameemah,nan ake bada labarin mahaifiyarta ce kuma kanwar mamar antu saleemah,har ma da rashin lafiyar da sameemah takeyi na bata gane komai,ni dama banyi mamaki ba dan ni kaina shaida ce sameemah ba ita daya bace,dan haka fatan samun sauki mukayi mata. Abinda mukafi girgiza dashi shine ashe mahaifinta ne sanadi kuma tash wahala tun tana yarinya na kokarin boyewa da kuma halayyar da takeyi dan ta nesanta yan uwanta daga garets,hakika ta bani tausayi matuka,ashe duk abinda muke cikin duhun kai,bamuyi amfani da lokacinmu da muke tareda ta hanyar da ta daceba ,mun cutar da kanmu mun kasa fahimtar matsalarmu har saida mukayi nesa da juna lokacij babu wanda yake gani kowa kafin muka fahimci kuskuren da muka tabka na asarar lokaci. Tare muke kwana da zainab wanda itama d'anta yayi wayo sosai,dayake suna jigawa wajen aikin mijinta sai sanda suka zo tukunna.da kuma anty saleema sai jinjira salma wanda aka maida mata sunan mahaifiyarta, duk kukan takemin bana gani sai ma kuka danake sakawa,sainaga kaman mahifiyata take nema,saida su zainab suka nusar dsni akan dole na jajirce daure damamrar zama uwa ta gari ,sanann na runtse ido na hukuntata idan batayi dadai ba nan gaba,ta hakane kawai zan yi mata tarbiyya sabanin yanda akayi mana. Saida akayi sadakar bakwai kafin kowa ya watse ya barmu dagamu sai mu,ni kuwa nacigaba da rainon little salma dan ba a boyemata sunaba. Shikansa umaruje yana zon yarinyar a ransa,dama jininsa ce yanzu kuma zai reneta tamkar yar sa.......... Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎45~46💎 💎*sameer a madubin gani*💎 Hakika lokacin da mutuwar salma ta doki kunnen mu ta gigizamu matuka.Tabbas mutum ba a bakin komai yakeba ,duk abinda kake allah yana kallonka. Shirin da muke na kaiwa sameemah wajen magani muka bari domin zuwa gida gaisuwar mutuwar salma. Tunda muka je kullum said nayi waya na tambayi ya jikin sameemah,saidai maganar daya ce kullum saukin bahaushe. Bayan sadakar uku muka taho saboda kowa yasan halin da muke ciki na jinyar sameemah. Bamu muka iso garin porthacourt ba sai wajen karfe takwas na dare,a lokacin na ajiye saleemah a gida na nufi wajen sameemah,itama saleemah bani gaisuwa tayi akan na kaiwa sameema duk da tasan ba amsawa zatayi ba. A zaune na sameta a dakin da ake killaceta ta sunkuya kaman wanda tayi bacci,tausayinta ne ya kamani musamman ganin kayan dayake jikinta tun wanda nasaka matane kafin mu tafi,banyi mamaki ba danna san bazata bari wani ya matso kusada ita ba,ga duhu da kuma sauro,wannan bai sa na damu ba saboda nasan ba cizonta zasuyi ba. Karisawa nayi gavanta na tsugunna,dagowa tayi a hankali tana kallon fuskata kaman mai nazarin wani abu,can kuma sai ta rungumeni da karfi,da alama tayi kewata dayawa,hakan yayimin dadi ba kadanba,duk da halittunta da siffarta sanjawa suke da kadan kadan amma hakan bai sa kida da rana daya naji kyamar matsowa inda takeba,saima tausayinta dayake kama zuciyata. Cikin dabara kaman ko yaushe na tsaftace mata jikinta kafin nasaka mata rigar ta,banyi niyyar barin wajenta ba dan na kudiri niyyar gobe zamu kaita wajen malamin da aka turamu wajensa. Washagari da safe nayi nayi taci wani abu amma taki kulani,nima nasan bazata ci ba kawai gwadawa nake ko za'ayi nasara wani lokacin,muna cikin hakanne su ummee suka zo tareda su alhaji musa,har da inna ramatu wacce ta biyo baba umaru dan taga jikinnata. Suna hada ido da sameemah tayi kanta da sauri tareda kaman kafarta da garzamata hakoranta,ihu take tana kara amma bata sauta ba saida muka hadu tukunna. Lashewa bakinta take wanda yayi ja da jinin inna ramatu kuma tana murmushin mugunta,kokarin komawa takeyi amma su baba umaru suka dauki inna ramatu zuwa asibiti dan suma tayi dan wahala. Ba karamin rauni sameemah tayi mata a kafa fa hadda cire mata naman cinya. Dukkan mu mamaki mukayi da abinda ya faru,sai a lokacin na kula ba abinci take bukata,so take ta dunga cizon mutane amma kuma ta kasa cizon wanda suke masoyanta. Wani ruwan magani aka sake yi mata wanka dashi wanda zai saka jikinta ya shika kaman bata da laka,sannan akasaka wani sasari a hannunta da kafarta nikuma na daure karshensa a kunkumina. Da haka aka kinkimota zuwa cikin mota kowa sai bugu kirjinsa yake. Driver alhaji musa ne yake tukamu sai alhajin a gefensa,a baya kuma nida ummee ne sai kuma sameemah da take cinyata a rike. Motar da take binmu kuma su baba umaru ne a ciki harda malamin da yayi mata magani,ba yanda ba ayi na baba umaru ya tsaya a wajen inna ramatu amma yaki yarda,a cewarsa likitoci zasu kula da ita. Tafiya Muke a hankali har mun kusa kauyen mun fita daga cikin gari,mutsuniya naji sameemah tafarayi kaman wanda ake tsikararta,saurin dubawa nayi naga idonta a bude,saidai bakikkirin suke kaman an zuba gawayi a cikinsu,wani rin mika tayi tareda yin wata kara saida muka rufe kunnuwanmu dan karta bata mana dodon kunne. Jijjigar datake ne yasa dole saida driver ya tsayar da motar,saboda tana koarin jawo muyi hatsari,kofar da take kusada mu ta banke da wani irin karfi tafita da gudu. Jana take saboda hannunta a daure yake kuma sarkar tana kunkumina,tirjewa nake tana jan mu yayinda suma malamin suke binmu a baya,gashin kanta ya tattashi sai gurnanai takeyi ,danni kaina kallon naci amanarta take min,dabarace ta fadomin ganin bazan iya tsayar da ita da haka ba saina nannade sarkar a jikin wata bishiya ina numfarfashi dannima a matse nake a jikin bishiyar sosai. Wani mutumine mai dogon gemu da cikar gwarzini yazo inda muke,kallo na karemasa dannasan ba malamin da muka zo dashi bane,kara tirjewa take tana ja da baya tareda sake daga sautin kukanta lokacin da mutumin ya tunkareta,wani abu ya shafa mata a goshinta take ta yi wata mika ta fadi a wajen kaman ta mutu. Motar muka koma domin karisawa gidan babban malamin,sai a sannan na kula aahe shine wanda yazo wajenmu a jejin,gidannasa babu nisa dan mun iso garin ma ashe. A wani dakin kumadu aka saka ta saidai wannan duk jikin dakin rubutun Qur'ani ne,hadda wasu addu'oin da baka sansu ba ma. Muna isa aka kaimu masauki domin muyi sallah azahar dan a ranar za'ayi mata rukiyya basai gobeba,dan yawan jingirtawar da akeyi yawan kara mallake jijinta da sujeyi .munayi sallah bayan munci abinci,dan abincinma dabawa mukayi saboda tashin hankalin da muke ciki. Kafin mushiga dakin da take saida ya kafa shaidu tukunna. Banda wacce take haila,banda wanda yakeda aljanu a jikinsa,haka kowa sai yana da alwala,kuma bakinsa bazai daina kiran sunann allah ba har a gama. Haka muka amince da duk sharadinsa kafin muka zauna a wajen,sameemah tana tsakiyar wajen an saka mata wata doguwar riga fara,bayan mun zauna ne malamin ya umarci wani a wajwn akan ya sinceta daga sasarin da take daure dashi. Mudai muna ganin ikon allah har yagama sunceta amma bata ko dago kaiba bare ta motsa daga yanda take. Karatu aka fara yana amsa kuwwa a cikin dakin,kadan kadan jikinta yafara rawa kaman ana jona mata shokin,bayan an dan dade da karatunne ta fara ihu tana yagar jikinta da karfi. "Kai Wai miye kuke hakane,ba dama ku barmu mu zauna lafiya mai muka muku haka,dan mutum daya bazaku barmu mu dauka a matsayin namu ba?" "Badaku nake ba kananan shedanu ,so nake shugabannaku dayake turoku yazo da kansa,ku fada masa shine ke nema,ku kuma idan nan da wasu mintina baku fitaba to sunan ku matattu" Cigaba tayi da ihun bayan ta tayi magana malamin yabata amsa,can kuma sai tayi shiru alamar abun ya lafa. Ganin malamin yafara karatun dayafi na farkone yasa muma muka fara babu tsayawa,fatar jikinta ce take sauyawa zuwa baka,ga farcuna da duka fito sunfi na farkon kafin zuwan mu nan,tsorone yashiga zukatanmu saidai bamu daina karatun da muke ba har saida mukaji ta fara gunji,malaminne yatashi da sauri ya debi wani ruwa a kofi ya watsa mata,bayan ta gigicene yasake diban wani ya zuba a cikin bakinta ta hafite da sauri tana kama makogaranta tareda sakin wani ihun dayafi na farko,magana ta fara cikin wata babbar murya, "Ka bukaci nazo amma kuma kana cutar dani ai ba haka mukayi da kaiba ko,zancen na sauta kuma bazai yiyu ba dan itadin muna tareda itane tun tana shekara uku a duniya" "KO tare aka haifeku da ita yau zaka barta,sannan kuma ka dawo mata da kuruwarta daka dauka,wacce kasaka mata a jikinta kuma yanzu zan fitar da ita ko kana so ko bakaso" "Ahah karka cire ruhin mu dayake jikinta ka fadi duk abinda kake so zamu baka,bakasan tsawon lokacin da muka dauka muna rainansa a cikin jikinta bane,saida lokacin tashinsa yazo sanann zaka bata komai,zakayi mana asara dayawa,dan haka duk abinda kake son a duniyar nan zan baka matukar zaka bar ruhin dayake jikinta lafiya,har nata ruhin ma zamu dawo mata dashi indai zaka bar wannan baxaka fitar dashi ba" "Eh shikenan na yarda da yarjejeniyar da mukayi dakai,zaka bani wani abu,sukuma yan uwanta zamu mantar dasu,amma da sharadin ruhinta ma zai zauna a jikinta kafin daya bak'in ruhin ya tashi" Mai kunnuwana suke jiyomin,ai malamin ya yadda da abinda shedanin ya fada kenan,har na tashi zanyi wani abu sai naji nakasa tashi daga inda nake ,murmushi fuskar sameemah tayi wanda daga gami ba ita bace wannan. Can Bayan wani lokaci muna zaune mun zubawa sarautar allah ido,vanda kiran sunan allah babu abinda nake a cikin raina,wani haskene yashiga jikin sameemah kafin ya bace kamar bai shigaba. Hakan yana faruwa malamin yayi sauri yah watsawa sameemah wani ruwa dan kadan dayake cikin wata jarka,wani kara tasaka kafin tafara cewa, "Ka cucemu ka yaudaremu saida muka dawo mata da ruhin ta sanann zaka juya mana baya,mai yasa zaka kafe ruhinta ta yanda bazamu iya kara dauke shiba bayan kasan munyi yarjejeniya akan bazaka cutar da ruhinmu dayake jinkinta ba sanan........." Saurin yin shiru tayi sanadiyyar wani ruwan da malamin ya zuba a bakin sameemah sannan ya matse bakin saida ta shaye shi,wata addu'a ya cigaa dayi kafim yayi mana alamar mucigaba dayi,muna cikin yine mukaga ta fara rike cikinta can kuma sai ta koma rike makogaro,shakewa muryarta tayi tafara kokarin amai. Wani bakin ruwa ta fara amarwa can kuma saiga kan wani abu kaman maciji bakikkirin,zuwa lokacin kadan daga cikinmu ne suke iya bude bakinsu suyi addu'a ,ciki kuwa harda yarannasa idon su yayi wuri wuri. Cigaba tayi da kokarin amai abin yana fita dogo dashi har ya kare fitowa daga cikin bakinta,motsi kadan abin yayi kafin yadaina motsin can kuma malamin ya zuba masa wani abu kaman farin gari nan da nan ya bace kaman bai daba wanzuwa ba. Kan sameemah dukka muka nufa wanda ta fadi tun lokacin da abin ya fita daga jikinta. Ru wan mag an in ya cigsbs da shafa mata,yana addu'oi kafin ya kalleni . "Mashaallah in allah ya yarda an samu nasara,saidai banida tabbcin tashinta,dan da kyar idan bai yi mata lahani a cikin ta ba lokacin daxai fito,musamman ma daya dade a jikinta,shine yake sakata komai sannan da dafinsa take amfani wajen kisa da kuma bada kariya ga kanta badan komai ba dan yasamu kariya jikinta har zuwa lokacin da zai mamaye jikinta. Yanzu munyu nasarar fitar dashi dama dashi suke iyah nemota har su san inda take,sannan kuma sun dawo mata da ainihin kuruwarta,dan haka ku gaggauta kaita asibiti a duba lafiyarta,sannan ga wannan ruwan shi zata dunga sha daga lokacin data farka har na tsawon sati guda,idan kuma ta manta wani abun kar a tursasa mata,in ma kuma babu matsala shikenan,zaku iya tafiya allah ya kiyaye ya kuma sawwake ameeen" Kinkimarta nayi da sauri muka nufi mota domin kaita asibitin,su alhaji musa da kuma baba umaru sai godiya suke masa,har sannan hankalin su bai dawo jikinsu ba sa abinda suka gani. Bamu wani dadeba muka iso asibitin cikin barrack din kasancewar gudu muke a motar ba kamar lokacin da muka tafiba. Muna zuwa ummee ta saka kayanta na aiki,duk da jikinta har sannan a sanyaye yake daga ka ganta kasan ba karamin kokari takeba kawai. Dakin taimakon gaggawa aka shiga da ita,inda aka shiga bincikar ina ne yake da matsala a jikinta,babu wani rauni a jikinta saidai duk ilahirin halittar cikinta ta gaji sosai wanda hakan yasaka ta shiga coma saboda shock din da jikinta ya shiga. Duk mun ji dadi da babu rauni a cikinta amma shiga coma din ma bai mana dadi ba sam. Dakin kulada ita aka mayar da ita,duk an manne hancinta da wayoyin dazasu dunga kai mata abinci zuwa cikin jikinta. Kasan cewar akwai ummee dazata dunga kulada ita sannan kuma akwai wasu nurse wanda suke shige da fice sai yazamana ba sai mun zauna tareda ita ba saidai mu dunga zuwa dubata kawai. Duk da cewa hankalin mu ba tashe yake kaman da ba amma kuma ba a kwance yake ba sam,domin yau kimanin sati biyu kenan da kawai sameemah wajen mai magani amma ko motsi batayi,saidai na'ura da take nuna cewa a tana raye ba ta mutuba. Tunda sameemah tashiga sati biyu da shiga coma hankali na yafi na kowanne lokaci tashi,saboda gani nake kaman bazata tashi ta dawo gareniba,a bakin kofar na tsaya ina kallonta yanda take kwance,ita da matacce basuda maraba,karisawa nayi a hankali har zuwa onda take kwance na zauna a kujerar da take gefenta,kama hannunta nayi na rike wanda karin ruwa yake shiga ta cikinsa,muna nan zaune har na kara kaina da katifar da,take kwance akai,can kamar a mafarki naji kaman tana motsa hannunta dayake cikin hannuna,basarwa nayi danna san bazai wuce gizo takemin ba kaman yamda ta sabayimin acikin mafarki,cigaba tayi da motsa hannun wanda zuwa lokacin kuma abin yawice gizo,yafara zama kaman gaskiya ,kodai da gaskene kai itace take motsi ???...... Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎47~48💎 💎*sameemah a madubin gani*💎 Na Dade ina kokarin bude idona domin naga hasken dayake cikin duniya amma nakasa samun damar hakan said yanzu,duk da dishi dishi nake gani amma nasan ba a gida nake ba. Abubuwan dasuka farune suka fara dawomin cikin kwalkwalwata,inajin na kamar bani bace,saidai nafison yanayin yanzu akan na baya,dan yamzu inajin kaman ina da yanci ba kaman lokacin baya ba. Motsa hannu na nayi sai naji kaman an rikeni ,juyowa nayi a hamkali amma vana ganin abinda yake faruwa sosai. Lokacin da idona ya fara komawa dadaine na hada ido da fuskar da na cire tsammani da sake ganinta a rayuwata,dakyar bakina yake motsawa dason furta sunansa akan harshena, "Ya.......hhh....sameeer" Murmushin da yayiminne idonsa cike da hawayen farinciki yasaka ni nima jin dadi,saboda yamzu na gane ba mafarki nake ba yah sameer ne a gabana. Bayyi magana ba said rungumeni da yayi a jikinsa kaman za'a kwaceni,karar murda kofa mukaji wanda yasa ya dam zare jikinsa daga gareni. Ummee ce tashigo itama fuskarta dauke da farinciki,bayan ita wasu nurse ne suka shigo amma daga baya suka tsaya,danna kula har yanzu tsorona suke,dan murmushi kawai nayi dan banga kaifinsu ba ko kadan. Ciremin karin ruwan tayi da kuma wasu na'urori a jikina saboda nasamu damar tashi na zauna Yah sameer ne ya taimakamin na tashi saboda rashin karfin jiki,tunda nace yah sameer ban sake cewa komai ba sai jijjiga kai kawai danake idan aka tambayeni. Haka nake ga kaman shine ainihin halina rashin magana,sainaga dama,dan banajin yin rashin kunya amma kuma vanajin yin magans ma saidai kawai kallo da ido.ummee ce ta kalleni kafin tace, "See my daughter now,bazatayi fadi abu da baki ba saidai ta nunawa mutum tana son abu,babu sakewa da mutum sai wanda ranta yaso zama dsshi,ko mutum zai kwana yana zolayarta sai taga dama ta kulashi,ko ba haka ba baba umaru" "Murmushi yayi irinna manya kafin ya daga kai alamar hakane. Dukka dakin dariya suka saka harda yah sameer da kuma anty saleemah wanda itama dazo dubani da taji na tashi. Farouq kuwa ta gudu yazo gefena yana dariya,yah sameer ne ya dorashi akan katifar danake a kusa dani,shima iya Murmushin kawai nayi masa banyi magana,abin yabani mamaki sosai kuma sai na tsinci kaina da jin hakan normal ne babu matsala. Kwana na biyu a asibitin na koma gida,duk da haka mutane basu bar zuwaba,harda zainab ma tazo daga gidanta,sameerah ce kawai bata zoba saboda abinda ya faru,nikaina na girgiza danaji abinda yah faru,inda nace idna komai ya daidata janze gida na gaishesu. A zaune nake a bakin gado ina tunanin abinda yafaru ni kadai,wani nayi dariya wani nayi jimami musamman kisan danayi da kuma rashin sallah,shiyafi damuna sai kuma zaman danayu a palastine wanda yamzu ma ina son sake zuwa dan akwai abinda van karisa ba tukunna. Jinayi an dafani ta baya hakan yasa na juya da sauri,dan yanzu bana jin sautin bugun numfashin mutum ko kuma sautin dayake yi daga nesa,sannan jikina baya warkewa da sauri kaman da ,hujin allaurar da akayimin a asibiti ma suna kan fatata basu goge ba ,ta haka na fa him I yanzu dadai nake da kowanne mutmu mai lafiya. Juyowa nayi muka hada ido da sameer, "Tunanin mai kike kedai,ba ance ki dunga hutawa ba" "Yanzu ma ai hutuwa nake tunda ba aikin danake yi " "Wannan ba hutune bane bawa kwalkwawa service ne,yakamata ki huta sosai komai yakoma normal tukunna" "Yah sameer na gode " "Godiyar kuma ta menene kike min yanzu" "Ta taimakona dakayi,ta kuladani da kayi,ta zama a kusadani da kayi,ta rashin jin tsorona dakayi ,ta rashin kyamata dakayi,bazan iya yimaka godiya a kan hakan ba dan allah kayafemin abinda nayi maka a baya,ka tayani bawa kowa hakuri dan......." "Shhhh,banason jin wanann daga bakinki sameemah,komai nayimiki ne dan allah da kuma soyayyar danake miki,babu abinda nake nema daga gareki sai ki soni kaman yanda nake sanki sannan ki kasancen mace ta gari kuma uwa ta gari a gareni" "Inshaallah zan yi kokarin wajen kasancewa haka a gareka,burina ka kasance bango a garemu mu iyalanka" Budemin hannusa yayi akan nazo jikinsa vanyi musu ba kuwa dan a lokacin ina bukatar wanda zaimin rarrashi,mun dade a haka kafin ya fita masallaci dan an kira sallah r isha. Nima alwalar na iyo na fara jera sallah iya adadin da jikina zai iya dauka,dan doke sai na biya bashi nsallalon a dake bina. Ina cikin sallah yah sameer ya leko dakin dayaga ina sallah ya barmin sakon na sameshi a dakinsa. Wanka na shiga na duje jikina sosai,lokacin dana fito mulke jikina nayi da lotion mai sanyin kamshi kafin na fito da wasu kayan bacci sabbi dal. Lokacin dana sakasu nikaina nasan nayi kyau sosai,bare kuma mabukacin na namiji ya kalleni,hijabi na dauko mai girma nasaka kafin na fito daga dakinnawa zuwa dakinsa. A hanya na ci karo da saleemah zata shiga kitchen,har na dauke kaina zan wuce tasha gabana da sauri. Sunkuyar da kaina nayi amma kuma saina ji tace, "Kiyi hakuri da abinda ya faru sameemah,duk da kinsan zan iya cutar dake idan na samu dama amma haka kika ceci rayuwata a hannun wannan mutanen,zuciyarki mai kyauce tun da bare kuma yanzu,hakika dab vansan kece kanwata data bata bane,babu wacce nake so kaman lokacin kina karama kullum har na girma sai na kalli hotonki da tunanin ina kike,nayi kewarki kasancwar nikaidai na tashi mace,ashe ban sanj ba kaddara zata kawoki har cikin gidana mu zauna tare a karkashin miji guda daya,kiyafemin abinda ya faru a baya,ina tabbatarmiki hakan bazai sake faruwa ba ,dama daga vangarena ne komai yake faruwa ke bakya tankamin har se na shiga gonarki da yawa" "Babu komai anty saleemah allah ya shige mana gaba" Dariya tayi kafin tace, "Hmm a baya ina ta mahaukacjn kishi ashe vansaniba ke bakida ikon morar mijinma,kai ai nikam anyi wawiyar yaya,yanzudai karna bata miki rai aje a yi amarci lafiya,kar ku damu zan hada komai kafin ku tashi,yau daya first in history zan shiga kitchen saboda kanwata gobe". Shigewa nayi zuwa dakin yah sameer din ita kuma ta nufi hanyar kitchen din domin debowa zuhrah ruwa. Lokacin dana murda kofar kirjina ne naji ya buda,abinda banyi mamaki ba gashi zai kasance,wai nice zan shiga dakin mijina kuma da tunanin bazan cutar dashi ba,sannan nasan bazan fito haka kawai ba face ya karbi hakkinsa a wajena. Saida na leka babu kowa a dakin kafin nasaka kafata a cikin. Zama nayi a bakin gado ina jiransa dannaji karar ruwa a bandak8n. Fitowa yayi da towel a kugunsa,ruwa yana zuba a jikinsa,kamshin sabulun ne ya daki hancina take kuwa ya saukarmin kasala mai nauyi a cikin jikina. Shikansa yakula da halin dana ahiga domin naga wani karamin murmushi a gefen fuskarsa,juyawa nayi na bashi baya domin yah shirya,amma maimakon haka sai damshin ruwa naji a hannuna dayake gefensa. Juyowa nayi numfashinmu yana gwauraya dana juna kasancewar kusancin dayake tsakaninmu bashida yawa,bakinmu ne yayi saiti dana juna hakanne yasaka yah sameer yunkurin sumbatata,ban nuna alamar zan hanashi yin hakan ba ko banza na tsaya naji mai ake ji,dan abune dana fiddda ran a rayuwata zan taba yinsa. Had'a bakinmu yayi waje daya da dan sakkanni kafin ko wannenmu ya ja baya yana kallon idanun dan uwansa dayake dauke da sako kala kala. Yah sameer ne yayi karfin halin yin magana kafin yace, "Turarenki Yana da matukar dadi,dam cikin kankanin lokaci har ya gama da kwalkwalwata,sannan wannan hijabin fah,daga gani akwai wani abu a cikin. Murmushi nayi tareda sunkuyawa,yayinda shikuma ya yaye hijabin dayake jikina,dan zare ido yayi ganin kayan dake jikina,kuma da alama ya yaba da shigar danayi. "Duk wannan ni'imar nikadai ne,mallakina ne batareda wani ba,ah na manta Ashe fah wani ya rigani ,dan har kyautar mota aak bayar akai" Harararsa nayi tareda kai masa duka a kirji,danna kula tsokana ta yake,jana yayi muka fada gadon ta baya,shafa man da bayyi ba kenan aka lula dani sabuwar duniyar da ban taba tsintar kaina ko tunanin zan shigeta ba,sai gashi gwarzon yayannawa ya nunamin karna sare da yin nasara,sannan ya taimakamin wajen nunamin yanda yancin rayuwa take,mai zanyi a duniyarnan daya wuce na yi masa biyyaya sannan na faranta masa rai.............(toh kunji masoya fah) Kaman yanda anty saleemah ta fada kuwa da safe tahada mana karin kumallo mai rai da lafiya,daga ni har yah sameer bamu muka tashi ba sai wajen karfe sha daya,kasancewar rashin bacci a idonmu tunda mukayi asuba muka kwanta kaman mun mutu. Bayan mun tashi dakina na nufa saboda sanja kaya,tunda banida kaya a dakinsa. Lokacin dana fito dukkansu suna zaune,yah sameer sai yuwa anty saleemah tsiya yake wai tayi abijci saboda kanwarsa,amma lokacin da suna zaune yayi yayi taki yin abinci saidai yan aiki suyi. Haka muka gama cin abincin cikin kwanciyar hankali,babu aiki saboda weekend ne dan haka zama akayu a falo ana tadi. Raba kwana akayi kwana bibbiyu kowa,anty Saleemah ce ta raba kuma mun yadda da hakan gaba dayanmu. Ranar litinin na koma aiki saidai yanzu banice mai bada training siadai zaman office kawai,da farko naso kin komawa aiki amma yah sameer yabani kwarin gwiwa hakan yasa na koma da goyon bayansa. A yanzu nayi kusan wata guda da warkewa daga ciwon dana ke fama dashi tsawon shekarun danayi a rayuwata,yanzu nagane cewa dukkan abinda yafaru dani ubana ne sanadi. Ranar dana ji labarin nayi kuka sosai,abin ya girgizani matuka,kaman yanda kowane d'a yake samun gata daga ubansa ni kuma nawa ubanne yajefani matsala,yanzu na daina ganin laifin soyayyar da mahaifin saleemah yake bata,koba komai shi bai halakar da ita ba kaman nawa uban. Tunda naji labarin abinda mahaifina yayi nakara ganin kimar mahaifiyata,fiyeda lokacin dana fara saninta a matsayin mahaifiyar tawa. Yanzu rayuwarmu ta daidaita da irin kowanne rayuwar da take faruwa a gidan ma'aurata masu kwanciyar hankali. Nida yah sameer mun saka lokaci sanda zanje zariya ganin gida,duk da banyi wani murna da zuwan ba amma kuma inason zuwa din. Ana gone zanje ina ta shirye shirye a daki,saidai komai yinsa nake cikin dauriya,tun safe nakejin tashin zuciya zuwa dare kuwa nafara amai ba tsayawa lokacin da ya sameer ya shigo dakinma a bandaki nake ina ta kwarara amaai. Shiryawa nayi muka tafi asibiti anty saleemah tana ta yimin sannu,ummee bata asibitin lokacin da mukaje wata ce ta dubani inda aka gano ciki a jikina mai kimanin wata d'aya da sati d'aya. Nayi murna sosai sannan na girgiza da jin lamarij,lokaci daya rayuwata sai sanjawa take a hankali. Gida muka dawo tunda babu wata matsala laulayine kawai shikuwa dole daurewa zanyi bar mu rabu da abinda yake cikina. Daga tafiyata yah sameet yayi akan sai cikina yayi dan kwari tukunna,nima naso hakan dan kwata kwata jikina babu karfi,komai cikin dauriya nakeyi. Lokacin dana tashi tafiya cikina yana da wata hudu ciff na kama hanyar gida kuma gidan gandu,wanda rabona dashi tun lokacin da aka kaini gidan ya sameer. Abayace a jikina baka tasha duwatsu sai yane sai hijabi dana dora akai,dam yanzu shigata kenan. Tare muka taho da farouq da akayiwa hutun makaranta. Na Dade a bakin gidan a tsayae ina kare masa kallo,abubuwa da dama da suka shafi rayuwata wanda nayi a gidan suka fara dawomin dallah,hakika ko naki ko naso gidan gandu ya taka muhimmiyar rawa a cikin rayuwata wanda bazan taba iya gogewa ba,shine gidan dana budi idona na ganni a cikinsa. Tunanin ummah hajara ne yadawo min cikin kaina,lokaci daya idona yafara zubar da hawaye dana tuna da uwata takaina d'aya tamkar da dubu,dai kuma mutuwar salma ma da ta dokeni ba kadan ba. Dawowa nayi daga tunanin danake kafin na kama hannun farouq muka shiga cikin gidan. Lambar asusu:3131951977 Lambar waya:09035784150 Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa. 💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎 *(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)* 💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu} 💎49~50💎 Sallama nayi lokacin dana shiga gidan abinda ban tabayi ba kenan a kundin tarihina na gidan. Inna Karima ce tsakar gidan tana diban itace,da alama wani abun zata dora,sakin baki tayi har yawu yana shirina zubowa da ta gane mai yin sallamr,bata amsa ba sai marabanku da zuwa da tace, Dakin mu na yanmata a da na nufah,wanda yanzu yake a matsayin na su hanifa da kuma sauran yam matan da suke sa'anninta harda yayunta. Kayanmu na ajiye a gefe nida farouq kafin na je iyo alwala domin nayi sallah. Bayan na idarne naji maganar baba umaru shida farouq a bakin dakin,fitowq nayi muka gaisa sai albarka yake sakamin ganin nasan ja daga yanda nake a baya sosai. Anan ne yake fadamin ai baba ramatu tama asibiti,tun cizon danayi mata a gidan malam kafarta ta rube tana rozayewa. kunyar kaina ce takamani ganin abinda nayi mata lokacin dana ganta a gadon jinyar tats. Aunty sameerah take tausar zuciyata dayaKe ita take wajenta,little salma tana bayanta tana bacci. "Kidaina fadar haka sameemah,nayadda yanzu duk wanda yayi ba daidai ba tundaga duniya yake ganin sakayya,dan haka bana jin komai na haushinki a rai na,kema ai ba'a hankalin ki kike ba,ki daina daga hankalin ki kinga bake d'aya bace yanzu,akwqi wanda alhakin kulada shi yake kanki" "Duk da haka anty sameerah abin akwai dimuwa a cikinsa,na manta banyi miki gaisuwa ba ,ya hakuri kuma" "Hakuri yazama dole saidai muce allah ya jikan wanda suka rasu" A sibitin na yini,inda umaruje dayazo kawo abinci ma inji hajiya mairo mukayi ta hirar yaushe gamo,little salma kuwa tayi bul bul da ita sanadiyyar kulawar da take samu a wajen ahalin gaba d'aya,koba komai naji dadin ganin bazatayi maraicin rashin uwaba,rashin uwa babu dadi nizan bada labarin hakan. Kwana na uku a gidan gandu na zazzaga ko ina har gidan Surayyah saida naje,ba karamin dadi tajiba da ta ganni,dan ta yayi wayo dan harta yaye shima da wani cikin,sai tsiya nake musu akan zasu tara garke. Har kyauyen su ummah hajara saida naje,suma sunyi farinciki sosai da samun lafiyata,musamman ma inna rabi sai tsokana ta take wai mai rashin kunya,sannan bata barin ta kwana,nidai Murmushi kawai nake mata dan ba sosai nake maida magana ba sai idan hakan yana da muhimmanci tukunna. Sati guda na dawo garij porthacourt hakanma yah sameer sai kirana yaka wai ya ishemu haka,saida na d'an koma seemah jar wuya kafin ya sarara min. Lokacin da muka isa gida anty saleema tayi mana girki muna zuwa muka sauka akai,sai tsiya take mana wai mun dauko gajiya,nidai ban kulata ba saida cikina ya dauka tukunna. Lokacin da cikina ya kusa watan haihuwa koyaushe sai ummee ta aikomin da magani,wani lokacin kuma tazo ta dubani,nidai na zuba ido kawwi naji girif tukunna. Cikin bayyi nauyi dayawa ba dan babau abinda yake hanani yi komai normal sao dan abinda baza'a rasaba. Lokacin da abu yazo gaff kuwa da daddarene kowa ya kwanta amma ni ina zaune kaman mayyah,inajin haushin su blacky a waje sai kuma kukan kwari. Tun ina daurewa amma naji abu sai gaba yakeyi,dukkan jikina rawa ya dauka saboda wani irin ciwo dayake shigata ta kowacce gaba ta jikina. Wayata na lalubo da kyar na bugawa sameer waya tunda yau ba a dakina yake ba yana dakin anty Saleemah. Ina jiyo hayaniyarsu lokacin da suka shigo dakin su biyu,sai kuma yah sameer dayake kiran ummee a waya yana fada mata abinda yake faruwa. Dakyar na yunkura na tashi anty saleemah taba jan hannuna,saidai kafin nakai ka tashin naji wani ciwon yaketa marata hakan yasa nakoma na zauna,nishi na fara babu tsayawa yayinda naji abu ya tokaro daga cikina zuwa wajen marata,salati nake yi tareda fadar wani abun davan wanda nibansan ma mai nake cewa ba. Kukan yaro naji a kasana hakan yasa na leka domin ganin mai yin kukan. Jinjira ce wadda cibiyarta har sannan take jikina sai kuka take,ita sanann da zo duniyar bata san komaiba sai yanda akayi da ita tukunna. Ummee ce tashigo da sauri,amma ganin yarinyar a hannun anty saleemah ga kuma mabiyya a gefe yasata sakin ajiyar zuciya tareda yin hamdala. Kokartawa nayi na tashi domin na nufi bandaki,dan ba abinda nakesonyi a lokacin sai yin wanka sannan kuma na samu na kwanta,dannagaji sosai. Aunty Saleemah ce ta biyoni bandakin ta hadamin ruwa mai zafi sosai,ina saka hannuna a ciki na cire da sauri tareda yimata kallon alamar tambaya,araina ina cewa anzo wajen. Itama kallona tayi tana bata rai,ganin banida niyyar sake saka hannuna yasa ta fita sauri ta kiramin ummee wacce take gyara yarinyar dana haifa yanzu. Haka ta tursasani ina tirjewa da komai saida na zuba wannan ruwan a jikina,gayyar bata fata da kuma zafin ruwa. Lokacin da na fito har turiri nake na ruwan zafi,zama nayi a bakin gado ina kallon ummee tana yiwa yariyar wanka,abinne yabani mamaki wai ni nahaifeta a cikina,abinda ko a mafatki bana kawowa ko kadan sai gashi yafaru,kuma fah ina sonta sosai,dan gabadaya hankalina yana kanta taya zan bata farinciki na kulada ita naga bata nemi abu ta rasaba,ashe haka iyaye sujeji akan y'ay'an su. Ina nan zaune har aka gama gyarata,ban zata ba saigani nayi ummee ta mikomin ita tana kallona,tubulbulcewa nayi tareda tambayar mai zanyi, "Oh wanine zai shayar da ita bakeba?" Karvarta nayi ina kallonta cikin sanyin jiki,towel din na same ina kallon ta inakallon maman,saita mata nayi a bakin ta kama,dan zafi saida na cije bakina,daga bayane dana naji zafin ya ragu. Tun kwana uku da haihuwata gidan yafara cika da mutane,saboda al'adar dakan yaji. Shikansa idan mutum yagani dauka zayyi sunan akeyi,anty saleemah ce ita da surayya akan komai sai shige da fice sukeyi. Ranar da ta cika kwana bakwai da haihuwa aka rada mata suna HAJARAH taci sunan ummah mu,wanda ranar ma saida nayi kuka na koshi,musamman yanda yarinyar ta dauko wani abu irinna mahifinta wanda yake kama da ummah nah,bazan taba mantawa da ita ba. Nida kaina na sakamata lakabi da ummulkhair saboda boye sunan,shikansa yah sameer ya ji dadin lakabin danayi mata dan ta cancan ci fiye da hakan. ** * * Shekarata biyu da haihuwa nayi niyyar zuwa garin palastine wajen mu'allim da kuma shaheedah,sai kuma wajen ogah binlad danna san yana ta nemana har yanzu. Tare muka tafi dukkanmu umarah,inda bayan mungama su hajiyah fatima da kuma anty saleemah suka dawo Nigeria nikuma muka wuce kasar palastine nida yah sameer da kuma Y'a ta ummulkhair. A bakin kofar gidan mu'allim muka tsaya nida yah sameer wanda yake gefen prison din yara dana zauna a baya,shiga mukayi da sallama matarsa ta amsa,bude baki tayi dan da alama ta ganeni. Gaisawa mukayi kafin ta kaini dakin mu'allim din wanda yanzu yah tsufa sosai karatu yake bayarwa a gida,dan tun randa na fada musu shugabansu yana munafurtarsu matarsa take fadamana yah daina zuwa kungiyar a gida yake karatu. Shima lokacin daya ganni yayi mamaki sosai,saidai yayi farinciki ganin yanda na koma uwa kuma mata ta gari abar alfahari ga yan uwa musulmi. A nan muka yini har dare kafin muka koma masaukinmu,washagari gidan su shaheedah naje,saidai mamanta tace tana kasar aurenta da yara hudu,sshaheed ne suke tare shima da matarsa da yara uku,ba wani gaisuwa sosai mukayi dashi ba dan ba shiri mukeyi ba. Ogah binlad kuwa danaje inda muke zaune van samesu ba sai filin wajen kawai,bansan kuma wazan tambaya inda suke ba dan haka dole na ha kura watakil sunyi wani wajen daban. Haka muka koma masaukinmu yah sameer yana ta yimin kallon alamun tambaya,shareshi nayi dan gaji sosai so nake na huta. Muna zuwa na fada bandaki nayi wanka nazo na bi lafiyar gado,ina dosana hakarkarina naji kukan ummulkhair a falo,shareta nayi na kwanta dan yarimyar ta fiye fitina ba laifi. Bankai gayin baccin na moreba naji yah sameer yans jijjiga kafada ta,tashi nayi na zauna ina lumshe ido tareda cuna baki. "Menene kuma yah faru" "Hhhhh uwata tayi kashi a tashi a gyara mata,kuma ma anyi sallah la'asar sannan ke kikacemin zamuje sha iska" "Uhh haba yanzu ba dama na huta wai,naga kashin kaima zaka iyha wankewa" "Kinga comon tashini kin faye bacci kwannan da kuma shagwaba baccin y is haka,kuma sonake ki bani labarin duk abinda yafaru dake a kasar nan" "Naji dama nasan zaka tambaya,yanzu bari na gyarata mu fita tukunna" Ta shi nayi babu yanda zamyi,kai rainoma babu dadi fah,ina yi mata wanka tana tirjewa tana rigima da haka na shiryata muka fita zaga cikin garin dan gobe zamu koma gida. Mun dade muna zagayawa ina fadaasa wajajen da mukayi aiki wani lokacin a ganomu muyi ta gudu. Dariya yadungayimin wai allah ya hada y'ay'an sa yar rigima da kuma daba,saida yaga naji haushi raina ya baci kafin ya daina yana bani hakuri,aikuwa yajawa kansa dan daina bada labarin nayi yayi ta tambayata amma nayi shiru. A Gidan hajiyah fatima muka yada zango lokacin da muka dawo dan itama anty saleemah tana can,ana ta dariya wai na dawo da tsarabar kasar palastine na ciki. Babu abinda zamuce sai allah ya barmu cikin sunnar manzon allah. Alhamdulillah nasamu sauyi mai kyau daga duhu zuwa haske,allah yahadani da miji gwarzo mai sona da kuma bani kulawa,ga kuma abokiyar zama dana samu wacce bazata cutar dani ba koda a bayan idona. Yanzu aiki na gaba shine yanda zanyi na inganta rayuwar gidan gandu daga rashin kyakykyawan muhalli da jahilci zuwa wayewar kai da kuma waje mai inganci. Idan allah yana taimakonka ba abinda zai gagareka musamman idan kasamu gwarzon abokin rayuwa kamar yah sameer. ALHAMDULILLAH ALA KULLI HALIN. Godiya ga allah subhanahu wata ala daya kawomu samun nasarar gama wannan littafin,allah yayi mana mai kyau da iyawarsa. Sannan godiya ta musamman ga wanda suka bani goyon wajen Daga taskar *sadi-sakhna* ______✍🏼