12/30/20, 10:50 AM - Messages and calls are end-to-end encrypted. No one outside of this chat, not even WhatsApp, can read or listen to them. Tap to learn more. 1/30/21, 8:05 PM - 111: Oct 17, 2020 Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: Lubna Sufyan *MARTABAR MU* *LubnaSufyan* _Free page_ 1 January 1985, Kano Nigeria. Tsaye yake bakin kofar gidan shi da yake haya anan unguwar Fagge, gidan da shine na biyu da ya kama duk a cikin unguwar a shekaru kusan hudu da auren shi saboda halin matar shi Maimuna. Halin da yanzun ya saka shi zullumin shiga cikin gidan, ko da wasa bai hasaso rana irin wannan zata zo mishi a rayuwar auren shi ba, ranar da zai tsaye a kofar gidan shi yana tattaro duk wani kwarin gwiwar da zai iya wajen shiga gidan. Dakyar ya iya sauke numfashi yana taka cikin soron hadi da shiga cikin gidan da sallamar da yasan ba lallai bane ta amsa. A zaune ya sameta kan kujera a tsakar gidan tana yanka alayyahu. Jikinta sanye da atamfa mai zanen tabarma da ta karbi farar fatarta, bakin nan dauke da janbakinta ja da a lokacin ko baka maya saka shi ba sai yai kwanaki biyu kan labbanka da alamun shi. Tayi mishi wani irin kyau, duk da cikin jikinta yasa kuraje fitowa a fuskarta. Ahmadi ya kasance cikin jerin mazan da kance "Farar mace ko da mayya ce..." Indai zasu samu suna so, tun bayan mallakar hankalin shi daya dora idanuwan shi akan Maimuna yasan tana cikin jerin matan da yake son kasancewa da ita har karshen rayuwar shi.  Shisa baiyi nauyin bakin fadin yana son ta ba, da yake ahalin Dikko gabaki daya abune mai wahala daga mazan su har matan su ace gashi yau sun fita daga gida sun auro bare. Koya ka shiga gida ka duba miji da mata sai ka samu wata halartacciyar alaka ta jini a tsakanin su. Ita kanta Maimuna din da shi Ahmadi dan mace da yar namiji suke, iyayen nasu ma in aka duba duka cikin ahalin Dikkon ne, ta bangaren mahaifiyar shi abokiyar wasa ce, ta bangaren mahaifin Ahmadi kuma Maimuna 'ya ce a wajen shi. Da yake su din boko ta shige su, sai aka dinga jinjina karancin shekarun Ahmadi duk da bayan karatun da yake shekarar shi ta karshe lokacin yana da tsayayyen hanyar samun shi ta kasuwancin takalma na manya da yara da Babban Yayan shi Ayuba ya saka shi a hanyar yi tunda kasuwanci ne silar arziqi kuma abin tinqaho ga ahalin Dikko gabaki daya. Ko da aikin gwamnati ka sami wani namiji nayi inka duba sai kaga ya hada da kasuwanci ko yayane. Hakan yasa ba'aqi bashi auren Maimuna ba. Amman surutun ya kara samo asali da Yayan Ahmadi wato Bala da yake nashi kasuwanci a asalin tsatson su wato jihar Katsina da bai ko da maganar aure ba. Amman wata goma cif bayan auren Ahmadi da Maimuna kowa ya fara sambarka, ba'a maganar komai sai albarka da take cikin auren wuri, gasu yanzun da dansu da yaci sunan Mahaifin Ahmadi din wato Mutaqqa suke kiran shi da Khalifa. Lokacin ne kuma Ahmadi ya kammala karatun shi da yake a bangaren lissafi inda aka tura shi yin bautar kasa a jihar Katsina. Ga albarkar kyautatawa iyali da yake gani ta wajen nasara kan duk wani al'amari da zai saka a gaba. Da yake Maimuna tana cikin matan da suke haihuwar da Hausawa kan kira gwarne, cikin yarinyarta ta biyu Zubaida ya shigane ko watanni takwas cikakku Khalifa baiyi ba, wayewar da suke da ita yasa suka dauki shawarwarin likita, Khalifa da lafiyar shi dimir har aka yaye shi. Yanzun ma tana shayar da Zubaida lokacin da ta sami ciki na ukku da yake a jikinta a yanzun. Da tsohon cikin Zubaida dole suka tashi daga gidan yawan da yake haya saboda rikicin da aka kwasa tsakanin Maimuna da daya daga cikin yan hayar. Sai bayan auren su ya fahimci ita din bamai hakuri bace ba, akan magana kalilan ma bakinta baya shiru. Dole ya samu wannan gidan mai daki biyu da suke a ciki yanzun suke zamansu su kadai, daman saboda tunanin bautar kasar da zai tafi da zaman kadaici da bashi da dadi shisa ya kama cikin mutane. Yanzun ma dai komai ya kusan zuwa karshe tunda tun kafin auren shi da Maimuna yana da filin shi da Yaya Ayuba yasa ya siya kusa da gidan shi. A cewar shi su kadaine maza da suke gari daya cikin yaran Alhaji Mutaqqa, shi Bala yana Katsina, kuma acan yake zaune da matar shi bayan auren shi. Ya kamata ace suna kusa da juna. A lokacin ma rabin kudin ne yake da shi, da yake Yaya Ayuba yana da hali saiya cika mishi, a hankali ya biya shi yake kuma gina tanqamemen filin da taimakon Yayan nashi. "Maimu uwargidan Ahmadi, fara jinin Dikko....fara hasken idaniyata" Ahmadi yai mata kirarin da yakanyi mata tun lokacin amarcin su saboda tayi mishi kyau ba dan kadan ba duk da babu jituwar kirki a tsakanin su kamar da "Hasken da ya kasa hanaka hango Maryama..." Ta karashe maganar kanajin daci da zafin kishin da yake dauke a muryarta, kai kawai Ahmadi ya jinjina, indai rikicinta ne kan karin auren da zaiyi ba sabon abu bane ba. Shidin tunda ya fara amsa namiji ya tsara rayuwar shi da mata biyu, ko da wasa baya hango kanshi zaune da mace daya tal. Sanin hakanne ya fadawa Maimuna tun lokacin hidimar bikinsu, amman dariya kawai tayi. Yanzun ne ya fahimci ma'anar dariyarta, bata dauki maganar tashi da muhimmanci ba sam a wancen lokacin. "Ina yaran?" Ya tambaya cikin son sauya zancen, bai jira amsarta ba ya wuce cikin dakin da jan kafet ne shimfide. Sai yaga dakin yayi mishi girma saboda babu jere, a hankali harsun fara kwashe kayayyakin su zuwa sabon gida tunda abu kadan ne ya rage a dayan bangaren da Maryama zata zauna. Shigar shi tayi dai-dai da tasowar Khalifa yana mishi oyoyo, Zubaida na son maimaita abinda Khalifan ya fadi cikin wani yare na daban. Dariya yayi sosai yana kamata ya dagata, duk lokacin da ko idanuwan shi ya dora kan yaran sai yaji wani nishadi na daban ya ziyarce shi. Yana son Maimuna, yayi wayon sanin dadin iyaye, amman yawancin kaunar shi ta yan uwace ya sani. Sai yanzun da yakejin kaunar Khalifa da Zubaida da bai taba sanin kalarta ba, da Zubaida a jikin shi ya zauna, dai-dai shigowar Maimuna da farantin da yake jere da kwanoni, karba yayi ba saita tsugunna ba saboda cikin jikinta. Aikam dakyar ta samu waje gefen shi tana zama. Abincin ya bude yana ganin shinkafa da miya harda naman kasuwa da ya saka shi jero addu'ar godiya ga Allah da ni'imar da ya wadatasu dashi. Musamman a lokacin da tattalin arziqin kasa ya shafi jihar Kano matuqa, mutane na cikin yanayi na rashi, idan ka samu abinda zaka mai bakinka koya yake ba karamar ni'ima bace, balle shi harda nama. Cokali ya dauka ya dibi miyar yana zubawa a gefe ya cakuda ya diba yakai bakin shi bayan Bismillah, lumshe idanuwan shi yayi saboda dadin abincin, indai ta wannan bangaren ne bayajin Maimuna. Yana kuma jin dadin yanda duk kalar rikicin da zasuyi baya shafar abincin shi da shimfidar auren su. Lafiyar shi na da muhimmanci a wajen ta kadan ba "Ko zaka ci abincin ne?" Ahmadi yai maganar yana kallon Khalifa daya girgiza mishi kai, shima yayi ma yaron tayine kawai dan sabo dayi badan zaici ba. Inba yana gida lokacin abinci yayi ba su hadu suci, sam Maimuna bata yarda da su saka mishi hannu a cikin abinci bayan sunci nasu har sun ture. Ba'a bata wannan tarbiyar ba, ba zata bari yaranta su dauka ba. Duk kaunar shi da su kuwa baya mata katsalandan akan tarbiyar su saboda zaiyi mata shaida tsaye take wajen saka su hanya me kyau. "Maimunata in dai girkine... Anya akwai abincin da zanci yakai naki dandano kuwa?" Ya fadi cike da kauna da yabawa, baki kawai ta tabe, tun haihuwar Zubaida kaf dangi da kalar soyayyarta da Ahmadi suka tafi a bakinsu. Yanda ko kunyar lokacin baya nunawa, a gaban kowa yake bata kulawa da dukkan zuciyar shi, sai ake alakanta hakan da zurfin boko da yayi. Shi kanshi bai hango tsayawar karatun nashi a Degree kwara daya kawai ba, yana da burin yin karatu mai zurfin gaske. Maimuna zata shiga aji biyu sakandire aka tsigeta aka aura mishi. Ganin kaunar da yakewa boko yasata nacin koyon turancin da baya gajiyawa da bata darussa akan shi wajen shi. Batason ko da gaba yaga wata a hanyar bokon nashi yaji ita din kamar ta gaza ta wani fanni, musamman yanzun daya sami aikin koyarwa a jami'ar Bayero din da taimakon wani Malamin su da jinin shi ya hadu dana Ahmadi din, shekarun zaman su kuwa da nacin Maimuna yasa ta kalaman da suke mata wahala a harshen turanci kadanne, lokutta da dama takan yiwa Ahmadi magana cikin harshen dan kawai tanajin dadin yabawar shi da kalar kwakwalwarta. Wani irin so takewa mijin nata da bata hadashi da komai ba, tun da karanci shekaru take da kishi na fitar hankali, kishin da ko kaya iri daya bataso ana hada mata da sauran yan uwanta, jibga kuwa tasha ta babu adadi lokacin da take gida kan ta kafe ba zata saka kaya kala daya da sauran yan uwanta ba. Kaf dakinsu itace yarinya tilo da take taya mahaifiyarta da suke kira da Yayya kishin matar Baban nata Inna da bata komai sai kokarin kyautata musu. Ita kanta Yayya takanyi mamakin inda Maimuna ta kwaso dabi'unta saboda tana da yakinin ba kalar tarbiyar da tayi mata bace wannan din. Maimunar ma inda zaka tambayeta lokacin da ta fara qin Inna ba zata iya tunawa ba, kawai ta wayi garine da tsanar yanda take ganin Inna ta saka kalar kayan da Yayya ta saka, ko kuma Baba ya siyo abu ya baiwa Inna a tsakar gida gabansu. Har ranta takanji tuquqin bakin ciki, da Inna bata aurewa Yayya miji ba, sam ba zata zo tana daga kafadu ta saka kaya kala daya da Yayya ba. Takan tuna kalaman mahaifiyarta lokacin da take da rai "Maimuna na rasa inda kika kwaso wannan kishin naki, wallahi na rasa. Allah ya rangwanta miki shi karya zame miki matsala" A zuciyarta bayan amin takan raya "Ni kadai zan zauna a gidan mijina, babu macen da zata zo ana siyo mana kaya iri daya da ita" Tun kafin tasan dadin auren kenan, ballantana yanzun da takejin kaunar Ahmadi na ratsa duk wani sassa na jikinta. Lokacin hidimar auren su da yace mata "Kinsan Ahmadin ki na mace biyu ne ko?" Dariya tayi sosai, duk zancen da yai mata na zama da mata biyu raha ta dauke shi, a zatonta labarin kalar kishin da take dashi yaji shisa yake zolayarta. Sai ranar daya dauketa dan suje taga ginin shi da yayi nisa ne tashin hankalinta ya fara ganin kalar tsarin ginin, a gigice suka dawo gida. Inda tai wani irin zaman dabas a kasa tana sakin kururuwar da Ahmadi yaga ko lokacin da labarin mutuwar Yayya ta riske su batayi irinta ba tana fadin "Tozartani zakayi? Ahmadi asirina zaka tona shisa kake tunanin hadani da wata? Ashe soyayyar da kake mun duk karyace? Kulawar nan taka duk yaudara ce?" Sosai kalamanta suka girgiza shi dan ya dauka sanar matan da yayi tun kafin auren su zai rage kadan cikin kishin daya kula tana dashi a kan shi, dan ko yan uwanshi da suke ciki daya bataso suna rabar shi. Balle kuma ayi maganar wasu can daban. Ranar ya dauka ya gama ganin tashin hankalinta, kwanaki biyu sukai cur bata bari sun runtsa ba a gidan. Shikuma lokacin ya kyalla idanuwan shi kan Maryama harma Yayanta yasan yana ciki, manya sun sani, an dai boye zancen ne saboda ya fada musu bai gama shiri ba sai ginin shi ya kara nisa za'a tsayar da zancen auren sosai. Da yake itama Maryama duk ahalin Dikkon ne, alakarsu tafi karfi da Maimuna akan shi, tunda Kakkanin Maimuna na wajen uwa da kuma na Maryama itama na wajen uwa abokan wasa ne na kusa, ba bare bace zai auro. Yanda Ahmadi ya dauka zancen sanin kowanne lokaci zai iya kara aure shine tashin hankali mafi girma da zasu shiga dashi da Maimuna, sai da aka tsayar da ranar auren shi. Sai da Maimuna tasan wa zai aura asalin tashin hankali ya fara. Ranar inda Allah yasota daga Khalifa har Zubaida suna gidan Yaya Ayuba. Dan ko gida bata kulle ba, kuka take wiwi, da kafafuwanta ta isa gidansu Maryama inda ta shiga babu ko sallama sai ruwan tijarar da ta sauke musu "Ashe kasa kuke jira ta rufe idanuwan Yayya kuci amanata, tunda kuke zuwa gidana badan zumunci bane da shirin ku aurawa yarku mijina ne...me yasa duk mazan dangi sai Ahmadi na? Me yasa zakuci amanata haka?" Duk yanda suka so ta kwantar da hankalinta fur taqiya. Kuka take musu tana surutai harda zagin da batasan lokacin da taji shi kwakwalwarta ta nade mata su ba. Sai da kowa a gidansu Maryama yai tunanin ko Maimuna tana da iskokai da ba asan dasu ba. Duk da akance kowacce mace nada nata, dalilin bayyana ne wasu da yawa basu samu ba. Sai da aka kira Gwaggon Maimuna din Bare da take aure nan kasa dasu, tukunna ta samu ta fitar da Maimuna daga gidan tana janta zuwa nata gidan. "Gwaggo auren cin amana zasuyi, Maryama fa suke neman aurawa Ahmadi na" Lallashinta Gwaggo takeyi sosai kafin ta kara fada mata maganganun da suka sake firgitata "Waye baisan Karime da shige-shige ba? Kaf dangi fa kowa yasan gidansu da bin bokaye. Kina ganin ita taki barin kishiya ta zauna a nata gidan. Biyu fa ta fitar, wallahi idan akace miki Ahmadin ma basu kyale shi haka ba ba'a musu. Babu wanda bai shaida kaunar da take tsakanin ku da Ahmadi ba..." Ai sai Maimuna ta kara dora hannu a kai tana rushewa da wani sabon kukan, sai yanzun take gane menene firgici "Na shiga uku ni jikar Hanne... Gwaggo karsu fitar ni daga gidana, karsu rabani da Ahmadi..." Kara riketa Gwaggo tayi "Ki share hawayenki, wacece Karime ballanta Maryama, ke kinsan in ba anbi ta karkashin kasa ba, mai Ahmadi zai da wata Maryama....yarinya duk ta gandame a gida ba mashinshini. Karki damu akwai Malamina dana aminta dashi, shine yaimun aikin wannan yarinyar da aka hada da baqar iska..." Hannu Maimuna tasa tana share hawayenta, dan indai Malamin da Gwaggo take magana shiyai mata aiki ya raba babbar yarta da bakar iskar da aka tura mata har tayi aure, to aikin shi naci. Dan tunda suka tashi tasan duk sa'annin yar Gwaggon suna da yara wajen hurhudu a dakunan mazajen su, a tarihin ahalin Dikko matansu da wahalar gaske su cika shekaru sha biyar ba a dakin mazajan su ba, wasu ma tun suna shekara sha uku, lokacin da za'ayi shabiyar din da goyon yaro. Amman yar Gwaggo takai shekara ashirin da bakwai kafin tayi aure. Bata bar gidan Gwaggo ba saida kwarin gwiwar Malamin Gwaggon zai mata maganin matsalar auren nan da Ahmadi yake so ya jajibo musu. Dan ko da ya dawo gidan ya rufeta da fadan da tunda suke duk tarin laifukan da takeyi bai taba mata irin shi ba akan zuwan da tayi gidan su Maryama hakuri ta bashi. A ranar kuwa ta kwana tayi juyi tana zubar da hawaye, tana kara tabbatar da asiri akayiwa Ahmadi, inda babu asiri shidin bazai taba daga mata murya akan wata mace ba. Ba'a cika sati biyu ba Gwaggo tazo gidan ta kawo mata magunguna da rubutun da zata sha ta shafe jikinta, sai maganin kuma a barbada a abincin da Ahmadi zaici. "Kinji asiri ne ko? Turaren ne ta goga tazo nan gidan dashi, har a kofar gida tayi miki barbade ya tsallaka" Kada kai kawai Maimuna tayi, mutum ba abin yarda bane, shisa kawarta daya Khadi tun tasowar ta, saboda rashin yardar da take da ita. A shekarar da ta wuce Maimuna ba zata manta ba, wajen sau hudu Maryama na zuwa gidan da sunan zumunci, ashe duk karyace, mijinta take kokarin aurewa. Wasu cikin kudaden da Ahmadi kan bata da ba wani abu take siye ba dan shidin mai kyautatawa iyalin shine ta diba tabawa Gwaggo dan ance gaba harda na tsari za'a karo mata da wanda za'a turo aljanin da zai katange gidan ko da su Maryama zasu gwada wani asirin. Ranar jikinta har bari yake da Ahmadi yakai lomar abinci, sai tashi tayi tabar mishi dakin tana wucewa bayi ta kulle, inda tai zaune tana garzar kuka, sai takejin kamar taci amanar zaman su, kamar bata kyautawa kaunar da Ahmadi yake nuna mata ba da ta barshi yake aikawa cikin shi abincin da yasha garin magunguna har kala biyu, ga lamurje da ta hada mishi da ruwan rubutu. "Kaga abinda hange-gangen ka ya janyo mana ko Ahmadi?" Ta furta tana wani irin kuka mai taba zuciya, sai takejin kamar ta tsallaka wani waje yau mai wahalar komawa baya. Sai dai me babu abinda ya canza, da duk rana da yanda maganar auren Ahmadi take kara kusantowa. Maganar tashin hankalin da Maimuna take ciki ba'a fadi. Ga laulayin ciki daya sakata a gaba lokacin, kalar kulawar da Ahmadi yake mata na kara hura wutar kishin shi, ko rufe ido tayi ta kwatanta raba kaunar shi da wata Maryama sai zuciyarta tayi kamar zata tarwatse. Sai yanzun take ganin gaskiyar Khadi, take ganin wautar da tayi wajen kokarin hanata shiga Malamai saboda rashin kyawun hakan a addinance. Khadi itace ta ukku a wajen mijinta, shigarta sai da tayi nasarar fitar da ta biyun daga gidan. Bayan fitarta ne yai dai-dai da rabon cikin da Khadi din ta samu, dan ta fadawa Maimuna cewa Malamanta sunce mata kishiyarce ta qulle mata mahaifa. Da tana ganin kamar haihuwa nufin Allah ne, sai yanzun ta gasgata zancen Khadi, kishiya ba abinso bace ko da ta batumbatumi ce. Ranar da kanta ta sami dan aike har gidan Khadi tace inta sami dama ta leqota. Kwanaki biyu tsakani kuwa Khadi tazo gidan. Kuka sosai Maimuna ta tusa mata "Khadi ki taimakeni, Malaminkin nan da yayi miki aiki kije mun wajen shi ko zai taimaka mun akan Ahmadi, dan Allah Khadi, wallahi ya kara auren nan zuciyata bugawa zatayi" Dariya Khadi tayi har tana saka Maimuna jin haushi "Ai gara da kika farka, idanuwan ki suka bude... In anyi duniya da Manzo kin kawo kukan ki inda za'a share miki" Wannan maganganun sun kara karfin amintakar da take tsakanin su. Kudade Maimuna ta baiwa Khadi masu yawan gaske, dan idanuwan ta sun rufe da zafin kishin da bata tunanin addu'ar neman sauki akan shi, ta saki Allah ta komawa yan tsubbun da ta aminta sune kadai maganin matsalar da take fama da ita yanzun. Sai dai wani sabon tashin hankalin ta shiga dan Malamin Khadi ya hango dole sai Maryama ta shigo gidan sannan zata iya nasara a kanta "Da ayaba akayi mishi wannan mallakar, da ace baki ma farga da wuri ba da yanzun sun shiga tsakanin ki da Ahmadi, dole sai ta shigo gidan za'a san yanda za'a karya sihirin..." Ya kuma tabbatar mata dole saita kara jajircewa daga ita har yaranta. Kullum cikin boye-boye magunguna take da take bankadawa ma cikinta da yara a matsayin karya tambaya da kuma kaikayi koma kan masheqiya. Wasu da inta jika Ahmadi yagani sai tace mishi maganin shawarane da Gwaggo ta hado mata, wani lokaci harya karba kanshi tsaye yasha shima, tunda ta gano wannan hanyar cewa bokon shi bata rabashi da magungunan gargajiya ba take bashi wasu kanta tsaye da sunan maganin Basir ko shawara ko sanyi. Kishin da yake cinta ne yasa ta zabi daga musu hankali daga ita harshi ko zai kara saka tai gabala akan shi ya fasa auren nan, amman kullum nuna mata yakeyi asirin da su Maryama sukayi mishi mai karfine dan bazai taba iya fasa aurenta ba. Yanzun ma kallon shi take yanda yake yabonta kamar ita kadai din ta ishe shi, harya karasa cin abincin yanayin hamdala "Sannun ki da kokari, Allah yai miki albarka" Ahmadi ya karasa yana mikewa ya tattara kwanukan ya fita dasu dan ya taimaka mata, duk idan ta wuce da turtsetsen ciki haka, koya dawo yaga gidan qwal saiya kara jinjinawa mata, ko a tunani ya hasaso kanshi da cikin jikinta sai ya hango yanda zai wuni shame-shame a kwance, amman ita harda kokarin girki, ko da tana laulayi sai yayi da gaske take kinyin girki, koyane saita lallaba ta dafa mishi abinda zaici. Shisa darajarta a zuciyar shi mai girma ce. Ganin da yayi magriba ta karato ya saka shi daura alwala kafin ya karasa dakin yana fadin "Bari in fita masallaci...." Batace mishi kanzil ba, sosai yake kewar hirarrakin su da yanda halin ko in kula din da take nuna mishi yake ci mai tuwo a kwarya. Haka yasa kai ya fice daga gidan. Ko da sukai sallar Magriba nan suka tsaya da wasu cikin unguwa danjin labarin Makka daga sabon Alhajin daya dawo satin daya fita wato Sambo. Da yake Ahmadi ba ma'abocin zaman majalissa bane ba, tunda Alhaji Sambo ya dawo basu hadu ba sai yau, yakan tsaya a lokutta irin haka a gaggaisa dan karamcin mutanen unguwar ba karami bane ba. Haka Alhaji Sambo ya dinga nishadantar dasu da labarai kayatattu yana kwadaita musu zuwa aikin Hajji duk idan halin hakan ya samu. Kiran sallar Isha'i ya tarwatsa taron nasu, inda ana idarwa kai tsaye Ahmadi gida ya wuce, yana shiga soron ya mayar da gidan ya rufe sanin ba bako zasu karayi ba, inma sunyin a kwankwasa yaje ya bude. Jin shirun gidan ya tabbatar mishi da yaran sunyi bacci, da ya shiga daki kuwa Maimuna kadai ya samu, yasan harta kaisu dakin da suke kwana ta kwantar, baisan kuka takeyi ba saida ya zauna gefenta "Subhanallahi.... Maimuna? Lafiya? Me ya faru? Ko jikinne?" Ahmadi yake tambaya hankali a tashe yana riko hannunta, kai take girgiza ma duk tambayoyin shi alamar a'a kafin tace "Me yasa ba zaka rayu dani kadai ba? Me kakw tunanin Maryama zata iya baka wanda ni ba zan iya ba? Ka fadamun dan Allah kagani, Wallahi Ahmadi zan maka komai. Karka tonamun asiri ka hadani da wata...." Kallonta yake yanda kwanaki basu wuce sittin ba suka rage a daura auren shi da Maryama, har a sujjadar shi addu'ar kwanciyar hankali da dangana yakewa Maimuna saboda kishinta ya fara bashi tsoro, sake rike hannunta yayi, cikin taushin murya ya fara magana "Da wanne yare zan fahimtar dake ba zan kara aure bane dan in wulakantaki? Maimuna baki yarda da kalar kulawar da nake miki bane ba? Shin a duk rana bana nuna miki yanda kike da muhimmanci a wajena? Ba zai canza ba dan na kara aure" Wasu hawayen ne suka kara zubo mata saboda yaki fahimtar tsoronta, yaki gane ba soyayyar shi bace bata yarda da ita ba, soyayyar ce batason rabawa da kowa, tsoro take kar auren nashi ya zama sanadin da za'a rabata dashi gabaki daya "In dai ba wahayin auren nan akayi maka ba dan girman Allah, dan datajar Ma'aiki da iyayen mu kayi hakuri" Hannunta ya saki, duk hakurin da yake a kanta ya fara gajiyawa, tanayi kamar bata taba ganin an kara aure ba, kiriri kiriri take nuna kamar haramci yake son aikatawa ba abinda musulunci ya yarje mishi ba "Maimuna kinga gara ki kwantar da hankalinki ko zamu samu zaman lafiya tunda auren nan ba fasawa zanyi ba" Hawayenta ta share tana saka idanuwanta cikin nashi "Tunda an shanyeka daman ya zaka iya fasa aure?" Rai a bace yake kallon ta shima "Wacce irin maganace wannan? Ba zaki daina baiwa sh Gwaggo damar darsa miki wasu zantuka marassa kan gado a rai ba ko?" Kada kai Maimuna tayi cikin zafin rai "Babu wasu maganganu da ake darsa mun a rai sai gaskiya. Yanzun daga ina kake tunda ka fita? Adalcinne kake son gwadawa bayan tun safe ka fice daga gidan nan, dan lokacin naka da zan samu ma tun kafin ka aurota sai ka raba mana tare" Kai Ahmadi ya dafe yana rasa ta inda zai fara shawo kan wannan al'amarin "Idan nace miki ba wajen Maryama naje ba zaki yarda?" Yanda take kallon shi ya sakashi dorawa da "Tunda nai maganar kara aure kike neman laifina a duk wani abu da zanyi, karyatani kike ko gaskiyata na fada miki. Halayen nan babu inda zasu kaiki Maimuna, karki rage kimarki a idanuwana wallahi" Yanda ya karasa maganar yasa wani abu tsinkewa a cikinta, da gaske an asirce mata Ahmadi, in har da bakin shi yake furta hango raguwar kimarta a idanuwan shi an asirce shi "Ashe kimata zata iya raguwa a idanuwan ka? Kaga dalilina na gudun aurenka ko? Kaga abinsa suke sa kana fadamun tun kafin ta shigo, wanne irin wulakanci zan gani kenan nan gaba?" Take maganar tana wani irin kuka da yakeji har ranshi shisa ya mike saboda bayason biye mata, bayason bata mata rai fiye da yanda yake a bace ko dan cikin jikinta. Kuma da a karo na farko ya zanta sirrin gidan shi da babban abokin shi Nasiru saboda tsoron kalar kishin Maimuna daya gani shawara ya bashi mai kyau, kalaman Nasiru sun zauna mishi sosai "Su mata ba'a biye musu, hakuri ake da halin su saboda wasu lokuttan kamar yara haka suke da karancin tunani. Laifine kayi mata da kara aure dole kuma tayi kishi, na kula shi kishin nan ya bambanta a tsakanin mata, kowacce da kalar nata. Kayi hakuri da duk wannan tashin hankalin da takeyi, da anyi auren zata hakura. Gani take kamar intaci gaba da daga maka hankali zaka hakura ka fasa. Kai dai karka biyeta, in ranka ya baci kabar mata gidan saika huce ka koma gudun biyewa zugar shaidan" Aikam shawarar Nasiru ta mishi amfani wajen kaucewa rikicin rashin dalili da Maimuna kan takale shi da shi. Yanzun ma dakin yaran yaje yana samun tabarma ya shimfida kusa da yar katifar su da suke bacci a kai ya kwanta. Yasan halin Maimunar shi, duk fadan da zasuyi bata iya bacci ba'a kusa dashi ba, da almatsutsan kishin nata sun sauka da kanta zata zo ta neme shi. Dan haka ya lumshe idanuwan shi yana musu addu'ar tabbatar alkhairi a wannan auren da zaiyi da kuma zaman lafiya bayan yin shi. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:05 PM - 111: Nov 1, 2020 2 May 1985, Kano. Da gaskiyar iyaye da kance kukan yaro yafi komai daga hankali, har kasan ranta take jin kukan Rayyan, a gaggauce ta karasa wankan, sabonta ne sai ta saka hijabi idan ta daura zani sannan take fitowa daga wanka, kamar yanda takan shiga da ita. Amman yanzun kam haka ta fito, hijabin ma a bandakin ta baro ta. Ganin ta lallaba Rayyan din yayi bacci shisa ta lallaba tadan watsa ruwan ta fito, ashe ba nisa baccin yayi ba. Tana daga labulen gabanta nayin wata irin mummunar faduwa ganin Maryama data mika hannu tana shirin daukar Rayyan "Me kike kokarin shafa mishi?" Ta furta tana karasawa da sauri ta hankade Maryama da take tsaye. Sallar la'asar ta idar, tana zaune tana jan casbi kamar yanda takan wuni tanayi, ko karanta wani littafin da take tunanin zai amfani rayuwarta tunda ta shigo gidan. Da yake da ta gama firamare tayi makarantar kwana har aji uku, da maganar auren su da Ahmadi a kanta ma ta karasa aji ukkun. Bata tsammaci tarbar kwarai a wajen Maimuna ba, amman tayi mamakin kalar kiyayyar da take nuna mata kamar itace mace ta farko data fara shiga gidan aure a matsayin mace ta biyu. Ba zata manta ranar da aka shiga da ita dakin Maimuna watanni ukku da suka shige dan karrama Maimuna a matsayinta na uwargida kamar yanda tsarin al'ada yake. Sam bata ga fuskar Maimuna ba tunda kanta a rufe yake kasancewarta amarya. Kalaman Iya Asabe da take fadin "Wanda duk yake a dakin nan yasan halin da kike ciki, dan kishiyar nan anyi mana, wasun mu fiye da daya. Sai anyi hakuri, ko da babu tsira mai nisa tsakanin ki da Maryama kanwa ce a wajenki a gidan aure. Saboda haka ga amanar ta..." Iya Asabe bata karasa maganarta ba Maimunar ta katse ta da fadin "Iya ki takaita kalamanki, indai amanar Maryama ce ban dauka ba, karku doramun nauyin da ba zan sauke ba..." Daga inda Maryama take zaune tana jin salallamin da duk wanda yake cikin dakin yakeyi cike da mamaki "Inda amana ba zaku rako Maryama dakina ba wallahi, ba zaku dauketa ku liqawa Ahmadi ba..." Ba zata manta yanda taji takun tafiya ana barin dakin daya baya daya ba. Har Iya ta kamata suka fice saboda yanda Maimuna sam taki sauraren nasihar da Iya taso tayi mata, tana barinta da furta "Allah ya saukaka" Kafin su fita daga dakin. Maimuna bata canza kalamanta ba ko bayan da Ahmadi ya hadasu da sunan yi musu nasiha "Ka dauki matarka ku fitar mun daga daki Ahmadi, ku fita ba sai kun haskamun yanda zaku kasance da juna tsayin daren yau ba, wallahi hakurina yana gab da karewa..." Maimunar ta karasa maganar da rawar Murya alamar kukan da take kokarin tarbewa. Ita kam zatace firgicin da ta tsinci kanta ya girmi wanda kowacce mace take tare dashi a darenta na farko. Daga ranar kuwa har yau babu wata magana ta arziqi data hadata da Maimuna, banda mugayen kallo da takan watsa mata duk idan ta wuce, tana jin labaran kishi, amman na Maimuna daban ne, ga yan uwanta da taga alama wajen zaman jegon Rayyan suna tayata. Ba tsoron biye rigimar da Maimuna takan takaleta da ita a duk rana takeyi ba, kalaman Ahmadi ne suke tausarta "Da bana sonki ba zan aureki ba Maryama, kamar yanda kauna ce tasani auren Maimuna kema haka. Idan ina da mutunci a idanuwanki zaki tayani kaucewa rigima da Maimuna, dan Allah ki kauda kai daga lamurranta, ki tayani wanzar da zaman lafiya a tsakanin ku gwargwadon iyawarki" Tun kafin zama karkashin inuwar aure ya hadata da Ahmadi ta tabbatar da nagartar shi. Ta dauka tasan soyayya a iya tsayin lokacin da suka dauka kafin auren su, sai yanzun take ganin banbanci. Yanda Ahmadi yake kula da ita, yake gudun duk wani abu da zai sosa ranta ya kara daga daraja da matsayin shi a zuciyarta. Saboda shi zata cigaba da kauda kai daga halayen Maimuna har Allah ya fahimtar da ita cewa su dukansu zaman aure sukeyi, kuma ita da niyyar mutu ka raba ta shigo gidan, babu inda zata tafi. Shisa take kokarin ganin bata shiga harkarta ba, bata taba ganin gidan da keda kishiyoyi kowa na abincinta daban ba tun tasowarta sai a nasu gidan. Ta dafa sau biyu, ba zatace ga abinda ya faru ba, Ahmadi ya ce mata kowa abincin shi zai dinga dafawa, abin har yanzun wani iri yakeyi mata. Ga yaran Maimuna da shiga rai, musamman Zubaida, ko dan Ahmadi har ranta take jin yaran. Kiri-kiri Maimuna ta hana mata rabarsu, ko inda take basa zuwa, buta wannan idan tata ce basa tabawa, in ta dan samu sunje kusa da ita to Ahmadi ya dawo gidan, kuma ranar itace da girki, shima kome zata basu kai suke girgiza mata a tsorace. Yau ma kukan Rayyan da take tajine yai mata tsaye, taso ta share, amman taji shigar Maimuna bandaki, kuma tasan sauran yaran suna makaranta. Tunanin ko an dora shi a samane ya fado shisa yake wannan gigitaccen kukan yasata tashi ta shiga bangaren Maimuna din, komin yanda basa ga miciji yaron baisan me duniyar take ciki ba balle zafin kishi irin na mahaifiyar shi. Tana shiga taga kuwa wajen mitsilniya yaja zanin shimfidar ya nade fuskar shi da shi, samu tayi ta cire mishi, ta gyara ne zata dauke shi taji shigowar Maimuna, bangazar da tayi mata da babu bango a kusa zata iya faduwa. Rayyan din Maimuna ta dauka tana saka shi a jikinta hadi da jijjiga yaron "Kashe mun shi zakiyi Maryama? Meya kawoki dakina?" Kalaman Maimunan taji har ranta, sun mata zafi matuka "Wacce irin magana ce wannan? Kukan shi naji yayi yawa, kuma naji kamar kin shiga bayi shisa nazo in duba" Cike da rashin yarda Maimuna take kallonta, Gwaggo Bare tayi mata kashedi karta bar Maryama na rabar mata yara, kafin ta shafa musu abinda in rayuwar su bata salwanta ba za'a sabauta su. Yanda tayi nasarar mallake Ahmadi ba zata bari tayi nasara a kanta ba sam. Karfi da yaji jituwa ta musu karanci tsakaninta da Ahmadi, laifinta yake gani yanzun a duk wata karamar magana da zasuyi. Ranar da aka daura mishi aure da Maryama ne rana mafi muni da tashin hankali a rayuwarta. Ba zata manta bayan fitar su shi da Maryama daga dakin yanda ta dafe cikinta tanajin kamar zai fito duniya ranar saboda yasan kalar tashin hankalin da take ciki. Kwanciya tayi a kasa tana sakin wani irin gunjin kuka zuciyarta kamar zata fado, a haka Ahmadi ya shigo dakin yana kamata "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un... Maimuna me kikeyi haka? Dan Allah ki rufamun asiri, kinga bake kadai bace ba... Kiyi hakuri, kiyi hakuri kisawa ranki salama, inda nasan kishinki yakai haka wallahi dana hakura da auren nan... Oh Allah na" Yake fadin yana sake riketa a jikin shi ganin yanda numfashinta har sama-sama yake saboda kuka "Wata zaka raba, Ahmadi wata zata dandani soyayyarka yau, dan Allah karkaje, karka hada mun jikinka da nata, karka cakuda kaunata data wata, Ahmadi mutuwa zanyi Allah idan nasan a wajen wata zaka kwana" Maimuna take maganar kamar bata cikin hayyacinta. Har yau ba zatace ga yanda akayi ya sulalace yabar dakin ba, bama zata tuna ko ta runtsa ko bata runtsa ba, a satin farkon nan ta wahala. Tayi mamaki da mata suke kiran nakuda tafi komai ciwo a sha'ani na rayuwa. Zata zabi haihuwa goma a jere indai za'a koma baya a goge Maryama daga rayuwar Ahmadi, ko haihuwar Zubaida data kwana hudu cikin matsananciyar nakuda kamar ba zatai rai ba bai kai mata zafin ciwon da takeji a zuciyarta duk idan Ahmadi ya kasance a dakin Maryama ba. A kwanakin bakwai bata tsaya tasan me suke ci shida Maryama ba, dan batai mishi karyaba washegari daya shigo mata daki kamar bai hada shimfida da wata ba "Idan abin kari kake jira zaku wuni da yunwa daga kai har ita, wallahi zan zabi mutuwa akan in dafa abincin da Maryama zataci" Da suka kwana bakwai ma ta karbi girki ko lafiyar kirki bata da ita, tana ganin Maryama da salo dan ta zuba mata wani abu tace zatayi girkin. Su Zubaida gidan Yaya Ayuba ta turasu sukaci abinci, itama daga can din aka kawo mata, washegari da taga ta shiga ta dafa tazo tayi mata maganar da ko amsa bata iya bata ba, Ahmadi na dawowa ya shiga dakinta da ya duba karfin jikinta tace mishi "Ba zan iyacin abinda duk ya fito daga hannun matarka ba, yarana ma ba zasuci ba ballantana a barbada mana abinda aka baka aka mallake ka" Yanda yake kallonta rai a bace bai ko girgizata ba "Maimuna yaushe ne zakiyi sanyi akan maganar Maryama? Da kika taso gidanku abinci kikaga an raba? Me yasa nine zan fara wannan al'adar dan kawai kin dauki zafin kishi kin saka a ranki" Batasan ko yanda ya nuna dan Yayya tayi hakurin zama da kishiya itama ya zame mata dole tayi wannan bane a fakaice ya taba zuciyarta, ko kuma maganganun da yake mata a fadace saboda Maryama sune suka tunzurata ba, amman bataso hawayen da suka zubo mata ba "Ni dai na fada maka, kai za'ayiwa asarar abinci saboda wallahi ni ba zanci ba..." Runtsa idanuwan shi Ahmadi yayi yana bude su a kanta "Idan akayi hakan shikenan? Idan kowa ya dafa abincin shi yayi miki?" Kai ta daga mishi, bai sake furta wani abu ba yasa kai ya fice daga dakin. Idan fushi yayi ma shiya jiyo. Ita kama tasan ba zataci duk wani abu da zai fito daga bangaren Maryama ba, su Khalifa ma daki ta sakasu taja kunnen su akan Maryaman ganin yanda take wani jansu a jiki. Dan Zubaida ma ca tayi mata Dodo Maryama take zama da dare, idan ta karbi abin hannunta zata zo ta cinyeta tana bacci. Yaran kuwa har ransu suka dauki hudubar mahaifiyar tasu "Bana so, karki sake shigomun daki, idan siqewa kikaji yanayi bance ki taimaka mishi ba....idan burgeni kike sonyi Maryama dan girman Allah ko numfashi karkiyi kusa dani..." Murmushi mai ciwo Maryama tayi, wani bangare na zuciyarta takeji a gajiye da halayyar Maimunar "Duk yanda bakyason ganina Ahmadi ya hadamu..." Ido a bude Maimuna take kallonta "Magana zaki fadamun? Dakina zaki shigo ki fadamun magana?" Wani murmushin Maryama ta sakeyi da yasa Maimuna takeji kamar ta dauketa da mari, kafin ta kai hannu a cikin ta tana shafawa, haka kawai yau sai takejin tana son bakantawa Maimuna rai ko yayane "In Allah ya yarda na dan yan watanni da nawa a hannuna" Tana karasa maganar ta juya da shirin fita daga dakin, tanajin tsakin da Maimuna taja a fili "Aikin banza aikin wofi, sai kin haifo ukku a tare zan san dai-dai kikejin kanki dani a cikin gidan nan" Labulen Maryama ta daga tana ficewa daga dakin, Rayyan da yayi shiru a jikinta ta mayar kan bayanta tana daukar zani ta goyashi. Zatayi karya idan tace bata girgiza dajin cikine a jikin Maryama ba, duk da bata saka idanuwa akan lamurranta, ko yawu bataga ta tsartar ba. Ta rasa dalilin da yasa maganar take daga mata hankali haka, nan gefen gado ta zauna duniyar nayi mata shiru. Yara uku ba wasa bane, ko da ukkun Maryama ta ajiye a gidan Ahmadi ba masu shekaru kamar nata ba, tunda ko yanzun tana morar yaran nata da dauke mun wannan, mikon mun wancen. Amman batason kwan Ahmadi a cikin wata macen, batason ya daga idanuwan shi ya kalli wasu yara a cikin gidan nan banda nata. Malamin Khadi ma ba haka ya buga mata kasa ba "Ki kwantar da hankalinki, ba wani dadewa zatayi a gidan ba tunda ba wai son gaskiya Ahmadi yake mata ba, kuma yanzun haka sati mai zuwa aljanun da Malam ya aika can kasar Masar zasu dawo da hadin turaren da zai karya sihirin" An kuma kawo mata turaren da ta yarfe gadonta da shi Ahmadi ya kwanta, duk wani magani da aka bata tayi amfani dashi tayi, amman ko ran girkinta Ahmadi ya leqa Maryama idan tayi magana saiya nuna rashin jin dadin shi "Kema ina zuwa dubaki ranar nata girkin, me yasa abin magana baya miki wahala?" Haka yace mata kwana uku da suka wuce, ganin washegari Maryaman zata karbi girki, kuma ya yini zir baya gidan, ta dauka ba zai kwasar mata mintina cikin lokacinta da sunan duba Maryama ba. "Namiji kenan..." Maimuna ta tsinci kanta da furtawa, ashe ciki Maryama take dashi amman ko da wasa Ahmadi bai furta mata zancen ba, sai yayi shiru abin shi, watakila da bataji a bakin Maryama ba sai ya nuna kanshine zata gani. Ahmadin ta da komai ya danganci rayuwar shi itace ta farkon sanin shi, da ita yakan shawarta sanar da Yaya Ayuba ko Nasiru wani lokacin. Rana daya wata ta shigo tsakiyar su da hakan "Allah ya kwashe miki albarka Maryama" Ta sake furtawa hawaye cike taf da idanuwanta, duk mazan duniya ta rasa wa zata kyalla idanuwa a kan shi sai Ahmadi. ** Da yake yau girkin Maimuna ne, kai tsaye dakinta Ahmadi ya wuce bayan ya dawo sallar Isha'i. Ya siyo kankana, da kan shi ya tashi ya fita zuwa kitchen ya dauko faranti da wuka ya dawo ya zauna "Ina Khalifa da Zubaida? Ba dai sunyi bacci ba" Kai Maimuna ta girgiza mishi "Yau ma gidan Yaya zasu kwana kenan" Ahmadi ya furta da murmushi a fuskar shi kafin Maimuna ta sami damar fada mishi, yanajin dadin kusancin da makotakar su da Yayan shi ta wanzar tsakanin yaran su. Shi kanshi ma yanzun ma sai sukai karfe tara a waje da Yaya Ayuban suna hirar su wasu lokuttan. Hakan ba karamin dadi yake mishi ba, a lokuttan da Maimuna ta hada mishi zafi sai yaji zuciyar shi ta sanyaya idan sunyi hira da Yayan. Duk da bayason rage mutuncinta a idanuwan dan uwan nashi, shisa ko da wasa bai taba gwada fadar laifinta ba ballantana ya nemi shawara. Duk fadan da zasuyi, sukan shirya, kuma yana yafe mata ko da bata nemi hakan ba, son da yake mata mai girmane. Yana gudun kar ya fadama Yaya Ayuba wani laifin Maimuna din, shi yazo ya yafe mata, Yaya Ayuban na kallonta da abin, sam ba zaiji dadi ba. Kankanar ya raba gida uku, ya dauki kashi daya ya saka a ledar, yanda yake jin wata irin gajiya jar a kasusuwan jikin shi yau zaiso ace zai iya baiwa Maimuna kankanar dan ta mikawa Maryama. Amman mitarta zatayi karshe harda rashin kunyar da ta koyi yi mishi tace ba zata kai ba. Shisa ya mike da kan shi yana kuwa cin sa'a Maryaman ta fito rike da buta a hannunta, murmushin nan nata tayi mishi "Maryama..." Ya furta cike da jin dadin ganinta, yana mika mata kankanar da ta ajiye butar hannunta tana dan tsugunna ta saka hannuwa biyu ta karba cike da girmamawa "Allah ya saka da alkhairi. Sannu da kokari" Murmushin shi Ahmadi ya kara fadadawa "Ya zazzabin? Yayi sauki ko?" Ya tambaya kamar dawowar shi bai dubata ba, kulawar shi daban take.Kai ta daga mishi cike da jin nauyi, tunda taga har wannan watan bata ga al'adarta ba, ta tabbatar da zarginta na cewa ciki take dauke dashi, ba wani canji takeji a jikinta ba, banda yawan kwadayin abinci mai manja, sai zazzabi da takan kwana dashi wani lokacin, amman lafiya kalau take jinta, wasu amaye amaye ko tashin zuciya duk Allah bai daura mata ba. Tana taso ta fadama Ahmadi zargin da takeyi amman nauyin hakan takeji sosai, banda yau da kishi yasa tayi ma Maimuna burga da cikin, ita kadai tasan da abinta. "Sai da safe, kisha maganin da na siyo indai kinji ya dawo, da safe sai mu fita a dubaki asibitin wajen aikin mu" Kai ta iya jinjina mishi "Allah ya hutar da gajiya" Ta furta tana juyawa daki, labule kawai ta daga ta ajiye ledar kankanar ta dawo ta dauki buta, kasala takeji yau sosai, dan tun taliyarta data dafa da manja ce da tayi saura taci da daren nan. Kan kunnenta aka kira isha'i tana kwance tana juye-juye a daki sai yanzun Allah yai mata fitowa. Alwala ta daura ta koma daki abinta. Ahmadi ma dakin Maimuna ya koma, yana karbar Rayyan daya saka babban yatsan shi a baki yana ta tsotsa "Gaka da alamomin hakuri amman sai rikici ko?" Ahmadi yai maganar kamar yaron zai fahimci me yake cewa, Maimuna da ta sakko kasan itama ta dauki wuka tana karasa gyara kankanar daya yanka, ta dauka tana mika mishi, hannun shi ya duba saboda yayi gaishe-gaishe da mutane "Ban wanko hannu ba" Dan kara matsawa tayi tana fara zare kwallayen jikin kankanar ta mika saitin bakin shi daya bude ta saka mishi a ciki, taunawa yayi yana jinjina kai "Wai... Daman yace mun me kyau ce wallahi, dana sani kwallo biyu na siyo..." Kallon shi Maimuna takeyi "Da zaki? Naga batai ja ba sosai" Ta karasa tana sakawa a bakinta itama, sake gyara wata tayi tana kara ba Ahmadi "Aikam da zaki..." Cewar Maimuna, kafin Rayyan daya fara mutsilniya a jikin Ahmadi yana kwakkwabe fuska yasata furta "Wallahi karka dagamun hankali, na rasa inda ka kwaso rigima" Dariya Ahmadi yayi "Me kake nufi?" Ta furta tana kallon shi, kai yake girgiza mata yana kawo bakin shi ganin ta gyara kankanar da ke hannunta, a nata bakin ta lunkuma "Ka wanko hannuwanka ka sha da kanka, so kake kace ni ya biyo da alama" Dariya yake sosai, dariyar da ta kwana biyu bata gani ba, gyara Rayyan yayi yana amfani da dayan hannun shi ya riko nata da take kokarin kwacewa tana dariya. Yayi kewar wannan rahar a tsakanin su, yayi kewar matar shi, kallonta yake da wani yanayi a fuskar shi "Nayi kewar ki" Cikin idanuwan shi ta kalla, ita kadai ce macen da take iya hada idanuwa dashi kai tsaye haka, har maza kance yana musu kwarjini, ko Maryama bata iya kallon shi haka. Maimuna kance "Kai din nawa ne, nawa ne ni kadai Ahmadi" Kuma ya yarda shi din nata ne, duk da bai kasance nata ita kadai ba kamar yanda taso, amman natan ne "Kaji ka, abinda muna tare a gida daya ko da yaushe, me yasa kake magana kamar ka dade baka ganni ba?" Numfashi mai nauyi ya sauke "Dan Allah mu daina fada, ki daina mun rigima, mu koma zaman mu kamar da" Murmushi tayi kawai, murmushin da yake ganin kamar yana da wata manufa data wuce nishadi. Haka suka kasance daren kamar satin amarcin su, har wajen biyun dare, da Maimuna lafe a jikin shi suna bacci. Da yake shi bamai nauyin bacci bane, kwakkwaran motsi ma yakan ji, cikin baccin yake jin kakarin aman da ya sashi bude idanuwa yana saurarawa, sosai yake jin ana kakarin, yaso zame Maimuna a hankali ba sai ta tashi ba dan ya fita ya duba, amman itama din ba nauyin baccin gareta ba "Ina zaka je?" Ta furta muryarta cike da bacci tana murza idanuwa "Kamar Maryama ke amai, bakiji bane ba?" Ya amsa kasa-kasa saboda dare, tsaki Maimuna taja "Munafuncine kawai, dan Allah ka koma ka kwanta" Da mamaki yake kokarin ganin idanuwanta saboda duhun da yake dakin. Rigar shi da yake tunanin tana ajiye wani waje kan gadon yake lalube har ya samota, kokarin sakawa yake a jikin shi Maimuna ta tashi zaune "Fitar zakayi kenan?" Ta bukata a harzuqe, hakafa kwanaki ta fito tana wannan kakare-kakaren, Ahmadi ya kwana zarya yana fita dubata. Shine yau daga dawowar shi dakinta zata sake bullo da wannan sanaben "Kasan dai yau kwanana ne ko? Halin matane baka sani ba Ahmadi? Munafuncine ba wani abu ba" Kai kawai ya girgiza yana sauka daga kan gadon "Bari in dubata...." Itama saukowa tayi, zuwa lokacin idanuwanta sun saba da duhun tana dan ganin shi, aikuwa hannu yaji ta riko mishi "Babu inda zakaje fa, kanajin ma kamar ta koma daki. Wannan ai shiga hakki ne" Fisge hannun shi Ahmadi yayi "Me yake damunki ne wai? Ina tausayinki ya tafi? Ko ta tafi daki bazan duba yarinyar mutane bayan naji sarai amai tayi ba? Kinga Maimuna ki fita idona kafin in saba miki" Ya karasa yana fara tafiya zuwa hanyar kofa, yanajin ta biyo shi, baibi takanta ba ya fice daga dakin, hasken farin wata ya haske tsakar gidan, ko takalma bai saka ba ya nufi bangaren Maryama, yana shiga ya sameta a zaune da fitilar kwai a dakin "Maryama? Jikin ne?" Kai ta girgiza mishi "Aa wallahi. Amai ne kawai, inajin kankanar dana sha na kwanta ce ta juya mun ciki" Kuma da gasken take, dan karatun littafin tarihin Annabi (SAW) Kamalalle takeyi bacci ya dauketa anan kasa inda ta saka filo, kawai farkawa tayi tana zufa, kafin taji wani amai ya taso mata, dakyar takai tsakar gida. Duk wani abu da yai saura a cikin nata kuwa saida ta fitar dashi, kuma garas take jinta banda yar galabaita da tayi. Ahmadi bai yarda da ita ba, tsugunnawa yayi yana saka hannu ya taba wuyanta ko da zazzabi, amman lafiya kalau yaji jikinta "Sannu..." Murmushi Maryama tayi "Yawwa... Kaje ka kwanta, kaga da safe zaka fita, gara ka huce gajiya" Kallonta yakeyi yana son tabbatar da lafiyarta "Babu wani abu da yake miki ciwo dai ko?" Kai ta jinjina mishi "Kin tabbata? Ki fadamun dan Allah" Murmushi takeyi sosai "Allah babu inda yake mun ciwo...dan Allah kaje ka kwanta" Numfashi Ahmadi ya sauke "Shikenan, Allah ya kara lafiya, idan da wani abin dai kizo ki tasoni kinji ko? Allah ya tashe mu lafiya..." Kai Maryama ta jinjina mishi, tana kara ganin dalilin da yasa kaf dangi kowa yakejin daman yar shi ce a gidan Ahmadi, ba zata gaji da godewa Allah da wannan damar da ta samu ba, har zai fita ya kara juyowa "Ko in miko miki ruwa?" Kai ta girgiza mishi tana nuna kwanon sha da yake a rufe "Kagan shi nan na dibo fa tun dazun..." Sannun dai ya sake yi mata kafin ya fita, ya gyara mata labulen dakyau saboda sauro. Kafin ya wuce inda ya samu Maimuna a bakin kofar dakinta tsaye "Idan cin amana dai kasa a gaba babu inda zai kaika wallahi" Ta karasa maganar ranta na suya, sai takejin kamar kamshin turaren da Maryama kan hayaqa a zuwan turaren wuta a jikin shi. Watakila wata sa'ar Malamin ta ya bata na fito da Ahmadi tsakiyar dare ta goga mishi wannan shu'umin turaren "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un... Dan girman Allah Maimuna ki saka ma ranki salama" Ahmadi yai maganar cike da gajiya, yana mamakin kishi irin nata, wani lokacin yana jin daman ya hakura sun rayuwa su kadai kamar yanda taso, daya kaucewa duk wannan rigingimun "Ta ina zan fara sakama raina salama bayan baka bani wannan zabin ba? Bance maka munafunci bane, kawai bata kaunar ganin na kebance dakai saita tsiri wani abin da zaka ha'ince ni" Rabata yazo yi, gara ya wuce ya kwanta, inya tsaya biye mata zaiyi. Kamar ba ita bace tagama mishi alkawarin zasu zauna lafiya dazun nan. Amman sai ta tare kofar, wani irin kishine turnuke da zuciyarta, kamshin turaren Maryama da hancinta yake jiye mata sai take ganin kamar wani abin sukayi a yan mintina daya dauka a dakin nata da sukai mata nisan awanni, tare mishi hanya tayi "Ka koma dakin nata mana, ka koma inda ka fito Ahmadi tunda haka kake so tun daga farko" Ta karasa maganar wani irin kuka na kwace mata, yana da nashi dakin, kudine da sun shigo hannun shi akwai hidimar da zaiyi dasu, bai karasa bangaren ba, kuma duk da haka akwai wani dakin da zai iya zuwa ya kwanta a bangaren Maimuna, dakuna uku yayi mata, harda dakin girki, bangaren Maryama dakuna biyu itama da na girki, har lokacin akwai tankamemen fili da katanga kawai yaja mishi, banda filin tsakar gida, wannan sai a hankali zai dinga gine kayan shi tunda ba sauri yake yi ba. Hannun ta ya kama ya cire daga kofar yana shigewa cikin dakin da ta bishi. "Wallahi Allah zai kamaka idan baka mana adalci" Runtsa idanuwan shi yayi yana bude su hadi da sauke numfashi, kukan da takeyi na kara taba zuciyar shi "Kamshin turarenta kakeyi fa, Ahmadi kamshin turarenta kakeyi ranar girkina. Wanne irin rashin adalcine wannan? Ko cikin da take dashi ne yasa kake wannan rawar kafar?" Juyowa Ahmadi yayi yana kallon Maimunar da mamaki "Ciki kuma?" Hawaye ne suka kara tsiyayo mata "Kana nufin kace mun baka sani ba?" Mamaki yake kan mamaki "Maryaman ce take da ciki?" Ya kara tambaya, kai kawai Maimuna ta jinjina tana rabashi ta wuce kan gado ta kwanta. Ya dade a wajen yana jinjina maganar, ko dan ita Maimuna macece shisa ta gane Maryama na da ciki. Har ran shi kuma yaji dadi, yanzun yake fahimtar kwadayin manjan da ake ta mishi abinci da shi kwana biyu. Murmushi kawai yayi yana karasawa kan gadon. Kukan da Maimuna takeyi na kara dagula mishi lissafi, matsawa yayi daf da ita yana rikota jikin shi, tun tana kwacewa harta hakura "Kamshin ta fa kakeyi" Ta sake fadi tana zame jikinta, mikewa zaune yayi ya cire rigar ya cillar a kasa, yana kara komawa kan gadon ya rikota "Kiyi hakuri Maimuna..." Kuka takeyi sosai, ya rasa kalar kishin nan nata, abin kuma yafi karfin shi, addu'a yake mata na samun salama, amman kamar tunzura abin yake karayi. Ya jima yana lallashinta "Karka kara zuwa wajenta in kama dakina" Amsata yayi da to, dan a zauna lafiya, da duk wasu sharudda da taketa kafa mishi, sannan tadan ji nutsuwa, ko rubutun data diga mishi a ruwa dazun ya fara aiki, na kokarin kwato shi daga hannun Maryama ne, Allah ya fara taimakonta da alamu, zatayiwa Khadi maganar wannan turaren na Maryama dan bata yarda dashi ba. Da zata iya ma da kanta zata tambayi Ahmadi taje gidan Khadi din suje wajen Malam tare, amman tsoro takeji, ta gwada sau daya, ta kasa karasawa, sai take ganin kamar wani zai ganta, kamar za'aje a fadawa Ahmadi inda taje. Tafi gane duk yan kudaden da zata samu ta ba Khadi din, duk wani abu da za'a karbo mata a karbo. Da wannan tunanin a ranta bacci yayi awon gaba da ita. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:06 PM - 111: Nov 1, 2020 3 1986 Kano. Yaron da yake rike a hannunta take kallo, yaran da duka satin shi biyar a duniya, wasu hawaye masu dumi na tarar mata cikin idanuwa. Amman zuwa yau tasan cewa kukan nan babu wani amfani da zai musu, kukan ba zai dawo mata da kaninta ba, ba zai canza kaddarar yaron da yake hannunta ta Maraici a satika biyu bayan haihuwar shi ba. Ba zatace tashin hankali bakonta bane ba, tasan shi a lokacin da ta raya Yayya, ta kuma san shi a lokacin da Ahmadi ya hadata da Maryama da ta zame mata Karfen kafa (Rufaida Omar). Tana kuma cikin shi har yanzun da Maryama ta ajiye kwai a cikin gidan Ahmadi, dan duk lokacin da zata ga giccinta ko kukan yaran nata Haris, sai taji wani abu ya tsirga mata. Kwance take a daki tun bayan da tayi sallar asuba satika biyu kenan da suka wuce, haka kawai jikinta yai wani irin sanyi, ba shida alaka kuma da fadan da sukayi da Ahmadi tasani, kishinta a duk ranar da yake dakin Maryama daban da abinda takeji yanzun. Ko daya shigo ya dubata ma da safe inda yake bata kalla ba, ballantana ta amsa dukkan tambayoyin da yakeyi mata. Tana jin shi harya fice, dakyar ta iya tashi ta watsa ruwa, Rayyan ma tayi mishi wankan. Gobe ko jibi take da niyyar yaye shi, a karo na farko da har zatayi yaye batare da wani cikin ba. Zatayi karya idan tace abin baya damunta, bata da kowa da yake fahimtar ta duk dangi, daga Gwaggo Bare sai Khadi. Yayyanta mata da suke ciki daya data gwada fada musu damuwar ta zancen su kusan kala dayane "Kiyi hakuri da kaddarar ki Maimuna, kowa da kika gani ba son kishiyar nan yakeyi ba, ki cire wasu zarge-zarge daga ranki tunda mijin ki na son ki" Shisa ta koyi kame bakinta a gabansu, son da suke ikirarin Ahmadi nayi matane dalilin komai, sunki fahimtar soyayyar nan tashi da yake matace yake rabawa da Maryama. Soyayyar da aka ga yana mata ce ta tsone idanuwan su Maryama harta shigo mata gidan miji. Yanzun kuma soyayyar da suka kasa nasarar dakushewa gabaki daya a zuciyar shice dalilin da take zargin suna son hana mata cigaba da ajiye yara a gidan Ahmadi. Ko da ta tambaye shi tana so taje gidan Gwaggo Bare a lokacin bai hanata ba, tana zuwa da kukanta ta shiga gidan, tana saka Gwaggon yin fatali da rariyar hannunta da take tankaden garin dawa tana mikewa ta tarbeta "Na shiga ukku ni jikanyar Munzali... Maimuna lafiya?" Cewar Gwaggo bayan ta taimaka mata ta kwance goyon Rayyan ta sabashi a nata bayan ta daure da zani. Kai Maimuna take jijjigawa kukan da takeyi yana kara yawaita "Gwaggo har yanzun shiru, ban taba wata shidda cikakku ina shayarwa babu wani cikin a jikina ba. Ina tsoron ko Maryama ta shafemun mahaifa..." Salati Gwaggo takeyi tana karawa "Anya su Maryama basu kwashe kayan su daga gaban Ma'aiki ba? Ina mutanen nan suke so sukai haqqi? Wato gaje gidan gabaki daya sukeyi shisa ake so a hanaki haihuwa. Wallahi bokan Karime yayi karya..." Bata bar gidan Gwaggo ba saida ta tabbatar mata da taji labarin wani Gwani da yafi Malaminta kwarewa, dan shi sha yanzun magani yanzun ne. Yasan ilimin taurari fiye da misali, zataje wajen shi ya buga musu kasa ya fayyace musu abinda yake faruwa. Koyayane har gida zatazo tayi mata bayani, sai a san yanda za'ayi. An kuma tabbatar mata da cewa da gaske daurin mahaifa akayi mata, cikin kogon maciji aka binne asirin, ranar yini tayi kuka kamar ranta zai fita, sanda Ahmadi ya dawo duka fuskarta a kumbure take, shine musababbin fadansu, tambayarta da yayi ko lafiya ta kuma amsa shi da "Rabona da lafiya tun kafin na yayibo mana Maryama, tun kafin ka bata damar da zatayi amfani da ita wajen kassarani" Tana ganin tashin hankalin da yake cikin idanuwan shi kafin ya karasa cikin dakin sosai yana tsugunnawa kusa da ita "Wani abin tayi miki? Da na fita tayi miki wani abinne?" Ahmadi yake tambaya, wannan karon cikin idanuwa Maimuna take kallon shi "Baka mamakin yanda har yanzun bani da shigar ciki? Ko ka bace lissafin watannin Rayyan?" Cike da rashin fahimta Ahmadi yake kallonta, bawai ya bata lissafin watannin Rayyan bane ba, amman bai kawo komai a ranshi game da batun ciki da Maimuna bata samu ba. Yasan haihuwa nufin Allah ne, kuma ya banbanta lokacin samuwarta a tsakanin mutane. Watakila wannan karin abin ya canza matane shisa. "Ba cikin wata na sha takwas yake ba? Satin daya wuce inajin kike mun zancen yaye shi" Kai Maimuna ta jinjina mishi "Kana sane kenan, baka dai mamakin yanda akayi bani da wani cikinne kawai" Numfashi Ahmadi ya sauke "Haihuwa nufin Allah ne Maimuna, ba lallai duka tazo miki iri daya ba" Kai take girgiza mishi, taso ya fahimceta ba saita mishi gwari-gwari ba "Ina tsoron ko an mun wani abune, ko an shafe mun mahaifa n...." Ahmadi bai bari ta karasa ba ya katse ta da "Subhanallahi... Maimuna... Wanne irin zancene wannan? Yaushe kika fara yarda da irin abubuwan nan? Me ya shiga kanki? Waye zai miki wani abu?" Idanuwanta cike da hawaye tace "Wa kasan zaimun wani abu banda Maryama? Yanda suka mallakeka suka shigo gidan nan shine suke neman duk wata hanya da zasu nisantani da kai" Ta karashe maganar cikin zafin zuciya da kunar rai, tana saka Ahmadi yin duk wani salati da zaizo bakin shi "Allah ya kare mun ke ya shiga tsakanin ki da kowaye yake son juyar miki da tunani haka. Maimuna dan girman Allah ki natsu kiyi amfani da hankalin ki kan zantukan da ake gaya miki" A tausashe yake maganar, kawai yanayin yanda yakeyi dinne ya kara tunzura zuciyarta "Baka damu ba shisa ba zaka fahimceni ba, tunda ita ta fara tara maka yara....ta fara fitowa tsakar gida tana daga mun kafada zata fara lissafin yawan yara dani...." Mikewa kawai Ahmadi yayi "Allah ya shiryeki ya yaye miki abinda ya shiga kanki. Saikin gyara lamurran ki wallahi" Yake fadi yana ficewa daga dakin, bayason tsayawa yaji maganganunta balle harya biye mata suyi fadan da idan basuyi ba yaga alama batajin dadi. Haka ta kwana ko wadattacen bacci bata samu ba saboda kunar zuci. A haka kuma ta wuni tanajin ta sama-sama. Su Khalifa ma na dawowa gidan daga makaranta, kadasu tayi gidan Yaya Ayuba, har abinci saci acan dan bata samu karfin dora tukunya ba. Bata kara mamaki ba sai da Ahmadi ya shigo gidan ko la'asar batayi ba, tasan ba girkinta bane ba, shisa ta kara mamakin ganin ya fado dakin nata "Maimuna..." Ya kira da wani irin yanayi a muryar shi da yasa gabanta yin mummunar faduwa, tana kuma mikewa daga kishingidar da tayi, tunda tasa Rayyan ya kwanta yayi bacci itama take nan gefen shi. Ganin yanda yake kallonta yasa ta mikewa tsaye gabaki daya "Lafiya? Me ya faru?" Ta tambaya, so yake ya bude bakin shi ya gaya mata rasuwar dan uwan da yasan duk a cikin  gidan su tafi shakuwa da shi, tsiran su ba wani mai yawa bane ba, duka shekaru biyu ya bata, kuma shi kadai ne take ji har kasan ranta duk a cikin yaran matar Baban nata da taki jinin ta bude idanuwanta tagani. Amman kowa yasan Maimuna yasan Audu, ko kasuwa yaje tsarabarta daban take da ta sauran mutanen gidan. Badume daya koma da zama bayan auren shi bai yanke zumuncin da yake tsakanin su ba, duk juma'ar duniya yana shigowa, kuma kowa yasan dan ita kadai yakanyi hakan, har gida yake zuwa ya dubata ya kai mata yan tsarabun da ya siyo. Kusancin su mai girmane, shisa aka rasa mai zuwa ya fada mata gobarar da ta afka musu tun a daren jiya, gobarar da tai sanadin rayuwar Audu, matar shi da yaran shi biyu, cikin ikon Allah tana barin Bilal, jaririn da satin shi uku da haihuwa. Lamarin da ya girgiza kauyen Badume da kewayenta, domin Audu mutum ne mai karamci da sanin ya kamata, tun zaman shi babu wanda zaice ga ranar da yaga fuskar shi ba dauke da murmushi ba. Mutum ne da yake samun shaidar arziki ko da baya waje. Ahmadi aka samu har wajen aiki, suna ganin kamar zai fi mata sauki idan taji daga bakin shi, shikuma yana juyayin yanda ba zata taba manta a bakin shi taji wannan lamarin ba. Da bakin shi ya fada mata zancen auren shi da Maryama, zancen da ya birkita mishi Maimunar shi ta yanda har yanzun bata dawo dai-dai ba, shi din mutum ne mai rauni, sam ba zai iya fada mata wannan zancen ba. Asalima yana ganinta yaji idanuwan shi sun ciko da kwalla, kwallar rashin Audu da ba ita kadai zataji shi ba, kwallar tausayin matar tashi da halin da yasan zata shiga. Bai iya komai ba sai hade dan sauran tazarar dake tsakanin su yana rikota jikin shi, zuwa lokacin harta fara kuka tun kafin ma tasan meya faru, jikinta ya gama bata koma menene ya faru ba abu bane me kyau. Ko ina jikinta bari yakeyi "Me ya faru? Ahmadi waya rasu? Ko Baba ne?" Take tambaya tana dagowa daga jikin shi, kai ya girgiza mata yana kokarin danne kwallar dake son zubo mishi. Dakyar ya iya cewa "Ki dauko mayafin ki..." Batayi musu ba, dan ko ina jikinta bari yake, mayafin ta dauko tana rike dashi a hannunta ta fice daga dakin, tama manta da Rayyan da yake kwance a cikin dakin, takalman ma, daya nata, dayan na Ahmadi daya cire a bakin kofar ta saka. Saida ya fito daga dakin ya kalleta cike da tausayawa, nata takalmin ya tsugunna ya dauka yana tura mata, kula tayi ta zare nashi, ta saka nata. Sannan ya dago yana saka takalman a kafar shi. Maryama da ta fito goye da Haris ya kalla, da idanuwan shi yai mata nuni da bangaren Maimunar, ganin har tayi hanyar waje "Rayyan yana bacci..." Ya furta a hankali, itama da alama hankalinta a tashe yake "Me yake faruwa?" Dan lekawa yayi bai hango alamar Maimuna ba, hakan yasa shi fadin "Audune Allah yayi mishi rasuwa, sunyi gobara jiya da dare, kamar da iyalin duka..." Yanda Maryama ta dafe kirji tana sakin wani salati daya fito da kuka yasa Ahmadi wucewa yabi bayan Maimuna, ta yanki hanya kuwa sai sauri takeyi. Kunya ya cire ya ajiye gefe yana karasawa da sauri ya kama hannunta ya rike. Ko da suka isa gidan ma bai saketa ba saida ya karasa da ita har cikin gidan. Inda ta samu tashin hankalin da bata taba tsammani ba, tayi suma ranar yakai hudu tana farfadowa ana gaya mata labari kala daya. Tun da dare data samu natsuwar da zata iya mikewa taje ta karbi Bilal da sai kuka yake a hannun Yayar Audu din wato Talatu. "Da kin barshi kin ji da kanki kawai Maimuna, ko tsayuwar kirki bakya iyawa..." Talatu ta karasa cikin kuka. Wata mata da Maimuna ba zatace kowacce ba a lokacin ta karbe zancen da fadin "Shima yaron zafin maraici ne yake taba shi, duk wanda suke shayarwa an gwada bashi mama fur yaki karba..." Hannu kawai Maimuna ta saka tana daukar Bilal batare da tace musu komai ba ta fice daga dakin. Waje ta samu a tsakar gidan tana zama da yaron a hannunta, tanajin kamar duk duniya shi kadai ne alakar data rage mata a tsakaninta da Audu, kamar babu jinin shi a jikinta, kallon Bilal take, kaunar yaron na ratsa duk wani sassa na jikinta, tana tuna yanda ko ranar suna shi satika uku da suka wuce harda ita ake tsokanar Audu da yaran sak shiya biyo, duk ya kwace ma Jummai matar shi kamanni da yaran nasu, kunya irin ta Audu murmushi kawai yayi ya fice daga gidan. Da tasan duk bankwana sukeyi da ta bishi sun dan zanta, da ta bishi ko yan mintina ta kara samu a tare da shi. Amman ina, ko ganin karshe da tayi mishi juma'ar data gabata basu wani dade ba, ruwa kawai yasha "Nayi yamma Maimuna, idan Allah ya bamu aron rayuwa a gidanki zanci abincin rana juma'a mai zuwa" Ta tuna kalaman shi, da suka saka hawaye masu zafi zubo mata. Tana kara rike Bilal a jikinta, wani irin zazzabine ya rufeta da tasan kaduwa da firgicine suka saukar mata da shi. Ance an gwada bashi mama yaki karba, ita kam gwadawa tayi yanzun, kamar Bilal yasan kalar kusancin da yake tsakanin ta da Audu ya kuwa karba, kafin wani lokaci yayi luf a jikinta. Aikam hakan ba karamin kara rikita kowa yayi a gidan ba, haka akaita koke-koke ana zantukan zumuncin da yake tsakanin Maimuna da Margayin. Ba ayi bakwai ba kuwa sai da ya zamana babu mai gwada karbar Bilal daga hannun Maimuna, masu tunanin cewa ma zasu rike shi basu furta zancen ba, dan ta nuna abune da ba zai yiwu ba. Rayyan ma da Maryama ta biyota dashi, kamar yasan wani abu mai girma ya faru, baiko gwada zai sha Mama ba, larabar tazo musu da sauyi mai girma gabaki dayan su. Tayi rashi babba, ta kuma karbi amanar da take tunanin babu wanda ya cancanci a yarda da yai rikonta sai ita, ta karbi Bilal da Ahmadi ya nuna goyon bayan shi dari bisa dari a kai. Ko bai auri Maimuna ba, shi din mai rike jinin Audu ne, akwai wannan kusancin a tsakanin su. Shisa har yanzun da take rike da Bilal, rashin Audu yake kara tabata "In shaa Allah in dai ina numfashi ba za kai maraici ba....babu wanda zai kalleka ya kiraka maraya" Ta furta a fili tana share kwalla, sosai take kallon yaron, yanda duk akance tana kama da Audu, yanda har ranar sunan Bilal da ake ma Audu tsiya aka dawo kanta bayan fitar shi cewa ai itama Bilal din kamanninta ne, yau sak Audu take gani a fuskar yaron, dogon hancin nan nashi, idanuwan shi da kowa kan tanka har akayi zaton baki zai kama su, komai na Audu take gani a tattare da Bilal. Rayyan da yake baccine ya farka ya rarrafo yana karasowa inda take zaune. Hakan yasa ta share kwallar da ta zubo mata. Hannun shi Rayyan ya mika ya kama na Bilal din "Kaga kanin da ka samu ko Rayyan?" Maimuna ta fadi, tana kallon yanda kamar Bilal ne yaji maganar da tayi ba Rayyan ba, dan shi ya sa dan karamin hannun shi yana rike yatsan Rayyan din, haka kawai yanayin yasa zuciyar Maimuna wani irin dokawa da karfi, a lokaci daya kaddara na budewa yaran shafin da a dogon tunanin Maimuna bata hango musu ba. 1991 Kano. "Rayyan..." Maimuna da duka yaran suke kira Ayya ta kira tana sakawa Shamsu riga a jikin shi. "Rayyan..." Ta sake kira, saboda taga giccin shi, shirin makaranta takeyi musu. Suzo su dauki safa kafin Ahmadi ya shigo ya samu basu shirya ba ya dora laifin a kanta. Dan akan makarantar yaran daga boko har islamiyya bayason wasa sam. Wani lokacin idan tayi mitar fadan daya koya sai yace zama da itane, ita ta koya mishi fada. "Wallahi Rayyan na fito sai na dake ka" Ayya tai maganar ranta a bace, tana balle maballin rigar da take jikin Shamsu "Ayya kina kiran Rayyan ne? Yana wajen Abbu" Bilal ya fadi, dago kai Ayya tayi "Kai ne ka wuce daman?" Kai ya jinjina mata yana saka murmushi kwace mata. Shekaru biyar kenan, a cikin shekarun tana da abubuwa da yawa da zatayi godiya domin su, ciki harda karin yara biyu da Allah ya bata, Rukayya sai Shamsu da take goyo yanzun. Duk yanda a fakaice bayan shekaru biyu da shigowar Bilal rayuwarta ta samu cikin Rukayya, Ahmadi nata kokarin tunatar da ita kan yanda yake fada mata komai na Allah ne, duk ta daga hankalinta akan rashin haihuwa, yanzun gashi nan komai da lokaci yayi Allah ya bata. "Hmm..." Kawai ta iya furtawa, ita kadai tasan wahalar da tasha kafin ta samu cikin Rukayya, duk kalar tsoronta saida Khadi ta rakata wajen Malam Mainasara, kuma zata gode Allah da ya bata wannan damar "Bakin aljani ne aka saka ya shafar miki mahaifa. Aikine akayi babba gaskiya" Rubutu ya bata na kwana uku, daya a barbada gishiri, daya a barbada sikari, dayan a saka lemon tsami. Sai wani tsinke kwakwa daya karya wajen gida takwas yana samun leda ya daure a ciki, yace idan ta dawo da tsinken za'a gwada aga idan rubutun yayi aiki ko akasin hakan. Zatayi karya idan tace bata dawo da shakku a zuciyarta ba, saboda maganar shi na cewa har yaranta Maryama take son cutarwa. Amman a tsayin shekarun nan ta yarda Maryama zatayi komai dan ta cutar da ita, dan yanzun takan biye mata idan ta takaleta, da wahala ta fadama Maryaman magana daya bata rama ba. Ta alaqanta hakan da yara uku duk maza da Maryama take gani ras a gabanta, Haris, Jabir, sai kuma Naadir. Shisa take daddaga mata kai har haka, ko da gadone ta fita a cikin gidan yanzun, tunda ita mazan ta biyu, sai mace guda daya. Duk yanda take jin cewar Bilal nata ne, duk kuma rashin banbancin da Ahmadi yake nunawa tsakanin Bilal da yaran shi ba zata hada shi a cikin magadan Ahmadi ba. Tasan wannan har kasan ranta. Akwai shakuwa mai karfi tsakanin su Khalifa da yan uwan su, zata jinjinawa Ahmadi ta wannan fannin. Tun tana nesa-nesa da ganin yaranta bangaren Maryama har ta fara saduda, na rana daya bata taba ganin Maryama tayi kokarin cutar dasu ba, a fuska ma bata nuna wannan alamar ba, duk da Gwaggo kance mata "Mugu bashida kammani, wanda yake kusa da kai yafi samun damar cutar ka Maimuna, kiyi kaffa-kaffa da yaranki" Tana kuma iya kokarinta, tunda har yanzun da wahalar gaske Maryama ta basu abu su karba, ko menene kuwa. Itama Maryama tun abin na damunta harya daina, bata kuma fasa gwada basu duk abinda suka samu tana baiwa nata yaran ko tana ci ba. A ganinta dai ta fita hakkin su tunda ta basu, zabinsu ne karba ko kin karba. Gara ma Bilal da ta rasa kalar yaron, tunda take sau hudu hannunta ya taba kaiwa jikin shi da sunan duka, shima akan Maryama ne, indai yana son abu ta bashi saiya karba yaci, duka dukan da tayi mishi har wani zazzabi tayi, zata rantse tafi shi jin zafin dukan. Tana son yaranta, tana son yaranta fiye da tunanin mai tunani, amman daban take jin Bilal, har a ranta daban take jin shi, bayan kauna akwai tausayin maraicin yaron da yake manne a zuciyarta. Gashi da manyance na ban namaki, kuma duk yafi shakuwa da ita a cikin yaran, zaka gansu suna tsakar gida suna wasa, amman yafi zabar zama a kusa da ita akan ya shiga cikin yan uwan shi suyi wasa. Ko kwance take shiru tana tunanin duniya sai Bilal ya shigo ya hana mata wannan tunanin, da shirmen shi da hirar shi takan ji sauki a ranta. Tana jinjina yanda Malam Mainasara yace Maryama zata iya cutar da su Khalifa, a karo na farko da take kyautata zaton ta akan Maryama "Idan baki tashi tsaye ba, sai ta sabauta miki yara, so take babban danta ya gaje komai na gidan, yafi kowa a zuciyar mijin ku" A kasan shakkun da takeyi akan maganar akwai tunani barkatai da ya jefa kwakwalwar ta, lokuttan da takan ga kowanne yaro zaune a kasa, amman Haris nakan cinyar Ahmadi, ko wasu lokuttan da zai baiwa kowa abu, sai taga ya diba cikin nashi ya karawa Haris, sosai zuciyarta ta cika da tsoron tabbacin maganar Malam Mainasara. Amman zata gwada shi taga idan aikin shi yana ci kafin ta yarda da bugun kasar da yayi mata. Dan harta gaji da wannan tarkacen Malaman na Khadi da Gwaggo, kowanne a cikin su fadar yanda ayyukan Malaman yake, sai a kanta ne hakan yake zama daban, sai a kanta ne aikin bayaci tunda ga Maryama nan daram a gidan Ahmadi, har dinki takeyi da a cewar Ahmadi ai daman tun a gida tanayin abinta. Gidan nasu kullum cikin mutane yake da sukan kawo dinkuna ko kuma suzo karba, dan dinkinne yasa Maryama harta datsa mata magana kwanaki "Ina da ayyuka da yawa a gabana, ina da hidindimu Maimuna, ki daina tunanin ina da lokacin yi miki wani abu. Wallahi banda wannan lokacin, gidane dai yanzun na fara zama a cikin, saiki bari idan Allah ya tsara zan rigaki kwanta dama sai kiga an fitar miki da gawata daga gidan nan" Maganganun sun mata zafi kuwa, sun kuma sakata tunanin fara sana'a itama, amman ta rasa, ta dai yiwa Ahmadi magana, yace zai tayata tunani, watakila ko takalma ne sai ya dinga kawo mata, ko ta tara kudade ta bayar sai ya saka mata a shagon shi ana juyawa, duk ribar saiya kawo mata abinta. Ko babu komai a ganin Maimuna zata samu wadatattun kudin da zataci gaba da naimarwa kanta da yaranta taimako wajen kariya daga sharrin masu sharri. Yanda Malam Mainasara yace tayi da rubutun haka tayi kuwa, sai dai tayi sa'a Ahmadi ya hanata fita da ranar komawar ta zagayo. Sai da akayi wajen kwanaki takwas tsakani sannan ta sami dalilin da tayi amfani dashi wajen fitar. Mamaki ta dingayi tana karawa, saboda karyayyun tsinkayen da Malam Mainasara ya batane ya juye cikin wani farin kyalle ya nannade, ya jujjuya a gaban idanuwansu ita da Khadi, ana bude kyallen saiga tsinke mike kyam kamar ba'a karya shi ba "Ma shaa Allah, aiki yayi yanda ake so. An samu damar karya sihirin" Farin ciki fal ranta, farin cikin da batayi wasu dakika tanayi ba, tsoro ya maye gurbin shi, jin Khadi tace "Saura raba soyayyar Haris da Ahmadi Malam, ya za'ayi da yaron?" Zungurinta Maimuna tayi cikin tashin hankali, Khadin na zabga mata harara, taga alamar ko kadan Maimuna ba zatayi hankali ba har yanzun. Har wani abin tausayine a batun daya shafi kishiya "Ni dai kar ayi mishi wani abu, idan sihirine a warware abin ya kaunace shi dai-dai da sauran yaran" Maimuna ta fadi cikin rawar murya, ba jan yaran take a jikinta ba sam, bata dai tsangwamar su, idan sun zo bangarenta su zauna, idan abincine suka samu su Khalifa naci sukan ci dasu, suyi wasan su. Amman Haris har rawar jiki yaron yakeyi idan ta saka shi ya miko mata abu, ko kuma Ahmadi ya aiko shi bangarenta, da gudun shi yakan shigo. Harda murmushin nan da duk idan yayi sai taga kamar Ahmadi. Batasan kome takeji akan su Haris kauna bace, tafi alakanta shi da shakuwa da kuma shiga rai irin wanda yara suke dashi, wani garin magani ya dauka ya bata "A ruwa zaki dan barbada yasha, shikenan" Karba dai tayi kawai badan zuciyarta ta aminta ba, haka ta dawo gida tana jinta kamar marar lafiya. Duk shigowar dasu Haris din sukayi ranar ta kasa ko da mikewa balle ta barbada maganin ta san yanda zatayi ta bashi. A haka Ahmadi ya shigo ya sameta, yaran suka tarye shi da gudun su suna fadin "Abbu sannu da dawowa" Kamar yanda suke kiran Ahmadi da shi, Maryama kuma Mami. Amman duk a cikin yaran Haris ya zabi ya dauka, sai ta bishi da kallo, bataso yanda ya tabbatar mata da zancen Malam Mainasara ba, sam bata zaci Maryama na da zuciyar wannan muguntar ba. Ita kam ba zata saka ido Ahmadi ya dinga nuna bambanci a tsakanin yaran ba. "Duk yaran baka ga kowa ba sai Haris kenan?" Ta bukata, tsareta Ahmadi yai da idanuwa, duk rashin kunyarta tana bala'in shakkar shi, yanzun ma tsintar kanta tayi da sauke nata idanuwan. Saida ya sallami yaran ya basu alawa da biskit din daya siyo musu tsaraba, suka fice daga dakin, sannan ya kara kallon ta "Me yake shiga kanki ne wani lokaci?" Kallon shi tayi itama "Ni babu abinda ya shiga kaina, amman kana nuna bambanci tsakanin yaran. Inma Haris kafi so bai kamata kana nunawa karara ba, ko ni zuciyata bata sosu ba, yara ai suna gani, kuma yaro baya mantuwa" Numfashi Ahmadi ya sauke, Allah ne shaida yana kaunar yaran shi, idan ma akwai wanda yakeji daban a cikin su Zubaida ce. Kaunar da yake ma yarinyar daban take, sai yake jin kamar tafi kowa bukatar kaunar shi, dan kasancewarta mace, ko kallon su yake yana hasaso yanda rayuwa zata kasance musu, sai ya dinga ganin su Khalifa sunyi aure da iyalinsu suna zuwa duba shi badan suna bukatar shi ba, dan kyautatawa kawai, amman yakan hango Zubaida har karshen rayuwar su tana bukatar kulawar shi, kuma ba zataji kamar ta girmi taimako daga wajen shi ba. Haris na da kwalafaci, a iya zaman da yake da yaran shi yana kula da dabi'un su, Haris na cikin yaran da suke yunwar kulawa, ko yanayin shi ka gani yanda yake so yayi komai dan ya faranta maka ko zaka kula shi ya isa ka fahimta, ba bambanci yake nunawa ba, kaunar su yake nuna musu dai-dai bukatar su, amman idan yai kokarin fahimtar da Maimuna zata sauya zancen shi zuwa wani abin. Shisa ya sake zancen gabaki daya "Yaya Ayuba kemun maganar kara bude wani shago, ina jin zan mishi zancen zaki kawo wani abu ko yaduka ne a siyo a juya miki...." Kai kawai ta iya jinjinawa, ta kula da maganar Haris ne bayaso ayi. Shisa ta kyale shi, washegari kuwa da safe saiga yaran sun shigo dakinta, tana hada shayi. Zuciyarta na rawa ta sami kofi ta shiga kitchen, anan ta kwanto maganin da yake nade cikin karbun zaninta, sai take ganin kamar Ahmadi zai fito ya ganta, barbadawa tayi a kofi tana saurin zuba ruwan shayi a ciki, dan shekawa tayi, ko bai shanye ba inta samu ya kurba hakan ma ya isa. Tana shiga daki ta ajiye kofin a kasa ta nufi inda Bilal yake rike da cokali mai yatsu da batasan inda ya dauko shi ba karya cake ido ko wani waje. Kama shi tayi ta karbe cokalin, kallonta yakeyi da ido kawai tunda da wahalar gaske kaji kukan shi. Tana juyowa taga kofin shayin da ta ajiye a hannun Rayyan, ya kuma daga ya kafa bakin shi "Rayyan...." Ta kira cikin tashin hankali, kafin ta karasa ta karbe kofin harya shanye. Dago shi tayi gabaki daya ta rikice "Na shiga uku ni Maimuna.... Na shiga uku, Rayyan...." Take furtawa tana tale bakin shi kamar hakan zai dawo da abinda yasha, kafin ta saka hannu tana taba fuskar shi, goshin shi da wuyan shi, har hannu tasa cikin rigar shi taji ko ya fara alamun zazzabi, bata taba tsorata irin haka ba, sauke shi tayi kasa dan sai buntsurewa yake yi tana tsugunnawa itama "Dan ubanka ka tsaya kafin in kwada maka mari" Ta fadi jikinta ko ina na bari da tashin hankali, dai-dai shigowar Ahmadi "Lafiya? Me ya faru? Me ya same shi?" Ya jero mata tambayoyin ganin yanda take a rikice "Kamar wani abu naga yakai bakin shi, kafin inzo harya hadiye" Ta furta muryarta na rawa, dana sani ne yai mata rumfa, saboda tashin hankalin da take ciki na rashin sanin mai maganin zaiyi tunda a kan idanuwanta taga karfin aiki irin na Malami Mainasara. "Bakwajin magana wallahi, na rasa me yasa kuke ajiye kananun abubuwa da yaran nan zasu iya dauka su hadiye...." Ahmadi ya karasa maganar yana daukar Rayyan da a lokacin duka shekarun shi basu karasa hudu ba "Me ka ci Rayyan? Fadamun kaji?" Kai Rayyan din ya girgiza mishi alamar shi baici komai ba. Babu dabar da Ahmadi bai mishi ba, amman yace shi shayi kawai yasha. Barin shi yayi tunda zai fita aiki, yace ma Maimuna din da taga ko zazzabi ya fara ta dauke shi ta kai shi asibiti, kudi ya dauka ya bata, duk da yakan ba kowaccen su kudi su ajiye tsaron laluri koda wani abu na gaggawa zai taso shi yana wajen aiki. Yinin ranar Rayyan wasan shi yake kamar komai bai faru ba, itace ta wuni ta kuma kwana da zazzabi. Har alkawari tayi na cewa in dai komai bai sami Rayyan ba, har abada ta daina bin Malamai zata cigaba da addu'a tana shan karya tambaya dai da kaikayi koma kan mashekiya, babu kalar addu'a da alkawurran da bata dingayi ba. Daga wannan zazzabin da takeyine ya juye mata laulayi mai zafin gaske. Ta sha wahala matuka, cikin da ta samu kuma na kara daga kimar aikin Malam Mainasara a idanuwanta. Bata yaye Rukayya ba kuma ta sami cikin Shamsu, kamar yanda tayi a haihuwar Khalifa da Zubaida, harma da Rayyan. Duk yanda Khadi taso su koma wajen Malam Mainasara kiyawa tayi, dan ta tsorata da lamarin shi akan Haris, batasan meye ya bata ba har Rayyan yasha, tsoro kuma ya hana ta furtawa kowa zancen, har aminiyar tata Khadi. A cikin shekarun biyar din nan, a gaban idanuwanta Rayyan, Bilal da sauran yaran suke girma, amman na Rayyan da Bilal ba ita kadai yake baiwa mamaki ba, har mutanen da duk zasu gansu. Kowa zancen yanda suke tasowa kamar yan biyu yakeyi, duk da akwai banbancin shekara daya da watanni har shida a tsakanin su. Amman hatta tsayin su dayane, dan hasken fata kawai Rayyan yafi Bilal, dan shi Rayyan farine tas-tas, Ahmadi ne yakan kaisu aski, hatta da askin iri daya akeyi musu. Kowa yan biyunta yake kira, idan baka sani ba ba zaka taba cewa ba yan biyu bane, ita kanta Maimuna bata gyarawa mutane in sun fadi. Balle kuma duk a cikin yaran Rayyan ake cewa yafi kowa kyau tunda shi yake kama da ita, shisa kamannin shi da Bilal ya baci, ko ita in ta gefen idanuwa suka gitta ko tana daga daki taji muryoyin su bata gane wanene a cikin su, balle duk kayan da Ahmadi zai siya iri daya yake siyarwa Bilal da Rayyan din. "Ka dauki jakar ka?" Ta tambayi Bilal din "Hamma ya daukar muna..." Ahmadi bai yarda da wani bai girmi wani da wasu shekaru ba, ko wata daya wani ya baka a cikin gidan saika bashi girman shi, kuma idan ya saka abu sai kayi. Da yake kaunar da take tsakanin shi da yaran mai girma ce, kowa bayason abinda Abbu zai mishi fada ko yayi fushi. "Allah ya tsare, ka kula da Hamman ka kaji ko?" Cewar Maimuna, duk da tasan Rayyan ne ya kamata ya kula da Bilal din, sai dai rigimar Rayyan a yan shekarun shi har mamaki take ba Maimuna, ga taurin kai kamar mutanen farko, idan abu yakeyi ko kashe shi zatayi saiya koma ya karasa, yanzun ma Ahmadi ya hana mata dukan shi, a cewar shi zai kangare. Taci gaba da mishi addu'a kawai. Amman ko yaran gidan Yaya Ayuba suka shigo, har wanda suka girmi Rayyan basa shiga gonar shi, duka yake musu, ga rikicin shi baya rabuwa, in ana fada dashi in bashi ya hakura ba, haduwa goma in kukayi sai ya kara cakumarka, abinda Maimuna ta kula dashi yan watannin nan, Bilal ne kawai zai shiga tsakani in ana fada da Rayyan din ya hakura. Wani lokacin in Bilal yaita janye shi sai fadan ya koma kan Bilal din, tana kuma kula da yaron baya taba daga hannu da sunan ya rama duk wani duka da Rayyan din zai mishi, sai dai in karewa zaiyi, har sai yaga zuciyar shi tayi sanyi tukunna zaka ji yace mishi "Ka daina fada Hamma, Ayya bata so, Abbu ma bayaso, nima bana so, ka daina" Amman idan ba Bilal ba babu wanda ya isa ya taba fadan Rayyan cikin dadin rai, yana kuka yana zillewa zata samu ta rufe shi a daki. Amman ko kowa ya manta inya fito saiyaci gaba. Har kuka tayi shekaranjiya akan taurin kan Rayyan, sai take ganin kamar abinda yasha ne yake saka shi wannan abubuwan, kamar tana da laifi a kaddarar Rayyan, kuka takeyi har a sujjada tana rokon idan wani laifin ne ma Allah ya jarabceta ta wani fanni bata kan yaranta ba, kishi da Maryama ba tasan yanda zata bari ba, amman bin Malamai ta hakura dashi, duk da yanzun tana jin kamar ta aiki Khadi a buga mata kasa akan Rayyan, amman tana tsoron a gano mata abinda zai kara daga mata hankali. Har waje ta fito taga Ahmadi ya tattara kan yaran "Ayya sai mun dawo" Haris ya fadi da murmushin da baka raba fuskar yaran dashi, sai ta tsinci kanta da mayar mishi da murmushin "Allah ya tsare, ku kula da kyau, ayi karatu kuma" Kai ya jinjina, ya juya kenan sukai karo da Rayyan, da kafin wani yai motsi ya dauke Haris din da mari yana saka Ahmadi karasowa ya tallafe mishi kai "Rayyan... Bana hanaka dukan yayyanka ba? Haris din ba Hamman ka bane ba? Ka bashi hakuri yanzun nan" Kallon Ahmadi din Rayyan yayi kamar zaice wani abu, sai kuma ya fasa yana kama hanya ya nufi waje, Bilal na rufa mishi baya da saurin shi. Numfashi Ahmadi ya sauke "Allah ka tausasa mun zafin zuciyar yaron nan. Allah ka tausasamun shi, kai kabani, Allah ka bani ikon sauke amana" Yake fadi a cikin ranshi,kwatankwacin addu'ar da yakanyi wa duka yaran duk lokacin da zasuyi wani abu ba dai-dai ba, musamman Rayyan da bayason yawan dukan shi saboda kalar yaran ta fita daban duk a cikin yaran. Haris da yake tsaye ya sadda kan shi kasa Ahmadi ya kamo "Haris saika dinga hakuri da kanin naka kaji ko?" Murmushi Haris yayi mishi "Ni na buge shi Abbu, bangani ba amman" Kai kawai Ahmadi ya jinjina, yana kama hannun Haris din, ya juyo ya kalli Maimuna da fuskarta take dauke da ban hakuri kan halayen Rayyan din, murmushin karfin gwiwa yayi mata "A dawo lafiya, ka kula da kanka" Ya furta a hankali "Kema haka" Ya fadi suna ficewa, daki ta koma tana sauke numfashi. Da tunanin halayen Rayyan manne a zuciyarta. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:06 PM - 111: Nov 1, 2020 04 1993, Kano. Zata iya cewa tunda Ahmadi yabarta tafiyar nan take shiri, kusan sati daya kenan. Sau daya ta taba tafiya mai nisan awa biyu. Wani lokaci ko da irin hakane, Ahmadi baya barinta "Tsoro ya miki yawa Maryama... Shisa banason kina nisa ke kadai" Yakan ce, kuma da gaskene, har tsiya akeyi mata a gida wasu lokuttan, ace da tazo a karkara ba zatayi kyawun gani ba. Dariya kawai takanyi ta kyale su, sau daya kafafuwanta suka taka kauyen Kankia da yake a jihar Katsina, shima rasuwa Mannira ce, matar Yayanta Deeni. Zata tuna yanda aka kai ruwa rana kafin a barshi auren Mannira, na daya bata kasance daga danginsu kamar yanda suka saba ba, duk da yanzun wasu na bijirewa auren dangin. Amman rabon tilar yarinyar su Laila ne kawai ya saka shi kafewa da watsi da maganganun da kowa yakeyi na yaren Mannira "Ka rasa wa zaka jajibo kana zaune lafiya da matarka sai banufiya, salon duk tazo yanda ta lashe maka kurwa ta lashe kurwar sauran yaran ko?" Maryama ta tuna maganganun Mahaifiyar su lokacin da yazo mata da zancen auren Mannirar, kowa a dangi da abinda yake fadi, mahaifin sune kawai ya bashi goyon baya, sosai ya dinga fada "Nayi bincike, iyayen yarinyar nan mutanen kirkine, suna zaune da kowa lafiya. Ita ma nagartacciya ce, addinin musulunci dai shi muke bi, kuma a sharuddan da aka kafa mana na neman aure, bamuda wani dalili na hana shi aurenta" Hakan yasa dole kowa ya hakura, amman badan anaso ba, yanda yan uwa suka daga hankalin su akan auren Deeni da Mannira, ko matar shi da zai hada zama da Mannirar bata tunanin ta damu haka, ko ita da suka zauna da Deenie suna zancen ta jinjina al'amarin matuka "Ni banki ka kara aure ba Yaya, da ba'a karawa nima da ina gidan wani ba Ahmadi ba, amman banufiya fa, ka dai kara duba lamarin" Dan yanda sukayi kaurin suna wajen shaidar da akeyi musu ta maita da tsafi na sanyaya jikinta "Duk musuluncin banufe sai yayi tsafi" Haka takanji ana fadi, tana kaunar Deeni har ranta, bata son abinda zaizo ya cutar dashi sam. "Ke dai kiyimun fatan alkhairi kawai" Deeni ya fadi yana dariya, sai gashi daga baya kowa na yabon kirkinta. Cikin kankanin lokaci ta shiga zukatan jama'a. Maryama da kowa sun alakanta hakan bayan rasuwar Mannira mintina kadan bayan haihuwar 'yarta mace. Mutuwar ta daki Deeni ba kadan ba, har akayi jana'iza baisan inda kan shi yake ba. Kowa ya budi baki ca yakeyi rabone kawai ya hada kaddarar Mannira da Deeni, shisa duk yanda akaso hana shi aurenta yaki ji, ashe ma zaman nasu bamai tsayi bane, tunda duka watannin su sha hudu. To lokacin ne tafiyar da tayi mai tsayi, shekaru kusan biyu kenan da suka wuce. Lokaci zuwa lokaci takan yi tunanin yarinyar, saboda tun a wajen rasuwa kowa ya kalleta sai yayi magana kan kalar idanuwanta. Tasan ba kasafai ake samun irin idanuwan a cikin mutane ba, musamman anan yankin Najeriya. Amman sai take ganin gara idanuwan yarinyar da taci suna Layla akan na wani bawan Allah data taba gani, har gobe ko ita kadai ta tuna sai tsikar jikinta ta tashi, saboda sak kalar idanuwan miciji, sai da tayi zaton ko tayi gamo ne. Ahmadi yaita mata dariya, yake cewa a wajen aikin su akwai wani bature nashi idanuwan kalar ganye, koraye ne sosai. To ita kam gara mata bature, wannan ba abin mamaki bane, amman a jikin bakar fata, dole abin ya girgizata. Shisa da taga Layla ta kara jinjina ma Ikon Allah, dan Shi ya banbanta halitta a tsakanin mutane, bata da kalar da zata misalta idanuwan Layla dashi, ko kyanwa kowacce da kalar nata idanuwan. Amman tabbas ta wata kyanwa kawai ta taba gani da kalar idanuwan yarinyar. Kalar surutun da akeyi tun a wajen rasuwar Mannira, sam Maryama ba zaci za'ayi bakwai yarinyar bata bi mahaifiyarta ba. Tun tana tsammanin bayan dawowar su labarin rasuwar Layla zai iso musu harta daina. Yau dinma har tasha Ahmadi ya rakata, da yake kwana biyu zatayi, daga ita sai Marwan ta taho. Sauran yaran tabar su wajen Maimuna da fuskarta babu yabo babu fallasa tace mata "Allah ya tsare, ki gaida su" Da tayi mata sallama, babu wani abu da zatayi da Maimuna zata zauna lafiya da ita. Shisa yanzun inta gaya mata maganar da taji ba zata iya dauka ba, ramawa takeyi. Yaranta ne kawai ta kula Maimuna na budewa hakora, kishinta sai yazowa Maryama da sauki tunda bata saka yaran a cikin rashin jituwar su. Hankalinta kwance tabarsu a gida, suma basu damu ba tunda ko unguwa zata fita a gida takan barsu. Ranta kal tanata kallon gari har suka isa kankia. Furaira uwargidan Deeni ta karbeta hannu bibbiyu, ta sauketa kamar yanda ta saba taryar su, shisa kowa a danginsu baya gajiya da fadar alkhairinta. Sai dai ta girgiza matuka da ganin dan uwan nata, damuwar da take shimfide akan fuskar shi mai yawa ce, duk da murmushin da yake mata da suke gaisawa, tana ganin yanda bai kai cikin idanuwan shi ba. Tunda ta isa ta jima bata ga giccin Layla ba, kafin daga baya yarinyar da take bacci ta taso ta fito. Farat daya Maryama tajita har cikin ranta, sai bayan Furaira ta basu waje da Deeni ne ta samu damar tambayar shi me yake faruwa, murmushin da yayi mai ciwone matuka. "Bana jin dadin tsangwamar da Layla take fuskanta daga wajen mutanen kauyen nan. Ko unguwa Furaira ta rage fita sai dole, tana iya kokarinta, amman ko taro ta shiga da Layla sai iyaye su fara janye yaran su, babu wanda ta taba cutarwa, bansan me yasa suke alakantata da maita ba. Dan Allah ya banbanta kalar idanuwanta da nasu sai suke dora alhakin hakan akan Mannira, suna zantukan da bana son maimaitawa...." Deeni ya karasa maganar yana sauke ajiyar zuciya "Wallahi a kwanakin nan ina tunanin mayar da ita hannun Inna...." Kai Maryama ta jinjina mishi, zancen na taba zuciyarta fiye da tunani "Allah ya kyauta ya rufa asiri, rashin ilimi cuta ce babba a tsakanin al'umma. Zan tafi da ita idan zan wuce, nasan Ahmadi ba zaiki ta zauna a hannuna ba, amman kaga ba zai yiwu inje mishi da zancen kai tsaye ba" Kai Deeni yake girgiza mata tunda ta fara magana "Karki dora mishi dawainiya, ga nashi yaran" Murmushi Maryama tayi "Babu wata dawainiya, indai zai amince in riketa, ina da sana'ata ko ka manta? Ba wani abu nakeyi da kudadena ba. In shaa Allah rike Layla ba zaimun wahala ba. Amincewar ka itace komai na" Numfashi Deeni ya fitar mai nauyi "Ni dai ina so ta tashi inda babu tsangwama, inda wani ba zai lakaba mata maitar da batada ita ba..." Kusan har karfe dayan dare suna shan hirar yaushe rabo da Deeni. Taji dadin damuwar da taga ta ragu a idanuwan shi kafin ta baro garin Kankia tare da Layla, wannan karin da tunani fal a zuciyarta, har ranta take jin kaunar yarinyar, ko dan Allah bai bata 'ya mace ba har yanzun, kuma tana so, inda wani zaman kirki suke da Maimuna ba zataki ko Rukayya ko Zubaida wata ta dawo dakinta gabaki daya ba, musamman tunda yanzun Maimuna goyon mace takeyi, yarinyar da aka mayarwa sunan mahaifiyar Maimuna suke kuma kira da Intisar. Amman abune da tabar shi a zuciyarta, tunda tasan furta shi matsala kawai zai janyo mata. Addu'a takeyi Ahmadi yabarta ta rike Layla. Harta isa gida, inda bata sami kowa ba cikin yaran gidan, tasan babu Islamiyya tunda ranar Alhamis ce, suna gidan Yaya Ayuba, tunda basu da wajen shiga daya wuce nan din. Daki ta wuce kanta tsaye tunda dai tasan Maimuna ba fitowa zatayi dan ta taryeta ba, ga jigatar hanya, saboda daga Marwan har Layla bacci suketa shirga, shi ta goyashi, Layla kuma tana sabe da ita, ga kayan su ga tsarabar da aka hadota da ita. Banda nishi babu abinda take dirkawa, fitowa tayi tsakar gidan da nufin yin alwala, in tayi sallar la'asar ko da taliya ce sai ta dora musu, tana da dakakken yaji, yunwar da take ji ba zata jira wata miya ba ko da tana da cefane. Ta idar da alwalar kenan ta shiga daki taji sallamar Zubaida "Mami sannu da zuwa" Zubaida ta fadi tana ajiye mata kular abincin da take rike da ita hadi da dorawa da "Gashi inji Ayya..." Kallon Zubaida tayi da wani yanayi daya girmi godiya shimfide a fuskarta. Ko a mafarki bata tsammaci wannan kirkin ba. Batama sakawa ranta ba "Kice nagode sosai Zubaida" Dan murmushi Zubaida tayi tana ficewa daga dakin. Saida ta fara yin sallah tukunna ta gyara zama ta janyo kular gabanta, dambun shinkafa ne sai kamshi yakeyi. Wani numfashi ta sauke tana daukar kular ta mike tsaye. Kitchen ta nufa ta sami filet ta zuba, ta saka mai da yaji ta dawo dakinta. Tas ta cinye ta mayar da ruwa tanayin hamdala, batasan ta gaji ba saida ta kwanta, kuma lokacin Marwan ya zabi ya tashi ya fara damunta da rikicin shi, dole ta kara mikewa tana zuwa ta zuba mishi dambun shima. Kewar su Haris na damunta, amman da yake ba hankali gare su ba ko suzo su duba suga ko ta dawo. Ko bayan Magriba da ta jiyo hayaniyar su bangaren Maimuna suka wuce, abin sai da yai mata wani iri, kamar ta aika Marwan ya kira su, shima sunata wasa da Layla tun dazun. Ganin Ahmadi ya sanyaya mata zuciya, da murmushin nan nashi ya shigo bangarenta "Mutanen Kankia..." Yai maganar cikin sigar tsokana, dariya tayi tana mishi sannu da zuwa, yana zama idanuwan shi akan Layla suka fara sauka "Ina kika samo mana yarinya haka?" Zuciyar ta taji ta doka, duk da babu alamar komai a muryar Ahmadin "Yarinyar wajen Margayiya Mannira ce" Dan ware idanuwa Ahmadi yayi "Allah Sarki... Girman dan mutum ba wahala, rayuwa kenan" Ya karasa maganar cike da tausayawa, yasan zafin rashin iyaye, duk da bai taso cikin rashin kulawa ba, musamman ace mahaifiya. Ita kuma Maryama kallon shi takeyi, ko zataji yayi magana kan idanuwan Layla din, amman wata hirar yajata da ita yana tambayarta hanya kuma yanda ta baro mutanen can din. Hira suke kamar sunyi satika basu ga juna ba, kirki irin na Ahmadi yakan bata mamaki duk tsayin shekarun nan da sukayi a tare. Bai tashi daga bangarenta ba sai da aka kira sallar isha'i. Tasan sai washegari zata karbi girki, dan haka sallama sukayi. Sai kuma lokacin taga su Haris da suke mata sannu da zuwa "Ba kun manta dani ba Haris?" Dariya yayi "A'a Mami, Ayya ce tai mana masa, shine mukace bama so da miya sai ta saka mana sikari, yayi dadi sosai ko Jabir?" Haris ya fadi, Jabir din ba daga mishi kai, surutun su suka cigaba dayi mata tana biye su dan bata da abokan hirar da suka wuce yaran nata, Haris ne kawai bai tsareta da tambayar inda ta samo Layla ba, su Jabir kuwa sai tambaya sukeyi tace kanwar su ce "Idon ta wani iri... Me yasa ba kalar namu ba?" Jabir ya tambaya yana saka Maryama dogon nazari kafin tace "Kowa da kalar nashi, kaima idan ka duba naka ba iri daya bane da na Naadir" Cike da rashin fahimta Jabir din ya leka idanuwan Naadir "Iri dayane Mami, ki kalla kiga" Kai ta girgiza mishi "Ba zaka gani ba sosai yanzun..." Hakura yayi ba dan yagane ba "Anan gidan zata zauna? Zamu dinga wasa tare?" Dan jinjina kai Maryama tayi "Nima ban sani ba" Wannan karin su duka suka hada baki harda Haris "Dan Allah Mami kibarta anan" Dariya kawai tayi, ba zatai musu wannan alkawarin ba sai ta fara yin magana da Ahmadi tukunna, idan ya amince mata zataji dadi, ita kanta tana son ta rike Laylar, batasan ko tana da rabon samun 'ya mace ba. Tunda ga maza nan har hudu a gabanta. * "Saboda na kawo Bilal? Shisa itama taje ta dauko yarinya kenan? Ahmadi mayyar zaka bari ta zauna mana a gida? Wannan yarinyar mai idanun mage zaka hada mana a cikin yara?" A tsayin shekarun nan ya zaice ya saba da rigimar Maimuna, ta karfi ta mayar da shi mafadaci, dan wani lokacin saiya balbaleta da fada yake samun kanta, wani lokacin kuma ficewa yake yabar mata gidan gabaki daya. Bako yaushe take bata mishi rai ba, saboda duk yanda yake jin Maryama, Maimuna daban take a zuciyar shi, ita dince karfin gwiwar shi, har yanzun ko matsala ya kwaso wajenta yake fara nufa, saboda yasan idan bata da shawarar da zata magance mishi matsalar shi zata raba nauyin matsalar tare da shi. Labarin soyayya kala biyu zai bayar da kan shi a dage, muryar shi dauke da alfahari, shine soyayyar mahaifiyar shi, sai kuma soyayyar da Maimuna take yi mishi, shisa ya fahimci kishinta, tana mishi son da yake da yakinin yanzun a fadin duniyar shi baida na biyun sa. Amman a lokaci irin wannan yana rasa me yake lullube kwakwalwarta haka, me yasa soyayyar shi bata sakata zaben kalaman da zata furta mishi, kishin shi yasa ta daina gudun bacin ran shi sam. "Ina manta cewa Bilal ba daga jikin mu ya fito ba wallahi, ki daina maganar nan dan Allah..." Ahmadi ya fara cikin taushin murya, amman kai Maimuna take girgiza mishi, tun jiya da safe da ta fita tsakar gida taga Layla sai da gabanta yai wata irin mummunar faduwa, babu shiri ta koma daki tana karanta duk wata addu'a da zata zo bakinta, gashi yarinyar bata da haske can da zatayi zaton ko daga kasar turawa ta fado musu cikin gida. Babu kalar tunanin da batayi ba a ranta kan yarinyar, ko da Ahmadi ya dawo ta tambaye shi saiya fada mata ko wacece Laylar. Bata manta lokacin da akaita surutun auren Deeni da Mannira a dangi ba, har Gwaggo bare na fadin "Mugun abinsu ne ya fara koma musu, shisa yaje ya kwaso mayya... Watakila ta lashe mana kurwar Karime duk mu huta" A lokacin abin dariya yayita bata, sanda labarin mutuwar Mannira ta riske su zatai karya idan bataji wani iri a ranta ba, duk surutun da ta dinga sha, ashe ma bata da rabon zama mai nisa a gidan auren, fatan samun Rahma tayi mata. Ta dauka tunda tayiwa Maryama gaisuwa a wancen lokacin ba zata sake jin ko da labarin Mannira bane ba. Sai ga yarta a cikin gidan ta, yar Mannira mai idanuwan aljanu, yarinyar da tun jiya ta kasa samun sukuni a cikin nata gidan saboda su Haris sun shigo mata da ita bangarenta. Har ranta ta dauka ko Maryama tazo da itane ta kwana biyu ta mayar da ita, sai yanzun da Ahmadi yazo mata da wani bayani da babu abinda ta fahimta a cikin shi sai cewar Layla din zata zauna ne a cikin gidan. "Ni dai ba zan zauna a gida daya da ita ba, sai kasan yanda zakayi da mu... Haka kawai muna zaman lafiya zata zo ta lashe mun yara" Rai a bace Ahmadi yake kallon ta "Wani lokaci sai ki dinga magana kamar baki da ilimi. Kina manta babu wani abu maita a addini ne, sai kambun baka... Kuma ita kadai kika fara gani da kalar idanuwa haka? Ko bakiga wanda aka haifa babu idanuwan bane gabaki daya? Kinsan karki fara mun fitinar da bata da karshe, na fada miki Layla zata zauna ne saboda girmamawa, ba wai shawararki nake nema akan hakan ba" Wannan karon itace take kallon shi, yanda ya rufe ido yana datsa mata maganganu har yana kiranta da jahila a fakaice saboda wannan dangin mayun "Ni kake kira da jahila? Ahmadi ni kake cewa jahila akan nace ba zan zauna gida daya da mayya ba?" Numfashi ya sauke "Kinga irin abin ko? Ni ban kiraki jahila ba, ki daina ce ma yarinyar mutane mayya tunda idan wani ya kira naki yaran da wannan kalmar ba zakiji dadi ba..." Ido cikin ido take kallon shi "Akan me za'a kira nawa yaran da mayu tunda basu hada hanya da maita ba? Ni dai na fada maka ba zan zauna gida daya da ita ba, ko ka kwashe ta da Maryaman kasan inda zaka kaisu, ko kuma ni kasan inda zaka kaini" Murmushin takaici Ahmadi yayi yana binta da ido "Kiyi duk abinda kike so, Layla kam zataci gaba da zama a gidan nan, in ba aure ko mutuwa ya rabata da shi ba..." Idanuwan Maimuna cike taf da hawaye take kallon shi, tana son tabbatar da cewa da gaske yakeyi wannan yarinyar da tun jiya take firgitata zai bar mata cikin gida "Ahmadi da gaske nakeyi ba zan zauna da ita ba. Dan Allah to ka raba mana gida" Ta karasa hawaye na zubo mata "Ke kinsan ko ina da hali ba zan raba muku gida ba saboda banason zumuncin yarana ya samu tangarda, balle kuma bani da wannan halin..." Mikewa Maimuna tayi, hawaye takeyi sosai, ta kowacce fuska Maryama ta zame mata bala'i. "Ni kam zan bar muku gidan, sai ku zauna. A banza ba za'a zo a lashe mun kurwa ba wallahi" Gyara zaman shi Ahmadi yayi baice mata komai ba, rigima take nema sosai. Ya rigada ya gama magana, ba zai biye mata ba. Kamar yanda yace Layla kama zama daram a cikin gidan. In tayi rikicin ta gama taga da gaske yakeyi zata hakura. Yana nan zaune yaga ta fito da jaka ta saka mayafi "Ina zakije?" Sai da ta share kwallar da ta zubo mata sannan tace mishi "Gidan mu" Yasan ba lokacin da ya kamata yayi dariya bane, amman dariyar ce ta kubce mishi, da kuruciyar su ma, duk fadan da takeyi dashi batace zatayi yaji ba sai yanzun da girma yazo musu, dariya yakeyi sosai da ta kara sosa ranta, wato bai damu ba, bai kuma dauki abinda takeyi din da wani girma ba "Tunda kaga mahaukaciya dole kayi dariya Ahmadi..." Ta karasa maganar cikin kuka tana daukar yar jakar da ita kanta batasan me da me ta zuba a ciki ba. Tasan idan akace ta bar gidan Ahmadi da sunan yaji ba zata iya ba, tunda ta aure shi, rasuwar Audu ne tayi kwanaki har bakwai batare da shi ba, kuma ko a cikin jimami na rashi, kewar shi na nukurkusarta. Yanzun ma tayi ne kawai dan ta razana shi, ganin kukan da takeyi yasa Ahmadi tashi, amman har lokacin murmushine a fuskar shi, jakar yake kokarin kwacewa ta janye, ya kama hannunta duk kokarin kwacewa da takeyi ya karbi jakar, da kanshi ya kama mayafinta yana cirewa "Ke yanzun da girman ki sai kiyi yaji? Kuma ina zakije ki barni? Ko bakisan Maimuna ce jigon rayuwar Ahmadi bane?" Wasu hawayen ne suka kara zubo mata, tana tsinewa ranar da Maryama ta dora idanuwanta akan Ahmadi har taji ya kwanta mata, tasata raba wannan soyayyar tashi da ita, shisa bata ga ranar da zata wayi gari da son matar nan ko kankani a zuciyarta ba. "Ni ba zan zauna da yarinyar nan a gida daya ba, ba zan zauna ba. Kabarni in tafi tunda su ka zaba a kaina. Ka nuna mun yanda banda wani muhimmanci a wajen ka" Kamata yayi suka zauna, kalaman da yasan da wahala taki yin laushi yake amfani dasu wajen tausarta, tasan yasan cewa shi dinne rauninta, soyayyar shi ita ce rauninta "Idan ta lashe mun yara fa?" Tayi maganar da wani irin sanyi murya dan gabaki daya ya gama kashe mata jiki "Ba zatayi ba, ki yarda dani mana...alfarma nake roko a wajenki Maimuna, ko saina tsugunna..." Ahmadi ya karasa maganar yana kokarin sauka daga kujerar, da sauri ta riko hannun shi tana girgiza mishi kai, murmushi yayi mata "Nagode... Dan Allah karki takali Maryama da maganar nan, alfarma dana roka ta hada da wannan, wallahi badan Bilal ta kawo Layla ba, itama da nata dalilin kamar yanda kike da shi" Taji shi, amman ita tasan gasa Maeyama takeyi da ita, tunda ta kawo Bilal gidan take bakin ciki, shine sai da itama ta nemo wannan mayyar ta kawo, kowa na da yara da kuma dan riko kenan a cikin gidan. "Kinga daman bata da mace ko..." Ahmadi ya fara, wani irin kallo da Maimuna ta watsa mishi yana saka shi yin dariya yana daga hannuwan shi ya hadesu waje daya cikin sigar ban hakuri "Ka tashi ka tafi wajenta idan kewarta ce tasa kake son yimun hirarta a daki..." Maimuna ta fadi wani irin kishi na taso mata, tashin yayi niyya tunda daman ya jimane haka saboda yana so ya fada mata zancen Layla. Amman maganar da tayi tasa shi yanke hukunci kara zama, yasan ana gab da kiran isha'i, sai yayi amfani da wannan damar ya fice gabaki daya. Maimunar tashi ta zama a lallaba, rikicinta sai shi. * Ba ko yaushe yake zama gidan Yaya Ayuba ba, ko da kuwa duka yaran gidan suna can. Lokutta da dama dawowa yake yai kwanciyar shi a daki, yasan ko Ayya tana tunanin yana can wani lokacin. Haka yakan haramtawa Bilal zaman ko da yana so, shi dai da bakin shi baya ce mishi ya taso su taho tare, idan ya taso din kuma baya hana shi biyo shi. Yau baima kula da ya dawo gida ba, zane yake sonyi, haka kawai tunda ya fara rike fensiri, tun ma kafin Abbu ya saka su makaranta zaiyi zane akan duk wani abu da zai samu. Ganin ko gawayi ya tsinto yana musu zane a jikin bango yasa Abbu din kwaso mishi litattafan da zai dingayi a kai. Yanzun ma gara yayi zanen shi, ko fada sukeyi idan aka rabasu akan takardun zanen shi yake huce haushin shi har sai yaji zuciyar shi tayi sanyi. Ba kasafai yake ganin kyawun abinda yake zanawa din da baya wuce mutane, dabbobi, kwari, ko duk wani abu da yake so ya zana din, amman sai ayita cewa yayi kyau "Allah yayi riko da hannayenka Rayyan, watakila kai kuma abincin ka a zane yake" Abbu ya fadi kwanakin baya, baigane asalin ma'anar kalaman ba, ya dai amsa da Amin ne kawai. Ya fara zanen yaji yunwa na naniqar shi, sai ya tuna fada yayi a makaranta bayan sun tashi, daya dawo baibi takan abinci ba. Tashi yayi ya fita daga dakin yana nufar kitchen, yasan inda Ayya take ajiye musu abincin su shida Bilal, nashi ya dauko da cokali, yana dawowa dakin ya samu Layla a ciki, hannunta rike da fensirin zanen shi, dayan rike da takardar da yai kwana biyu yana aiki a kanta, a karo na farko da yaso gwada zana wani a cikin gidan, ya kuma zabi daya fara da Bilal, ta dakuna takardar, tana kuma kokarin kara bi da fensirin a kai. Kwata-kwata tun ranar daya sauke idanuwan shi kan yarinyar batayi mishi ba, bayason mage, basu da ita a gidan su, akwai a gidan Yaya Ayuba, kuma in dai zai shiga gidan zasu dauke dan ansan tsoron ta yake, a cewar Hajja Mama, matar Baffa kamar yanda suke kiran Yaya Ayuba din, tun yana yaro bayason mage, da ya gani kamar zai shide, shisa bayason Layla, idanuwanta na mishi kama dana jaririn magen gidan Baffa daya gani. Gashi duk inda yayi cikin gidan sai yaga kamar tana bin shine, lokutta da dama Haris ke zuwa yayi sauri yaja hannunta dan kamar shi kadai ya kula da bayason yarinyar na zuwa kusa da shi. Kuma akan kunnen shi rannan yaji Ayya tace mayya ce, baiyi mamaki ba. Tunda itace mutum ta farko daya taba gani da kalar wannan idanuwan, da gaske mayyar ce, shisa duk inda yabi cikin gidan sai ya ganta. Yar kular abincin ya ajiye a gefe yana karasawa cikin dakin, fensirin ya fara fisgewa daga hannun ta, kafin ya fara kokarin karbar takardar da take rike da ita, bayason yasa karfi ya karba, kamar yanda da dukkan zuciyar shi bayason ko yaya ne jikin shi ya hadu da nata, dan a tsorace yake, kokari yakeyi na ganin bai kalli fuskarta ba "Saki mana..." Ya furta, amman sai ta maqale kafada, ran shi bashida wuyar baci "Mtswww, ki saki nace, ta ina ma kika shigo mana" Rayyan yake fadi yana sake jan takardar, itama ja tayi ta kuwa rabata gida biyu, cikin tashin hankali Rayyan yake kallon takardar da take hannun shi, kafin ya kalli ta hannun Layla din, wani malolon bakin ciki na mishi tsaye a makoshi, baisan lokacin da ya dauketa da wani irin mari ba, dai-dai shigowar Bilal daya karasa da gudu yana tare hannun Rayyan daya daga zai sake mata wani marin, dayan hannun shi kuma yana ture Layla da ta gigice ko kuka ta kasa saki saboda azaba "Hamma... Me tayi maka? Baka ga yarinya bace?" Bilal yake tambaya cikin tashin hankali yana juyawa ya kalli Layla da sai lokacin ta samu ta fashe da wani irin kuka "Ban sani ba, daka shigo baka ga abinda yake hannunta bane ba? Me yasa zata shigo mana daki?" Hannunta Bilal ya rike yana rasa ta inda zai fara lallashinta "Amman ai karama ce, me yasa zaka mareta?" Bilal ya sake tambaya, dan shi sam baiga dalilin da zaisa duk girman Rayyan ya mari 'yar yarinya kamar Layla ba. Duk da saurin hannun shi akan kowa yake sauka. Ko jiya yayi mishi magana daya mari  Shamsu saboda bai gani ba ya diga mishi ruwa. Yan kananan yaran gidan babu mai zuwa kusa dashi, wani lokacin ko wasa sukayi yayi sallama da gudu zakaga kowa na neman wajen boyewa. Wanda suka girmi Rayyan ma shakkar shi sukeyi, ko Khalifa yakan rabe gefe yaba Rayyan hanya, bamai so wani abu ya hadasu sam "Ka fita da ita, wallahi zan kara dukan ta idan taci gaba da kuka" Bilal hannun Layla ya kama yana janta suka fice daga dakin. Rayyan din nabin su da wani irin tsaki. Yanajin yanda bai daki wahalar kwanan shi biyu da yayi yana wahala ba sam, da Bilal bai shigo ba ya samu ya jibgeta da ya samu saukin tafasar da ran shi yakeyi yanzun "Mayya kawai" Ya furta yana jin wata tsanarta a ran shi, a gefe daya kuma Bilal ne yake ta kokarin lallashin Layla daya samu tayi shiru, sai yatsun Rayyan kwance akan fuskarta. Baisan menene maraici ba, duk da yaji idan Ayya tayi baki wata rana suna maganar yanda shi din maraya ne. Itama kuma yaji ance marainiya ce, haka kawai yake jin tausayin yarinyar. Ko ido suka hada saiya tsinci kan shi dayi mata murmushi. Ko kadan basu da masaniya akan yanda kaddara ta bude musu sabon shafi. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:06 PM - 111: Nov 6, 2020 05 * Kwanakin shi a lissafe suke, yana son makaranta, har kasan ran shi yana son makaranta. Yana kuma son karatu, musamman yanda Allah ya bashi baiwar kwakwalwa, da wahalar gaske ayi abu sau daya a gaban shi bai dauke ba. Kawai abu dayane ya kasa fahimta a shekarun shi goma sha bakwai yanzun a duniya. Duk lokacin da Abbu ko Ayya zasu nuna suna son abu, lokacin zaiji har ranshi babu abinda ya tsana sama da abin, yana so ya bari, yana so yaso abinda suke so ko dan yanda yake ganin halayen shi sun kasa raba zukatan su da tarin kaunar da sukeyi mishi. Ya wuce Bilal da aji daya, amman zai iya tuna lokuttan da Bilal din yake daukar nashi litattafan ya duba ko an basu wani aiki da baiyi ba dan ya taya shi. Da gangan zai bar takardun shi babu rubutun komai, kawai dan yanda Abbu ya nuna yana bala'in kaunar su da karatu, bawai dan tambayoyin sun gagare shi amsawa ba. Ba a makaranta kawai hakan ya tsaya mishi ba, duk wani lamari na rayuwa da zamantakewar yau da kullum, kar dai Abbu ko Ayya su nuna ga yanda suke so, dan zaiyi abu daban da wannan din ne. Bai fara kawo sakamako mai kyau ba sai da yazo aji hudu a makaranta, ranar da kalaman Abbu suka tunzura shi "Nasan asarar kudina kawai nakeyi Rayyan, da ka daina zuwa makarantar nan zaifi mun, amman dai zanci gaba da biya dan in nunawa Yaya Ayuba cewa zancena gaskiya ne, babu abinda zaka iya ganewa indai bangaren makaranta ne" Daga ranar hatta Malaman shi mamaki sukeyi, irin yanda lokaci daya ya canza haka. Har kaguwa yayi lokacin jarabawa yayi dan ya kawowa Abbu, aikam na biyu yazo a ajin nasu lokacin. Da kan shi yazo ya nunawa Abbu, karba yayi batare daya nuna wani jin dadi a fuskar shi ba "Dan kayi wannan baya nufin za'a dore" Shine kalaman Abbu, sune kuma kalaman shi a duk lokacin da zai kawo mishi wani abu daya danganci kokarin da yayi a makaranta. Tunda ko hira baya zama suyi, idan hirar shi tayi tsayi da wani to Bilal ne. Yanzun ma makaranta zasu tafi, harya gama shiryawa tsaf, amman Bilal ko wanka bai fito ba. Takalman shi ya dauko yana fitowa bakin kofa ya ajiye, silipas din da yake ajiye ya zira ma kafafuwan shi da nufin ya shiga bangaren Ayya ya dauko musu ruwa. Shi kayan sanyi ba damun shi sukayi ba, bama yaso sam, da an kawo pure water yake zuwa ya sungomo leda daya yazo dakin su ya ajiye. Ya duba ya kare shisa ya fito. Yana karyo kwana suna cin karo da Layla da tsayin shi bai hana idanuwanta sauka cikin nashi ba "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un..." Ya furta da karfi, zuciyar shi na wani irin dokawa, bayason ganin yarinyar sam, sai yaga kamar mage ce ta gitta mishi, yanzun ma ko ina na jikin shi bari yakeyi, har zuciyar shi. "Ina kwana" Ta furta a hankali, duk da tasan ba amsawa zaiyi ba, zuwa yanzun da zata iya hana kanta gaishe da Rayyan ko shiga sabgar shi da ta daina. Amman duk abinda zata shirya ma kanta da ta sauke idanuwanta kan Rayyan din komai yake kwance mata. Kallonta yayi ran shi a bala'in bace "Dan ubanki ban hanaki zuwa inda nake ba? Mayya ce ke? Sau nawa zan gaya miki idan ina waje ki daina zuwa?" Rayyan ya furta har lokacin zuciyar shi bata daina dokawa ba. Wasu irin hawayen bakin ciki Layla taji sun taru a cikin idanuwan ta, bashi bane mutum na farko daya kirata da "Mayya" ba, ba kuma shi bane zai zama na karshe, ko Ayya takan fada wasu lokuttan, su kadai ne suke fada a cikin gidan gabaki daya. A waje kuwa da wahalar gaske ka furta kalmar bata fasa maka baki ba, ta karfi da yaji ta zama mafadaciya ta gaske. Kullum saiya mata kashedin zuwa inda yake, amman a haka yake aikenta, a haka yakan sakata aiki, tana iya dawowa daga aiken shi ya hauta da masifar ta daina zuwa inda yake kamar bashi ya kirata ba. Har mamakin shi takeyi, sai kace mai jinnu. Bata zabi zuwa duniya da kalar idanuwanta ba, asalima idan da an bata zabi zata dauki irin na kowa, bata kuma zabi fitowa daga jikin mahafiyar ta ba, balle a dinga alakanta su da Maita, kalma mafi ciwo a duniyarta gabaki daya. "Hanya ce, kuma kowa wucewa yakeyi Hamma..." Layla ta fadi itama nata ran a bace "Rashin kunya zakiyi mun?" Rayyan ya bukata yana sata kallon shi da idanuwanta da bayaso, tana kara hautsina mishi lissafi, ita kadai ce ta raina shi haka duk gidan, ita kadai ce take kallon shi kamar bata tsoron shi, take kallon shi kamar shi din bai isa ba "Idan nace ba rashin kunya nai maka ba zaka yarda ne?" Tayi tambayar tana sake tsare shi da manyan idanuwanta, kamar da take mishi da mage na kara bayyana, baisan lokacin daya dauketa da wani irin mari ba. Kafin ta wartsake ya kara dora mata wani duk a kunci daya. Ba marin shi bane ba ta saba sha ba, kawai a lokutta irin haka sai ta rantse da Allah a duniya babu wanda ya tsaneta sama da Rayyan, kullum kuma neman dalilin tsanar takeyi ta rasa. "Matsa daga nan kafin in tattakaki, wawiya kawai" Rayyan ya karasa maganar da wani irin tsaki, yana saka hannu ya tunkudeta harta kusan faduwa tukunna ya wuce. Gabaki daya ta hargitsa mishi lissafi, da yasan zai ganta, sam ba zai fito ba, ruwan daya hakura saiya dawo makaranta sai ya dauka. Abbu yagani, ran shi a bace yake ko magana bai mishi ba ya raba zai wuce "Rayyan gaisuwar ma ba zan samu ba kenan yau ko?" Baice komai ba ya shige abin shi, kai kawai Abbu ya jinjina. Da gaske ne jarabawa ta rayuwa takan zo ma bawa ta fanni daban-daban. Inda wani ya bashi labari tashi jarabawar zata so ta bangaren Rayyan ne ba zai taba yarda ba. Yana tuna kalar shakuwar shi da yaran a lokacin da yake dan karamin shi. Sai da ya dauka a cikin yaran shi gabaki daya mazan babu wanda zasu shaku dashi kamar shi da Haris, lokaci daya Rayyan ya sauya kamar wanda jinnu suka shafa. Yanzun Rayyan ne zai nuna sam bayason magana da shi, zai karya idan yace abin baya mishi ciwo, yana kula da yanda idan ya nuna yana son abu to Rayyan din yaki abin kenan, kamar a duniya yana rayuwa ne dan ya bakanta mishi. Karatun shi ma sai da dabarar da Yaya Ayuba ya bashine da yai amfani da ita tukunna ya samu kan shi. Shisa ko da wasa yaki nuna mishi yana jin dadin yanda yake maida hankali. Yanzun ma ya kula sam ya daina jin ya Rayyan din yake ciki a makaranta. Ko wani abin akace su siya saidai Bilal yazo ya fada mishi. Bai cika tashi tsayuwar dare ba, amman matsalar Rayyan tasa dare dai-dai ne baya tashi dan kawai yayi mishi addu'ar samun salama. Zuciyar da yake da ita tafi komai dagama Abbu a hankali, zuwa yanzun ko sallama akayi dashi a unguwa yasan ba zai wuce an kawo karar Rayyan din ba. Ko lokacin samartaka fada bai taba hadashi da wani ba, ammam sai gashi zuwan shi police station takwas duk akan Rayyan. Kuma ba yan waje kawai ya tsaya ba har cikin gida babu mai rabar shi, kusan kullum sai yayi ban hakuri cikin gidan akan Rayyan. Yama daina mishi fada, nasiha ce wasu lokuttan, wasu lokuttan kuwa sai dai yabi shi da addu'a kawai, yanzun ma "Allah ya shirya" Ya fadi yana wucewa. Rayyan kuwa dakin Ayya ya shiga, idan kasan gidan su a baya, kazo yanzun zakayi mamakin yanda aka gyara ginin yayi dai-dai da zamani, saboda rufin asiri dai-dai misali Abbu yana da shi. Ya taka matakin Professor kamar yanda burin shi yake, ga kasuwancin shi da Allah yake saka mishi albarka saboda shi mutum ne mai yawan taimako da kyautatawa iyalan shi. Shisa sam baya kukan rashi, rayuwa sukeyi mai natsuwa. Duk da tsayin shekaru bai canza zaman da yake tsakanin Maimuna da duka yaran suke kira da Ayya sai kuma Maryama da suke kira da Mami. "Rukayya babu ruwa ne a dakin?" Rayyan daya shiga kitchen ya duba bai gani ba ya fito falon yake tambaya. Da saurinta ta mike, har ranta tana kaunar Yayan nata, haka ma sauran yan uwan nasu, amman baya shiga cikin su, baya shiga sabgogin su, zatayi karya idan tace batajin kishin Bilal wani lokacin, saboda kusancin da yake tsakanin shi da Rayyan din. Ayya ba fada takeyi ba, amman sunsan cewa ba daga jikinta Bilal ya fito ba, saboda ko a makaranta da asalin sunan Baban shi yake amfani. Sai take ganin kamar ya kamata ace sunfi shi kusanci da Rayyan din. Fridge taje ta duba tana dauko mishi leda daya na ruwa ta fito ta kawo, tun kafin ya karba yace "Ba mai sanyi ba Rukayya... Bana son ruwa mai sanyi" Kai tadan rausayar, bai shiga cikin su bama balle su san me yake so ko meye baya so. "Hamma duk an saka a fridge... Sai dai ko idan zaka ajiye ya huce..." Karbar ruwan yazo yi "Kabari in kai maka daki" Kai ya girgiza yana karba "Zaka karya in hada maka tea?" Kai ya sake girgiza mata, saboda ya fara jin maganar da sukeyi tayi mishi tsayi. Bayason kananun surutai marassa dalili "Ko zaka ci wani abin" Daga idanuwan shi yayi yana mata wani irin kallo daya sata komawa ta zauna. Kusanci take nema a tsakanin su ko yayane, kamar ko da yaushe bai bata wannan damar ba, zai fita daga dakin kenan Ayya ta fito daga dakin baccin ta "Rayyan..." Ta kira tana saka shi runtsa idanuwan shi kafin ya budw su a hankali "Ayya ina kwana..." Ya fadi yana dan juyawa "Kaci gidan ku... Daka shigo bakasan inda nake ba halan?" Kai ya jinjina "Ayya....ruwa kawai na zo dauka, ban san kin tashi ba kuma" Kallon shi kawai tayi, tasan karya yake, da bata fito ba sam ba zaije su gaisa ba. Idan zaiyi yini biyu bai sakata a idanuwan shi ba baya damuwa, Bilal ne idan shigowa goma zaiyi gidan saiya zo ya nemota, wani lokacin sai taga kamar yana son rage mata damuwar Rayyan ne, musamman idan yasan Rayyan din yayi wani laifi. Haka zai wuni yana lallabata kamar shi yayi mata wani abu. Kuma da gaske yana rage mata damuwa ba kadan ba. "Allah ya shirya mun kai" Cewar Ayya, Rayyan na ficewa daga dakin. Kan shi tsaye dakin su ya wuce ya ajiye ruwan. Dai-dai shigowar Bilal "Yaushe zaka daina cin zalin yarinyar can ne? Kai baka duba maraicin ta?" Dan fitowa yayi yaga Layla na tsaye tana hawaye, ga yatsun Rayyan kwance a kan fuskarta. Bai tambayeta me ya faru ba, hakuri kawai ya bata dan yasan a gidan babu wanda zai daketa idan ba Rayyan din ba. Duk idan kaga hawaye a idanuwanta to shine. "Karka kara batamun rai Bilal..." Rayyan ya fadi, shiru Bilal din yayi ya kyale shi. Idan ma surutu yayi yana iya kara jama Layla wani dukan. Duk saurin hannun Rayyan saika shiga harkar shi tukunna. Amman banda Layla, da alama ko numfashi tayi kusa dashi laifine. Har mamaki Bilal yakeyi, kuma ko aike Rayyan din zaiyi, gashi tunda yasan idan ya aike shi ba zaiki zuwa ba, takanas zai leka ya kira wani yaro cikin gidan ya bashi kudin yace a kai Layla ta siyo mishi, kuma da wahala aiken ya kare da dadi, dan sai ya nemi wani dalilin da zai daketa. Kuma na rana daya bata taba kin zuwa aiken shi ba, duk wasu kananun ayyukan shi ita din yake sakawa. Shirin makaranta ya karasa suna fita tare da Rayyan din, su duka sabon sune sai sunje makaranta suke karyawa. Gara Rayyan ya siyi biscuit a hanya "Hamma kai da biscuit" Bilal ya fadi yana dariya. Ba zaka taba raba aljihun Rayyan da biscuit ba, ko jakar makarantar shi ka duba zaka samu, kuma bayason mai zaki. Haka zai ta daukar abin shi dai-dai yana ci. Babu wanda baisan amanar da take tsakanin shi da biscuit ba, har Abbu wasu lokuttan yakan siyo sai ya baiwa Bilal din yace yaba Rayyan. Yanajin wani iri duk lokacin da Abbu ko Ayya zasu kyautatawa Rayyan din sai abin ya biyo ta hannun shi. Sai yake jin kamar suma zasuji ya kwace musu kusancin daya kamata ace yana tsakanin su da dan nasu. "An hana ci ne?" Kai Bilal ya girgiza mishi "Kaima idan kana ci kasa hannu, ban hanaka ba ai" Kai dai Bilal din ya sake girgizawa, shi bama komai yake ci ba. Babur suka tare suna hawa su biyun zuwa makaranta daya kamar yanda suka saba. * Bilal bai bude ledar da Aisha ta bashi ba sai da yazo gida. Harya natsu ma, duk gidan shi da Bilal ne suka fara makaranta daya daga firamari har yanzun suke sakandire a ALIC. Kuma yasan Aisha tun tana firamari, yana mata magana ne saboda tana mishi yanayi da Layla, daga rawar kanta har idan tayi dariya. Idan alewa yagani zai siya yakan siyi guda biyu ya bata daya. Aji dayane a tsakanin su, yanzun yana aji hudu ita kuma tana aji uku, kusan duk wanda yake ALIC yasan Aisha da Bilal. Danma shi wani lokacin yana tare da Rayyan, ita kuma tsoron Rayyan take ji, ba ita kadai bace, kusan duk wani wanda yake cikin makarantar tsoron Rayyan din yake ji. Garama Aisha saboda Bilal yana dan mata magana wasu lokuttan. Amman idan baka ganshi da Rayyan ba zaka gan shi da Aisha. Wata irin shakuwa ce mai karfi a tsakanin su, zuwa yanzun har yan gidansu sun san Bilal, musamman wani lokaci da tayi rashin lafiya ta kwanta asibiti, yaje yafi sau biyar, hatta da Baban Aisha sai da yasan shi a lokacin. Da yake yana da wani irin shiga rai, haka cikin kankanin lokaci ya shiga ransu suma. Har wata Yayar Aisha din ta dinga tsokanar shi "Bilal din Aisha..." Murmushi ya dingayi saboda kunyar da ta dinga sakawa yanaji. Yanzun ma bude ledar yayi, biskit ne kala-kala da cin-cin, a cewarta bikin abokin wasanta akayi. Kayan bikin ne ta kawo mishi. Bayason kayan zaki haka, kawai dan Aisha ce shisa ya dauki cin-cin daya ya saka a bakin shi. Baiji shigowar Rayyan ba sai hannun shi da yagani cikin ledar yana daukar biskit guda biyu "Kai ba zakai sallama ba" Waje Rayyan ya samu ya zauna, kamar baiji maganar da Bilal din yayi ba "Ina ka samo biskit kai kuma?" Murmushi Bilal yayi "Aisha ce sukayi biki, shine ta kawo mun" Kai Rayyan ya jinjina "Yara kanana daku wai soyayya. Allah ya shirya" Yanayin yanda Rayyan din yai maganar ne ya ba Bilal dariya. Zaka rantse da Allah wata shekara goma ya bawa Bilal din ba daya da doriya ba "Waye yace maka soyayya mukeyi?" Tabe baki Rayyan yayi "Zan fadama Ayya su fara shiri, ba zakai karatu ba, gara Abbu ya kaika kasuwa kawai a aurar da kai...ka kawo biskit din nan ko guda biyu a kai ma Ayya dan ta ga abinda surukarta ta bayar..." Dariya Bilal din ya sakeyi yana fadin "Hamma..." Dariyar shima Rayyan yakeyi "Jibi yanda idanuwanka suka cika da kunya. Bilal... Allah ya shiryeka to" Biskit daya Bilal ya dauka yana jifan Rayyan din da yake dariya dashi. Bai cika magana ba, amman randa duk ya saka shi gaba da tsokana sai ya rasa bakin ramawa. Musamman yanzun akan Aisha yafi samun damar tsokanar shi da yawa haka. Ko Rayyan din aka tsare ba zaice ga asalin yanda soyayya take ba balle kuma shi. Kawai yanajin Aisha har ran shine, baisan ko haka soyayya take ba, amman yasan ko dariya tayi sai ya ga kamar Layla, idan tana mishi surutunta ma, kominta yana mishi kamar Layla. Zai rantse lokutta da yawa har idanuwan Layla yake gani a cikin nata. Shi dai yasan Layla ce dalilin kusancin shi da Aisha, Layla ce sanadin fara maganar shi da Aisha, idan akwai wani abu bayan wannan baisan shi ba. Saboda duka gidan Layla ce kawai take kula da ran shi ya baci, kowa kawai dauka yake ran Bilal baya baci, ba'awa Bilal laifi, ba zai manta ranar da tace mishi "Hamma na rana daya ka nuna ranka ya baci, ka daina bari a cikin ka" Murmushin da yakan yi ko da ranshi a bace yake shi yai mata "Waye yace miki raina ya baci" Dariya tayi "Murmushin ka baya kaiwa cikin idanuwanka. Idan kayi murmushi ko kayi dariya harda idanuwan ka kakeyi, idan ranka ya baci idanuwanka basa dariya... Bansan ya zan maka bayani ka gane ba" Numfashi kawai ya sauke "Me yasa ba zaka fadama Hamma Rayyan ya bata maka rai ba?" Kai kawai ya jinjina mata. Kuma tun daga ranar ko a haduwa sukayi tai mishi magana yanayin murmushi zata ce "Waya bata ma Hamma Bilal rai?" Ita kadai take ganewa, kuma ita kadai yakan fadama ran shi ya baci wani lokacin. Ayya damuwar Rayyan kawai ta isheta, shisa baya taba nuna yana cikin matsala, ko rashin lafiya saiya kwanta sosai da sosai ake ganewa. Sai yayi ciwo a tsaye ya warke babu wanda yasani sai Layla. Yanzun ma mikewa yayi yana ficewa daga dakin, wata irin yunwa yake ji, bangaren Mami zashi yaga ko ta dafa wani abin da yake ci, tuwo Ayya tayi miyar taushe, bayason dafaffiyar albasa, ko a dafaduka aka saka saiya tsince tas yake iya cin abincin. Yanzun tunda Rayyan ya zuba yaga tayi yawan da baisan ya zaiyi ya tsince ba, shisa ya hakura ya fito kawai. Bai karasa bangaren Mami da yake lallabawa kar Ayya tagan shi ba, yasan bataso yana cin abincin Mami din, amman zuwa yanzun sai dai ta bishi da ido kawai, tunda taga ba zata iya hana shi ba, shine abu guda daya da Bilal ya taba gardama mata a kai, ta hana shi yaki hanuwa, amman kome zatace yayi baya taba nuna mata bayaso ko a fuskar shi kuwa. Layla yaci karo da ita "Hamma..." Ta furta da fara'a a fuskarta "Me kuka dafa Layla?" Bilal ya tambaya "Wake da shinkafa ne, akwai miya. Amman yayyanka kayan miyar Mami tayi, bari ingani dai..." Ta furta tana juyawa ta koma ciki, ta kai mintina kusan goma kafin ta fito da filet a hannunta da abinci harda cokali a ciki. "Na ciccire albasar, amman saika duba akwai kadan a ciki..." Karba yayi yana murmushi "Ni nace bana cin albasa?" Dariya Layla tayi "Ba saika fada ba, kana barin shi a plate din abincinka da yawa...." Wannan karin shi yayi dariyar "Ke kam Allah ya shiryeki" Yanajin dariyarta harya wuce, tun a hanya ya fara cin abincin saboda yunwar da yakeji, harya karasa daki "Kai ba zaka daina cin abincin matar can ba, Ayya ta hana, sai an barbada maka abu tukunna ko?" Saida Bilal ya hadiye abincin da yake bakin shi tukunna yace "Abu nawa Ayya ta hanaka baka daina ba? Kuma kasan zato babu kyau ko a addini..." Cewar Bilal din yana kara cakuda abincin hadi da diba ya saka a bakin shi "Ni daban, kai daban, bana so kana cin abincin ta, amman ba zaka jini ba" Shiru yayi ya kyale Rayyan din, idan wannan maganar ce sun saba, Ayya tagaji, shi dinne ya kasa hakura har yanzun. Duk cikin karatun duniya da ake mishi babu wanda ya rike da kyau irin cewa Mami zata barbada mishi abu yaci. Abincin shi yaci gaba daci kan shi a tsaye, yana ganin Rayyan din ya mike ya dauko uniform din shi da safa "Wanki zakayi?" Kai Rayyan ya girgiza "Me yasa zan wanke, Layla zata wanke mun" Yanda yayi maganar zaka rantse da Allah Layla din yar aiki ce a gidan ba 'ya ba. "Layla baiwar kace? Me yasa kaci ka takurama yarinyar nan ne wai?" Kallon shi Rayyan yayi "Me yasa ita bata damu ba sai kai?" Kai kawai Bilal ya jinjina, yana kallon Rayyan din ya fita. Ba shiga bangaren Mami yakeyi ba, idan ba wani yaron zai daka ya ruga ya shiga bangaren nata ba, itama sam bata shiga harkar shi tunda rashin kunya yake mata kamar zai daketa. "Layla!" Ya kira, itama sai lokacin da ta zubama Bilal abinci ta samu ta zuba nata, tana zaune da remote a hannunta da ta kasa tsayawa waje daya taji ya kwala mata kira "Rayyan ne ko?" Mami ta tambaya, duk da muryar su shida Bilal din ba ko yaushe ake banbance taba, amman tasan idan Bilal ne zai shiga har ciki, ba zai tsaya daga bakin kofa yana kwala ma Layla kira haka ba. Cokalinta ta mayar cikin abincin tana mikewa, marin da yayi mata yau da safe ta fadama kanta tana zaune zai zo nemanta, zatayi banza da shi, haka ma tacewa Mami data shiga tana kuka "Ina zaune zai kirani, kinsan Allah Mami ba zanje ba nima, kowa yayi harkar shi" Murmushi kawai Mami tayi, ita yanzun ta daina tsoma bakinta a tsakanin su. Tun tasowar Layla idan Rayyan din yai mata wani duka har ranta Mami take ji, tayi fada da Ayya yafi a kirga kan cin zalin Layla da Rayyan yakeyi. Sau biyu ta taba kaiwa Abbu kara, duka lokutta biyun kuma tana shan kunya, dan ko muryar Rayyan din Layla taji da gudu take fita, sai ta dauki ido kawai ta saka musu. Yanzun zata shigo tana kuka shabe-shabe, tana fadar yanda ita da Rayyan sun raba hanya, sai ya aiko kiranta ta ajiye koma meye takeyi ta tafi. Kamar yanzun da ta ajiye abinci, jikinta har kyarma yakeyi ta fita "Ki wanke mun" Ya fadi yana ajiye uniform din a kasa "Yanzun idan na gama cin abinci" Kallonta yayi "Idan ba zaki wanke mun ba ki fadamun, tun dazun bakici abincin ba sai yanzun?" Kayan ta tattara tana turo labbanta gaba, ta wuce ta koma ciki, tana jin tsakin da Rayyan din yayi. Sai da ya dafe kirjin shi duk da yayi kokarin ganin bai hada idanuwan da ita ba, amman sai da taja zuciyar shi ta doka. Ita kuwa cikin daki ta shiga "Ni fa zan taimaka in wanke mishi Mami, amman shine wai ba zan gama cin abincina ba, zaiyi fushi ya dauka" Murmushi kawai Mami tayi tana kallon Layla harta wuce da wankin tana kuma cigaba da mita. "Allah ya kyautata kaddarar da take tsakanin ku Layla. Allah ya kare maraicin ki" Shine addu'ar da Mami take bin ta da ita a lokutta irin haka. Har tsoro takeji idan taga sunyi wani abin ita da Rayyan. Ko yara batajin suna cewa Hamma Rayyan ya basu abu, amman wani lokacin zakaga Layla da abu kuma tace shi ya bata. Har kudi a cikin aljihun makarantar shi duk idan ya bata wanki "Ki mayar mishi da kudin shi" Mami kance idan ta nuna mata ta tsinta, amman sau biyu ta gwada tana shan maruka, yana fada mata yanda bayaso tana zuwa kusa da shi "Hamma zai sauke Jujun shi a kaina Mami" Ta bawa Bilal kuma sau biyu shima ya mayar mishi, saiya Bilal din ya dawo mata dasu yace mata ca yayi ta rike, yana sane yake bari, ba zai bata da hannun shi bane ba. Ba kuma zai bude baki yace ta dauka ba. Shisa har a ranta Mami tana tsoron kaddarar da take tsakanin Layla da Rayyan din. Bata da wanda zata furtawa ne kawai, tunda ita ba wasu kawaye gareta ba, sirrinta yana cikinta, gara ta zanta damuwarta da Haris da ta fadawa wani can. Shikuma yanzun ya sami gurbin karatu a Zaria, duk da yakan yi kokarin zuwa wani lokacin duk karshen wata, idan karatu yayi tsanani kuma sai yakai wata uku ma bata saka shi a idanuwanta ba. Tana nan zaune, sai da Layla ta gama wankin tukunna ta dawo ta zauna tana daukar abincin "Har abincina yayi sanyi" Ta furta cikin yanayin mitarta "Ki dumama" Cewar Mami, kai kawai ta girgiza "Nifa bama na son wanki, Mami kinsan bana son wanki, shine Hamma yake sakani" Murmushi kawai Mami tayi, indan Layla ce ba gajiya takeyi da mita ba musamman akan Rayyan. Haka ta gama cin abincin tana mitar ta tashi ta wuce kitchen, kwanonin ba yawa garesu ba, ta daifi so ta wanke, sam batason aiki a kanta. Duk da akwai miya da yawa, Mami tace ko taliya sai a kara dafawa, gara tayi wanke-wanken saita fi jin dadin zama tayi kallonta a nutse.  * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:06 PM - 111: Nov 11, 2020 06 "Abbu...Sannu da zuwa" Huda da take zaune a cikin falon ta fadi cike da farin cikin ganin shi, idan kaga yanayin autar ta Ayya zaka rantse tayi satika bata ga Abbun ba, a maimakon kwanaki hudu "Huda" Cewar Ahmadi yana dorawa da "Ke kadai? Duk ina kowa? Ina Ayyar ku?" Da murmushi a fuskar Huda har lokacin tace "Kowa yana daki, Ayya tana sallar isha'i" Numfashi Ahmadi ya sauke, a gajiye yake jin shi, ko dan tun da suka isa Abuja bawai sun zauna waje daya bane ba, hidimar da ta kaisu kawai sukeyi "Ma shaa Allah, Ke kinyi sallar dai ko?" Kai ta jinjina mishi "Tun dazun ma... Hamma Bilal ne daya shigo sai yace inje inyi" Wannan karin Ahmadi ne yayi murmushi "Madallah da Hamma Bilal...bari inzo kafin ta idar" Ya karasa maganar yana ficewa daga dakin. Kan shi tsaye bangaren Maryama ya nufa, ita da Jabir ya samu zaune a falon suna cin abinci. Jabir suna gaisawa ya dauki filet din shi yana ficewa "Sannu da dawowa...kayi zuru-zuru" Maryama tai maganar cike da kulawa, yar dariya Ahmadi yayi "Yanzun nan? Ko dan ba zama mukayi waje daya ba, kinsan ni da nayi zirga-zirga sai fuskata ta nuna" Murmushi tayi "Hutu ne yai maka yawa" Ta karasa maganar da sigar tsokana tana mikewa, tana jin dariyar da yakeyi. Ruwa taje ta kawo mishi, bata ma gwada mishi tayin abinci ba tunda girkin Maimuna ne, tasan ko yana so ba zai taba ci ba. Wani lokacin ita kadai takan yi tunanin ko duka maza haka suke da adalci irin Ahmadi, sosai yake duk wani kokarin shi na ganin yayi adalci a tsakanin ta da Maimunar "Ya kuke? Fatan dai kowa lafiyar shi kalau... Na shiga in duba yaran a daku nan su dana shigo, ina jin basu dawo daga sallar isha'i ba" Kallon shi takeyi "Anya kuwa? An idar da sallah, sai dai ko in sun tsaya wajen abokai ana hira. Duka lafiyar su kalau. Alhamdulillah" Kai ya jinjina "Alhamdulillah, ina Layla?" Murmushin ta Maryama ta fadada "Fushi take mun dan na mata fada kan saka kananun kaya" Dariya yayi "Layla manya... Yaran ne basajin magana, ni da ina yaro abinda za ayi mun magana ma bana farawa, idan akayi sau daya kam bazan bari a maimaita ba..." Numfashi Maryama ta sauke, zata ce duk wani abu da ta saka Layla tanayi, bangaren aiki kuwa in ba tana makarantar boko ko ta islamiyya ba cokali bata bari ta daga. Girki tun tana koya mata har yanzun babu wani abu da bata iya girkawa ba. Tana da rigima, sosai tana da rikici, amman idan ba tabata kayi ba babu ruwanta da kai, ga fadanta baya rabuwa da wuri saboda mita da take da ita, kusan Maryama zatace duka yaranta sun biyo sanyin hali irin nata, kau da kai da sanin ya kamata irin na baban su. Jabir ne ma bashi da hakuri idan ka tabo shi. Sai Layla tayi wani abin sannan take tuna cewa ba daga jikinta yarinyar ta fito ba. Matsalar da suka cika samu da Layla bai wuce yanda a rayuwarta take bala'in son kananun kaya ba, idan zata wuni da dogon wando da yar riga yafi mata dadi, gara ma ranakun asabar da Ahmadi ya ware yana zama a gida. Shine zaka ga tana yini yawo da hijabi, kamar duk gidan shi kadai ne take jin nauyi ko shakka kar yai mata magana. Amman da yan shekarunta ko atamfa ce skirt din sai tace a sha mata shi, ga kirar jiki da Allah yayi mata, wasu lokuttan Maryama kan jinjina kalar jikin da Layla take da shi, shisa take tsoron shigar da takeyi. Bataso, amman da duk rana da take kokarin ganin ta rabata da kananun kaya, da ta daina sai mata, kudinta duk idan ta tara akwai gidan su Farida, nan cikin unguwa, islamiyyar su daya da Layla din, kuma ajin su daya, sana'ar gwanjo mahaifin Farida yakeyi, dila-dila yake kawowa daga kwatano, hakan yasa matar kan bude itama tana siyarwa cikin gida. Sai dai Maryama taga Layla ta shigo da abinta, duk yawancin kudadenta yanzun a can suke karewa, kuma sukan mata saukin kayan saboda sanayya. Idan ma tayi mata fada sosai, kwana biyu tana saka atamfa haka zakaga dakyar take motsawa saboda matsewar siket din da yake jikinta. Zatayi karya idan tace abin baya damun ta, sai ta tuna zancen da mutane kanyi na cewar "Dan riko wahalar sha'ani gare shi" Wasu ma sukan ce "Maraya akwai wahalar riko" Duka biyun take gani akan Layla wasu lokuttan, amman duk wani abu da zaifi karfinta da addu'a take hada shi, Laylar ma addu'a takeyi mata, saboda girma take karayi, halittarta ta 'ya mace na kara fitowa, shisa yanzun Maryama ta numfasa kawai tana fadin "Allah dai ya shirya mana, yaran yanzun magana har sai bakin ka yayi tsini" Mikewa Ahmadi yayi "Amin thumma amin. Abinda yafi tsini kam bakin ka zaiyi. Idan sun shigo nasan zangan su..." Ya fadi yana dorawa da yi mata sallama, daman lafiyarta da ta yaran ya shiga dubawa kamar yanda ya saba ko aiki ya dawo, balle kuma tafiyar kwanaki hudu. Yayi kewar su ba kadan ba. Yana fita dakin Maimuna ya wuce, inda ya sameta ta fito falon tana zaune, yanayin fuskarta yake kallo, girma bai hana shi gane rigimar da take shimfide a kan fuskar ba "Uwargidan Ahmadi..." Kallon shi tayi tana kauda kai, tunda ta fito daga daki Huda ta fada mata ya shigo ya fita take kallon agogo, mintina sha ukun sai take ganin su kamar awanni sha ukku dan tasan yana wajen Maryama ne. Wani irin tuquqin kishi da shekaru basuyi komai wajen rage mata ba take jin yana taso mata "Magana fa nake yi..." Sake kallon shi tayi "Ai na dauka a can zaka kwana" Yanayin yanda tayi maganar ne yasa shi dariya "Hmm..." Ta furta, ba yau ya saba mayar da ita mahaukaciya ba daman "Yi hakuri... Na shigo kina sallah, shine nace bari inje mu gaisa kafin ki idar" Cike da rigima take kallon shi "Ko dawafi nakeyi ai kasan na idar tun dazun dai. Sai kayi zaman ka kunata labari, kuma tunda girkina ne, kwana hudu bangan ka ba, ya kamata ace ka bari na fara sakaka a idanuwana tukunna kaje duk inda zakaje" Murmushi Ahmadi yakeyi, zuwa yanzun indai rikicinta ya saba da shi "Ba za'a kara ba Uwargida. Kiyi hakuri..." Numfashi ta sauke "An dawo lafiya?" Ta fadi ciki-ciki har lokacin, sai da ya tabbatar ya jata da hira ta daina amsa shi dai-dai tukunna ya mike "Da kaci abinci dai sai kayi wankan" Kai ya girgiza mata "Bari dai in watsa ruwan, kafin in fito kin hadamun abincin..." Ahmadi ya karasa maganar yana soma tafiya. Mikewa tayi itama, so yayi ya wuce bangaren shi, amman yana son ganin su Rayyan, haka kawai ya kasa hakura, musamman da yasan in ba a hanya ya hadu da Rayyan din ba, ba zaije yayi mishi sannu da zuwa ba. Kowa zaije amman banda shi, yaso ya tambayi lafiyar yaran daya bayan daya, amman yana gudun jin ance Rayyan din yayi wani abu bayan tafiyar shi, Allah ne shaida da shi yake kwana a ran shi, da shi yake kuma tashi. Ko waya tayi kara sai gaban shi ya fadi, sai yayi zaton ko Rayyan ne ya dauko wata maganar da yayi nisa da gida. Akan Rayyan ne yasan cewa zai yiwu ka haifi da ka dinga jin zuciyarka na rawa duk sanda zaka gan shi, yanzun da yake nufar dakin su Rayyan din sai yaga kamar yayi mishi nisa. "Oh Allah..." Ahmadi ya furta jin yanda zuciyar shi ke rawa "Allah idan jarabta ce ka kadarta mu ta fado akan Rayyan, Allah ka bani karfin zuciyar daukar ta. Allah na yafe mishi duk wani laifi daya taba mun, wanda na tuna da wanda na manta. Rabbi ka shiryamun yarona, Kai ka bani amanar shi, kai ka sakamun kaunar shi, Allah karka sa ya zama rauni na" Shine addu'ar da ya tsinci kan shi da yi, duk da ya kasa samun natsuwa, musamman daya tinkari dakin yaji wani irin wari da tashin hankali bai barshi fahimtar ko na meye ba farat daya, sai da ya kara kusantar dakin sannan ya gane warin sigari ne, badan cutarwar da takeyi ba, cutarwar da yagani da idanuwan shi akan abokin aikin su da bature ne dan kasar amurka, haka da wahala ka ganshi batare da sigari ba, kullum cikin buka ma cikin shi hayaqi yake, lokaci daya ya fara wani irin tari daya kwantar da shi, kafin ace kansar huhu ce tayi mishi muguwar illa a sanadin taba. Ko sanda sukaje asibiti duba shi kafin a mayar da shi kasar shi inda ya mutu a can, yanda yake kokawa da numfashin shi Ahmadi zaiso duk wani mashayin sigari ace yana dakin asibitin dan yaga tashin hankali da illar da sigari takeyi ko zai yarda ya daina cutar da kan shi. Shi ko warin ma idan yaji sai zuciyar shi ta dinga tashi, tana daya daga cikin abubuwan da yaki jini "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un..." Ya furta a fili yana kasa kwankwasa kofar dakin jin warin sigarin da zuciyar shi taki taya kwakwalwar shi karyata cewa ba daga cikin dakin su Rayyan warin sigarin yake kara fitowa ba. Wani irin bacin raine da yake shirin danne firgicin da yake ciki ya saka shi tura dakin batare da sallama ba, haske ne gauraye da dakin saboda akwai wutar lantarki. Rayyan na zaune akan kujera ya dora hannayen shi kan teburin da yake gaban shi, Bilal na tsaye, inda ya juyo saboda turo kofar da su duka suka ji anyi "Abbu..." Bilal ya kira da wani irin yanayi da yafi tashin hankali a muryar shi, Ahmadi kuwa kallon su yake, dan yanzun ya kara tabbatar da cewa daga dakin su warin sigarin yake fitowa. Tunda gashi nan cike da shi "Sigari, Rayyan sigari kake sha yanzun kuma?" Cewar Ahmadi da wani irin bacin rai da disappointment na gaske tattare da muryar shi, yanayin da ya saka Bilal fadin "Ba shi bane Abbu, ba Hamma bane" Da wani yanayi Ahmadi yake kallon Bilal, Rayyan kuwa yana zaune inda yake, ko motsi baiyi ba balle wani yai tunanin zai tanka, asalima idan ka shigo dakin zaka rantse da Allah abinda yake faruwa bai shafe shi ba, wani ma zai iya cewa bai taba sanin Bilal din da Ahmadi ba ballantana yabi takan abinda suke tattunawa "Kar kaimun karya Bilal, warin sigari tun daga wajen dakin nan anaji, karka ce mun daga kofar gida ya taso ya zabi ya tattaru cikin dakin ku" Kai Bilal ya girgiza "Ba ina nufin ba'a sha sigari bane, ina nufin ba Hamma ya sha ba" Duk da alamu sun nuna Ahmadi bai gama yarda da zantukan Bilal din ba, amman akwai wani hope daya cika idanuwan shi, da gaske so yake ko yane a karyata mishi zargin shi. Abin zai mishi yawa idan ya zamana Rayyan dinne. "Bilal..." Ahmadi ya kira cike da kashedi, sauran karshen sigarin daya rage Bilal ya dago hannun shi yana nunawa Ahmadi da fadin "Ba shi bane Abbu, ni ne" Ya karasa maganar muryar shi na fitowa can kasan makoshi "Bilal" Wannan karin da mamaki Ahmadi yai maganar, badan baya ganin samari sa'annin su Bilal da wanda ma basu kaisu ba da shan abinda yafi sigari, sai dan haline da ko a mugun mafarki bai hango Bilal din dayi ba "Sigari Bilal? Ina kuke so in saka raina, kamar Rayyan bai ishi sakani juyi duk dare ba, sai ka fara kaima ko? Hawan jini kuke son ganin na samu? Kun kyauta mun kenan yanzun? Um? Bilal ka kyauta mun?" Kan shi Bilal ya sadda kasa, yanajin wani abu na taso mishi tun daga dan yatsan kafar shi har zuwa kirjin shi inda yai mishi karan tsaye a zuciyar shi. "Allah ya kyauta" Ahmadi ya fadi yana juyawa ya fice daga dakin, zuciyar shi zafi takeyi, duk da wani bangare na zuciyar shi da yake jin kamar bai kyauta mishi ba wajen jin dadi da ba Rayyan bane ya sha sigarin, a lokaci daya wani abu da baiyi tunani bane yaji ya karya a zuciyar shi, kamar Bilal ya karya yardar da yayi mishi ne. Saboda ko a cikin mutane yakan yi alfahari da halayen Haris da Bilal, yakan ce zai shaidi yaran nashi su biyu akan komai. Idan shima yace zai fara rashin jin nan baisan inda zai saka kan shi ba. Da yawan mutanen da suke zagaye da shi kanyi zaton hakurin da yake da shine raunin shi, yana mamaki yanda mutane suke daukar hakuri a matsayin rauni. Sam hakuri ko da yayi yawa baya taba zama rauni, idan baka da karfin zuciya ba zaka iya hakuri akan lamurra da yawa ba, sai juriyarka ta kai wani mataki ne zaka iya kauda kai akan wasu abubuwan. Hakurin shi ne karfin zuciyar shi, yaran shi sune raunin shi, yaran shi sune cikon farin cikin shi, tunda ya same su duk inda zai juya da tunanin su manne da zuciyar shi. Kaddara ce ta bashi Layla da Bilal, duk da jinin shi na yawo cikin nasu, amman basu da gadon shi, shisa a duk cikin yaran Bilal ne kadai ya taba siyan fili da sunan shi, takardun na ajiye ko Maimuna bata san da shi ba, yana jin yaran inda yake jin su Haris. Da gaske yake wani abu ya karye a zuciyar shi, baisan wani zazzabin tashin hankali ya rufe shi ba saida ya watsa ma jikin shi ruwa yaji tsikar jikin nashi na mimmiqewa da alamun wani sanyi da yake ratsa shi. Ko da Maimuna ta shigo yayi duk wani kokarin shi na ganin bata karanci damuwar da yake tattare da ita ba, abincin da ta kawo haka ya dinga saka shi a baki yana taunawa yana hadiyewa, lomar da yaji ta kakare a makoshin shi sai ya bita da ruwa. Da tayi magana kan canjin yanayin shi ca yayi mata "A gajiye nake jina Maimuna, kamar gajiya ke son saka mun zazzabi" Da ta bashi maganin zazzabi bai musa mata ba ya karba yana hadiya tunda da gaske yanajin zazzabin. Sai dai barawon bacci ma kasa samu yayi duk da ya raya daren ne da salloli yana rokama yaran nashi karin shirya, addu'ar tashi na yawaita akan Bilal, Rayyan da kuma Layla. Saboda yanda yake jin kamar duk wata kaddara da zata same shi ta bangaren yaran da wahala ta wuce kan su ukkun, tunda su kadai ne suke caja mishi kai har haka. * Tunda Ahmadi ya fice daga dakin babu wanda ya motsa a cikin su har lokacin, Bilal jin shi yake kamar iskar da yake shaka bata kaiwa cikin shi, kamar iskar dakin gabaki dayanta tayi mishi kadan, hakan ne yasa shi takawa yaje inda makunnin fankar dakin take yana kure gudunta gabaki daya. Tsaye yayi a wajen yana sauke numfashi cikin son yaji ya koma mishi yanda yake da kafin maganganun Abbu. Sai dai me, yana juyawa yaji komai ya jagule mishi, ganin Rayyan ya dauko zaro kwalin sigarin shi daga cikin aljihu yana zaro lighter din shi, ya bude kwalin ya zaro kara daya ya saka a bakin shi yana riketa a tsakanin labban shi, kafin yayi ma karshen sigarin rumfa da hannun shi ya kunna wutar lighter din gudun kar iskar fankar ta hure mishi "Hamma..." Bilal ya kira da duk wani bacin rai da zai iya dorawa a kan muryar shi. Satika ukku da suka wuce yana kwance Rayyan din ya shigo dakin, sai da gaban shi ya fadin jin warin sigarin da yake yi "Hamma warin sigari kakeyi, daga ina kake?" Shine tambayar da yayi wa Rayyan din yana mikewa zaune babu shiri, da wani yanayi a fuskar Rayyan din yace "Da gaske? Warin kaji a jikina?" Kai Bilal ya daga mishi yana tabbatar mishi, baice komai ba ya taka inda suke ajiye turarukan su ya dauki daya yana fesa ma jikin shi, hadi da dan daga hannayen shi yana shakar iskar ko zaiji warin sigarin da Bilal yace yaji yanayi "Yanzun fa?" Ya bukata, yana saka Bilal din binshi da wani irin kallo "Daga ina kake? Me yasa kake warin sigari?" Kujera Rayyan yaja ya zauna batare da yace komai ba, hakan yakan yi duk idan Bilal yayi mishi tambayar da yasan idan ya amsa mishi ita zai sake bude mishi kofar jifan shi da wasu sababbin tambayoyin ne. Daga waje yake, kuma yana warin sigari ne saboda ya sha, idan ya amsa Bilal zai fara tambayar shi dalilin da ya saka shi shan sigari, kuma shi da kan shi baisani ba, wucewa yazo yi yaga wasu gungun samari anan kasan layin su sun taru suna ta sha, baisan meye dayan abin ba, sigarin kawai ya iya ganewa, kuma haka kawai yaji a duniya babu wani abu da yake son yi banda ya sha sigari. Shagon da yaje siye sai da mutumin ya tambaye shi har sau biyu idan sigari yake son siye "Malam idan babu ne ka fadamun in tafi" Rayyan ya fadi maimakon amsa tambayar da mai shagon yayi mishi "Akwai, wacce iri?" Cewar mai shagon da wani yanayi a muryar shi "Ni dai kabani kowacce iri" Hakan kuwa ya siyi sigarin da sai bayan an bashi ita da lighter din daya siya yabar shagon tukunna ya duba kwalin yana ganin an rubuta aspen a jiki. Zuqar farko da yayi wani irin tarine ya sarqe shi kamar zai shide, amman yana gama dawowa ya sake gwadawa, har ya sha kara biyu bai gane dalilin da yasa mutane suke sha ba, banda bakin shi, da makoshin shi da yaji suna wani qauri-qauri, kirjin shi a cike yake fal da hayaqi. Daga ranar ne kullum idan ya fita sai ya busa yakai kara biyar, har zuwa yanzun ba zaice ga dadin sigari ba, ba zaice ga dalilin shi na sha ba, abu daya zai iya shaidawa, yanda idan yaji yana son sha din jikin shi har wani iri yake yi mishi. Ya gane dalilin da yasa ake cewa sigari na da wahalar barin sha, duk sanda zai sha a waje zai saka minti a bakin shi dan ya daina warinta, amman shekaranjiya har Ayya sai da tace "Ni kam bansan inda hancina yake dibomun warin sigari ba" Sanda ya shiga ya dauki abinci, hakan yasa shi yana shiga daki ya sake kayan jikin shi yana kuma watsa ruwa. Bilal a satika ukkun bai gaji da tambayar shi ba, shikuma bai daina yi mishi shiru ba, har sai jiya da yaji yana son ya sha, amman bayason fita daga gida kuma, saboda zaune yake yana zane, yanzun daya zana jarabawar shi ta gama sakandire yana zaune jiran sakamako ya fito, yakan tsinci kan shi da jin kadaici na rashin abinyi. Musamman idan Bilal yana makaranta, shisa zanen ne kawai abinda yake debe mishi kewa, ba abokai yake dasu ba ko a cikin unguwa ballantana yace zai fita suyi hira. Idan yagaji da zama a daki yakan fito ko zai ga giccin Layla, haka zai ta mata aiken rashin dalili har saita kosa ta mayar mishi da magana yaga yasa ta kuka tukunna, to jiyan sam bai ganta ba, sanda ya aika a kirata ance mishi kanta yake ciwo ta sha magani ta kwanta. Zai iya cewa harda son ya ganta da yakeyi, ya duba yaga ya jikinta da kuma kin son ganinta da ya hade mishi waje daya ya kara mishi son busa hayakin, ko ba komai zai kalli yanda ya gwanance yake fitar da samfur samfur na hayakin cikin satika kadan haka. Ya zuqa sosai yana fito da hayakin Bilal ya shigo, bai ma gama ba ya koma mishi ciki yana saka shi fara tari "Hamma..." Bilal ya fadi da bayanannen tashin hankali yana karasawa inda Rayyan din yake hadi da mika hannu zai karbe sigarin, Rayyan ya janye hannun shi yana fadin "Meye haka? Ka daina yi kamar baka san ina sha ba" Ya san yana sha, tun ranar farko da yaji warinta a jikin shi, da yana da abokai ne ma sai yayi zargin wani daga cikin sune yake shan sigarin suka zauna waje daya har jikin shi ya dibo warin hayakinta, amman Rayyan ne, bashi da zuciyar hakuri da mutane har suyi sabon zama abokai, koya kaso jurewa shine zaiyi fada da kai ya daina maka magana. "A waje kake sha, me yasa zaka fara a cikin gida? Me yasa? Idan Ayya ta gani fa? Idan Abbu yagani me zaka ce?" Sake kai sigarin shi Rayyan yayi a bakin shi yana zuqa hadi da fitar da hayakin "Dan Allah, dan girman Allah ka kashe, idan dole ya zame maka sai kasha, kayi a waje, kar kabari Ayya ko Abbu sugani... Ni dai na roke ka" Bilal din ya fadi kamar zaiyi kuka, idan har zuciyar shi na zafi akan wannan sabuwar dabi'ar da Rayyan ya kwaso musu, baisan me Ayya da Abbu zasuji ba, maimakon halayen Rayyan din su gyaru, kullum kara watsewa suke kamar ba'a mishi addu'ar shiriya "Hamma..." Bilal ya kira yana kallon yanda Rayyan din yake cigaba da busa tabar shi kamar bada shi yake magana ba. Idan yayi wani abin Layla tace "Jujun ne ya motsa" Sai abin yaba Bilal dariya, amman yanzun da gaske ya fara yarda da maganarta, Rayyan ba zai rasa almatsutsai ba, in ba haka ba, kana zaune lafiya ba zaka tattago abinda zai saka ran kowa da yake kusa da kai ya baci ba. Tsaye yayi har sai da ya gama shanye sigarin, dan yasan idan gidan Radio zai bude a wajen saboda surutu Rayyan ba zai kula shi ba. Karshen da ya ajiye kan tebir Bilal ya dauka ya saka a aljihun shi "Ka rufa mun asiri, ka boyeta inda wani ba zai gani ba" Daukar kwalin Rayyan yayi yana sakawa cikin aljihun wandon shi. Yana sake gyara zama a cikin kujerar da yake zaune, yana kallon Bilal din ya dinga feshe dakin da turaruka. To yau ma da yayi sallar isha'i a waje ya tsaya suna zancen wasan kwallon kafa da matasan unguwa shisa bai shigo gida da wuri ba, ganin lokaci na jira, kuma yasan Ayya na can tana tunanin dalilin da yasa har lokacin bai shiga ya dauki abincin ba yasa shi yi musu sallama ya shigo gida. Yayi niyyar wucewa bangaren Ayya kai tsaye, sai kuma yaji yana son shiga bayi, shisa ya nufi dakin su, inda ya sami Rayyan zaune yana shan sigarin shi kamar yana abin kirki. Fada yakeyi kamar zai ari baki, ya karasa ya kwace karshen sigarin kenan ya kasheta jikin tebirin da yake ajiye ya sake bude baki zaiyi magana Abbu ya shigo. Tun tasowar su akwai kananun laifuka da Rayyan din zaiyi ya dauke mishi su, zuwa yanzun kuma ko a aiko Rayyan ya kira shi bai fada mishi ba, zai ce ya fada shine ya manta baije kiran ba, irin kananun abubuwa haka da zai iya dauka na laifukan Rayyan duk yanayo. Shisa yau sam karyar cewa shi yake shan sigarin batayi wahalar fitowa daga bakin shi ba sam. Musamman da yaga abinda yake cikin idanuwan Abbu, yanda ya nuna ba zai iya jure wata gurbatacciyar halayya daga bangaren Rayyan din ba. Sai dai maganganun shi sun daga hankalin Bilal fiye da yanda yayi zato, ya dauka maganganun sun taba zuciyar Rayyan, sai yanzun da yake kallon shi ya sake kunna sigarin shi kamar komai bai faru ba, kamar Abbu bai fadi abinda ya fada ba "Anya akwai hankali a tattare da kai kuwa Hamma? Ko zuciya ce kai ba'a halliceka da ita ba, da gaske sigarin kake kara kunnawa? Baka ga halin da Abbu ya fita a ciki bane halan? Baka ga me kasa nayi ba?" Karan sigarin Rayyan ya cire daga bakin shi, saboda baiga dalilin da zaisa Bilal ya tsare shi yana mishi fada kamar kanin shi ba "Me nasa kayi?" Ya bukata yana tsare Bilal din da idanuwa, dariyar takaici mai sauti ce ta kwacewa Bilal din "Tambayata kakeyi? Hamma tambayata kakeyi?" Yana kallon yanda kowa a gida yake fadin ba'a batawa Bilal rai, jinsu kawai yake, ko suce Bilal na da hakuri, Bilal baya fada, Bilal baya fushi, suna magana kamar a duniya babu wanda yake da halaye nagartattu kamar Bilal, bayan rana bata fitowa ta fadi baiga kalar rashin hakurin Bilal ba, baya saukewa akan kowane sai shi, yanzun ma ga bacin rai nan bayyane a fuskar shi "Ka daina girmamani kana kirana Hamma, kana kuma hadawa da ihu a karshen zancen ka" Karasawa Bilal yayi inda Rayyan din yake yasa hannu ya dauki kwalin sigarin da ya ajiye da lighter din, hannu Rayyan ya dago, kallon da Bilal yayi mishi yana saka shi mayar da hannun "Woo... Allah ya baka hakuri" Rayyan ya fadi yana dariya ganin yanda ran Bilal din ya baci da gaske, shikuma a cikin abinda ya faru duka baiga wani abu na bacin rai ba, sigari ce ya fara sha baisan dalili ba, yanzun kuma bashi da wani dalilin dainawa. Shi baice Abbu yaji haushi dan ya sha sigari ba, baice Bilal ya dauki laifin da ba na shi ba, yana kallon shi tun tasowar su yana hakan, so yake yanda bai taba tambayar shi dalili ba, shima ya daina tambayar shi dalili akan abubuwa irin haka. Yana kallo Bilal ya fice daga dakin, mikewa yayi yana shiga wanka abin shi, idan Bilal ya gama fushin ya huce zai neme shi ya sani. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:06 PM - 111: Nov 14, 2020 07 Bai fara dana sanin neman gurbin karatu a jami'ar Ahmadu Bello da take garin Zaria ba sai da ya samu. Bai san sa'a bace ko kuma matakan su daya tsallake ko kuma sanayya ta manyan mutane da Abbu yayi ta saka shi samun abinda ya nema. Kawai dai yasan ya fara dana sani ne daga jiya da Haris ya dawo har dakin su ya shigo da sallamar shi yana zaune, maganar shi ta farko bayan sun gaisa ita ce "Abbu yake fadamun ka samu gurbin karatu a makarantar mu, shine ko ka kira ka sanar dani. Naji dadi wallahi, saboda duk bangaren lafiya dai ne" Tsayawa yayi yana kallon Haris da yake magana kamar ya fada mishi ya zabi karantar fannin daya danganci kwakwalwa da sanin halayyar dan Adam wato Psychology saboda ya kasance waje daya da shi. Ya zabi fannin ne saboda yana son fahimtar wasu daga cikin halayen shi, wasu cikin tarin tambayoyin da yake tunanin bangaren zai amsa mishi akan kan shi, badan wani dalili ba. Kuma ko ba komai kaunar da yake ma uniform zai kasance yana saka farar rigar nan lokaci zuwa lokaci. Saka uniform ne abu daya da yayi kewa bayan gama sakandire din shi. Haka kawai sai yaga duk kayan da zai saka ba zasu kai yanda yake saka uniform yin kyau ba. Wani lokaci can baya kaunar da yake ma uniform ta saka shi tunanin aikin soja, sai dai har kasan zuciyar shi yaji haka kawai ba zai iya nisa da gida ba, kuma bayason takurar da take tattare da aikin, yana da taurin kan da yake da tabbacin zai wahala a aikin. Zuciyar shi ba tada sanyin da zata lankwasu yayi biyayyar da yaji ana labarin yiwa manya. Shisa bai kara barin tunanin ya dame shi ba, kafin ya yanke hukuncin zabar fannin da ya zaba yanzun, yayi tunani kala-kala, ayyuka barkatai sun zo ran shi. Sai dai zuciyar shi tafi rinjaye akan Psychology din ne. Haris din kuma yana bangaren lafiyar yara ne wato Pediatric.  Ba shiga harkar kowa yake ba a gidan banda Bilal, anso hada su daki daya. Tashin hankalin da ya dinga yine yasa su Abbu suka bar su shida Bilal a daki daya. Lokacin da yaji labarin bangaren da Haris ya samu gurbin karatu da Bilal kawai yayi zancen "Hamma zaiyi kyau da likitan yara...ko a gidan nan ka kalli yanda su Intisar ke son shi. Ko masallaci muka fito ba zaka rasa ganin shi rike da wani yaron ba" Murmushi Bilal yayi "Duk yaushe ka kula da Haris haka?" Harar Bilal yayi "Dan bana shiga harkar kowa baya nufin bana kula da abinda yake faruwa" Jinjina kai Bilal yayi "Naga alama ai, ko Ayya zancen da tayi mun kenan. Sanyin halin shi ne yasa yara suke manne da shi, ga kyauta kuma, ba zaka raba aljihun shi da dan biskit ko alawa ba" Rayyan kwanciya ya gyara yana yin shiru, surutun Bilal ya cigaba da yi har saida ya kule "Wai bacci kayi ko wulakanci ne yasa kayi banza ka kyaleni ina ta zuba ni kadai?" Ba baccin da yakeyi, ya lumshe idanuwan shine, yana jin shi, a duka zancen shi babu wanda zai bada amsa, a wajen shi hirar ta rigada ta kare, ya fadi abinda yake son fada. Duk da yaso hirar tayi tsayi sai Bilal din ya kunna shi da maganar da yayi kan yaushe yake kula da halayen Haris. Yana so ya mayar da shi kamar baisan abinda yakeyi ba. Shisa sam mutanen da yake ji a ran shi basu da wani yawa, saboda halayen su na saurin cakar da shi. Jiyan ma kallon Haris ya dinga yi, har ya gama surutun da zaiyi. Ganin ba amsa shi zai ba yasa ya tashi ya fita daga dakin. Yanayin fuskar shi ma ya bala'in bata ma Rayyan din rai, saboda haka kawai ba gayyato shi yayi ba, baice ya shigo daki ya same shi ba. Da suka gaisa bai sashi zama ya fara mishi hirar rashin dalili ba, yazo yasa yanajin kamar yayi mishi laifi. A fuska ya nuna baiji dadin shirun da yayi ba. "Tsalle kake so inyi mu rungume juna saboda zamu kasance a makaranta daya ko me?" Rayyan din ya furta cikin sigar mita yana karasa maganar da jan tsaki. Yana da dalilai da yawa da yasa baya shiga harkar kowa. To yau ma yana haduwa da Haris din yake tambayar yaushe yake da niyyar zuwa ya fara hada-hadar registration "Ko zamu tafi tare gobe ne?" Kai ya girgiza mishi, da alamar kosawa a muryar shi yace "Zan taho da kaina Hamma..." Dan jim Haris din yayi, yana son duka yan uwan shi, ba su kadai ba, shi mutum ne na mutane. Wasu lokuttan Rayyan na saka shi son tambayar shi ko ya taba mishi wani abune da bai sani ba shisa yake karayin kicin-kicin da fuskar shi duk idan sun hadu. Shi bayaso ya bata ran kowa sam-sam, ko wani yagani cikin bacin rai yakan yi kokarin ganin yaja shi da raha har saiya murmusa. Tun tasowar su abu kadan Rayyan bai taba duba cewa ya bashi shekaru kusan ukku ba, haka zai kama shi da jibga kamar ganga. Da suka fara hankali kuma baya magana da shi, in zasuyi haduwa goma idan bai mishi magana ba zai rabe gefe kamar bayason wani abu ya hadasu. Ranakun duk da Rayyan ya fara mishi magana to na farko ba zai manta ba, rashin lafiya yayi harya kwanta asibiti, da sukaje duba shi yayi mishi ya jiki, amman yana iya yin jinya. Rayyan din ya shiga dakinsu da sunan duba shi, bayan sallama zai iya mintina goma a tsaye ya jingina bayan shi da bangon dakin, har sai in shi ya gaji da jin shirun yai yawa yace "Rayyan..." Sannan fa zai amsa da "Ya jikin ka?" Bayan ya amsa wannan da wahalar gaske ya kara cewa wani abin zai juya ya fita daga dakin. Wani lokacin yana ganin Rayyan din yayiwa sauran mutanen gidan haka. Amman shi Haris wani irin mutum ne mai son kulawa. Bai saba a share shi ba, ko waje ya shiga kirkin shi na sawa kaga mutane zagaye da shi, kowa na son kula shi, kowa na mishi fara'a banda Rayyan. Bai gajiya ba, cikin sanyin murya yace "Registration din su da dan wahala Rayyan, da mun tafi tare sai in tayaka, kaga ba sanin kan makarantar kayi ba" Kallon shi Rayyan din yake yi, gabaki daya surutun ya ishe shi, tsayuwar da yayi ma ya gaji da ita "Zan taho idan na shirya..." Yanayin yanda yai maganar yasa Haris din jinjina kai kawai "Allah ya bada iko ya taimaka..." Ya fadi, ko amin din a zuci Rayyan ya fadeta ya raba Haris din yana wucewa daki. Ya guji jami'ar bayero saboda Abbu da tarin abokan shi da yake da tabbacin ba za'a rasa a duk wani fanni da zai nemi gurbin karatu ba. Duk da Abbu din yana bangaren lissafine. Amman yana da matsayi a makarantar da ko da mu'amala bata hadaka da shi ba, yasan kasan sunan shi, kasan kuma ko waye shi. Baya bukatar wannan attention din na mutane, da ma ace Abbu zai shiru da bakin shi, yanda yake alfahari dasu ba zai barshi yaki nuna cewa shi din ba nashi bane ba. Kowa zai dauki ido ya saka mishi, wasu da yawa zasu dinga tsammanin gaisuwa daga wajen shi a duk haduwar da zasuyi. Ba zai iya wannan rayuwar ba. Yanzun ya tsallaka Zaria ma, Haris yasa shi harya fara dana sani. Dadin shi daya kawai, Bilal yace shima nan din zai nema "Na dauka Bayero kake so, saboda ka burge Abbu" Kai kawai Bilal din ya jinjina yana furta "Kana da matsala" Ya fita ya kyale shi. Har ran shi daman yaso ya roki Bilal din daya zo ABU shima, tunda har ya hango yanda zaiyi rayuwa a makarantar shi kadai. Tunda yana da yakinin ba zaiyi aboki ko daya ba, watakila sai dai iya gaisuwar cikin aji idan ta zama dole. Yana lissafin yanda da wahala ya iya hada satika hudu cikakku bai shigo Kano ba, har kasan zuciyar shi yake jin yanda zaiyi kewar Bilal din "Har da Layla" Wani bangare na zuciyar shi ya fadi a lokacin, zai kewar ganin ya sakata kuka. Yana da wannan tabbacin, amman bayajin tana cikin dalilin da zai sashi zarya tsakanin Kano da Zaria duk bayan wasu yan kwanaki. Sai bayan da Bilal yace zaije Zaria. Sai yaji son yazo duk bayan wasu kwanaki sunki fita daga kan shi, ya fadama kan shine zai dinga zuwan ne kafin Bilal ya sami gurbin karatu. Idan ya samu kuwa watakila sai hutun karshen zango na watanni shidda. Yunwa yake ji, ko abincin rana baici ba, yasan da gangan Bilal yaki shigowa dakin. Saboda sunyi fada da rana, shine dalilin da yasa ma Rayyan ko yunwa baiji ba, ran shine ya baci. Bilal yafi kowa sanin yanda yake da saurin hawa haka yake da saurin sauka, amman sai suyi fada wani lokacin shi ya gama fushin Bilal yana mishi fisge-fisge. Daya shigo zai zubo musu abinci su dukan su, da Ayya na aiko musu da shi, Bilal ya koyi kinibibin zuwa ya zubo. Sai Ayya ta daina turowa a fada musu ta ma gama abinci ko da suna jin yunwa in bata bayar an kawo ba. Tunda idan aikowa tayi zai saka dan aiken ya karbo mishi. Abinda bai sani ba shine Ayya ta daina ne saboda shi, saboda wannan yunwar ce kawai dalilin da yake saka shi shiga bangaren ta wani lokaci harta gan shi, tana iya aikawa a kira shi a dawo ace mata an kwankwasa dakin shiru, idan Bilal yana nan kuma yace a shiga, an shiga an same shi yana bacci. Idan ya tashi kuma ko an fada mishi ba zuwa yake ba wasu lokuttan, sai ta taka har dakin da kanta ta mishi tas, shima sai dai yaita kallon ta ko yace "Ni na manta ne Ayya" Shisa take kyale su, wanda duk yunwa ta dama yasan inda zaije ya dibi abinci. Tashi yayi yana saka takalman shi da suke bakin kofa ta cikin dakin yana ficewa. Ya karya kwana kenan da nufin shiga bangaren Ayya ya hango Layla. Sai da zuciyar shi ta doka "Subhanallah..." Ya furta kasan makoshin shi, tana karasowa ta zabi ta sauke idanuwanta cikin nashi. Duk fadin wajen sai a cikin nashi idanuwan ne zata nemawa nata masauki "Mayya..." Ya fadi yana kallon yanda ta kara ware mishi idanuwan "Me yasa ba zanzo waje ba sai kinsan yanda kikayi kika biyoni?" Kallon shi takeyi, duk ranar bata saka shi a idanuwanta ba, asalima tun jiya da rana rabonta da shi. Har rigar shi daya bata guga ta shiga taje ta kai mishi baya nan. Islamiyya da zata fitane da kuma kashedin da yayi mata na da yamma zai saka rigar yasa ta bude dakin ta ajiye mishi rigar. Da ta bari ya dawo ta gan shi tukunna. Tana da mukullin dakin su, da hannun shi wata rana ya kama hannunta ya saka a ciki "Idan ya bace saina karya ki Layla" To wani lokacin yakan sa ta share musu dakin, ko idan ya aiketa yace ta kai mishi daki. Duk da idan tayi shara sai ya maimaita, wata rana ma bayan ta gama zai kai mata duka ya karbi tsintsiyar "Kina mace baki iya share waje da kyau ba, fita kafin in kwada miki mari..." Dalilin ya daketa kawai yakan nema tasani, shisa yake sakata shara, ko son ya wahalar da ita, tunda sai ya maimaita, da wanki ma idan ya bata tana kawowa ya jujjuya zai nade rigar ko wandon ya lafta mata "Haka ake wanke kaya? Banda maita zuwa duk inda nake me kika iya a rayuwar ki?" Yakan sata ta dibo ruwa a bokiti ya kara tsoma kayan ya wanke, ya bata ta shanya, wata rana ma tana tsaye tana kukan dukan da yai mata. Yanzun ne ma zata wanke mishi kaya wata ran baya ko duba hannuwan, wuyan rigar da wajen aljihun. Yake karba ya ajiye. Ta dai rasa dalilin da duk wahalar da take sha a hannun Rayyan haka kawai wani lokacin idan ta dauki wasu awanni bata ganshi ba sai taji tana son ganin shi. Da ta ganshin kuma zai fita daga ranta, saboda sai ya fada mata maganar da zataji tayi dana sanin son ganin nashi. Har lekowa tayi dazun, bata gan shi ba ta koma, sau biyun da aka leko akayi mata magana a daki sai da taji gabanta ya fadi, tana mikewa da sauri zaton ta shine ya aiko a kirata, sai taji wani abu kamar dissapointment a lokutta biyun da kiran ya kasance ba daga shi bane ba. Yanzun ma shanya uniform dinta da ta wanke ta fito yi a igiyar dake bayan bangaren nasu, tana sane ta zagayo ta nan, da fatan ko zata ganshi a ranta, saboda tun dazun take tunanin ko bashi da lafiya, ko wani ya bata mishi rai shisa yayi shiru da yawa haka. Tana hango shi wani murmushi ya kwace mata, murmushin da tayi kokarin boyewa daga kan fuskarta, murmushin daya dishe gabaki daya bayan kalmar shi ta "Mayya..." Da ya jefeta da ita. Badan bai saba fada ba, itace ta kasa sabawa har yanzun, sosai kalmar take mata zafi, musamman idan daga bakin shi ta fito, tana jin maganar da take son mayar mishi na mata kaikayi akan harshe. Amman sai ta zabi yau da taqi biye mishi. Ta juya kenan yace "Layla..." Kowa idan zai kira sunanta sai taji kamar Laila yake fadi da harafin "i" maimakon harafin "y" da take amfani da shi. Rayyan ne kawai yake kiran sunan ta yanda take jin tana furta shi a bakinta. Hatta Mami bata kiran sunanta yanda take so, yana ba harafin "y" din da yake ciki hakkinsa, tun tana mita tana gyarama sauran yan gida da mutane yanda take so a fadi sunanta harta gaji ta kyale su. "Sam idan kana tare da yan gargajiya ba zasu barka yin gayu yanda ya kamata ba" Shine abinda take fadama kanta a ko da yaushe. Ko maganar kananun kaya Mami tayi mata sai wannan tunanin yazo ranta. Ita Mami yar gargajiya ce, tunaninta yaki tafiya da zamani, taki gane cewa yanda sukayi tasu rayuwar daban da yanda ta yanzun take. Zabinta ne taci gaba da gudanar da rayuwa kamar zamanin da, amman ita kam tana jin ya kamata a kyaleta ta tafi a zamanance. Ko kallone ba zaka rabata da fina-finan amurka ba. Saboda yanayin 'yan cinsu yayi mata. Yanda suke gudanar da rayuwar su tayi mata. Shisa take da wani irin buri nayin zurfi a karatu, zatayi wayewar da babu wanda zai kuskura ya alakantata da maita, zata zama tana zagaye da wayayyun mutane da idanuwanta ba zasu saka su fadin komai ba sai yanda suke jin daman ace suma sun sami idanuwa irin nata suma. Wayayyu da zasu fuskanci cewa maita bata da wani yare, asalima a musulunci bata da tushe. Ta tambayi duk wani Malami da yake a islamiyyar su ana tabbatar mata da maita bata da tushe a addini, kambun bakane kawai musulunci yai magana a kai. Ta rasa dalilin da yasa ake hada yaren nufawa na mahaifiyarta ana fadin duk yawancin su mayu ne. Mami kan jaddada mata da cewa mahaifiyar ta ba mayya bace duk idan ta shiga da kuka wani lokacin kan Rayyan ya kirata da mayya. Yanzun kam yanda ya kira sunanta yasa taji zuciyarta ta wani kumbura ta cika kirjinta taf, har murmushi tayi, gabaki daya ya wanke bacin ran da ya sakata yan dakika da suka wuce. Bata juyo bane sai ma tafiya da ta fara yi, hannun taji ya riko yana juyo da ita da karfin da yasa ta fadin "Hamma hannu na" Gyara rikon da yayi ma hannun nata yayi yana murdawa sai da taji idanuwanta sun tara hawaye "Dan Allah kayi hakuri" Ta furta cikin rawar murya, idanuwanta kan rage bashi tsoro idan suka cika da ruwan hawaye haka, sai yaga sun kara sake mishi launi, sakin hannunta yayi, yana kallon yanda ta yarfe shi tana murzawa. Bude baki yayi zai magana, Maimuna da ta leqo ta gansu a tsaye tana saka shi mayar da bakin shi ya rufe "Ina wuni..." Layla ta furta tana kokarin mayar da hawayen da suke cike da idanuwanta bayan ta, wata irin harara Maimuna ta zabga mata, kamar surutai taji, kuma sai muryar tayi mata kamar ta Rayyan, shisa ta leqo, sanin in dai surutun shi ya yawaita to da Bilal ne. Zaka iya kirga maganar shi, itama a fuska da yanayi zakaji yanda yake yinta kan dole. Yana iya bata maka rai kayi shiru ka kyale shi, sai da gabanta ya fadi da ta gan shi tsaye da Layla, sai taga kamar data fito yana rike da hannun Layla din, daga ranar farko da ta dora idanuwanta kan Layla bata kaunarta ko kadan, kuma ta tabbatar da Layla ta san haka. Ko tare suka shigo da su Haris sai ta koreta, itama Layla din a nata bangaren hakane, Ayya na daga cikin jerin mutanen da bata kaunar gani, da hankalinta ita ce ta farko da ta kirata da mayya. Gashi ko a hanya suka hadu cikin gidan sai ta bita da harara, tana gaishe da itane saboda Abbu, dan a yanda taki jinin Ayya ko Mami bata isa tasa ta gaisheta ba, darajar Abbu take ci, dan tana jin shi har ranta, batayi wayan sanin iyayenta ba, gara mahaifinta zata iya tuna fuskar shi, sai kuma tsillin hotunan da Mami ta samo mata nashi bayan ya rasu sanadin gajeruwar rashin lafiya. Na rana daya Abbu da Mami basu taba bari taji maraici ba, komai da take so Abbu yana mata, a fuskar shi ma bai taba nuna cewa ita din ba daga jikin shi ta fito ba. Haka dakin Maimuna banda ita da Rayyan duka suna zaune lafiya da sauran yaran, babu mai nuna mata tsana ko wariya. Gara ma Intisar wasu lokuttan takan mata magana taqi amsata. Shisa bata damu dan bata amsa gaisuwar ba yanzun, juyawa tayi zata tafi abinta, muryar Rayyan ta katse ta da fadin "Na ce na gama magana da ke?" Tsaye tayi cak, Ayya da take kallon su da mamaki bayyane a fuskarta ce tayi magana "Rayyan..." Ta kira cike da mamaki, idanuwan shi ya dauke daga kan Layla yana mayarwa kan Ayya, jin tayi shiru yasa shi cewa "Ayya" Cike da mamaki har lokacin tace "Me zatayi maka?" Dan ita batasan lokacin daya fara magana da Layla haka ba, zata tuna lokacin kuruciya da, har saida ta fara jin wani iri kan yanda Rayyan din ya addabi yar mutane, haduwa goma zasuyi sai ya kwada mata mari, akwai tabon da har yanzun yana gefen goshinta inda Rayyan din ya hankadeta ta fadi, ranar ita kanta Ayya hankalinta ya tashi, dan bayan Maryama ta dauke Layla sai da ta daki Rayyan din. Hakan ba yana nufin taji kaunar Layla ko kadan a ranta bane, yanzun da suka fara tasawa, inba Abbu ya aiko Layla ba, yarinyar bata fara shigo mata daki. Ta san dai Bilal ne da babu yanda zatayi da shi akan nacin Maryama da yakeyi, bata da matsala da yaran Maryama din, Haris ne daman, kuma shekarun nan sun sa yaran ya shiga ranta, da wahalar gaske ma kayi zaman awa daya da Haris bai shiga ranka ba. Wani lokaci anan falon ta yake cin abinci. Sauran yaran ne in dai tasan abu daga bangaren Maryama ya fito bata bari suci, Bilal ne kawai yake shigo mata da shi har daki kuma ya zauna yaci. Tama gaji da magana tunda dariya yakan yi yace "Ayya..." Da yanayin nan nashi da yakan yi duk idan tayi mishi maganar za'a barbada mishi wani abu a abincin. Kamar bai yarda yana iya faruwa ba. To tasan yana magana da Layla, ko tace Laylar ta nace mishi, kwanakin baya har zancen tayi mishi "Bilal kaima ka fara koyon taurin kai, idan nayi magana ma ba jina zakayi ba. Banason yarinyar can tana naniqe maka, kafin ta lashe maka kurwa... Ko dan Maryama ta fara lashewa, ragowa ce Layla zata samu, kaga saika hada kayan ka gabaki daya ka koma can, in rasaka hankalin su ya kwanta ita da uwar rikon ta" Dariya Bilal din yayi kamar a duk ranar babu wanda ya fadi wani abu da ya saka shi nishadi irin maganganunta "Dan ubanka sai kaje kayi ai, tunda kaga ka fini tsayi, ka rainani ai" Yana dariyar yace "Yi hakuri, haba Ayyata, ni na isa" Harar shi tayi tana wucewa abinta, haka ya bita yana mata hirar shi har saida ta huce. To batajin tana da matsala da Bilal, kowa ma kulawa yakeyi shi, kusan halin shi na mata shige da Haris, bambanci shine zakagani a fuskar Haris idan ka mishi abinda baiso ba, Bilal kam ko kayi tunanin ka bata mishi rai sai dai yayi dariya kawai. Amman Rayyan, zuciyarta rawa takeyi mata, saboda Rayyan daban ne, su Rukayya ma baya magana dasu mai nisan da taji yanayi da Layla din. Yanda ya tsare yarinyar da idanuwa yake yanzun yasa ba zuciyarta ba har kafafuwanta ma rawa taji sunayi. Tana can tana tsoron Layla karta lashe kurwar Bilal, ashe lallabowa tayi wajen Rayyan, shiru yayi yana kallonta "Tambayar ka nake kana jina" Yanda yakan yi duk idan bayason yin magana an saka shi yayi dole shi yayi da fuskar shi yanzun ma "Ina magana da ita ne Ayya..." Ya amsa, yana saka kirjinta wani irin lugude, ko ita Rayyan baya tsayawa yayi wata magana da ita. Bilal ma ta kanga yana bin Rayyan din idan yana son magana da shi. Asali yaune rana ta farko tun tasowar shi da taji yace yana magana da wani har ya tsayar dashi dan basu gama ba "Rayyan..." Ayya ta kira wannan karin da bayanannen tsoro a muryarta "Idan nagama zan shigo" Ya fadi yana dauke idanuwan shi daga kan Ayya. Hannun Layla ya kama yana fisgarta cikin yanayin da yasata binshi dole, suna barin Ayya tsaye ta saki baki cike da mamakin abinda ya faru a gaban idanuwanta. Cike da ta'ajjabin da gaske a gabanta Rayyan ya damki hannun Layla batare da tunanin abinda yayi ba dai-dai bane a tafarkin addini idan bai guji bacin ranta ba, idan ma ji yake dan in aka bibiya ta wani bangaren ya hada jini da Layla, kuma sun taso gida, ai hakan baya nufin ita din muharramar shi ce. Bayan wannan ma, yaushe Rayyan ya fara magana da Layla, yaushe ya sakata cikin jerin mutanen da yake kulawa, harma kusancin su ya kai na ya damqi hannunta ya jata subar waje kamar akwai zancen sirrin da sukeyi da bayaso ita taji. Rayyan fa, Rayyan dinta da take daukar kafafuwanta, ta karya matsayinta na mahaifiyar shi mai cikakke iko da hakki a kan shi ya taso yazo har inda take ya gaisheta, taje dakin su dan kawai ta saka shi a idanuwanta. Shine yau take ganin kusancin da tayi shekaru tana neman ta samu a tare dashi yana nunawa akan Layla, akan mayyar yarinyar da taki jinin ta wayi gari ko a tunaninta tajita, balle kuma ta saka ta a cikin idanuwan ta "Bayana kike son gani Maryama... Sakani raba Ahmadi dake bai isa ba? Kassarani kike neman yi shisa kika kawo wannan mayyar..." Ayya take fadi muryata na rawa, cikin tashin hankali kamar wadda ta samu tabin kwakwalwa. Gabaki daya hankalinta idan yayi dubu kowanne a tashe yake "Tafdin... Na rantse da Allah ba'a isa ba...ina tunanin wuta a makera ba zanji tashin ta a bayan gari ba" Duk tsoronta akan Rayyan, duk tunaninta akan halayen shi ta alakantasu ne da abinda tayi kuskure ya sha, sanadin da kawancen su da Khadi bai koma kamar da ba, saboda tayi da ita su koma wajen Malam taqi, sai tama dinke mata, sam ta daina labarta matsalolinta da ita. Gwaggo ce a lokacin kafin rasuwarta, idan ta matsa sai tace mata tana karbo taimako a wajen Malamin Khadi. To dan Rayyan ne ta dinga amso karya tambaya, da yana yaro in ta danne shi tana samu ta dura mishi, daga baya ba zai sha ba, banda abinci sai ruwan leda, ko ya tarya a fanfo, ko zobo ta hada Rayyan baya sha sam. Bata san ba abinda yasha bane yake dawainiya da shi sai yanzun, bata dauka Maryama na bibiyarta da yaranta ba har yanzun sai yau "Minna, Neja da Bidda ma ubansu yayi kadan wallahi, balle kuma wata yar banufiya da uwar rikon ta..." Cewar Ayya, bacin rai da tunanin barkatai na maye gurbin tsoronta, tana murna yaronta ya sami gurbin karatu a jami'ar da ake ji da ita a fadin Najeriya, kuma Abbu sai alfahari yake da fannin da zai karanta shine ake neman kassara shi "Wallahi da sake..." Ayya ta furta tana samu taja kafafuwanta da sukai mata mugun nauyi tana komawa daki, kanta harya fara sarawa da tashin hankalin da take tunanin ya kunno mata kai. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:07 PM - 111: Nov 14, 2020 08 Da wani yace mishi zai iya shekara daya a wani gari daban, nesa da Bilal, nesa da Layla da bai taba tunanin kewarta zata danne shi haka ba zai karyata. Dare da yawa ya sha farkawa ko shan ruwa da yakan yawan yi ko kuma wani abu daban ya tsinci kan shi da kasa komawa bacci, saboda kawai yana tunanin Layla. Yana tunanin ko tana kewar shi ko batayi, ranar da zai tafi bata neme shi ba sam, yafi mintina talatin a tsaye kofar daki yaki fitowa yana jira ko zata shigo tayi mishi sallama, amman shiru, sai da ya taka ya sameta har bangaren Mami, duk da bai shiga ba a bakin kofa ya tsaya yana kwala mata kira, ko da ta fito sai ya rasa abinda zaice mata. Lokutta da dama yakan zabi shiru saboda kalaman shi basu da yawa, baisan yanda zai fadi abinda yakeji ba, baisan me ya kamata yace mata ba, shisa ya zabi "Tafiya zanyi..." Kai ta dan daga mishi "Allah ya tsare... Zaka dinga zuwa kaman Hamma Haris?" Dan daga mata kafadu yayi, yana rasa amsar da ta dace ya bata, abubuwa ne masu tarin yawa a ran shi, ya motsa labban shi kenan ta dago idanuwanta tana saka zuciyar shi dokawa. Ya kasa sabawa da kalar su, kamar yanda ko kan hanya yaga giccin mage sai yayi da gaske ne baya zurawa da gudu. Sanin da wahala ya kara cewa komai ya sata yin murmushi "Allah ya saukeka lafiya. Banda fada da mutane" Baisan murmushi ya kwace mishi ba sai da tace "Inalillahi... Hamma...murmushi kayi ko wani abune ya fadamun a ido" Kai kawai ya girgiza wannan karin har zuciyar shi da yake ji cike da wani irin duhu a lokutta da dama yaji murmushin "Kin rainani ko?" Dariya tayi mai sauti "Ni na isa" Numfashi ya sauke mai nauyin gaske, yana kokarin kallon cikin idanuwan ta wannan karin. Ya rasa kalaman da zaiyi amfani da su wajen misalta asalin abinda yake ji. Dakyar ya iya jan kafafuwan shi ya juya yana tafiya. Sanda ya sake waiwayowa sai yaga bata nan. Abin ya mishi wani iri sosai. Yaso ace ta tsaya, yaso ace ta jira shi harya bace mata, amman batayi hakan ba. Bayan tafiyar shi yanayin yana yawan fado mishi a rai, musamman idan yayi kewarta. A cikin shekara dayan, kusan idan ba karatu bane yayi mishi zafi, duk watan duniya yana hanyar Kano, kawai ya kula da abu dayane a shekarar game da Ayya. Batason yawan zuwan da yakeyi, da ta ganshi zai ga tsoro a cikin idanuwan ta, har magana tayi mishi wani zuwa "Rayyan ba zaka natsu waje daya ba ko? Taya zaka fahimci karatu kullum kana hanya?" Cikin idanuwa ya kalleta, yaso ya fahimci dalilin canzawarta lokaci daya amman ya kasa, yawan magana na saka shi ciwon baki wasu lokuttan, kuma idan maganar tai tsayi zaiji ta fara hau mishi kai, shisa baice mata komai ba, har tayi mitar ta gama. Sai da ya mikene tukunna yace "Zan gaisheki ne daman" Yana juyawa "Allah ya shiryeka..." Shine kalamanta da yaji kafin ya fice daga dakin. Bai fasa zuwa ba, gajiyar da yayi jiya ita ta hana mishi tafiya gida, da ciwon kai na gaske ya fito daga wajen jarabawar shi ta kare shekarar farko a jami'ar. Amman a daren ya hada kayan shi yana ajiyewa, yaji dadin hakan dan yana dawowa masallaci wanka ya shiga. Lokacin da yaje babu yanda Haris baiyi dashi ba da su zauna tare a gida daya, amman yaki. Shi sun kama gidane anan Layin Kasuwa. Da Rayyan ya tashi sai ya nema a Rufasi. Gidan nasu daki shidda ne, guda daya Abbu ya biya mishi shi kadai, sanin halin shi. Banda sallama babu wani abu da yake hada shi da wani a cikin gidan, sau dayane da akace wani Emmanuel bashi da lafiya za'aje duba shi ya bisu. Acan ya barosu saboda baisan ya zai zauna ayi hirar da suke tayi da shi ba. Sunayen su ma bai sani ba, Emmanuel din saida yaje asibitin ya gane shi. Lokacin da yaje ya sami da yawansu a gidan, suke fada mishi yanda suke tsara shara da wankin bandaki, idan wannan yayi wannan ma sai yayi. Sai dai shi baya jira, shiga biyar idan zaiyi a rana, komin wankin da akayiwa bandakin saiya kara wankewa, ya sha jin suna gulmar shi "Dan sarkin masu tsaftar Rufasi da kewaye" Daya cikin su ya taba gwada tsokanar shi "Gaye sarkin tsafta..." Kallon "Yaushe muka fara wasan nan" Rayyan yayi mishi ya wuce yana barin shi a wajen batare daya samu damar karashe zancen ba, babu wanda ya sake gwada tsokanar shi a cikin su kaf, koya zakayi mishi fara'a fuskar shi bata canzawa, kullum fuskar shi a hade take, ga cikar gashin girar da yake da ita sai yasa ake kara ganin abinda turawa suke kira da "Frown" bayyane a fuskar tashi. Ko a aji an shaida Rayyan, yakan amsa tambaya idan yana cikin yanayin ko kuma wata rana yayiwa Malami. Amman idan ba kai ka fara mishi magana ba, ko kusa da shi ka zauna zaiyi tamkar bai ganka ba. Na shi miskilancin daban ne, babu wanda zaice ya taba ganin shi yana yawo da wani, shi kadai yake al'amuran shi a cikin makaranta, duk kuwa yanda wasu a aji suke son kulla abota dashi, daga gaisuwa sai kaci sa'a zaka sake fito da magana daga bakin shi. Ko fita zaiyi daga gida wani lokacin a ranshi yake furta "Allah yasa kar wanda yai mun magana yau. Bansan me yasa mutane basa gajiya da magana ba" Shisa yau ma yana gama shirin shi tsaf, ya saka wandon jeans, takalmin sneakers ne a kafar shi, sai riga baka da ta amshi farar fatar shi, sai kamshin yakeyi saboda ya yarda da turare, kuma daya fito wanka sai da ya busa sigarin shi. Bilal kance yana warin hayakinta duk idan ya sha, shisa yanzun yafi da ta'ammali da turare, kawai ya tsinci kan shi da kara shinshina jikin shi bayan ya gama shirin, jakar shi daya shirya kaya a ciki ya dauka yana fitowa, mukulli yasa ya kulle dakin, ya saka shi a aljihu kenan kamar daga sama yaji ance "Rayyan ba dai tafiya ba da sassafen nan, kana kewar gida ne da yawa haka?" Juyawa yayi yaga wanne mai karfin halinne, ya tsani magana da mutane, yafi tsanar magana da mutanen da baisani ba, idan kana so ka bata mishi rai kayi mishi magana da sassafe haka "Cikin abubuwan da aka haramta ya kamata ace akwai magana da sassafe" Ya kan fadima kan shi, kallon gayen yayi, Saminu yaji ana kiran shi, ya rike sunan ne saboda surutun shi, surutun da yasa gayen sam bai mishi ba. Idan yana daki a kwance da daddare muryar shi tafi ta kowa tashi. Lokutta da dama yasha lumshe idanuwan shi ya hasaso ya shiga dakin su Saminu da yake kusa da nashi ya kwada mishi mari. "Kamar ana korar ka?" Saminu ya sake fadi yana washe ma Rayyan din hakora kamar ya san shi. Hannu Rayyan ya mika mishi sunayin sallama, yanajin wani yarr a jikin shi saboda hannun Saminun da yake da lema alamun ya taba ruwa, kilan ma baki ya kuskure ya sakada yatsu a ciki yana wankowa. Yatsina fuska Rayyan yayi cike da kyama, yana da bala'in tsantsani, shisa ko a cikin makarantar bako ina yake cin abinci ba, yafi son soyayye kuma, ko ya siyi lemo da biskit yafi mishi natsuwa, akan ya siyi abu yaci zuciyar shi taita tashi a banza da wofi. Yanzun ma raba Saminu yayi yana ficewa daga gidan. Nufin shi ya fita harya samu acaba da zai kaishi tasha, sai ya tsinci kan shi da takawa yana cigaba da tafiya, kafin wani lokaci ya gan shi kofar gidan su Haris, bayason yaji kamar bai kyauta ba, duk da yanda kasan cuta haka yake avoiding din Haris a cikin makaranta, yana iya hango shi daga nesa ya sake hanya. Duk da Haris din yaki fushi, har aji yakan same shi idan ya kwana biyu bai ganshi ba, wata rana kuma har gidan yakan je da yar kular shi ya kai mishi abinci "Ni na dafa, duk me zan kawo maka ni na dafa..." Haris din ya fadi ranar farko daya kawo mishi abinci, baici ba saida ya tafi, ya kuma ji dadin wake da shinkafar da miyar kifi. Dan ya kwana biyu baici abinci ba a lokacin, to kusan saiya zamana idan yaci abinci ba soyayyen abu ba, to Haris ne ya kawo mishi, ko nashi rishon mai amfani da kalanzir dana wuta bai taba kunnawa ba. Ba ruwan zafi yake wanka dashi ba komin sanyin da akeyi kuwa, ba kuma girki ya iya ba balle ya dafa. Jiyan Haris ya same shi har aji yayi mishi fatan nasara da cewa "Naga yau zaku gama jarabawa... Nikam sai ranar laraba in shaa Allah" Baisan ya akayi bakin shi yayi nauyin cewa Haris zai tafi gida ba yau, daya huta yanzun. Gashi tsaye a kofar gidan yana tunanin shiga, bama shigar bace ke mishi wahala, abinda zai fada din ne tashin hankalin shi. Yana nan tsaye yayi sa'a Haris ya fito, da mamaki yake kallon Rayyan, dan bai tsammace shi ba, bayan sun gaisa ne yake fadin "Sai kayi tsaye a bakin kofa? Da ban fito ba fa? Ka shigo" Kai Rayyan ya girgiza "Zan tafi gida ne, shine na biyo" Murmushi Haris yayi, yaji dadin biyowar kuwa. Dan mutane kanyi mamaki idan yace musu Rayyan din kanin shine, duk da akwai yanayi na kamanni da zai nuna cewa akwai alaka ta jini a tsakanin su, amman halayyarsu tayi hannun riga "Ka kyauta daka biyo, nagode da zumunci. Allah ya tsare hanya. Nima in shaa Allah ranar laraba dana fito daga exam zan taho gida" Kai kawai Rayyan din ya daga mishi yana juyawa. Jakar shi ya sakewa kafada saboda ta daman ta gaji, anan ya rataya tun fitowar shi. Daga gidan su Haris din kai tsaye titi ya fita yana samun mashin zuwa tasha. Kamar ya runtsa idanuwan shi ya bude su ya ganshi a gida haka yake ji, idan ba kwakwalwar shi ce take mishi karya ba, kamar zumudin zuwa gida yaji yanayi. * Sam tunda Rayyan ya dawo hankalin ta yaki kwanciya. Baccin kirki ma bata samu tayi, gashi hutun yayi mata tsayi, daya tafi makaranta sai taji hankalinta ya kwanta sosai. Ko babu wani abu Rayyan din yayi nisa da gidan, yayi nisa da Mami da Layla. Bikin  Zubaida ma da za'ayi nan da wata biyu bai tsaya mata a rai kamar yanda take so taga Rayyan ya koma makaranta ba. Gashi yanzun yafi da yin nesa da ita, jiya badon Rukayya ba sai girkin da ta dora ya babbake, yanata qauri, sam a hanci ma bataji ba, tazo jikin window din dakin ta daga ciki ta labe tana leke. Ba karya kunnuwanta sukayi mata ba, tabbas taji muryar Rayyan din yana kiran Layla. Shisa ta labe ko zata ga fitowar ta, taga alama idan ba jan ido ta nuna akayi karamin tashin hankalin da aka kwana biyu ba'ayi irin shi a gidan ba, to Layla ba zata kyale mata yaro ba "Shegiya mayya mai zubin yan ruwa. Yarinya baki tafasa ba kina kauri. Wai yar yarinyar nan harta san ta kashewa maza murya. Kai ni Maimuna naga ikon Allah" Ta furta ita kadai, dan sambatu shine abokinta tun da Rayyan din ya dawo, kusan kullum zaka ganta manne jikin window, tun yaran na magana har sun kyaleta. Huda takan aika idan bata makaranta tace taje ta dubo mata idan Rayyan yana nan, ko ta saka mata ido idan ta gansu da Layla tazo ta gaya mata, abinka da kuruciya randa ta gansu kuwa tun a gaban shi tace "Ayya tace dana ganka da Adda Layla inje in fada mata" Da gudunta kuwa ta karasa har dakin Ayya din, inda ko mintina biyu bata hada da shiga ba Rayyan din ya rufa mata baya, tana cikin rattafowa Ayya zance, sai da ya kamo hannunta ya juyo da ita sannan ya wanketa da maruka har biyu "Karyaki zanyi idan kika sake dibo gulmata kika kawo, kina jina, karyaki zanyi wallahi" Yake fadi yana girgiza Huda da take wani irin gigitaccen kuka da ba ita kadai ta rude ba, har Ayya da ta fisgeta, babu wanda Rayyan bai daka ba a gidan, daga Khalifa da sam baya shiga sabgar shi sai kuwa tace Huda, ita kadai ma take ganin yana dan yiwa fara'a wasu lokuttan. Amman ranar saboda ta kawo zancen Layla shisa yake shirin kurmantata "Ni zaka daka Rayyan, ba ita zaka daka ba. Ka dakeni saika nuna mun ka girma kafi karfina. Tunda ni na sakata..." Ayya take fadi tanajin zuciyarta na wani irin zafi "Ayya..." Rayyan ya kira ranshi a bala'in bace, saboda gani yake shi akayiwa laifi, sam bayason gulma, yaga alama kuma Ayya da kanta take so ta koyawa Huda "Dan ubanka nace ni zaka daka, akan waccen shegiyar yarinyar ne kake neman nakasa kanwarka, kake kuma tsareni da ido" Kai yasa yana ficewa daga dakin yabarta. Ranar yanda taga dare haka taga rana, washegari sai da tayi wa Bilal zancen "Wai meye tsakanin Layla da Rayyan? Yarinyar nan duk sai ta lashe muku kurwa ko?" Da yake kansu a hade yake, dariyar shi ya dinga mata, cikin salo ya canza maganar. Sai ta hakura ta kyale shi, to yanzun Huda da take sakawa ta gano mata me yake faruwa tsoron Rayyan takeyi, ko ta aiketa idanuwanta zasu tara hawaye "Hamma zai karyani Ayya... Allah zai dakeni" Dole ta kyaleta, sauran yaran ma babu wanda zaije tasani, idan ma sunje din dawowa zasuyi suce mata basu ga komai ba. Mami ta jima tana sakata kwanan zaune, yanzun kuma ta kawo mata alaqaqai tana sakata tuna satin amarcin Mami din da kalar bakin cikin data hadiya. "Wallahi Maryama ke ba alkhairi bace a rayuwata" Ta fadi rannnan da takaici ya qumeta, harda kwallarta. Yanzun kam lissafinta yazo karshe, tunda dai gobe Rayyan din zai tarkata ya koma makaranta, itama ko na kwana talatin ne kafin fitina ta dawo dashi zata samu ta maida hankalinta kan maganar bikin Zubaida. Idan san samune ma Rayyan din yai zaman shi har sai lokacin bikin tukunna. Addu'ar da takeyi baji bagani shine Bilal ya samu gurbin karatu a jami'ar, idan suna tare da Rayyan din acan zaifi dadewa baizo gida ba. Tana kara gayawa kanta harda rashin Bilal a kusa dashi yasa ya kasa zama waje daya. To Bilal din ya fada mata cewa sunayen farko ya fito babu nashi a ciki, idan Allah ya taimaka sai jeri na biyu da suke tsammani a cikin satin tukunna. Da yake sunyi hutun islamiyya duk suna gida ranar, yaran nata ne suka rage mata tunani, dan suna zaune sunata hira harda Bilal, sai dariya suke. Daga bakin kofa ma zaka iya jiyo rakadin su, Rayyan ya shiga da sallama, yana saka wani irin shiru biyo bayan amsa sallamar tashi da sukayi, kamar basu bane suke ta hira yan dakika da suka wuce. Kamar yanda baisan taya zai fara hira dasu ba, haka suma basu san abinda ya kamata suyi a gaban shi ba. Duk kuwa tarin kaunar da suke mishi, kowa gudun yin kwakkwaran motsi yakeyi kar su bashi dalilin da zaisa ya juya, dan yana tsaye yaki karasawa "Ka shigo mana to, kayi tsaye kamar dan sanda" Cewar Bilal, yana saka har Zubaida bin shi da kallo, dan Bilal ne kadai yake da kwarin gwiwar yi ma Rayyan din magana haka, ita ma sai tayi sa'a yake gaishe da ita. Yana iya wucewa ta wuce, zata kuma yi karya idan tace hakan baya bakanta mata rai sosai. Tana shekararta ta karshe a jami'ar Bayero inda take karantar Mass Communication. Mijin da zata aura a makarantar suka hadu lokacin tana shekararta ta biyu, yanzun kuma yana aiki da gidan jaridar Rana. Dan kusan duk bangaren karatun su daya da ita, kawai shi din journalist ne. Wani lokacin har mamaki Zubaida takeyi na yanda ko kadan Rayyan bai damu da su ba. Tasan kowa abin nacin ran shi, ba dai sa tattaunawa ne, aikam karasawa Rayyan din yayi ya zauna kan hannun kujerar da Bilal yake,  a hankali Bilal din yaci gaba da jansu da hira har kowa ya saki jiki, amman da ido Rayyan yake binsu, yau dai yayi kokari tunda har saida aka kira sallar Magriba tukunna duk suka tashi. Ayya taji dadin shigar tashi, ta manta ranar karshe daya zauna ya hada mintina sha biyar cikakku a cikin dakin nata. Duka abinda basu sani ba shine maganar da Bilal yayi mishi "Kai kasan ko na zauna ni bansan me zance ba, ku bakwa gajiya da surutu" Rayyan ya fada a takura "Ko bakace komai ba idan ka zauna Ayya zataji dadi, saboda Allah ko tausayinta bakaji? Uwa uwa ce (Batul Mamman) Rayyan. Ace sai dai Ayya tazo inda kake, kai ba zakaje ka gaisheta ba idan ba yunwa ce ta koraka ba... Babu wanda zai fada maka baka kyautawa, nima dana fada maka ba lallai ka saurara ba, tunda kai babu wanda ya isa ya saka a hanya" Bai amsa Bilal din ba harya fice daga dakin. Da rana ya aiki Layla ta siyo mishi batirin tocila din shi da yake amfani da ita a makaranta, yasan zai iya siya idan yaje, kawai yana son dalilin da zai ganta ne, tunda yasan washegari zai koma makaranta, duk ranar aiken rashin dalili yake kirkira yana mata, sanyinta ne yake mishi wani iri, kamar ba Layla ba yau, harar da takan watsa mishi duk idan tagaji ba taso ta fada mishi tana kuma tunanin baya ganinta yau babu. Sosai ya dinga sakata kananun abubuwa amman sai yaganta da sanyi-sanyi, shisa da ta kawo mishi battery din yace "Menene? Me yake damun ki?" Kallon shi tayi da idanuwanta, itama ba zatace ga asalin abinda yake damunta ba, kamar zatayi zazzabi take ji, ga wani irin ciwo da takeji kasan cikinta nayi, inya tsira mata har cikin bayanta da cinyoyinta da suka rike takeji "Kawai bana jin dadine" Ta furta a sanyaye "Shine baki fadamun ba?" Cikin ido ta sake kallon shi, yanajin dadin ganin masifar da take cike da idanuwan nata "Yanzun nake ganin Layla" Ya furta a ran shi "Idan na fada maka zai hanaka aikena ne?" Numfashi ya sauke, a ranaku da ba yau ba zai bige bakinta, amman a kasan maganar da tayi yana ganin da gaske bata da lafiya. "Kai me yake damun ka?" Ta tambaya saboda yanda ya tattare girar shi yau ya wuce misali, da alama akwai abinda yake ran shi, kafadu yadan daga mata "'Hamma..." Ta kira a kagauce, inda yasan yanda takeji zai fada mata in yayi niyya koya sallameta taje ta kwanta "Ki barni ni dalla can. Bilal ne wai ina zama a dakin Ayya" Dariya tadan yi "To ka zauna mana, abune me kyau ai" Da alamun neman taimako ya kalleta wannan karin "Labari sukeyi in sun zauna. Bansan me zance ba" Numfashi ta sauke "Ka zauna kawai, ko baka ce komai ba ka zauna" Dan jim yayi kafin ya jinjina kai a hankali "In tafi shikenan?" Kallonta yayi, tayi rau-rau da idanuwa "Allah Hamma cikina na ciwo" Kallon nata dai yaci gaba dayi, a hankali ta dan daga kafarta da ta gaji da tsayuwa tana sake ajiyeta, ta daga dayar ma, yana kallon ta, so takeyi ta tafi "Hamma mana" Layla ta sake fadi kamar zatayi kuka "Haka kawai duk inda nayi kina bina, yaune zaki dameni da kina son tafiya?" Azabar ciwo ta fara damunta, da gaske yau batasan kalar ciwon nan daya addabeta ba. Ganin da yayi idanuwanta na tara hawaye yasa shi fadin "Ki kwanta in kinje, kowa ya aike ki kice nace ki kwanta. Idan na hadu dake saina dakeki" Juyawa tayi kawai ta fice. Bilal da Layla suka saka shi zuwa dakin Ayya ya zauna yau. Suna kuma dawowa sallar Magriba ba bai koma ba. Nan daki yayi zaman shi, har akayi isha'i ya sake fita, da suka dawo Bilal ne yaje ya dauko musu abinci a bangaren Ayya ya dawo, sukaci, zanen da Bilal din yaga yanayi yasa shi ficewa ya koma dakin Ayya, dan yasan ko maganar duniya zaiyi Bilal din bashi da lokacin shi. Sanda ya dawo ma kwanciya yayi yana barin shi kan takarda. Alamar bacci ma Rayyan bayaji, abinda yake kanshi yake son fitarwa, abinda yayi sati manne a kwakwalwar shi. Hoton Layla, ba wasu kaya bane a jikinta ranar, uniform din islamiyya ne da hijabin take ruwan kasa mai cizawa, tana tsaye nesa da gida kadan ita da Farida, da littafi a hannun Farida din da alama suna duba wani abune, gefen fuskarta kawai yagani, sai yayi mishi kyau sosai, yanayin ta a hakan, da ta kare mishi idanuwanta. Tun ranar hoton yake manne a cikin kanshi, kamar yana son ya fito da shi fili kafin ya bace, ya kyale shine da nufin idanuwanta su tarwatsa mishi hoton, sai dai a satin ta saka idanuwan shi cikin nata yafi a kirga, amman tana barin wajen sai hoton ya dawo mishi, shisa yau yake son fito da shi, yana da tabbacin ba zai gamu a ranar ba, amman zak fito da taswirar, sai yayi sauran aikin ko idan ya koma ne. Ko ba komai zai sami abinyi kafin kewarta ta danne shi. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:07 PM - 111: Nov 17, 2020 09 Shi sam baiga dalilin da Haris zaice tare zasu koma makaranta ba. Ya fahimci zumudin da Bilal yakeyi, duk da baiji shi ba sam a tafiyar farko da zaiyi. Yanzun ne yake jin dadi da Bilal din zai kasance makaranta daya da shi. Amman yana da tabbacin surutun da zasu dingayi shi da Haris kafin su sauka Zaria kan shi yayi ciwo. Shisa ya zabi yau din a matsayin ranar da zai koma, kawai saboda Haris yace zaiyi gaba, amman ya nace ya zauna jiran shi. Yau ma tunda ya tashi yake jan jiki, duk da hakan na da alaka da hankalin shi gabaki daya da yake kan Layla. Sam baiji motsin ta ba, ya dade a bakin kofa da safe yana ganin shige da ficen yaran gidan har suka tafi makaranta, amman bai ganta ba, yaso ya tambayi wani ko jikin ne yasa bata fito ba, amman gaisuwar da suka dinga mishi ce tasa bakin shi yin nauyi saboda surutun har ya fara hawar mishi kai. Haka ya gaji ya koma, ga kasa da baisan waya shigo da ita dakin ba, sai da ya kara sharewa sau biyu tukunna yaji ya taka tsakar dakin da ya sha tayal ya mishi dai-dai. "Kai fa muke jira... Kana ganin har biyu ta wuce, dare kake so muyi?" Bilal ya fadi yana shigowa dakin, kafafuwan shi Rayyan ya bi da kallo "Kai ka shigo da kasa, ban san sau nawa zance ka dinga cire takalminka a bakin kofa ba, har takalmi na siyo na yawo a daki, amman baka amfani da naka" Numfashi Bilal ya sauke, yana zare takalman daga kafar shi, ya saka hannu ya dauka yana fitar dasu bakin kofa, kwana biyu da Rayyan din baya nan wannan ka'idojin na shi duk ya manta su, karasawa yayi ya zauna gefen gado "Yanzun ba zaka wanke hannun ka ba, ka taba takalmi haka zaka kama kofi, yasa na daina hada kofuna da kai" Numfashi mai nauyi Bilal yaja yana fitar wa "Hamma ka sama mun lafiya, hannun ka ne ko nawa? Maganar da ake so kayi ba ita zakayi ba, sai kace bakin ka ya gaji da magana, amman baya taba gajiyawa kan tsegumi" Duk surutun shi sama-sama Rayyan din yake ji, hankalin shi yayi nisa wajen tunanin ina da ina takalman Bilal din suka taka, wacce kazantar ya kwaso da su ya kuma saka hannu ya damuka, wannan matsalar shi ce kamar yanda ya fada, amman Rayyan din bayason yaje ya taba mishi wani abu da wannan hannun nashi daya dauki takalma. Ya dauka surutu da mutane ne abinda yafi tsana a zamantakewa, sai da ya fara girma yagane kazanta ce abinda yafi tsana, tsantsanin da yake da shi ba karami bane ba. Lokutta da dama baka raba shi da karance-karance kan kwayoyin cutukan da suke rayuwa da mutane a mu'amalar yau da kullum. Yana son lafiyar shi, yana bala'in ririta lafiyar shi, tana jerin abu na farko da yake roka a dukkan addu'ar shi, shisa yake kara taka tsantsan idan ya tsare da iyawar shi, Allah saiya taimake shi. Dan ya kula mutane basu da wani buri daya wuce su ja mishi amai da gudawa. Haka shekaranjiya da suka dawo daga masallaci Bilal ya siyi wani rake, kuma har yake mishi tayi, tun suna hanya ya fara gabza kamar bashi da hankali. "Ka tashi dan Allah ka shirya mu tafi" Bilal din ya fadi yaba dorawa da "Hamma..." Ganin da yayi kamar Rayyan din baya jin shi, sai lokacin ya kalle shi "Meye? Karka dameni, kuyi gaba da Hamma Haris mana, dole sai kun tafi dani?" Ya karasa maganar yana mikewa, shi ya gama shiryawa, Layla ce baigani ba "Ni na gama shiryawa, ka tashi..." Rayyan ya furta kamar an mishi dole, mikewar yayi, kafin yai wani motsi Haris ya daga labulen dakin tare da yin sallama, idanuwan shi ya tsayar kan Bilal dan yasan ko Rayyan yayi wa magana kai tsaye ba lallai ya amsa shi ba "Kun gama? Yamma nayi" Kai Bilal ya daga mishi "Yanzun zan kiraka daman" Rayyan kuma Haris din yake kallo, muryar shi can kasan makoshi yace "Hamma..." Daga Haris din har Bilal kallon shi sukayi a tare, fuskokin su dauke da mamaki "Layla fa?" Ya furta har lokacin muryar shi daga kasan makoshi ta fito, kamar maganar na mishi wahalar gaske "Bata da lafiya, ko makaranta bata je ba, tana ta amai jiya da dare, sai da sukaje asibiti da...." Daga kan kalmar bata da lafiya bayajin wani abu ya kara zuwa kwakwalwar shi, zantukan duk da Haris yakeyi iya kunnuwan shi suka tsaya lokacin daya fara takawa, wuce Haris din da yayi a bakin kofa ya katse mishi maganar da yakeyi, takalma ya zira. A tsayin rayuwar shi ba zai iya tuna ranar karshe da ya taka bangaren Mami ba, ko Layla zai kira daga bakin kofa yake tsayawa ya kwala mata kira, idan bata nan Mami kan fito ko ta aiko a fada mishi bata nan, idan ita ta fito da kanta ta fadi juyawa yakeyi. Itama kamar tasan ba karamin taimako tayi mishi na saukakewa kanta yi mishi magana, haduwa hamsin in zasuyi zai matsa ta wuce ne, fuskarta ma baya kallo balle tasa ran zai gaisheta. Inda sabo ta saba, a yaran dakin Ayya daga Khalifa sai Bilal ne suke gaishe da ita ko da yaushe, amman sauran sai randa suka ga dama, idan tayi musu magana dai suna amsawa, kuma babu wanda zatace ya taba mata rashin kunya. Amman ta kula ba ita kadai bace, kowane Rayyan baya kulawa, shisa bata taba kullatar shi ba. Amman yau babu wani tunani ya shiga dakin yana fadin "Layla..." Mami da take kitchen tana wanke-wanke sai da taji gabanta ya fadi, dan yau sai taji kamar a cikin dakinta Rayyan yayi magana, hakan ya sata tsame hannuwanta daga cikin ruwa tana fitowa, ganin shi tayi a tsaye, yau ya sauke idanuwan shi akan fuskarta "Mami ina Layla?" Ya furta, yana kara mata mamakin da takeyi, kafin ta iya cewa "Tana dakinta" Dan yau ikon Allah take gani muraran, bata taba jin sunanta a bakin shi ba, ta manta ranar karshe daya kalli fuskarta yayi magana da ita. Balle kuma ace ya taka dakin ta, amman yau Rayyan ne da kafafuwan shi a cikin dakinta, lallai kam abin babba ne. Shikam harya fara takawa yayi tunanin baisan inda dakin nata yake ba, juyowa yayi, Mami da tasan tambayar da zaiyi ta daga hannunta tana nuna mishi, baice komai ba ya nufi dakin. "Allah Kai Ka san dai-dai..." Mami ta furta a hankali tana komawa cikin kitchen dan karasa wanke-wanken ta. Tana barin Rayyan daya taka har kofar dakin da Mami ta nuna mishi yana Kwankwasawa "Layla!" Ya kira yana saka Layla da tun da ta farka cikin dare, magungunan da aka bata a asibiti suka saketa ta rasa abinda yake mata dadi a duniyar gabaki daya. A islamiyya ta sha cin karo da darussan da sukayi magana akan al'ada, menene ita al'adar da hukunce-hukuncen ta a tsari na addinin musulunci. Kuma tun da suke aji biyu a sakandire ta kanji wasu a ajin suna zancen. Sai dai babu wanda taji yana labarin ana shan irin wahalar da take sha tun jiya, mararta take ji tamkar wani ya saka shebir a ciki yana kwashe duk wani abu da bai mishi ba. Ko numfashi dakyar take iya fitar da shi, bayanta da cinyoyinta a rike su. Har suna sakata tunanin ko jijiyoyin duk dayane suka fara daga bayan nata zuwa cikin cinyoyinta. Ciwo ne da bata taba sanin irin shi ba. Dan ita kabarta da zazzabi, shima sai Mami tayi da gaske zata zauna waje daya. Bata taba wata rashin lafiya da ta kwantar da ita waje daya haka ba. Tana juye-juye ne taji muryar Rayyan, dan kara dakuna fuska tayi dan a tunanin ta cikin kanta ne, dan ko dazun tayi tunanin harya wuce makaranta. "Layla!!" Ya kara fadi yana doka kofar fiye da sau daya kamar yanda yayi da farko, bata san lokacin da ta sauko daga kan gadon tana karasawa inda kofa take ba, kama hannun tayi ta murza tana bude mishi "Hamma..." Ta fadi cike da mamaki, da gaske shine "Me ya same ki?" Rayyan ya furta da damuwa kwance a fuskar shi, yanayin da ya dirar mishi da bakunta tunda ba sabawa yayi ba, idanuwanta ta sauke cikin nashi "Ki daina kallona!" Yai maganar a tsawace yana sakata sadda kanta kasa, idanuwanta na fara tara hawaye, nashi idanuwan Rayyan ya lumshe yana bude su a kanta, dai-dai lokacin da mararta tai wata irin murdawa, sai da ta rike kofar tana kiran sunan Allah, ba ita kadai ta rikice ba, hatta shi Rayyan din yanayinta ya ruda shi "Wai me yake damun ki? Me asibiti suka ce yana damun ki? Kin sha magani?" Kai kawai ta iya daga mishi, ganin dakyar take a tsaye yasa Rayyan din kama hannunta da yake jikin kofar yana janta suka shiga cikin dakin. Komawa tayi kan gado ta kwanta, yanda duk zata misalta ciwon da take ji ta kasa, ko idanuwanta ta kasa budewa tunda ta kwanta. Tana jin Rayyan ya mika hannu yana daukar mayafin da takan rufa da shi in taji sanyi, duk da ba bargo bane, zanin gadone babba, warware shi yayi yana budewa ya rufa mata. Kafin ya samu wajen zama kan durowar da take gefen gadon. Kallon yanda lokaci zuwa lokaci Layla takan kara runtsa idanuwanta alamun tana cikin azabar ciwo yakeyi. Jin yanayin yake har cikin ran shi, shi bai taba ganin tayi rashin lafiya haka ba tun tasowar su. Yana nan zaune yana kallon yanayin ta Mami tayi sallamar daya amsa batare daya dauke idanuwan shi daga kan Layla ba "Me yake damun ta wai? Ko za'a koma asibiti" Murmushi Mami tayi "Ai da sauki, an bata magunguna kuma ta sha" Kai Rayyan yake girgizawa tunda Mami ta fara magana, yana dago kai ya kalleta "Layla ce Mami. Bata rashin lafiya irin haka... Kinsan bata rashin lafiya irin haka" Ya karasa maganar da wani yanayi a muryar shi. Kamar baisan yanda zai fadi kalaman ta fahimce shi bane. Itama Mami batasan yanda zata fara gaya mishi ciwon da Layla takeyi bana asibiti bane ba, yanda zai fahimci asibiti sunyi iya nasu kokarin, zai wuce nan da wasu yan kwanaki. "Nasani, zataji sauki karka damu..." Kai kawai ya jinjina, tana ganin yanda bai yarda da maganganun ta ba, ya dai mayar da hankalin shi kan Layla ne yana kara gyara zama. Sake ficewa Mami tayi daga dakin, anan tabar Rayyan zaune, sosai ya nutsar da hankalin shi akan Layla, har sai da yaga yanayin ta ya canza da alamar bacci ya dauketa. Amman ko motsi tayi sai gaban shi ya fadi, gabaki daya komai yake ji baya mishi dadi. Kamar daga sama yaji ana fadin "Hamma kai muke..." Hannun shi ya daga guda daya yana dakatar da Bilal, dayan hannun yakai bakin shi da furta "Shhh..." Kafin ya mike tsam yana fitowa wajen dakin, ya dan koma ciki yana fisgo Bilal da ya shiga suka fito, muryar shi can kasa yace "Meye?" Kallon shi Bilal yake da mamaki "Ban gane meye ba, kasan kai muke jira har la'asar tayi ko?" Numfashi ya sauke, gabaki daya ba yajin yana da natsuwar wata tafiya yau "Ni kam sai gobe" Baki Bilal ya bude yana kallon shi, so yake yaga ko dan murmushine a fuskar Rayyan din da zai nuna cewa wasa yake maganar da yayi, amman babu, da dukkan gaskiyar shi ya fadi "Sai gobe? Kasan Hamma Haris na da abu mai muhimmanci da zaiyi goben ko?" Cikin idanuwa Rayyan ya kalle shi "Nace kar ya tafi ne? Ban tuna lokacin da nace wani a cikin ku ya jirani ba, kun tambaya na fada muku yau zan tafi. Yanzun kuma nace sai gobe, me yasa kake da matsala da hakan?" Ba maganganun bane suka batawa Bilal rai, yanayin da Rayyan din yayi maganar, babu alamun bacin rai ko jin haushi, kamar yana ma karamin yaro bayani, saboda bai dauki abinda yayi a matsayin wani abu ba "Hakane..." Bilal ya furta yana juyawa, dan dakuna fuska Rayyan yayi dan yaga kamar ran Bilal din ya baci, bayan a duka maganganun da yayi bai ga abin bacin rai ba. Kiran sallar la'asar da yaji anyi yasa shi ficewa daga bangaren Mami, sai da yaje dakin shi ya daura alwala sannan ya fita masallaci. Yana dawowa kuma kan shi tsaye bangaren Mamin ya kara wucewa, sanda yaje a bandaki ya samu Layla ta tsugunna saboda aman da taji yana taso mata, kuma batama wani ci abinci ba balle tace "Layla... Amai zakiyi? Amai kikayi?" Rayyan ya fadi yana jin ruwan da yake takawa a bandakin saboda babu takalma a kafafuwan shi har cikin ran shi, amman wahalar da Layla take ciki tasa ko amsa ta kasa bashi, da kan shi ya tari ruwa a famfo yana janyo bokitin kusa da ita, kofin da yake ciki yai amfani da shi wajen zuba mata ruwa a hannuwanta da ta miko mishi ta wanke fuskarta, shi ya kama hannunta tana mikewa ta ficewa daga bandakin ta koma ta kwanta. A ran shi tunanin inda Mami taje tabarta ita kadai a halin da take ciki yakeyi, ran shi na kara baci. "Ba dole kiyi rashin lafiya ba, ki kalli bandakin da kike shigowa dan Allah..." Ya furta, duk da wani zai shiga yagan shi tsaf-tsaf, amman a idanuwan Rayyan yayi mishi datti. Omo daya gani ya dauka ya zuba a bokitin yana wanke bandakin, har karamin tawul din daya gani da baisan kona menene ba ya dauka ya goge bangon bandakin. Ko kadan bayason ganin datti, dan jirwayen ruwan da zaka gani na ruwan wanka a bandaki, na dakin su sam ba zaka gani ba, ya goge ko ina qal-qal. Sai da ya wanke kafafuwan shi sannan ya fito daga bandakin. * "Muje kawai Hamma... Barin wa Ayya sallama, idan mukai la'asar sai mu tafi" Bilal ya fadi muryar shi a sanyaye, cike da rashin fahimta Haris yace "Rayyan din fa" Kallon shi Bilal yayi "Yace sai gobe zai tafi, janyo shi zanyi?" Murmushi Haris yayi, kafin Bilal din ya dan dafe kai yana fadin "Kayi hakuri...Allah ya batamun rai ne" Murmushin dai Haris ya sake fadadawa "Rayyan manya... Allah ya shirya" Bandakin su da yake cikin dakin Bilal ya shiga ya daura alwala ya fito "Kaga ni ina da abinda zanyi a makaranta gobe da safe in shaa Allah. Amman ka jira Rayyan din sai ku taho tare" Tun da ya fara magana Bilal yake girgiza mishi kai, ya taho shi kadai kamar yanda yake so. Da tun farko bai wahalar dasu ba yace shi kadai yake son tafiya. "Ka bar shi Hamma... Da mun dawo sallah tafiya zamuyi..." Kai Haris ya jinjina yana mikewa. Alwalar yayo shima suna fita masallaci tare, suna dawowa shi ya shiga dan ya fito da jakunkunan su da na Bilal ne guda biyu. Shi kayan shi basu da yawa, Rayyan kuwa jakar shi karama ce, babu abinda yake tafiya da shi. Daga gefen jakar takardun zanen shi ne daya nannade su ya soka. Shi kuma Bilal ya wuce bangaren Ayya inda ya tsaya daga bakin kofa yana fadin "Ayya zamu wuce..." A kasan murmushin alfaharin da tayi akwai damuwa shimfide, gidan har yayi mata wani irin shiru. Da Rayyan ya tafi daman ta saba, dan ko yana cikin gidan sai tayi kwana biyu bata saka shi a idanuwanta ba, amman Bilal, a duk cikin yaranta babu wanda ta shaku da shi kamar Bilal, banda Ahmadi shine namiji na biyu a rayuwarta da yake gane akwai damuwa a fuskarta tun kafin ta furta, yake zama har sai yaga tayi fara'a sannan. Bilal ne kuma ka dai yake dora bukatunta akan nashi. Ko bangaren ya zaba na karatun shi tasan saboda ita ne "Wai duk cikin ku babu wanda naji yana sha'awar lissafi....ko yar kara ba zakuyi wa Abbun ku ba" Ta fadi wani lokaci can baya, sosai Bilal yayi dariya, musamman da Zubaida tace "Wallahi Ayya idan zaki tsareni bansan ya akayi na wuce lissafi a shekarar farko fa, kowa na kallona a matsayin yar Abbu a ajin, suna tunanin zan baro A, dakyar D ta fito..." Nan aka bude caftar tattauna lissafi, shi bai taba bashi matsala ba, kuma Rayyan yana ganewa matuka, idan waje ya shige mishi duhu daya nunawa Rayyan din yake warware mishi "Kina son wani ya karanci lissafi ne Ayya?" Kai ta dan rausayar "Naga wahala yake baku ai" Murmushi kawai yayi, sai ranar daya amso takardar samun karbuwa a ABU ne ya nuna mata lissafine gurbin daya samu "Bilal..." Ta fadi tana jin kaunar shi har kasan zuciyar ta "Ki mun addu'a kawai Ayya" Shine abinda ya fadi, addu'a kam bata gajiyawa da yi musu ita. Tun da satin tafiyar tashi ya kama take jin yanda zatayi kewar shi. Ko na rana daya Bilal din bai taba zuwa wani waje ya kwana ba, yaran nata girma sukeyi a gaban idanuwanta, amman zuciyarta na kallon su yan kanana. A wajenta har karshen lokacin da Allah ya ara mata tare dasu ba zata daina ganin yarintar su ba. "Allah ya tsare mun ku, Allah ya baku sa'a a karatun ku. Ka kula da Rayyan kamar yanda ka saba" Ta karashe maganar da yanayi mai nauyi a muryarta "Sai gobe shi, ya fasa tafiya yau" Da mamaki Ayya take kallon Bilal "Saboda me? Bashi ya zabi yau din ba" Kallon 'Rayyan ne Ayya' Bilal din yayi mata "Kawai ya fasa tafiya yau din ne" Ita fa sam zaman shi a Zaria yanzun ya fiye mata zaman shi a garin Kano. Saboda zai nisanta shi da Mami da kuma Layla. Ko kadan bata kaunar ganin yana wata mu'amala da su "Yana ina?" Dan jim Bilal yayi, saboda bayason bata mata rai, yana da tabbacin idan ya fada mata Rayyan na dakin Mami ranta zai baci sosai. Amman a lokaci daya ba zai iya mata karya ba "Yana wajen Layla ko?" Ta tambaya zuciyarta na wani irin zogi, ta rasa ta inda zata fara bullowa al'amarin Rayyan. Shekaranjiya suna tare da Khadi da zuwanta aikin hajji shekaru bakwai da suka wuce yasa duk yan unguwa suna kiranta da Hajiya Dije. Taso tayi mata zancen Rayyan din dan tana da yakinin ba zata rasa shawarar da zata bata ba. Amman sai ta tsinci kanta dayin nauyin baki "Bilal tambayar ka nakeyi" Ayya ta fadi rai a bace, kai ya dan daga mata "Bata jin dadine, yana bangaren Mami... Mu..." Ai Ayya bata barshi ya karasa ba, kanta har wani shuu yakeyi saboda tashin hankali. Numfashi kawai Bilal ya sauke yana wucewa dan yasan Haris na can yana jira. Ko baiyi niyya ba zai bi shi Zaria yau, saboda bayason ganin kowanne rikici ne Ayya zatayi a cikin gidan yau. Ita kuwa kanta tsaye dakin Mami da zata kirga iya shigar data tabayi daga zuwanta gidan zuwa yau ta nufa, tana shiga ta fara kwalla mata kira "Maryama... Ke kinsan wallahi bokan ki yayi karya... Ke din banza balle kuma yar rikon ki. Ki fito tun wuri ki warware abinda kika kulla" Dan tana da tabbacin karatun da Maryama taga Rayyan ya natsu yanayine bata so, shine abinda ya tsokane mata ido yasa take neman sabauta mata yaro. Hango wata kofar daki da tayi a bude yasata takawa tana karasawa. Abinda tagani yana saka duk wata jijiya ta jikinta tsinkewa. Rayyan ne da kayan wankin Layla da tayi bata kwashe ba ta ajiye can gefen gado suka dinga shigar mishi ido, ga kuma zaman da yakeyi. Hakan ya sashi mikewa, idan yana wani abu da hannuwan shi yana rage mishi tunani, ko zane ko aiki, ko karatun makaranta, sosai suke hana kwakwalwar shi tunanin komai sai abinda yakeyi din. Yana daga wata hijab yaga mp3 din Layla hade da earpiece, shi ya sakama kunnuwan shi ya kunna, kusan wakokin yan kasar sudan da sukayi tashe wato Sahwa ne cike da mp3 din, su yake ji, ya saka mp3 din a aljihun shi. Kayan yake ninkewa a nutse, shisa sam baiji hargagin da Ayya takeyi ba, baima san tana bayan shi ba sai da yaji an dafa shi, juyowa yayi ya cire kunne daya na earpiece din dan yaga kamar magana takeyi "Uban me kakeyi? Na shiga uku ni Maimuna... Rayyan kayan su naga kana linkewa kamar? Me kakeyi a dakin Maryama? Yaushe ka fara shigowa dakin ta?" Dakuna fuska yayi yana kama hannun Ayya hadi da janta, bin shi take da matukar mamaki, saboda komai ya kwance mata, suna zuwa tsakiyar falon sukaci karo da Mami da ta yanke karatun azkar din bayan la'asar da takeyi ta fito saboda jin tashin hankalin da Ayya. Hakan nasa Ayya fisge hannunta da Rayyan ya riko "Maryama ki kiyayeni, wallahi ki fita idona. Kin aure mun miji, kamar hakan bai isheki ba, na saka miki ido akan Bilal, bai isheki ba kin biyo Rayyan? Dauki dai-dai zaki mun kenan" Murmushi Mami tayi, ta rasa kalar zargi irin na Ayya. Duk tsayin shekarun nan basu sa ta fahimci cewar bata da lokacin bibiyarta ba. Ko akan Ahmadi batajin zata iya bibiyar Ayyar, duk kuwa tarin kaunar da takeyi mishi. Idan bin Malamai ne Ayya take magana tana da kudin da zata iya basu. Kawai babu abinda ya fiye mata zaman lafiyarta a kabari ne, zata kwammace tabar mata Ahmadi idan za'a bata zabi tsakanin hakan da bin Malamai. Amman a duk rana gani takeyi bibiyarta takeyi. Zuwa yanzun shagunan dinkinta biyu, ana kawo mata dubbanin kudi duk karshen watan duniya, ga hijabai da take dinkawa a cikin gida, sari akeyi garuruwa. Ga hidimar yaranta, sam bata da lokacin wani abu, kawa kwara daya bata da ita da zata nuna tace abokiyar shawara, idan abu yasha mata kai da bata son tattaunawa da Ahmadi, Haris ne abokin shawararta. Yau Rayyan ne kawai zai hanata fadawa Ayya maganar da zata kwana tana juyi. Alkawari ne tayiwa kanta, ko dan zumuncin da ke tsakanin yaran su ba zata taba mayar mata magana a gaban su ba. Shisa ta girgiza kai kawai yanzun ma tana fadin "Allah ya kyauta" Ta juya "Na fada miki, ki kyalemun yarana, kome zakiyi ki kyalemun yarana, ba zai miki kyau ba kina bibiyar mun yara" Runtsa idanuwan shi Rayyan yayi yana bude su akan Ayya "Ayya..." Ya kira muryar shi can kasa, baice yana son Mami ba, bai kuma ce bayason ta ba, bayajin komai a kanta sam-sam. Yanajin abu a game da Ayya da Abbu, amman shi kan shi ba zaice ko meye ba, lokutta da dama idan yagansu zuciyar shi nayin duhu, musamman Abbu, ko gwada magana yayi da shi sai kan shi ya fara sarawa, shisa lokutta da dama yake zabar ya wuce batare da yace mishi komai ba. Ya sha jin tana fadar cewa Mami zata barbada musu abu, shisa bayacin abinta. Lafiyar shi nada muhimmanci a wajen shi, kuma idan Ayya tace za ayi abu, ya tabbata za ayi. Maganar da suke a tsakanin su bata da yawa, amman bata taba mishi karya ba, ita da Bilal na jerin mutanen da ya aminta ba zasu taba cutar da shi ba. Amman hakan baya nufin yana son hayaniyar da Ayya take yawan yi da Mami din, bai taba mata magana bane kawai. Yafi zabar ya wuce yayi abinda yake gaban shi. Yau dinne yake jin shi sama-sama. Ga Bilal da yaga ran shi ya baci kan maganar da bata kai ta kawo ba, Layla da har yanzun baiga alamar tana jin saukin da Mami ta kira mata ba. Ga Ayya yanzun da tazo tana wasu maganganu "Ayya dan Allah ki tafi. Kin ga Layla bata da lafiya. Kuma dakyar tayi bacci" Kallon shi Ayya take, tsoro bayyane a fuskarta "Dan ubankan shanyewar da akayi maka har takai haka? Ni kake fadawa dakyar Layla tayi bacci? Inalillahi wa ina ilaihi raji'un..." Ayya ta karasa kamar zata fasa ihu saboda tashin hankalin da take ciki, abinda ko a mafarki bata hango bane yake faruwa a gabanta "Ka zo ka wuce ka koma makaranta kafin ranka ya baci wallahi" Numfashi Rayyan ya sauke, ran shi ya gama baci, babu wani bacin rai kuma da Ayya zata kira banda wanda yakeji yana taso mishi yanzun "Zan koma makaranta. Sai gobe in shaa Allah" Cikin idanuwa take kallon shi "Idan na isa, idan ina da wata daraja a idanuwanka zaka wuce ka koma makaranta yau" Maganganunta yake ji sun danne shi da wani irin nauyi, amman duhun daya taso mishi na son bijerewa maganar da tayi ya rinjayi koma meye ya fara shirin tasiri akan shi. Hannun ta ya kama yana janta har kofar dakin Mami din "Zan koma Ayya... Sai gobe zan koma" Ya fadi yana juyawa, baki a sake Ayya take kallon Rayyan harya juya yana komawa dakin Layla. A gaban idanuwanta, ba zatace ga yanda akayi ta isa daki ba, amman har wani jiri-jiri take gani saboda tashin hankali. Tana shiga daki a kasa ta zauna dabas, jikinta babu inda baya rawa. Tunda take da Rayyan ko da wasa bai taba gwada tayata wani aiki ba, asalima magana da ita wahala take mishi. Waccen shekarar da tayi jinya ya shiga dakin dai ya zauna, amman baice mata kanzil ba, harta ji sauki haka zai shiga ya samu waje ya zauna. A fuskar shi babu alamar damuwa ko wani abu, idan ma su Zubaida da suke zaune suna surutu tashi yake ya fice kamar surutun nasu ya fara hawar mishi kai kamar yanda yake fadi. Amman yau Rayyan ne har yake fada mata Layla tana bacci, Rayyan ne da hannun shi tagani ya linke kayan Layla. Wasu hawaye nasu dumi ne suke zubo mata, ta jima a wajen, ko sallar Magriba dakyar ta samu tayi ta, tana zaune tana sharbar kukan ne Ahmadi ya shigo, dan duka yaran suna gidan Yaa Ayuba. Da haka zasu shigo su sameta tana wannan kukan. Harta fara kewar Bilal tun ba'a kwana ba, tasan shine kawai baya iya daukar awanni bai ganta ba, ko leka kaine sai yayi "Ayya nace tun dazun banganki bane fa... Kina lafiya dai ko?" Ba zai taba gane yanda kulawar shi take kara mata son shi ba. "Subhanallah, Maimuna... Lafiya? Me ya faru?" Ahmadi ya fadi yana karasawa cikin dakin sosai, kamar haka take jira ta sake fashewa da wani kukan "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un..." Ahmadi ya furta cikin bayanannen tashin hankali "Duk ina yaran? Suna lafiya? Dan Allah kiyimun magana" Dan harya fara zufa saboda tashin hankali, muryar Ayya na shakewa saboda kuka ta soma fadin "Tunda kake, Ahmadi tunda Rayyan ya mallaki hankalin shi ka taba ganin ya tayani aiki? Ko da shara ce?" Cike da mamaki Ahmadi yake kallonta, ya dauka sun gama yanke hukunci addu'a ita ce kawai abinda zasu dinga bin Rayyan din da ita, ba zasu kara bata ransu akan shi ba. Idan ma sun bata ran nasu zasu yafe mishi da sun huce ko Allah zai sanyaya zuciyar shi. Tunda fushin su zai kara jefa shi cikin wani yanayin ne, kuma idan bai manta ba yau Bilal yace zasu tafi makaranta, hatta kudin Rayyan din ya hada yaba Bilal, to me zaiyi wa Ayyar haka da take wannan kukan. "Idan nace maka Rayyan na linkewa wasu can daban kayan da suke sakawa abin ba zai baka mamaki ba?" Bata ma rufe bakinta ba take ganin wani sabon mamakin karara a fuskar Ahmadi, hannu takai tana share kwallarta, wasu sabbi na samun damar zubowa, kada kai tayi cikin kunar zuciya "Yanzun zaka yarda dani ko? Yau zaka yarda matarka na bibiyata, zaka yarda yarana take so ta rabani da su. Ahmadi na kauda kai iya yanda zan iya... Da Allah nake rokon ka kayi mata magana ta kyalemun yaro, ta kyalemun yarona" Ta karasa tana sakin wani gunjin kuka. Tabbas zancenta ya daure mishi kai matuqa. Yasan Rayyan, a cikin yaran shi yanzun babu wanda yake kula da takun shi kamar Rayyan. Idan da gaske Ayya takeyi yana linkewa su Mami kaya to tabbas zargin da takeyi na da tushe, duk da a kasan ranshi yasan Mami ba zata tabayin abinda zai cutar da wanin shi ba. "Kiyi hakuri, zan mata magana. In shaa Allah babu abinda zai faru. Dan Allah kiyi hakuri ki daina kukan nan..." Ahmadi yake fadi, dan kukan nata ya kara daga mishi hankali, bai fita daga dakin ba har saida ya tabbatar ta daina kukan, da kan shi ya zubo mata abinci ya kawo mata ruwa. Sannan ya nufi bangaren Mami. Duba jikin Layla yayi ya shiga yi, ya samu tana bacci, daga nan ya wuce bangaren shi, bai yiwa Mami zancen ba sai bayan sunci abincin dare harma sun kwanta sannan yace "Maryama me yake faruwa ne?" Numfashi ta sauke "Me kake so ince maka? Na dauka ta gaya maka abinda ya faru" Kai ya jinjina "Baya nufin bana son ji daga bakin ki" Murmushin takaici mai sauti Mami tayi, kafin ta labarta mishi iya abinda tasan ya faru tana dorawa da "Rayyan bai tana shigowa bangarena ba, idan ya taba lokacin yarinta na manta... Amman yau ya shigo saboda Layla... Ina tsoro, har raina ina tsoron wannan kaddarar ko wacce iri ce, saboda ina hango tarin tashin hankalin da yake cikinta" Wannan karin Ahmadi ne ya sauke numfashi, gabaki daya abin ya saka jikin shi yayi sanyi, idan da gaske saboda Layla ne Rayyan din ya shigo ba Mami bace kawai a tsorace, shi kanshi zuciyar shi yaji tana rawa. "Allah karka doramun kaddarar da bazan iya dauka ba, Allah ka dubeni da Rahmar ka ka saukakama yarana kaddarar su..." Daren kusan Ahmadi, Mami da Ayya kanta kwana sukayi suna juyi. Ayya na jinjina aikin bokan Maryama da yanda ya zame mata dole ta kira Hajiya Dije su tattauna wannan al'amarin. Mami na tunani amanar Layla da take hannunta, tana kuma tsoron abinda zuciyarta take sanar da ita yana faruwa tsakanin Layla da Rayyan din da bata jin sun sani. Ahmadi kuwa gabaki daya lamarin ne yake sanyaya jikin shi, yaran nashine yake ganin kamar sunyi kankanta, kamar ma basu da hankalin hango kaddarar da take bibiyar su. Rayyan ne kaddarar su Rayyan ne suke tunanin zai zama tushen komai. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:07 PM - 111: Nov 22, 2020 10 BAYAN SHEKARA UKU Ita kadai tasan cikin kalar fargaba da tashin hankalin da take a shekarun nan. Yanda duk taso ta nisanta kanta da Hajiya Dije ko dan gudun suje inda za'a binciko mata abinda zai daga mata hankali sai ta kasa, Rayyan na bata tsoro, yanda yake manne da Layla duk idan ya dawo makaranta yana karya mata zuciya. Musamman yanzun da take ganin suna kara girma, yaranta na wani irin girma da har mamakin shi takeyi. Ita ce harta aurar da Khalifa da Zubaida. Kuma duk lokacin da zata sami Ahmadi da maganar takan ga gajiyawa a fuskar shi, kamar ya gaji da yanda ta kasa daukar ido ta saka akan Rayyan din da Layla kamar yanda yayi "Ya kike so inyi? Ko akan dukan da yakeyi mata nayi magana tsini ne kawai bakina baiyi ba. Kinsan halin Rayyan, abinda ya ga dama shi yakeyi" Ahmadin yace mata wani lokacin, ita ko dukan bata so, batason wani abu na hada danta da Layla. Batason ganin shi a bangaren Mami sam-sam. Rayyan din ya kara mata tsanar matar kamar zata hadiyi zuciya haka takeji duk idan taga giccinta. Yau da kanta ta shiga kitchen, har Rukayya na mata tsegumi "Ayya saboda su Hamma zasu dawo shisa kika ce ke zakiyi girki..." Dariya kawai tayi, wannan karin sun dade, watansu na hudu kenan rabon su da gida. Duk da ta wani fannin dadewar tayi mata dadi bana wasa ba. Hakan na nufin aikin da Malam Ma'azu kwano kamar yanda Hajiya Dije ta kira shi yaci. Daman tace a borno yayo karatun allo, a haka idan ka ganshi zaka raina shi, sai dai aiki yake kamar babu gobe. Tashin farko dubu goma Ayya ta ajiye mishi na bugun kasa, inda yace ta saka tafin hannunta kan wani rairayi da yake cikin falankin katako. Batayi musu ba ta saka, duk da tasan zancen gizo ba zai wuce na koki ba, ba nan bane wajen farko da sukaje da Hajiya Dije, kuma duk maganar shige dayace, Layla na rike da kurwar Rayyan, danma yana da dakakkiyar zuciya da sai abinda tace ne zaiyi. Wannan ma suna shiga ta fara labarta mishi matsalarta akan Rayyan din, kafin yace yasan kasa zata nuna mishi komai, ta saka hannunta akan yashin, suna zaune suna kallon yanda yake rubutu yana sharewa yana sakeyin wani, kafin yayi numfashi mai nauyi yana dago kai ya kalli Ayya "Yaron ki zai zama shahararren mai kudi, akwai nasarori da suke biye da shi. Shisa abokiyar zamanki ta kasa zaune da tsaye a kan shi. Saboda taje an duba mata yanda kaf gidan ba za'ayi mai arziqin shi ba. Yarinyar da kike magana da ita aka, idan baki tashi tsaye ba duk abinda zai samo a kansu zai kare, ke kanki ga katanga nan naga ana ginawa tsakanin ku" Wani irin numfashi Ayya taja, tana duban Hajiya Dije, zuciyarta na wata irin dokawa "Yaushe Maryama zata kyaleni in huta?" Murmushin "Na fada miki ai" Hajiya Dije tayi mata "Da nace miki ki dinga nemar wa yaranki ko da tsarine ca kikayi kamar Maryama ba zata iya cutar da su ba. Kin daiji da kunnuwan ki yanzun ai" Kai Ayya ta jinjina mata, taji kam, ba waje daya ba biyu ba, kuma ta gasgata tunda zuwan karshe da Rayyan din yayi, saboda ta mishi magana akan Layla yasa shi daina shiga bangaren ta gabaki daya har suka koma. Sosai abin ya bata tsoro, ashe katanga ake mata da dan data tsugunna ta haifa, dan daya fito daga cikinta. Rashin imani irin na Maryama ba zai misaltu ba. Aiki Malam Muazu yace za ayi sosai akan Rayyan din "Gaskiya kudin ki zaiyi yawa, saboda za'a yanka raguna baki da fari guda daya, da zuciyar su za'ayi aikin, sai an hada guda biyu za'a musanya su da ta danki da take rike a wajen su... Aikine babba, zan kuma baki garin maganin da nake so ki tabbata ko yayane shi yaron yaci dan ya karya katangar da take tsakanin ku" Hakan kuwa akayi, kudaden duk daya bukata ta bashi su. Daman yace zata ga canji, ba karamin dadi take ji ba ganin yanda Rayyan din ya zauna a makaranta har tsayin wata hudu,mutumin da baya iya hada satika hudu batare da yazo Kano kona kwana daya ba. Shisa take shirya girkin nan da kanta. Duka zata hade abincin ta barbade, har Bilal ma yaci dan shima yana bukatar duk wata kariya da zata ba Rayyan. Dan ma shi tana kula da yanda yake janye jikin shi daga bangaren Maryama, ya rage shiga kamar da, hakan ba karamin dadi yake mata ba. Gabaki daya cikin nishadi take a duka ranar. Saima da taji sallamar Bilal, da murmushi dauke a fuskar shi. Su Rukayya kance basa bambance muryar Bilal da ta Rayyan musamman yanzun da suka zama Samari, sannan idan a fisge ka kalle su zaka iya dauka Bilal ne, sai ya shigo sosai zaka ga Rayyan ne. Kamannin su har Abbu suke ba mamaki, yana kara jinjina karfin dangantaka ta jini, duk da mutane da yawa kan iya yin kamanceceniya batare da alaka ta komai ta hadasu ba. Sai dai Rayyan yafi Bilal din haske, kuma yanzun ya dan fishi tsayi duk da su duka dogaye ne, Ayya kan cewa Abbu itama ai doguwar ce duk idan yace tsayin shine yaran suka biyo. Yanzun kuma Bilal na tara suma a kan shi, Rayyan kuma yana asketa kasa sosai sosai, kuma ya tara kasumba a fuskar da ta saka shi wani kwarjini na daban, Bilal gemu ne da samarin yanzun suke ajiyewa da har dariya yake baiwa Ayya. Wani lokacin ma fayau zakaga fuskar shi, ya aske komai. "Ayya..." Bilal ya furta yana fadada murmushin shi, kafin ya karasa cikin dakin yana zama kan kujera hadi da sauke numfashi "Yan Zaria" Ayya ta fadi tana saka Bilal din yin dariya, yayi kewarta matuka "Harma mun zama yan Zaria kenan Ayya... Ina kowa? Wallahi nayi kewarki da yawa..." Sosai Ayya take murmushi, tasan yayi kewarta, tunda yana iya kiranta sau biyar ma a rana. Itama idan ta cika awa hudu bata ga kiran shi ba sai ta neme shi. Rayyan ne ma harta saba, a cikin watannin nan hudune da take tunanin aikin Malam ne ya kirata sau biyu, daga gaisuwa yayi shiru, sai tace ta dinga tambayar shi makaranta da lafiyar shi da ya dinga amsa ta dai-dai "Ayya gaisuwa ce kawai" Ya fadi a hankali, da yasan yanda taji dadin gaisuwar da ko sau dayane a wata ya kirata. Tunda yai wayar hannu sai a wajen Bilal ta sami lambar shi saboda yanda bai taba gwada kiranta ba. Idan sunyi magana to Bilal ya bashi wayar shi ya gaisheta, shima daga yanayin yanda zai magana tasan a kunne kawai Bilal ya saka mishi wayar batare daya shirya ba "Duk idanuwanka yayi zuru-zuru" Dariya mai sauti Bilal yayi "Jarabawa ce Ayya... Sai kinga Hamma, gara nima tunda komai na samu ina ci" Numfashi ta sauke, ai baizo ba ballantana ta gan shi. Da kanta ta mike tare da fadin "Allah yasa an rubuta a sa'a, bari in dauko maka abincin ku..." Kitchen ta wuce ta dauko mishi kuloli guda biyu da cokula, mikewa Bilal yayi ya amsa yana ficewa daga dakin zuwa dakin su, tunda ya karya kwana ya hango Layla a tsaye, jikinta sanye da wandon jeans ruwan bula da riga ja a jikinta, sai hula, tayi mishi kyau tun ta gefen ta daya hango, yana jin zuciyar shi ta matse a kirjin shi, cikin shekarun nan ya fahimci muhimmanci da Layla take da shi a rayuwar shi. A cikin shekarun ne kuma yayi kokarin janye jikin shi saboda yanda kusancinta da Rayyan yake wahalar da shi. Suna zaune su biyu zata zo waje, daga nesa zaka ga yanda idanuwanta suke kafe kan Rayyan, lokutta da yawa in ba kuka Rayyan din ya sata ba, sam bata kula da yana waje. Idan Rayyan yana nan idanuwanta a rufe suke daga sauran abubuwan da bashi ba. Ranar da Rayyan ya riko hannunta ji yayi wani abu na budewa a kirjin shi, shisa yanzun yake tashi yana basu waje, yafi mishi kwanciyar hankali, abinda bai gani ba bazai bata mishi rai ba sam. Wani lokacin idan Rayyan ya kai mata wani dukan har a zuciyar shi yake jin zafin, amman daya kirata zata sake dawowa. Zaka rantse da Allah rashin kirkin da Rayyan yake mata take so. Bashi da inda yake jin sauki-sauki sai wajen Aisha. Yanzun ma daya huta yayi la'asar wajenta zai tafi ko zuciyar shi zatayi sanyi-sanyi. Da ba kulolin abinci bane a hannun shi sam ba zai karasa inda suke ba, ya koyawa kan shi nisanta da Layla, musamman in tana tare da Rayyan haka. Numfashi yaja yana fitarwa, duk wani karfin hali da zai iya ya tattaro yana takawa har inda take tsaye a bakin kofa, kafin yaga Rayyan da yake tattaro shara. "Hamma Bilal..." Layla ta fadi cikin sigar gaisuwa batare da ta kalle shi ba "Layla..." Ya amsa a sanyaye, yana shirin karawa da tambayar lafiyarta Rayyan ya dago, da bayan hannun shi ya kai ma Layla wani duka da yasa Bilal runtsa idanuwan shi kamar a kan shi hannun zai sauka, ya bude su a hankali yana ganin Layla da ta kauce tana kara turo baki "Nace bai sharu ba kika tsaya gardama dani... Uban meye wannan?" Ya karasa maganar yana nuna mata wata kasa da batasan daga inda ya sharota ba, saboda har karkashin gadon dakin nasu sai da ta share, kujerar shi da teburi kuwa daga su tayi ta ajiye a gefe, sif din kayan su har samanta sai da ta taka kujera ta share, haka ta sake takawa ta gogo daga saman zuwan jiki, tasan halin shi, dan yatsa zaisa ya dangwalo yaga ko da kura babu "Wallahi shara hudu nayi Hamma" Ta furta a gajiye, Rayyan din najan wani tsaki "Ba abinda kika iya sai shirme..." Ya fadi yana saka abin kwashe shara ya tattare kasar ya mika mata, karba tayi tana juyawa, shima cikin dakin ya shiga. Inda Bilal ya rufa mishi baya yana samarwa kulolin da suke hannun shi mazauni a tsakar dakin. Rayyan links din jikin rigar shi yake cirewa, dan manyan kayane a jikin shi, wani yadi ruwan kwai da ya sake fito da hasken fatar shi "Ayya na tambayar ka" Bilal ya fadi badan ya tsammaci amsa daga wajen Rayyan din ba, bai bashi amsar ba kuwa ya wuce yana nufar bandaki, dan ruwa kawai yake son watsawa. Tun da safe kafin su taho yace Layla ta bude dakin ta share musu. Yana saka kafar shi yaji kamar ya taka kasa. Wayarta da ta saukaka mishi komai yanzun ya kira "Baki share dakin nan ba Layla" Ya furta bayan ta daga, kafin ta amsa shi ya dora da "Ki zo yanzun" Gardamar da ta tsaya mishi da rantse-rantse yasa shi cewa ta dauko mishi tsintsiya. Sanda ta kira shi take fada mishi taci jarabawar aji shidda wato WAEC mamaki ya dingayi yanda rayuwar take wani irin sauri. "Wayar waye wannan din?" Shine tambayar da yayi mata a madadin tayata murnar cin jarabawar da ta fada mishi tayi "Wayata ce, Abbu ya bani saboda naci exams dina" Yanayin muryarta yasa shi gane ta turo bakinta ne take mishi magana "Saina fasa bakin ki kina mun magana haka" Shiru tayi, ya kashe wayar daga bangaren shi, kusan kullum sai ta kira shi, yana dagawa kuma gaisuwar shi itace "Lafiya? Ko maitar ce ta motsa? Me yasa kike kirana?" Amman ranar duk da bata kira shi ba, haka zai saka wayar a gaba yai ta kallo, ko yana aji wayar na silent, rabin hankalin shi yana kan darasin da ake musu, rabin hankalin shi na kan wayar. Ranar kuma saiya nemi dalilin da zai kirata, ko yace ta duba dakin su taga ko wani takalman shi ruwan kasa suna nan, ko kuma wata takarda da yasan babu ita sam-sam. Kawai yana dai son yaji muryarta ne. Yana fitowa daga wanka ya samu har filattai Bilal ya kawo, sai da ya samu riga da wando marassa nauyi ya saka a jikin shi ya feshe da turare kamar zai fita wani waje. Sai daya zauna yake jin gajiya sosai. Filattan ya mika hannu ya dauka yana tashi tsaye. Inda ruwan leda yake jingine ya karasa ya fasa yana daukar guda daya. Bandaki ya shiga ya kara dauraye filattan ya dawo ya dauki cokulla suma ya dauraye. Bilal na kallon shi harya gama, da kan shi ya bude kulolin, wake da shinkafa ne, sai miyar kaji da kamshinta ya cika dakin. "In zuba maka ko saika yi wanka?" Rayyan ya bukata yana kallon Bilal "Ka zuba mun" Kai Rayyan ya girgiza "Jikin ka baya maka danqo?" Wani irin kallo Bilal yayi mishi "Da ruwan sikari nayi wanka da safe? Ko motar sikari muka shigo?" Murmushi Rayyan yayi da yake wahala kagani a fuskar shi. Amman sam jikin shi baya mishi dadi rana ta fito ta fadi bai cakar da Bilal din ba, bai ga hawaye a fuskar Layla ba, ko basa tare yana son yaji muryarta ta canza ta cikin waya alamar ta kwade shi a cikin tunaninta yafi a kirga "Daga tambaya?" Ya fadi yana mayar da hankalin shi kan abincin da yake zubawa a filet "Akan me jikina zaiyi danqo to?" Shiru Rayyan din yayi yana kyale shi, yana gama zuba abincin ya mayar da kulolin ya rufe, nashi filet din ya dauka yana gyara zaman shi kan kujera saboda yunwa yakeji ta fitar hankali, ko karin safe baiyi ba. Biscuit ne leda daya a cikin shi duk ranar. Bilal ya riga shi gama cin abincin, yana kallon shi ya wuce bandaki yayo wanka ya fito. Shadda ya saka a jikin shi harda hula, kafin wani lokaci ya fito das da shi. Wata leda Rayyan din yaga Bilal ya bude jakar shi ya zaro "Na fita..." Ya furta a hankali yana wucewa ya zira takalman daya fito dasu. Bangaren Ayya ya shiga yana samunta a zaune "Sai ina haka? Anata baza kamshi" Dariya yayi a kunyace "Zan dan fita ne Ayya... Amman kafin Magriba in shaa Allah zan dawo, idan ba inda zakije da motar ki..." Kafin ya karasa maganar ta katse shi da fadin "Kaje ka dauki mukullin yana kan gado..." Murmushin godiya yayi mata yana cire takalman shi ya wuce har can cikin dakin nata ya dauko, ya fito ne tace "Ka gaishe ta" Cike da kunya yace "Ayya..." Dariya tayi sosai, shima dariyar yayi yana wucewa har wajen motar Ayyar daya bude ya shiga. Saboda ita ya koyi tuqi tunda ta siyi motar da shiya fara sanin zata siyeta dan tare ma sukaje. Sai da ya tsaya yayi la'asar a hanya kafin ya nufi Kinkinau inda gidansu Aisha yake, har harabar gidan aka bude mishi ya shigar da motar yana fitowa, tsaye yayi a wajen ya kira wayarta. Daga inda yake tsaye yana hango ta tana saka hijabinta a bakin kofar da zata hadaka da cikin gidansu, kamar ta kasa jira ta saka daga cikin gida saboda zumudin da takeyi na son ganin shi. "Allah ji nake kamar na dade banganka ba" Ta furta bayan sun gaisa, dariyar shi yayi, yana kallon yanda sosai kominta yake mishi kamar Layla, har shigen yanda take magana, yanzun girma yasa yana ganin banbanci sosai a tsakanin su. Saboda tunda yake da Aisha zai kirga ranakun da ya taba ganin kalar kayanta, saboda hijabai take sakawa, hijabanta kuma masu hannune dogaye sosai har suna share titi, inba ranakun da ta saka abaya ba, ya hangi kala kalar kayan nata ta kasa. Layla kuwa hijabi wahala take mata, ranaku dai-daine zaka ganta da hijabi, ko in zataje islamiyya ko kuma tana idar da sallah ta fito daga daki kafin ta cire. Yana son kalar shigar Aisha, saboda tattare take da mutunci na gaske, yanda Layla take saka kananun kaya ko skirt din da take tafiya dakyar a cikin shi yakan mishi tsaye a rai. Musamman idan yaga fita zatayi a hakan, zaita tunanin tarin mazan da zasu ganta da wannan shigar. Sai yaga har wani haske ke gilmawa ta cikin idanuwan shi saboda kishin da yakan taso mishi. Amman ita ko a jikinta, hannuwa Aisha ta tafa a saitin fuskar shi, tana saka shi ware mata idanuwan shi da sukafi komai yi mata kyau a tattarr da shi "Tunanin me kakeyi?" Kafadu yadan daga mata yanayin murmushi "Kinyi kyau" Ya furta a madadin tambayar da tayi mishi, kanta ta saddar kasa cikin jin kunyar shi "Kaima kayi kyau ai" Kai ya girgiza mata "Idan banyi kyau bama ke ba zaki gani ba" Dariya tayi sosai, akwai gaskiya a al'amarin shi, kullum kyau yake mata, tun bata da hankali har yanzun da tayi, soyayyar da take mishi mai girma ce, ba zata taba barinta taga wani aibu a tattare da shi ba. Yau ko da wani ne zai kawo mata zance marar kyau akan Bilal tana da yakinin zuciyarta ba zata taba aminta ba, ita bata ma yarda da yanda Ummi yayarta take cewa Rayyan yafi Bilal dinta kyau. Rayyan da ko fara'a bayayi, Bilal kuwa ko hada idanuwa kukayi zai maka murmushi. Ko kamar da ake cewa sunyi ita bata gani, nesa ba kusa ba Bilal yafi mata Rayyan kyau. "Son da kike maine Allah. Amman Rayyan yana mun kyau tun muna makaranta" Ummi ta fadi, haushima taji ta tashi tabar mata wajen. Da aji daya Ummi ta wuce ta, ita tun waccen shekarar ta zana jarabawa, jamb ce bataci ba, kuma ta nace sai ABU zataje. Ita Aisha bata taba tunanin zuwa wata ABU ba, dan duk kawayenta BUK suka nema. Saboda Bilal, dan ta samu damar ganin shi kullum ta biyewa Ummi suka nemi gurbin karatu a ABU din wannan shekarar tunda ita tayi sa'ar cinye jarabawar ta jamb. "Sanda zan bar Zaria fa lokacin zaki shiga aji uku, haka ni zan dawo gida ki barni da kewar ki" Cewar Bilal da ta fada mishi inda ta cike "Zaka gane yanda nake ji duk idan kazo zaka koma" Dariya yayi sosai "Ramawa kike sonyi shisa kika zabi Zaria kenan ko?" Ya tambaya yana sata dariya itama. Yanzun ma hira sukeyi, Aisha ce kawai take rike shi da hira haka har baya sanin lokaci yaja. Mamakin jin kiran magriba da akeyi sukayi "Aisha kingani ko? Nace ma Ayya kafin Magriba zan koma" Yanayin yanda yai maganar ya sata yin dariya "Laifina ne kenan?" Kai ya daga mata. Dakyar sukayi sallama bayan ya mata alkawarin zai dawo gobe. Sai lokacin ya mika mata ledar da take hannun shi. Wasu takalma ne da yar ajinsu take siyarwa yayi mishi kyau, taki biyu ya sai mata kala daban-daban. Duk da batasan ko meye ba taji dadi har ranta, Bilal na da kyauta, lokutta da yawa inta juya cikin dakinta taga wani karamin abu da Bilal ya siya mata sai taji ya dan saukaka mata kewar shi. Anan masallacin unguwar su Aisha yayi sallar Magriba, sannan ya wuce gida. * Babu abinda Layla ta dauki gyaran da Mami take yawan yi mata kan kayan da take sakawa banda takura da rashin wayewa irin ta Mami. Ita ta kasa gane yanda duniya take tafiya da zamani yanzun sam. Lokutta da dama Mami na sakata jin daman ace ta fito a kasashen turawa ne, da yanzun ta kai shekarun da zata iya zabarwa kanta duk abinda take so, idan ma gidan zata bari tayi zaman kanta zata iya yin hakan. Ko facebook data bude, yawancin shafukan da take bi na fina-finan kasashen waje ne, sai kuma na jaruman su. Musamman ma su Kim Kardashian, sai kuma mawaka irin su Rihanna, Drake, Chris Brown da sauran su, dan tafi son wakokin wrap. Takan ji wakokin kasashen sudan, yanayin al'adarsu na burgeta matuka. Lokutta da dama ita kadai a daki tana amfani da mp3 dinta tun kafin tayi waya ta saka earpiece tana gwada kalar raye-rayen da takan gani a fina-finai. Sosai zakayi zaton ta koyi rawa idan kaga yanda take karya gabobin jikinta. Yanzun kuwa da tayi waya abin ba kama hannun yaro, videos ne da ita kaca-kaca, a jikinta take jin da ace tazo a kasar jamus ko amurka babu abinda zai hanata zuwa makarantar koyon rawa. Ana zuwa gasar da takan gani a fina-finai. Sosai abin yake mata kyau idan ta hasaso, musamman idan ta cire fuskar jaruman ta dora musu ta Rayyan. Wani lokaci abin na bata dariya matuka "Hamma da rawa" Takan fadi ita kadai, sai dai ko baiyi ba ita a kanta rawar tayi mishi kyau, musamman ace ita da shi a tare "Perfect..." Layla take tsintar kanta da fadi idan ta hango ta da Rayyan din, tun kafin ta gane ma'anar soyayya take kallonta a fina-finai, shisa sam bata sha wahalar gane me take ji akan Rayyan din ba, tunma kafin tasan da gaske son shi takeyi. Duk da wani lokaci yana fita daga ranta na yan dakika, wasu ranakun harna yini daya "Mayya..." Kalmar na bakanta mata rai sosai, kuma da gaske ne, akan shi ita din mayyar ce, kome zai mata zuciyarta har tsalle takeyi idan tagan shi, kuma bata fasa daga waya ta kira shi sai dai idan bata da kati. Ko da ace shi da Bilal basa ABU ita kam batajin zata zauna karatu a garin Kano, saboda babu yanda za'ayi abarta ta zauna hostel idan dai a BUK ko Polytechnic take. Shisa bata fadawa kowa ba sanda zata yanki jamb, zabinta na farko ABU din ta saka, tana son samun abinda ake kira "full high institution experience" a turance. Batason sa idon Mami, rayuwar jami'a take son barjewa yanda ya kamata. Ta kuma yi sa'ar samun 181 a jamb din, ta tsallake dakyar. Tasan me take so, fannin turanci ne ta zaba saboda tana son samu aiki da wata babbar jarida ko gidan radio. BBC ne harinta, ko ba komai watakila tana da rabon zuwa kasar waje. Shisa ta gama tsara yanda komai zai fito, bata shiga tashin hankali ba sai lokacin da aka fara saida fam din jarabawar tace daliban da zasu sami gurbin karatu. Saboda gefe Mami ta koma tana fadin "Duk makarantun da suke garin Kano? Sai kinje Zaria? Zubaida data gama karatunta kinga tabar gari. Khalifa kan shi cikin garin nan yayi nashi karatun, babu inda zakije, gara ma kiyi magana da Abbunku a sama miki gurbin karatu ko a legal ne idan BUK din ba zata samu ba" Kuka tayi ranar kamar idanuwanta zasu tsiyaye, dan kiri kiri taga Mami na neman ruguza mata tarin burin da take da shi, a tsayin zamanta da Mami bata taba jin maraici ba sai ranar, watakila inda iyayenta suna raye zasu taimaka mata wajen ganin ta cika burinta ba suyi kokarin zame mata katanga a tsakaninta da abinda take son zama ba. Da Abbu yasa aka kirata ma kuka ta fashe mishi da shi "Abbu dan ina mace bazan iya tafiya wani waje karatu ba? Dan ina mace bani da 'yan cin zabi? Me yasa Mami ba take son hanani? Karatu ne fa ba wani abu marar kyau ba. Ita ya kamata ta karfafa mun gwiwa in cika burina" Ta karasa tana wani irin kuka, sosai yake kula da duka yaran. A duk gidan kuma daga Layla sai Jabir ne sukayi wata irin wayewa, rayuwar turawa ita suka saka a gabansu, garama Layla ba sosai takan nuna ba, amman Jabir sai da ya tabbatar har turancin shi ya gyara shi yanda idan yana magana zaka rantse da Allah ba'a kasar najeriya yayi karatu ba, to Layla ma yaji haka take lankwasa harshe "Jabir turai" Shine tsokanar da yakan yiwa dan nashi idan yaji yana magana wani lokacin, ko Layla yakan tsokaneta "Ke da Jabir sai kun tauna harshen ku wata rana" Kuma da gaskiyar shi, Jabir shine ya fara sakata son gyara turancin ta, haka suke zama kullum tsayin shekara uku suna wannan wahalar, Mami idan tagan su takan ce "Ikon Allah, lallai sa kai wanda yafi bauta ciwo, da Qur'ani ne kukewa wannan nacin, ba'a kasar Kano ba, har zagayen Najeriya sai an san da zaman ku" Dariya kawai sukanyi dan a ganin su ita ba zata taba ganewa ba. Ko Jabir din "Languages" yake karanta a BUK, kuma yanzun da yake shekara ta biyu, a tarihin department din ba'a taba samun dalibi mai kokarin shi ba. Abbu ma kance "Da alama Jabir zaka samu gwamnati ta dauki dawainiyar karatun ka zuwa kasar waje in har kaci gaba da tafiya a haka" Itama Layla wannan burin take da shi, amman Mami na neman hanata. Shiru Abbu yayi dan baisan me ya kamata yace ma Layla din ba. Har ran shi yana son su da karatu, a matsayinta na 'ya mace musulunci yayi mata wata daraja mai girma, suma kuma ya basu 'yancin kareta da dukkan karfin su. Ya fahimci Mami tunda sunyi zancen tun kafin yasa ta turo mishi Layla "Kana kallon yanda nake fama da Layla kan wannan rayuwar turawan data dorawa kanta... Ina ga ta bar inda babu idanuwan kowa?" Mami din ta fadi muryarta na karyewa, har ranta tana tsoron barin Layla Kano. Karatu duk inda kake zakayi. Shima kuma ya aminta da abinda tace din, amman yanda Layla take kuka a gabanshi ya karyar mishi da zuciya "Abbu idan kaima ka hana zaku sakani yin wani tunani daban" Layla ta furta tana tashi tabar shi anan zaune. Ya jima shiru, maganganunta sun jefa shi wani tunani daban, harga Allah yafi basu kulawa ita da Bilal sai Haris da yanayin shine son kulawar. Amman ita da Bilal na minti daya bayason suji rashin iyayen su, yasan zafin maraici duk da yayi wayon sanin nashi iyayen, su da basuyi wannan wayan ba baisan abinda sukeji ba, yana kokarin ganin basuji komai ba. Bayason Layla taji kamar dan bata fito daga jikinsu bane suke son zama katanga tsakaninta da burinta. Yana ganin tayi yarinta ta fahimci cewa basa nufin komai a kanta sai alkhairi, komai da zasuyi dan su kareta ne badan komai ba. Abin ya dame shi, kwana yayi yana juyi, washegari kam yana tashi daga aiki saida ya biya wajen abokin shi Nasiru dan ya nemi shawarar shi, bai boye mishi komai ba "Ina tsoron tafiyar ta karatu wani gari, har raina ina tsoron hakan saboda ita macece" Murmushi Nasiru yayi "Kai kasan indan tani ne yara mata ba zasu wuce matakin sakandire ba, Allah yasan Nabila tayi karatune saboda miji bai fito ba sanda ta gama, Zainabu fa? Ita da kanta ta zabi auren da miji ya fito, sakandiren ma bata samu gamawa ba" Kai Abbu ya jinjina mishi, duka shine shaida, yanda Nasiru yasan sirrikan shi, haka shima, suna neman shawarar juna a dukkan lamurran su "Meye muke gudu Ahmadi? Lalacewar yaran ce abin gudu, gani muke idan suna gaban idanuwan mu zamu fi kare su yanda ya kamata. Ni ma tunanin da nakeyi kenan yasa nake son nisanta matan da zurfin karatun boko...sai dai rayuwa ta koyamun ba dabarar mu a tarbiyar yara... Ka duba Bashari, a gaban idona tarbiyar tashi take ta tabarbarewa, duka, zagi babu wanda bamuyi ba, yanzun ba addu'a muka koma ba? Shine aka fara samun dan cigaba" Numfashi Abbu ya sauke "Hakane, kana ganin in barta ta tafi?" Kai Nasiru ya girgiza mishi "Ba ina cewa kabarta ta tafi bane kai tsaye, ina fada maka karka labe a bayan gudun lalacewar tarbiyya wajen hanata zuwan. A gaban idanuwanka abinda kake gudu zai iya faruwa, kai dai kayi iya yinka wajen tarbiyar, ka kuma roki Allah ya kare abinda idanuwanka ba zasu gani ba..." Maganganun Nasirun sun kara daure mishi kai, duk yanda yaso ya furta da bakin shi cewa yabar Layla ta tafi Zaria yaki, shawarar shi duka akwai kofar zabi daya barma Ahmadin. Haka Yaya Ayuba da ya same shi da zancen "Ba gari ba, kaga Nadiya Madina tayo karatunta, duk kuwa da tarin surutun da akai tayi a kai. Gata ta kammala ta dawo lafiya tana dakin mijinta. Kamar yanda kace Nasiru ya fada maka ne, tarbiya iya yinka zakayi, sauran da yafi karfin ka ka hada da addu'a. Karka barta ta tafi sai kana da yakinin duka zuciyarka ta amince maka da tafiyar, idan baka aminta ba hakurin zaifi zama alkhairi. Idan bata fahimce ka ba yau, wata rana zata fahimce ka" Akan shawarwarin nasu yaita tunani har kwana biyu kafin ya natsu da barin Layla ta tafi, ranar har tsakar dare ya tashi yayi sallah yana rokon Allah daya kare mishi yaran shi, ya rabasu da abokai gurbatattu. Dakyar ya shawo kan Mami "Shikenan, Allah yasa hakan ya zama alkhairi" Shine maganarta da wani irin sanyin murya daya taba shi. Layla tayi murna kamar zata goya Abbu. Neman hutun kwana daya yayi a wajen aiki da lokacin jarabawar nata yazo, da kanshi ya dauketa suka tafi har garin Zaria, kwana daya sukayi ta zana jarabawar suka dawo. Ya fadawa Ayya zaije Zaria, dalilin ne bai sanar da ita ba, saboda bai jima da sukayi rikici akan karar Rayyan da Layla ba, idan taji zataje Zaria karatu wani sabon tashin hankalin da bai shirya ba za'ayi a gidan. Cikin ikon Allah Layla ta ci jarabawar inda ta sami gurbin karatu a jami'ar Ahmadu Bello. Ba ta da kalaman da zata dora farin cikinta a kai ranar, Abbu da kanshi yaje Zaria ya amso mata admission letter dinta, kuma a hankali ita da Mami suke shirin tafiyar tata, tana kokarin ganin duka ranakun batayi wani abu da zai bata ran Mamin ba, kananun kaya ma ta daga musu, dogayen riguna take ta fama dasu. Abbu kuwa aikawa yayi aka kira mishi Bilal ranar daya amso admission letter din Layla. Yana shigowa bayan sun gaisa ya zauna, Abbu ya mika mishi takardar, amsa Bilal yayi yana dubawa, duk kuwa da Layla ta fada mishi, yayi mata murna sosai da sosai "Nagani Abbu, ta fadamun..." Dan lokacin da ta gaya mishi inda ta cika a jamb dinta ta dora da "Babu wanda na fadawa fa, kai kadaj na gayawa" Cikin idanuwa ya kalleta "Me yasa?" Ya tambaya cikin son sani, dan daga mishi kafadu tayi, kawai saboda shi dinne, saboda tasan zai goyi bayanta, zai tayata son abinda take so, zai karfafa mata gwiwa "Saboda kawai kaine" Ta karasa maganar tana saka shi furta "Hmmm" Cikin rashin sanin abinda ya kamata yace, lokutta irin haka sai ta saka yaji kamar yana da wani muhimmanci mai girma a rayuwarta. Sai ya ganta tare da Rayyan take karyata mishi hakan. Sai da Abbu ya gyara murya tukunna yace "Layla kanwa ce a wajen ka, ko bance ka kula da ita ba zakayi. Amman ina so da bakina in roki alfarmar nan, Bilal ka kula da ita, dan Allah ka kula da ita, kudin amana ne a wajena, akan Layla ina so in raba amanar da kai" Wani irin nauyi Bilal yaji kalaman Abbu sunyi mishi, nauyi sosai "Ka kula da ita kamar yanda kake tunanin zan kula da ita, a zaman da zatayi a Zaria ka kareta daga dukkan abinda zaka iya kamar yanda kake tunanin ina kare ku, alfarma ce nake nema a wajen ka" Wannan karin dakyar Bilal yake fitar da numfashi saboda nauyin da kalaman Abbu sukayi mishi, abinda yake roko a wajen shi abune mai girma, amana yake bashi, ya kuma san daraja da hukunci hakan a matakin addini "In shaa Allah Abbu zanyi kokari" Ya furta muryar shi can kasan makoshi, kai kawai Abbu ya jinjina, dakyar Bilal din ya iya tashi dan duk gabban jikin shi a sanyaye yake jinsu, har yakai kofa Abbu yace "Bilal..." Juyowa yayi "Ka kula da Rayyan, ka kula da Hamman ka" Ya karashe maganar cike da roko a idanuwan shi, bai taba cewa Bilal din ya kula da Rayyan ba, saboda yana ganin yanda yake wannan kokarin a duk rana, ya kuma sha jin Ayya nawa Bilal din wannan rokon, yau din Abbu wani irin rauni yake ji naban mamaki, shisa kalaman suka subuce mishi, kai kawai Bilal ya iya daga mishi, da nauyin zuciya ya fice daga dakin Abbu yana nufar bangaren su, inda ya hango Layla ta dora hannunta akan kafadar Rayyan da alama akwai abinda take fada mishi, tureta yayi yana fadin kalaman da Bilal baiji ba, yana kallo Layla ta juya, Rayyan din na kamo hannunta ya dawo da ita. Lumshe idanuwan shi yayi zuciyar shi na wani irin dokawa, ta ina zai fara? Wanne alkawari ne ya dauka mai girma haka? Ya daukar wa Abbu alkawarin zai kula da Layla kamar yanda Abbun zai kula da ita, idan tana matsayin yar shi, idan tana matsayin kanwar shi bayason tana rungumar namijin da ba muharraminta ba kamar hakan ba komai bane ba, bayason ta kusa da Rayyan, Abbu yace ya kareta daga dukkan abinda zai iya. Abbu ya kara da fadin ya kula da Rayyan, akwai tarin ma'anoni da yake tattare da kalmar "kulawa" Ta ina zai fara kare Layla daga dukkan abinda zai iya? Ta ina zai fara idan abin farko da yake son kareta daga shi Rayyan ne? Ta ina zai fara kula da Rayyan idan bai hana shi daukar ma kan shi zunuban da suke tattare da wannan rungume-rungumen da sukeyi ba? Ta ina zai fara hana shi abinda ya shafi Layla? Ta ina zai fara kula da su idan matakin farko ya hada da rabasu da junan su? Kaddarar su mai girma ce Kaddarar su ta fara tun kafin sanin su. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:07 PM - 111: Nov 23, 2020 11 Kallon Abbu takeyi, bakin shi motsi yakeyi, da alama magana yakeyi, sautin maganar tashi ce bata karasawa kunnuwanta. Sosai take kallon shi tana kokarin fahimtar sauran zantukan da yakeyi tunda ta daina ganewa daga "....Tare da Layla zasu koma Zaria, itama ta sami gurbin karatu acan..." Duk abinda ya fada kafin wannan kalaman batajin suna da wani muhimmanci a wajenta, abinda yake fada bayansu kuwa bata ma ji ba sam-sam. Ko bayan nashi bakin ya daina motsi, ta bude nata yafi sau biyar tana rufewa cikin rashin sanin abinda ya kamata ta fadi. Tashin hankali take ciki, irin wanda bata taba hangowa ba, a gaban idanuwanta abinda take tunani ba matsala bane yake zame mata katuwar matsala. Wanne irin Malami ne wannan mai zafi Mami take da shi, zuwa yanzun Ayya zata iya rantsewa duk wani sirri nata a hannun Mami yake. In ba haka ba, babu yanda za'ayi data like wata kofar sai Mami ta sake huda mata wata. Duka yaushe ta samu kan Rayyan din haka, yaushe ta samu harya dauki waya ya kirata. Wannan zuwan ne har sau biyu da kan shi ya sameta yana gaisheta. Kuma ita da idanuwanta bata ganshi tare da Layla ba, har wani bacci takeyi mai cike da natsuwa a tsayin hutun nan da su Rayyan din sukayi. Saboda tana ganin duk kudadenta da ta bawa Malam basu tashi a banza ba, aiki yaci. Ashe tana bacci Mami nacan tana wargaza mata abinda ta kashe maqudan kudi wajen ganin ta kulla. Ta rasa kalar bala'in nan, ta kuma rasa yanda zatayi da karan tsaye da Mami tayi mata a makoshi. "Layla naji kace zataje Zaria... Ahmadi Layla..." Cewar Ayya tana kallon shi kamar wadda bata cikin hayyacinta, wannan rikicin da yake gani cikin idanuwanta shi yake gudu yasa bai fada mata maganar tafiyar Layla Zaria ba. Wani zaiyi tunanin yana tsoron rikicin Ayya ne, kuma ba haka bane ba, yana gudun abinda zai bata mata rai sosai da sosai. Saboda yasan matar shi, kusan tare da juna suka mallaki hankalin su, babu kalar rikici da shirmen ta da baigani ba tun kuruciya. Ta rigada ta sakama kanta tunanin cewa Mami na bibiyarta, abinda duk zai fada mata kuwa ba sauraren shi zatayi ba, ya sani. In ba ranar da Allah ya nuna mata tagani da idanuwanta cewa Mami bata bibiyarta ba, ba zata taba cire wannan tunanin daga ranta ba. Shisa ya kasa samun kwarin gwiwar fada mata Layla zataje Zaria. Yasan tunanin farko da zata fara bana cewa Layla da kanta ta zabi Zaria bane, sam Ayya ba zatayi wannan tunanin ba, idan yace mata bada son ran Mami za'ayi tafiyar ba zai ja musu wata matsalar, kishin shi zaisa ta dauka yana kokarin goyon bayan Mami ne, yanzun dole ya nuna mata yana tare da ita dari bisa dari ko dan a samu zaman lafiya "Eh, ta samu gurbin karatu a can, tana son karantar bangaren yaren turanci" Abbu yai maganar cikin taushin murya, kallon shin dai Ayya takeyi, kafin wata dariyar ta kwace mata "Idan dole ya zame mata sai tabar gari zatayi karatu, duk garuruwan da suke cikin Najeriya sai Zaria? Kuma kana kallo kabarta? Me yasa sai Zaria idan ba Rayyan take son tabi can din ba. Na rokeka, Ahmadi na rokeka daka raba Maryama da yarana, na kara rokon ka daka ja nata kunne ta kyalemun ahalina amman kayi biris dani" Ayya take fadi tana haki saboda bacin rai "Dan Allah ki kwantar da hankalin ki Maimuna" Wani irin kallo ta watsa mishi "Gayamun kake in kwantar da hankalina? Ka damu da kwanciyar hankalin nawa ne? Ka damu dashi? Da ka damu da kwanciyar hankalina da baka bar Layla ta bimun yaro har Zaria ba... Wallahi sam abin nan ba zai yiwu ba..." Ayya ta karasa muryarta ba karyewa saboda wasu hawayen bakin ciki da taji sun cika mata idanuwa, hannunta Abbu ya kamo cikin sigar lallashi, ta fisge tana mikewa "Na gaya maka ka ja mata kunne bakayi ba, na fada maka... Karka ga laifina idan zaman lafiya yayi karanci a cikin gidan nan" Cewar Ayya tana wucewa ta fita daga dakin, yanda ta doko kofar saida Abbu ya runtsa idanuwan shi. Wannan abin shi yake gudu shisa ya zabi yau daren tafiyarsu Rayyan din tukunna ya fada mata. Ko rikici zatayi bayaso tayi a gaban yaran, duk da in dai ana sabawa da rigimar Ayya, to zai iya cewa duk wanda ya ke kwana yana tashi a cikin gidan ya saba. Amman wani lokaci sai tasan yanda tayi ta fada maka maganar da zata zo wuyanka tayi tsaye. Shi jiya ma da yaje wajen Yaya Ayuba yake bashi shawara tunda dai yana da rufin asiri, kuma yana da hali ya kamata ace ya sami yar karamar mota an ba su Bilal, saboda zirga-zirga. Tunda Yaya Ayuba ya kula da yanda yake yawan ganin sun zo gida daga makaranta, shima nashi yaran biyu da suke karatu a Bauchi motar ya hadasu da ita. Kuma ya dauki shawarar Yaya Ayuba. Akwai 'yar karamar mota a gidan da yakan dauka wani lokaci, ko in za'a kai Mami unguwa. Tunda ita Ayya tana da abin hawa. Ya kuma rigada ya kira Bilal tun dazun yace su taho da Rayyan, shigar da sukayi kuwa a fuskar Rayyan zaka fahimci yanda yake a takure, dan ko zama cikin kujera sosai yakiyi, a gefen hannun kujerar da Bilal ya zauna shima nan ya samu ya zauna. Yana saka Abbu jinjina wannan lamari. Ace ka haifi yaro, kiri-kiri yana gudunka, shekaranjiya Rayyan na hango shi yayi baya yana komawa inda ya fito, abin yayiwa Abbu ciwo ba kadan ba. Ya kasa sabawa da yanda Rayyan yake baya-baya da shi. Ko lambar wayar Rayyan din bashida ita, baya kuma zaton Rayyan yana da lambar shi a waya shima. Inda ace ya yarda da sihirine, yana kuma da abokin gaba, tabbas zaice an saka mishi hannu ne, an shiga tsakanin shi da danshi. Amman yasan bashida abokin fada, babu wanda zai kuma zarga da lokacin batawa wajen bibiyar rayuwar shi. Dauke idanuwa yayi daga kan Rayyan yana mayarwa kan Bilal bayan sun gaisa "Daman naga zirga-zirgar da kuke tsakanin Kano da Zaria tayi yawa, ga Layla kuma yanzun. Shisa nace wannan karin ku koma da mota, kunga duk idan zaku zo ba sai kunyi ta jigilar zuwa tasha ba" Murmushi Bilal yayi yana tashi ya karbi mukullin motar da Abbu ya dago hadi da cewa "Allah ya kara arziqi da lafiya Abbu...mungode..." Ya koma ya zauna yana kallon Rayyan "Hamma ga mota Abbu ya bamu" Kamar Rayyan din baya dakin, sai lokacin ya dago da idanuwan shi yana kallon Bilal "Kai kasan ban iya tuqi ba, me yasa kake fadamun?" Rayyan ya karasa maganar yana dan kankance idanuwan shi saboda yanda kanshi yake bala'in sarawa tun da Bilal yace mishi Abbu yana kiran su. Sanda yake dosar dakin Abbu din ji yake kamar ana zare mishi rai. Kafafuwan shi ma rawa suka dingayi kamar ba zai iya karasawa ba, shisa kallo daya yayiwa Abbu ya mayar da kanshi ya sauke. Muryar Abbu dinma cikin kunnuwan shi kara mishi abinda yake ji takeyi. Jikin shi yayi wani irin dumi kamar gidan biredi. Duk akan za'a bada wata mota ne aka kira shi ya shiga wannan halin. Duk ranar bayajin dadin jikin shi, shisa ko da Bilal yayi mishi magana baiyi gardama ba ya mike, yasan halin Abbu, in har magana yake sonyi dasu da gaske, idan ma baije ba shi zaizo ya same su har daki, da kuma yasan yanda Rayyan din yake ji duk idan sukayi kusanci taku goma a tsakanin su da bai fara zuwa kusa da shi ba, balle harya shigo dakin da yake yana saka iskar duk da take dakin tayi mishi kadan, zai rantse ko meye a tsakanin su da Abbu, yana girma ne abin ma yana kara girma. Ga mugaye mafarkan da yake fama dasu daya runtse idanuwan shi. Rabon shi da bacci da daddare batare da taimakon wasu kwayoyi ba harya manta, zuwa yanzun saboda karatun shi yana fahimtar abubuwa da yawa da suka shafi kwakwalwar shi, yana kokarin ganin ya fassara matsalolin shi scientifically batare da zargin iskokai da yakan ji ana hada shi dasu ba. Yasan yana da matsaloli kala-kala, ciki harda abinda ake kira depression a turance, yanayin da kwararrun likitocin daya gani a fannin kwakwalwa sun kasa taimaka mishi wajen gano abinda ya haddasa mishi depression din. Kuma shine ma a fadar su ya jaza mishi insomnia. Shisa baya iya bacci da dare, babu wanda yasan baya iya bacci da dare tun tasowar shi. Har Bilal da suke kwana waje daya su tashi baisan baya iya bacci da dare ba, tunda zai kwanta ya huta, zai saka hakarkarin shi a kasa, lokacin kuma duk da zaiji baccin to yana runtsa idanuwan shi ya fara wasu irin hargitsatstsun mafarkai da baya iya tuna farkon su balle karshen sune suke tashin shi. Da farko-farko magungunan da aka bashi kala biyu wato Anti-depressant sun dan fara mishi aiki, tunda yana bacci, amman magungunan suna saka mishi wani irin qunci na daban, sun kara mishi rashin hakuri da mutane. Abu kadan ne yake harzuqa shi fiye da yanda yakeyi da. Daga baya ma guda biyu sun mishi kadan, bayajin komai idan ya sha. Yanzun a halin da yake ciki guda hudu asibiti sukace ya dinga sha. Kuma ba'a bayarwa da yawa, na sati biyu suke bashi, idan ma ya shanye kafin lokacin yasan ba zasu sake siyar mishi ba. Sai dai cikin gidan da yake haya akwai yaro daya daya kula yana siyar da kwayoyi, a wajen shi Rayyan yake siya, akwai wanda suka fi na asibitin karfi, kuma suna taimaka mishi ba kadan ba. Yanzun ma so yake ya tashi yaje yayi wani hadin da zai batar mishi da ciwon kan da yake ji. Inda yasan maganar wata mota ce Abbu zai mishi sam bazai zo ba. Idan waje baya kama dole ya hau mota ba, bata dame shi ba. Ko makaranta yana rigan Bilal fita, daya saka earpiece da wayar shi zai taka da kafafuwan shi, yafi zabar yayi tafiya akan ya hau mashin. Saboda ita kadaice abinda yakan taimaka mishi ya samu natsuwa wasu lokuttan. "Jikin ka baya maka ciwo?" Bilal kan tambaye shi wani lokaci, kafadu yakan dagawa Bilal din kawai tunda baisan yanda zai fara mishi bayani cewar wannan doguwar tafiyar da yakeyi wani lokaci ita kadaice katangar da yakeji a tsakanin shi da tabin hankali, lokutta da dama yanajin kamar zai ta kurma ihu saboda duhun da yakeji cikin kan shi. Wasu lokuttan har sallah ma bai samun nutsuwa idan yayita, kullum cikin neman wani abu da zai saka mishi natsuwar zuciya yake amman ya rasa. Haka yake rayuwa badan yanajin dadinta ba, amman babu wanda yake fahimtar haka. Wani lokacin yakan ji dariya daga dukkan zuciyar shi idan ya addabi Layla. Ko yana ganin yanda take son kwala mishi wani abu a cikin idanuwan nan nata da suke fadar mishi da gaba amman babu yanda zatayi. Shisa idan bai ganta ba bayajin dadi, Layla kan samar mishi da natsuwa wasu lokuttan. Mikewa yayi, daga Abbu har Bilal binshi sukeyi da kallo harya fice daga dakin, kafin Bilal ya mayar da idanuwan shi kan Abbu da yake kallon kofa har lokacin da wani yanayi a fuskar Abbun da Bilal yakeji har cikin zuciyar shi. Shima mikewa yayi "Abbu sai da safe" Wani numfashi mai nauyi Abbu ya sauke yana fadin "Sai da safe Bilal, Allah ya tashemu lafiya. Allah kuma ya saukeku lafiya idan bamu kara haduwa da safe kafin ku wuce ba" Kai Bilal ya jinjina "Amin. Zamu shigo ma ai in shaa Allah..." Sallama yayiwa Abbu yana fita, dakin su ya nufa inda ya sami Rayyan a zaune da kofin ruwa a hannun shi. Da alama hankalin shi na wani wajen dan ko sallamar da Bilal yayi bai amsa ba. Shikuma yayi shirune saboda yanda kan shi yake sarawa har lokacin, yaki jin numfashin shi ya koma dai-dai. Iska bata kai mishi inda ya kamata, kwayoyin da ya sha yake jira su narke su fara mishi aiki ko zai dawo dai-dai. Shisa yake zaune shiru yana sauraren ikon Allah. Bilal gado ya hau ya matsa can yana kwanciya saboda baccin da yake idanuwan shi, kuma ya kasance cikin jerin mutanen da baccin su yake da muhimmanci a wajen su, sam abinda yake shiga tsakanin shi da bacci to gagarumine. * Idan tace yanda taga dare haka taga rana batajin zatayi karya. Bacci ko da ya saceta to barawo ne tabbas, haka ta kwana tana juyi, ta kwana tana tunanin a duniya abinda tayiwa Mami mai zafi haka da take son taga bayanta. Kamar ba ita ta aure mata miji ba, kamar ba ita tayi mata babban laifi ba, kamar ba ita ta sakata raba soyayyar Ahmadi da take ji har kasan ruhinta ba. Duk ta hakura, duk ta kauda kai, badan kishinta ya ragu ko kadan ba, ko giccin Abbu tagani ta bangaren Mami sai taji kamar zuciyarta zata fado. Ranar karshe da taga Abbu yana dariya da Mami numfashinta barazana ya dinga yi mata. Dariyar Abbu ita kadai take son jin sautinta, a yanzun inda zata baiwa Mami duk wani abu data mallaka ciki harda dukiyar Abbu din ta fice tabarta daga ita sai shi zata mika mata da gudu. Amman Mami tabbas mayya ce, bata hada jini da nupawa ba kamar Layla, amman watakila kafin Allah ya dauki ran Mannira ta baiwa Layla kankarun maitar, ta kuma zo dasu cikin gidan nan ta raba su da Mami. Duk abinda tayi mata bai isheta ba, tana hango tauraron Rayyan da Malam ya fada musu mai haskene sosai, shisa take son dishe shi. Saboda bata tsoron Allah, bata tunanin ya kamata ta kyaleta ta huta haka "Allah ya isa tsakanina dake Maryama, wallahi ba zan yafe miki ba. Kin hanamun natsuwa, kudin dana tara ma kina neman sakani asarar su wajen malamai, me nayi miki haka?" Ayya ta dinga fadi tana juyi har wayewar gari, kan kunnenta aka kira sallar asuba. Dakyar ta mike tana gabatar da sallah, addu'ar nemarwa yaranta tsari tayi tana mikewa ta wuce kitchen tunda tasan Rukayya ko da zata fito sai ta gama karatun Qur'ani da azkar dinta na safe. Kuma tana son su Bilal suci wani abu kafin su fita, akan ce "Mayu sunfi samun damar kama mutum idan ya fita baiyi karin safe ba" To su da Mayya zasuyi tafiyar tasu kacokan, gara ta basu duk wata kariya da zata iya, kafin ta samu ta kira Hajiya Dije dan samun mafitar wannan bala'in, farraku take so ayi ma Layla tsakaninta da Bilal da Rayyan. Gara ayi musu katanga ta bakin karfe yanda zata sama musu lafiya duk kowa ya huta. Ko nawane kuwa zata kashe dan ganin an rabasu, da ita Mami take magana. "Mu zuba mugani Maryama. Ke din banza" Ta fadi tana kara cigaba da fere doya. Saboda tana tunani sai taga aikin yayi mata sauri sosai, dan harta soya doya da kwai kafin wani lokaci. Aikam kamar daga sama taga Rayyan ya fado kitchen din "Ayya yunwa nake ji" Ya furta da wani yanayi na rauni a muryar shi. Magungunan da yasha ne yasan suka wawake mishi ciki haka, kuma rabon shi da abinci tun jiya da rana, baici na dare ba saboda bayajin dadi. Yau dakyar ya fita masallaci, a hanyar dawowa kuwa har wani haske yake gani yana gilma mishi ta cikin idanuwan shi, a daddafe yayi wanka ya sake kaya yana yanke shawarar zuwa wajen Ayya din ta bashi koma meye yaci kafin yunwa ta kashe shi "Ga doya na soya muku daman, in hada maka shayi?" Ayya ta bukata tana kallon fuskar Rayyan din, dan gani takeyi kamar zai iya juyawa kowanne lokaci yace tafiya zaiyi. Yaushe rabon da tagan shi da sassafe haka. Kai kawai ya daga mata yana bude kular ya dauki doya daya yana sakawa a bakin shi. Yunwa yake ji sosai, shayin Ayya take hada mishi, batare daya kalleta ba yace "Kar ki saka mun sikari da yawa Ayya" Bata saka mishi din ba, tana gama hadawa ta sami faranti ta zuba mishi doyar a ciki, da kanta ta dauko mishi zuwa falo yana biye da ita da kofin shayin shi a hannu. Ajiye mishi tayi, dai-dai lokacin da Rukayya ta fito daga dakin "Hamma..." Ta furta cike da mamaki tana dorawa da "Ina kwana" Kallonta Rayyan yayi "Rukayya. Lafiya...ya kika tashi?" Wani murmushi da tayi mishi sai tasa yanajin wani iri, saboda tanayi kamar ya bata wani abu. Taji dadi har ranta, rabon dayayi magana mai tsayi da ita harta manta, yaushe ma tagan shi balle yayi mata magana "Alhamdulillah, yau zaku koma makaranta ko?" Zama Rayyan yayi yana jin kurbar shayin hadi da kallonta, idan tasan yau zai koma meyasa take kara tambayar shi, shisa bai son a fara wasu kananun gaishe-gaishe, suna jan surutun da bai kamata ba. Kai kawai ya daga mata yanaci gaba da karyawa abin shi "Allah ya tsare muku hanya ya kaiku lafiya" Kallonta ya karayi dan shine kawai amsar da zata samu yana cigaba da abinda yakeyi, itama kitchen ta wuce abinta. A hakan ma itace da godiya yau tunda har an kulata anyi magana da ita. Yana karasa cinye doyar ya tashi da kofin da plate din a hannun shi, daya shiga kitchen saida ya wanke su yana mayarwa inda yaga Ayya ta dauko su tukunna ya fito, ita kuma tana bakin kofa tana kallon shi, zuciyarta cike taf da kaunar yaron nata, yanzun take kara tabbatar da duk a yaranta babu mai sanyin hali irin na Rayyan, tun yana dan karamin shi yake da sanyin hali, lokaci daya ya canza, tayi sakaci da ta dauka abinda yasha ne, sam bashi bane ba. Mami ce ta shiga tsakaninta da yaronta ta juyar dashi ya koma haka. Amman Allah yana nan "In zuba maka ka tafi da itane? Ko zakuci a hanya?" Dan jim Rayyan yayi, doyar tayi mishi dadi, yasan kuma inba gida ya dawo ba, babu wani abu da zaici mai dadi. Girkin Bilal hadiyewa kawai yake batare daya tsaya yaji dandanon a bakin shi ba saboda yanda yake a hargitse. Amman gara rashin dadin girkin tunda a gaban shi akayi, ya kuma daina cin abinci a waje yanzun tunda Bilal din yana girka musu. Kwanaki yace "Bansan zan kewar Hamma Haris ba sai yanzun. Bilal kasheni zakayi? Meye wannan ka dafa?" Harara Bilal din ya watsa mishi, duk da shima a lokacin kawai yana tura taliyar ne badan yana gane kanta ba "Surutun duk da ba'a so kayi shi kakeyi, wallahi zan daina dafawa in dinga siya a waje" Hakan da Bilal ya fadi ne yasa Rayyan din yin shiru, amman da gaske yake yayi kewar Haris a makarantar. Tunda abincin shi da dadi, kuma ranaku dai-daine baya dafawa ya kawo musu, wani lokacin ma har miyar da zasu kwana biyu idan yazo yana musu. Amman abinda Bilal yake dafawa yana da tabbacin ba abincin mutane bane ba. "Akwai ne?" Ya bukata yana kallon fuskar Ayya, saboda bayason su wanda zasuci a juye musu, kuma suzo sai sun sake dafawa "Saboda ku na dafa daman ai..." Ayya tayi maganar tana murmushi, shiru Rayyan yayi yana tsayawa. Hakan ya bata amsar da take bukata. Manyan robobin da takan zuba kayan miya ko saura abincin inta rage ta saka a firij ta dauko tana juye musu doyar ta fito ta bawa Rayyan din. Yana karba ya fice daga dakin, sosai zuwan shi ya ragewa Ayya damuwar data kwana da ita, gaskiya wannan Malamin ya cancanci duk tarin kudin daya amsa a hannunta, aikin shi mai karfine, ta dauka Mami tayi nasara. Dole ta kara komawa wajen shi yayi mata wannan aikin, tunda da tana tunanin tayiwa Hajiya Dije magana ne su sake wani Malamin da yafi shi zafi. Rayyan kam dakin su ya wuce yana ajiye doyar da fadin "Ayya ce ta zuba mana. Ni naci amman..." Kai Bilal ya jinjina mishi, shi ba iya cin abinci yakeyi da sassafe haka ba. Jakun kunan su ya dauka ya kai mota, daman duk ya saka na Hindu a ciki. Ya dawo ya dauki robar da Rayyan din ya ajiye. Tun jiya da rana ya siyo ruwan roba tunda yasan Rayyan da shan ruwa kuma ba siya zai ya tafi da shi ba. To yanzun tunda motar su ce, duka ledar ya saka musu a ciki, ya dawo yana fadin "Duka abinda zaka dauka ne ka fito da shi?" Kai Rayyan din ya daga mishi "Yayi kyau" Bilal ya furta yana ficewa, tunda suka tashi Rayyan din yaga Bilal na sha mishi kamshi, yayi tunanin duniya ko yayi mishi wani abu ya kasa tunawa, shi bayason Bilal na mishi haka babu wani dalili. Sai yana saka shi jin babu dadi sam-sam. Mikewa yayi tunda yasan Bilal din zaije yayi sallama da Ayya ne, dakin ya kulle yana saka mukullin a aljihun shi. Wajen motar ya karasa, gajiya da yayi da tsayuwa ya saka shi taba murfin bayan motar yana samu Bilal bai rufe ba, nan ya shiga. Ba zai zauna a gaba Bilal din na mishi wannan kumbure-kumburen ba. Bilal kuwa wajen Ayya yaje sunayin sallama, da nauyin jiki ya fito saboda tana kara fada mishi ya kula da kan shi, ya kula da Rayyan. Tana kara mishi nauyi akan wanda Abbu ya dora mishi. A hanya ya hadu da Layla da ta saka hijab, sai yaga tayi mishi kyau sosai, fuskarta fayau babu kwalliya yau. "Hamma ina kwana" Ta fadi da bacci cike da muryarta, bata ma jira ya amsa ba ta wuce. Zumudi ya hanata bacci daren jiya. Sai wajen karfe uku da rabi na dare, sai taga kamar tana rufe idanuwanta Mami tazo ta tasheta, ta samu tayi sallah. Nasiha tun da Abbu ya amince da tafiyarta Mami takeyi mata, yau dinma tana gama shiryawa taga Mami a ranta tace "Ni kam naga ta kaina... Wa'azi da asubar nan" A fili kuwa murmushi tayiwa Mami har hakoranta suka bayyana. Mamin ma murmushin tayi "Yar nema, yau ni akeyiwa wannan murmushin da bai kai zuci ba ko?" Dariya Layla tayi sosai, wani lokacin yanayin kular Mami har mamaki yake bata "Dan Allah ki rufamun asiri Layla, ki kula da kanki, karki ji tsorona, karkiji tsoron me zance, kiji tsoron Allah dan Shi yana ganin ki a inda ni bana ganin ki. Ki kula da kanki, idan duk kina da matsala kinsan kirana kawai zakiyi ko?" Kai Layla ta daga mata, yanayin muryar Mamin na sanyaya mata jiki "Allah ya tsare mun ke a duk inda zaki shiga. Allah ya taimake ki ya baki sa'a, Allah ya banj aron rayuwa inji ki a gidan Radio din da kike buri" Da sauri ta matsa tana fadawa jikin Mami din "Karyani Layla" Mami ta fadi muryarta na rawa, kwalla cike da idanuwanta, a kasan kewar Layla akwai tarin shakku da tsoro da ta kasa kawarwa daga zuciyarta. Babu yanda zatayine, Layla da Abbu sun rinjaye ta, sunki fahimtar tsoronta. Shisa ta zabi ta bi Layla da addu'a kamar yanda Abbu ya fadi "Allah Shi ne yake tsarewa, Shi ya tsare mana su har zuwa wannan lokacin...ba tsoron mu ko dabara ba" Numfashi ta sauke a fili tana zagaya hannuwanta ta rike Layla a jikinta sosai. "Ina son ki Mami, da yawa fa" Dariya kawai tayi, da Layla da Jabir basa gajiya da fada mata suna sonta, ko a gaban waye Jabir zaice yana son ta, musamman idan tayi mishi abinda yaji dadi. Kalaman na sanyaya mata zuciya ko da bata mayar musu ba, abune da bai yawaita a al'adar mu ba. Su kam sun mayar da shi kamar tun tasowar su sun sabajin ana fadin kalaman a tsakanin iyaye da yaran su. Tana son yaran, tana jin su a ranta, kawai batason dabi'ar nasaran da suka daukarwa kan su. Musamman Jabir ma yanzun da yake ganin sai ta daga kai take hango shi, kuma kai tsaye zasuyi magana batare da sun tauna ba, suna ganin sun kai matsayin da zasu fadi duk abinda yake ransu, ga taurin kai, idan har suka kafe akan abu dai-dai ne to babu wanda ya isa yace musu ba haka bane ba. Halayen turawa shi suka daukarwa rayuwar su, kamar da suka shiga islamiyya haka suka fito batare da islamiyyar ta ratsa su ba. Addu'a ita take bin yaranta dasu har na Ayya ma, Allah ne shaida bata tashi daga wajen sallah bata hadasu duka a addu'o'inta ba. Haka sukayi sallama da Mamin, bacci take ji idanuwanta har wani yaji-yaji yakeyi. Shisa sanda Bilal yazo daukar kayanta bata samu ta gaishe dashi ba sai yanzun. Abbu ya gaya mata ya basu mota, kuma tasan motar, tana zuwa ta bude bayan motar ta shiga. Ko kadan batayi tunanin Rayyan yana ciki ba harta ja murfin ta zauna. Numfashi ta sauke, Rayyan kuma idanuwan shi a lumshe suke, dan yasan yau zai samu yayi baccin safe tunda motar gida ce bata haya ba. Kawai yaji ana shigowa, hakan yasaka shi bude idanuwan shi, gyara kwanciya yayi yana juya kan shi ya kafa ma Layla ido. Itama zama ta gyara tana dan juyawa taga an mata quri "Wayyoo Allah..." Ta furta da karfi saboda gabanta ya fadi sosai "Hamma" Ta furta har lokacin da tsoro a muryarta "Baki da hankali? Da safe zaki zo kina mun ihu a kunne?" Ita bata neman tashin hankali, tasan ko tafiya zasuyi zai zauna a gaban mota ne. Shisa ma ta bude bayan motar ta shiga abinta. Baccine a idanuwanta har sun mata nauyi "Kayi hakuri, dan girman Allah Hamma, wallahi bansan kana nan ba sam sam, ina kwana" Ta karashe a gajiye, hararta yayi yana jan wani tsaki dai-dai lokacin da Bilal ya shigo motar ya zauna. Juyawa yayi yana kallon su hadi da sauke numfashi "Me kuke nufi?" Ya bukata, tunda shi yasan su duka Abbu ya baiwa mota, baice ya zama direban su ba balle su kame a bayan mota gabaki daya "Wani ya dawo gaba" Ya fadi yana kallon Rayyan daya kauda kai "Magana fa nakeyi" Cikin ido Rayyan ya kalle shi "Kana shamun kamshi tun da safe" Ya fadi kamar wani dan karamin yaron da kaiwa dukan tsiya kazo kuma kana yiwa dariya. Layla Bilal ya kalla, ita kuma ta kalli Rayyan din kamar tana neman izinin shine kafin ta koma, shikuma ya rigada ya lumshe idanuwan shi. Numfashi Bilal ya sauke yana runtsa idanuwan shi ya bude su a lokaci daya. Tuqi zaiyi, yana bukatar gabaki daya natsuwar shi, idan ya biye musu zasu birkita mishi lissafi, hakan yasa shi gyara zama, addu'a yayi yana jan motar suka fice daga gidan, sun kama hanyar da zata fitar dasu daga Kano kenan Rayyan ya bude idanuwan shi yana ganin Layla a zaune a kusa da shi "Mayya ce ke? Dole sai inda nake zaki zauna?" Wani abu taji ya tokare mata zuciya yanayin yanda Rayyan din yayi magana. Inda ta tashi ta koma gaba ya bude ido kamar yanda yayi tana da tabbas zaice wani abu, dole saiya nemi dalilin da zai sata dana sanin tafiyar nan, bayan tun da satin ya kama take tunanin yanda zata zauna mota daya da shi, nishadin duk da takeyi ya dishe mata shi "Hamma ka tsaya in dawo gaba" Layla ta fadi da wani yanayi a muryarta, ta mudubin gaban motar Bilal ya kalle su "Na dora wayata a kujerar, kuyi zaman ku" Kafin ta karayin magana ya kunna radio din motar yana kure maganar "Ka fasa mana kunne Bilal!" Rayyan ya fadi a masife, ko kallon su Bilal baiyi ba, balle kuma suyi tunanin zai saurare su, ba yanda za'ayi su rabashi da nutsuwar shi yana tuqi. Matsawa Layla tayi tana kara bada tazara tsakaninta da Rayyan din, jingina kanta tayi da jikin motar tana rufe idanuwan ta, duk yanda take jin ranta na mata susa bai hana bacci dauketa ba, Rayyan kallonta yakeyi duk da yasan bacci ya kamata yayi. Yanajin inama ace haka zata zauna, yanda zuciyar shi tayi wani luf a kirjin shi abin ya mishi dadi, amman yasan tashi zatayi, bude idanuwanta zatayi ta hargitsa mishi komai kamar yanda ta saba. Baisan me yasa zata zo da idanuwan mage ba. Idanuwan shi na kafe a kanta, tana ta baccin ta, a cikin baccin ta juyo kwanciya, ganin da yayi kamar wuyanta zaiyi ciwo yasa shi girgiza kai kawai, babu wani abu da zatayi dai-dai, baccin ma ba zatayi shi dai-dai ba. Yana wannan mitar a zuciyar shi ya mika hannu ta baya dan ya dauko ruwan da Bilal ya ajiye, sai jin kan Layla yayi saman hannun shi, kamar ya mika ne dan ta kwanto, da dayan hannun shi ya tallabe wannan, yana zare shi a hankali, ruwan ya dauka sai ya dan janyo jikin shi yana gyara zama yanda kanta zai kwanta a kafadar shi da kyau. Robar ruwan ya bude yana sha sosai, ya mayar ya kulle, yanajin Layla ta kara gyara kwanciyar ta a jikin shi, tana kwantowa sosai. Wani irin dokawa zuciyar shi takeyi kamar zata fito daga kirjin shi "Mayya..." Ya furta a hankali yana sauke numfashi, sosai ya jingina kan shi da motar yana lumshe idanuwan shi, bugun zuciyar shi yake saurare da yake ji har cikin kunnuwan shi, kafin wata natsuwa daya kwana biyu baiji ba ta saukar mishi, bacci mai sanyi na dauke shi, baisan sanda ya jingina nashi kan dana Layla da yake kafadar shi ba. Kawai abinda ya sani wannan karin baccin nashi babu mugayen mafarkai ko daya. Ta gaban mudubi Bilal ya hango su, yanajin kamar an soka mishi wani abu a kirjin shi, sosai zuciyar shi ke dokawa kamar mai shirin samun matsalar bugun zuciya. Shi yake bukatar kulawa Shi yake cikin matsala Shi yake bukatar Abbu da Mami su fadawa Rayyan daya kula da shi * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:07 PM - 111: Nov 26, 2020 12 Kan shi ciwo yake kamar zai rabe gida biyu. Dan bai iya takawa gida ba, sai da ya hau mashin. Da yake ba surutu yake son yi ba, canjin dari da ya baiwa mai mashin dinma da hannu yayi mishi alama daya tafi "Allah yasa kar in ga kowa, Allah yasa kar kowa ya ganni" Rayyan ya furta a cikin kan shi. Bayason mutane, baya kuma son 'yan cikin gidan da suke haya fiye da sauran mutane, saboda suna saka shi yanayin magana a lokuttan da ko kadan bayason yi. Gashi yanzun Bilal yace ya dinga yiwa mutane murmushi idan sun mishi magana, baisan ya zai fara ba, motsa labban shi kawai yakeyi wasu lokuttan, tunda bayajin yin fara'a sam-sam. Ya gaisa dasu, baisan kirkin me Bilal yake so ya dinga musu ba "Ko rashin lafiya ta kamaka ba fata nake ba, su dinne mutanen farko da zasu taimaka maka tunda kuna gida, kasan abubuwan nan, kasan hakkin makota Hamma" Bilal din ya fada mishi "Bana son su" Shine amsar daya baiwa Bilal din "Su ma na tabbata ba son ka sukeyi ba. Ka dinga murmushi dan Allah in zaka gaisa da mutane, ka dan saki fuska ba kamar an maka dole ba" Bilal saiya dinga mishi magana kamar baisan dolen akayi mishi yake gaisawa da su ba. Hakkin musulunci kawai yake saukewa. Kamar barawo haka yake sanda wajen shiga gidan, sam baya so wani ya gan shi. Kusan da gudu ya karasa dakin su yana daga labulen ya shiga da sauri "Subhanallah..." Bilal da yake zaune ya bude kular abinci ya fadi, dan sosai Rayyan din ya bashi tsoro "Assalamu alaikum..." Cewar Rayyan, amsawa Bilal din yayi yana girgiza kai kawai. Taliya ce da miya sai soyayyen dankalin turawa, rabon su da dora tukunya a wuta harya manta, sai dai ko in sunyi marmarin shan shayi zasu dafa, amman Aysha na musu kokari matuka ta fannin abinci tunda tazo makarantar. Bilal baiyi mishi tayin abinci ba, tunda yasan sai yayi wanka, aikam ficewa daga dakin Rayyan yayi. Sai bayan yayo wankan ya dawo ya sake kayane ya zauna yana mayar da numfashi Bilal yace "Abinci fa?" Kai Rayyan din ya girgiza mishi "Babu abinda kaci fa duk yau" Tunda tare suka fita, kuma yasan babu abinda Rayyan din zaici a waje banda biskit, idan ya samu kalar wanda yakeci din kenan. "Zanci sai anjima" Rayyan ya furta yana kwanciya kan katifar da yake zaune a gefe, sai yaji wani dadi a ran shi daya kwanta din, kamar gajiyar daya kwaso ta dan sake shi. Wayar shi da Bilal ya janyone yaga yau din Alhamis, numfashi ya sauke "Azumi kakeyi ko?" Ya tambaya "Me yasa baka gajiya da surutu? Dan Allah ka kyaleni ni" Rayyan yayi maganar cikin alamar gajiya. Murmushi kawai Bilal din yayi. Bai taba gane azumin alhamis da litinin baya wuce Rayyan ba sai wannan dawowar da sukayi. Sai yake tuna ranakun da Rayyan din zai wuni baici komai ba, duk surutun da zai mishi. Sai sun dawo sallar Magriba tukunna, ko in yayo alwala ya shigo daki an kira, Bilal zai ga ya sha ruwa, ko yaci dabino. To bai taba kawo komai a ran shi ba, tunda Rayyan na da shan ruwa, kuma dabino kamar biskit ne a wajen shi, da wahala ka raba jakar shi da su, ko cikin kayan shi ka duba zaka samu. Zurfin ciki irin na Rayyan baya gajiya da bashi mamaki, shima ranar alhamis din daya san azumi Rayyan yakeyi, alhamis din kuma daya tabbatar da abinda ya dade da sani, wajen Rayyan din yaje daga nasu bangaren, ya same shi a can karkashin wata bishiya, inda yake shimfida darduma ya zauna idan basu da darasi ba kuma yason komawa gida. Tunda wani lokaci ko baiyi niyya ba idan ya zauna cikin aji sai an sami wani mayen yayi mishi magana. Ko mintina biyar da isa baiyi ba sai ga Layla da tun daga nesa take fadin "Hamma Rayyann!" Tana daga mishi hannu da fara'a a fuskarta, yana kallon Rayyan din ya lumshe idanuwan shi yana bude su a kan Layla da take karasowa, doguwar rigace ta atamfa a jikinta, dinkin da ake kira "Fitted gown" a turance, dan tabi jikinta sosai, sai mayafi data dan rataya a wuyanta, ga dauri ta kafa, fuskarta da kwalliya marar nauyi. Da wahala ta wuce ka baka sake kallonta ba, kafin kaga idanuwanta jikinta ne zai fara jan hankalinka, balle kuma idan ka tsayar da hankalinka akan fuskarta da take da wani irin kyau mai sanyi. Dan Bilal sai da yaji jikin shi ya dauki dumi, hakanne yasa shi sauke idanuwan shi daga kanta "Hamma..." Ta sake furtawa tana dariya, kwana biyu bata gan shi ba, Bilal din kuwa kullum sai yaje ya dubata yana tambayar ko tana bukatar wani abu. Amman yau kwana biyu bata saka idanuwanta akan Rayyan ba, tunda suka zo makarantar ita take yawon nemo shi duk rana. Jiya da gangan taki zuwa inda yake, ko shi zai nemeta, amman shiru, yau ta kasa hakuri ne, sai da ta zagaya ta gefen da Rayyan yake tukunna ta kalli Bilal "Hamma ina wuni" Murmushi yayi mata "Layla..." Ya furta yana yin shiru tunda hankalinta gabaki daya ya koma kan Rayyan "Jiya banganka ba" Ta fadi tana nazarin fuskar shi, shiru yayi ya kyaleta, baisan ko a satikan nan da tazo Zaria ta fahimci yanda yake matuqar sonta a kusa da shi bane, shisa jiya ta hana mishi ganinta. Kwana yayi yana juyi duniyar ta hade mishi waje daya. Ya gwada kiran wayarta yafi sau ashirin yana fasawa, saboda baisan me zaice mata ba, ba shida wani dalili da zaiyi amfani da shi. Shisa ya hakura. Yau da safe harya nufi hanyar department dinsu sai ya dawo kuma. Shine yanzun take ce mishi jiya bata gan shi ba, kamar bata san inda yake ba idan ta tashi ganin na shi. "Hamma..." Ta kira ganin da tayi na cewa yau miskilancin yake ji fiye da ko yaushe, zama tayi gab da shi bata damu da yanda rabin jikinta a kasa yake ba, rike Rayyan ko in hango shi tayi ta rungume shi bai taba damunta ba, hankalinta sam bai taba gaya mata cewar shi din ba muharramin ta bane ba, saboda bata dora abin akan mizanin addini, al'ada kuwa ba damun Layla tayi ba sam. Yanzun ma kanta ta kwantar akan kafadar Rayyan duk da tasan zai iya kwadarta bai hanata ba "Hamma..." Ta furta da wani yanayi a muryarta, tayi kewar shi, jiya kawai da bata gan shi ba kewar shi take ji har cikin ranta. Rayyan bai tsammaci zata kwanta mishi a kafada ba duk da ta zauna kusa da shi, wani irin tsalle zuciyar shi tayi kamar zata fito waje saboda wani irin yanayi da yaji ya tsirga mishi, tureta yayi tana shirin dawowa ya matsa da sauri "Azumi nake Layla" Yai maganar yana mikewa tsaye gabaki daya, turo labbanta tayi. Shi kuwa Rayyan numfashi yake mayarwa, tun rannan yake tsintar kan shi a wannan yanayin duk idan jikin su ya hadu waje daya. Bilal kallon su yakeyi, zuciyar shi kamar zata fado kasa, idan Rayyan baya kallon Layla da wata fuska data wuce yan uwantaka ya tabbatar ba zai tunanin azumin shi ba dan ta kwanta a jikin shi, tunda tanayi lokutta da dama, bai taba damuwa ba, karshen abinda zaiyi shine ya kamata ya bambare yana fadin "Mayya ce ke? Duk wajen nan sai kin hadu da jikina? Me yake damun ki?" Ita yake fadawa kalaman, amman Bilal sukeyi wa zafi, musamman idan yaga Laylan ta sake komawa ta mannewa Rayyan din duk da zafin kalaman shi da suke shimfide a idanuwanta. Ya rasa yanda zaiyi da su, ya kuma rasa ta ina zai fara hanasu wannan rike-riken junan da sukeyi. Yana kallo Layla ta mike itama tana shirin tafiya "Ina zaki je?" Rayyan ya bukata yana tsareta da idanuwa "Ina da lecture, kawai zan ganka ne daman" Kai ya jinjina, farar riga ce kal a jikin shi da wandon jeans, saiya dora jacket a sama, ko maballan bai balle ba, kawai ya dora ne, taku hudu yayi yana karasawa inda Layla take tsaye, mayafin da yake wuyanta yaja yana daga shi, wani dan ziriri ne, kai kawai Rayyan ya girgiza. Shi baiga amfanin mayafin ba tunda babu abinda ya rufe, bayason yanda maza suke kallonta duk idan ta wuce, wancen satin da yake wando ta saka saita dora kimono a kai, duk da haka sai da yace wa wani dan ajin su "Ko zaka dauke ta hoto ne?" Ganin irin kallon da yake bin Laylan da shi bayan ta wuce, murmushi kawai gayen yayi yana barin wajen. Kawai bayaso wasu maza na kallon ta, shisa ya bi bayanta, ya taba ganinta da rigar kuma yaga da madauri baisan me yasa bata saka ba. Hannunta ya kama ranar "Ina madaurin rigar nan?" Cike da rashin fahimta tace "Yana cikin jakata" Jakar ya karba da kanshi ya bude ya dauko, sannan ya mayar mata da jakar cikin hannunta. Da kan shi ya zagaya madaurin yana soka shi a mazaunin shi ya taho da shi ta gaba ya daure mata yanda ya taba ganin ta daure, saida ya rankwashi kanta daya gama yana sakata fadin "Wayyoo Hamma" Ta dafe wajen dan taji zafi sosai, kara kai mata rankwashi yayi ta kauce, idanuwanta cike taf da hawaye ta kama hanya. Dan sam Rayyan baya damuwa da mutanen da suke waje, bama ya damuwa da yanda saboda idanuwanta yanzun tana cikin 'yan matan da aka sani a fadin makarantar cikin kankanin lokaci, ga turancinta da yake burge mutane. A ajinsu ma kowa so yakeyi yai kawance da ita, har maza suna mata magana, kawai dai ba kowa take kulawa ba, a matan ma baifi mutum biyu suke yawo tare ba, saboda ta kula duk sunfi kowa wayewa a cikin ajin, kuma daku nan su da juna babu nisa a hostel, floor daya suke, hawa na ukku. Suna ma zuwa wajenta a dakin su. Jacket din da take jikin shi Rayyan ya cire. Sai da ya rankwasheta "Me nayi? Me nayi ni?" Layla take tambayar shi kamar zata fashe da kuka, rigar ya zagaya yana kafa mata idanuwa,  hannunta ta zira a ciki, tana saka dayan ma, ya gyara mata zaman rigar data sauka tana rufe bayanta sosai, maballi daya ya kama yana ballewa, bude baki tayi zatayi magana ya katseta da fadin "Bakin ki zan fasa in kikayi mun surutu...wuce ki bani waje ni" Wucewar tayi kuwa, kafin ta juyo tana kallon Bilal da yake zaune yana kallon ikon Allah "Hamma sai anjima" Kai ya iya daga mata, yana kishin ganinta a haka, bai taba magana a kai ba, bai taba kokarin hanata shigar da takeyi ba, a zuciyar shine bayason abin, amman Rayyan yayi wani abu a kai, a gaban idanuwan shi ya nuna mishi dalilin da yasa idan yana waje Layla bata ganin kowa sai shi. Baisan me yake ji a ran shi ba, ranar kuma da suka koma gida ya manta yake mishi tayin abinci kai ya girgiza yana amsawa da "Zanci anjima" Sai lokacin Bilal din ya tuna "Kana azumi fa ko?" Kallon shi Rayyan din yayi "Ni na fada maka?" Kai kawai ya girgiza mishi, tun ranar kuma yana kula da shi a ranakun litinin da alhamis, azumi baya wuce shi. Ba dai yason kowa yasani ne tunda badan wani yakeyi ba. Har mamakin mutanen da kamar jira suke ayi musu tayin abinci su sanar cewa suna azumi ne, kamar dan wani suke ibadar. Abinda kakeyi dan Allah, a haka sai ladan yayi tafiya batare da sanin ka ba, idan har ka tsarkake niyyarka, ya kamata ibadunka da ba farilla ba su zamana tsakanin ka da wanda kakeyi domin shi. Abincin Bilal ya karasa cinyewa yana mikewa ya dauko ruwa ya sha hadi dayin hamdala. * Hanjin shi har daurewa yakeyi sanda suka dawo daga sallar Magriba. Gashi baisan abinda zaici ba. Ruwan zafi kawai ya dora a tukunya da nufin ya sha shayi, baiga Bilal ya dauki kulolin Aysha ba sanda zai fita, balle yace watakila in zai dawo zai taho musu da abinci. Baiso a dame shi shisa yana shiga yaja labule ta ciki ya tura kofar dakin, ko babu wuta gara yayi fifita da wani ya dago labule neman Bilal ya saka shi yin maganar da bai shirya ba, balle kuma yau yan nepa suna jin mutunci, tunda suka dawo akwai. Ya juye ruwan zafi a kofi kenan ya saka Lipton yaji ana Kwankwasawa, karamin tsaki yaja yana yin shiru, idan aka gaji za'a tafi, yasan idan Bilal ne zai tura dakin tunda yasan yana ciki. Sake Kwankwasawa akayi, ya kara jan wani tsakin. A fusace ya mike tsaye yana bude kofar dakin, ga mamakin shi Layla ya gani tsaye sai maida numfashi takeyi, ta rungumo wani kwando da kuloli a ciki, kamar zatayi kuka tace "Hamma ka amsa, hannuna zai karye" Tsautsayine ya sa ta saka riga da siket, da zata hau mashin har kofar gidan su Rayyan. Keken da ta samu kuma yaki shiga da ita lungun. Har ca tayi ta kara mishi kudi saboda kwandon data dauko amman yakiya. Haka ta tako tana tafiya tana kwashe mishi albarka saboda nishin da take dirkawa, ga kwandon hannu daya sai cirewa yakeyi idan ta rike, sai rungume shi tayi. A jigace ta isa gidan su Rayyan din, hannuwanta duk sunyi sanyi. "Idan ba zaka amsa ba ka matsa daga kofar" Tayi maganar cikin tsiwa ganin Rayyan din yana tsaye yana kallonta. Hannun shi daya daga yasata tunanin kwandon zai karba, tallafe mata kai yayi "Rashin kunya" Ya furta yana matsawa, ba zai karba ba tunda tayi mishi surutu, karasawa tayi cikin dakin tana ajiyewa a kasa, inda ya tashi ta zauna tana mayar da numfashi "Banfa samu mashin har gidan nan ba, akan hanya napep ta ajiyeni, da kafata na shigo wajen nan..." Dakin Rayyan ya bude saboda yanda zuciyar shi take dokawa ba zai rufe daki daga ita sai shi a ciki ba. Ya rasa lokacin da ganinta ya fara hargitsa tunanin shi har haka, kuma bai saka idanuwan shi cikin nata ba, ya koyi kallon har fuskarta batare da idanuwan shi sun shiga cikin nata ba "In da na tashi nan zaki zauna?" Ya bukata yana karasawa wajen ya rankwafa, hannunta ya kama ya fisga yana dagata "Hamma dan Allah, wallahi nagaji, nagaji ni" Hannun ya sake rikewa sosai "Da daddare kika biyo hanya?" Duk da ko fita kayi yanzun din za kaita cin karo da mutane, unguwar tasu dalibai sunfi yawa, dare sai kaga kamar rana ne, amman wani abu a zuciyar shi baison yanda ta fito da magriba haka "Abinci zan kawo maka, ba kana azumi ba? Dan Allah ka sakeni" Ta karasa muryarta na rawa, tun azahar yau ta gama darasinta, tana komawa hostel ta fara aikin yi mishi girkin nan saboda ta siyo kifine sai tayi mishi sauce ta dafa wake da shinkafa. Anisa da suke daki daya taso tayata, tunda wani lokaci har girki sukan hada, tace karta damu zatayi in yaso sai Anisa din tayi wanke-wanke. Ba tsafta bace bata da ita, kawai halin jujun Rayyan ta sani, zai iya tambaya idan ita kadai tayi girkin, kuma ba zata iya kallon shi tayi karya ba, yana ganeta, ta sha gwadawa bakinta yanayin jini "Karya ne" Yake fadi a duk lokuttan yana kara kai mata wani dukan, sakar mata hannu yayi yana komawa wajen shi ya zauna. Tsaye tayi a wajen tana murza hannunta, shikuma ita yake jira ta zuba mishi, hakan ta kula da shi, bata dauko faranti ba, a dakin ta samu da cokali, sai da ta dauki ruwan leda tana fita wajen dakin ta daurayo su sannan ta dawo "Kazama, a bakin kofa kika zubar mun da ruwa ko?" Bata kula shi ba, turo labbanta tayi kawai, sai lokacin ta cire hijabin da yake jikinta tana ajiyewa kan teburin da yake cikin dakin. Bai taba mata maganar kayan da take sakawa ba, amman tasan bayaso, har wata zuciyar na fada mata kishi yake shisa, ba karamin dadi take ji ba kuma. Jacket din shi guda hudune a wajenta yanzun, kuma duk idan ta saka kayan da baisone yake bata. Kamar yana yawo da jacket dinne yanzun ko zai ganta da kayan da bayaso, dan kwanaki a jakar shi ya fito da jacket din. Kuma Rayyan sam bai damu da yawan mutanen da suke waje ba idan ya tashi yi mata abu, kamar ma baya ganin su haka yakeyi. Abincin ta zuba mishi tana neman waje ta zauna, ya fara ci yaga yanda take bin duk cokalin da zai kai a bakin shi da kallo, kai ya girgiza yana ajiye farantin da ya daga, ya gyara zaman shi sosai "Me yasa zakiyi girki ba zakici ba?" Tasan baya tambayeta dan ta bashi amsa bane, shisa tayi shiru, ita batama san tanajin yunwa haka ba sai yanzun da taga yana cin abincin. Cokali ya dauka yana mika mata, zata saka cikin abincin ya dakatar da ita da fadin "An taba marin ki cikin ido? Ba zaki tashi ki wanko shi ba, kazama kawai" Mikewa tayi tana daukar sauran ruwan da ta ajiye a gefe ta daurayo cokalin ta dawo. Tare suka cinye abincin tana kara zuba musu wani. Abin bai mata wani iri ba, zuwanta makarantar wannan ne karo na wajen biyar da suke cin abinci tare, na farkon ta kusan raba dare data juya yanayin su tare take hangowa sai wani murmushi ya kwace mata da ba zata ce ga dalilin shi ba. Da yake yana cin abinci da sauri, kafin taci guda daya yaci uku, baisan dalilin da zaisa ka tsaya yanga in zakaci abinci ba. Da kanshi ya dauki kular yana kara mata ya zuba mata miya a kai, abincin da yawa tayi. Yasan Bilal in dai ba wani abu yaci a wajen Aysha ba, zaici, in baici ba da safe sai su dumama suci abinsu. Layla na karasawa, ruwa kawai ta sha, batama gama ba Rayyan ya mike "Tashi muje" Kallon shi tayi da tashin hankali a fuskata "Ina zamu je? Hamma kabari abinci ya tsarga mun, yanzun fa nagama ci" Kallon da yayi matane yasata mikewa ta dauki hijabinta tana buga kafarta, duka Rayyan ya kaimata tana kaucewa dan ta gan shi "Zaki wuce ko saina kwada miki mari?" Ya bukata, fita tayi daga dakin, shima takalmi ya zira a kafafuwan shi yana fita, baisan ko Bilal ya dauki mukulli ba, shisa ya janyo kofar kawai, gidan su ba'a taba yin sata ba. Kusan ko yaushe Bilal kan yabi halayyar yan gidan. Ko baka rufe daki ba, wani zai janyo maka. Haka sukeyi, in shanya kayi hadari ya hado ma za'a kwashe maka, inka dawo a kawo maka. Suna da kirki matuqa. Shisa bayajin dadin yanda Rayyan yake hade musu girar sama da ta kasa. Shiya fara yin gaba Layla na biye da shi, cikinta take ji har wuya, inda tasan ba zai bari abinci ya natsa mata ba, da bata cika cikinta haka ba. Ganin har sun kai titi suna tsallakawa yasa ta fadin "In mukai nisa fa ba zamu sama abin hawa ba" Dan juyawa Rayyan yayi ya kalleta, hannunta yake shirin kamawa ta kauce "A kafa? Hamma a kafa? Tafdin... In dai rakani zakayi nagode...amman ni wal..." Da sauri yace "Karma ki rantse, zakiyi azumi yarinya... Ki zo mu tafi" A kafa yake jin tafiya, saboda yana son dan takawa tunda ya cika cikin shi, kuma ko ba haka ba, a ranshi yana jin yin tafiyar tare da ita, ko tana so ko bata so ba matsalar shi bane ba, duk yau ganinta ne yadan nutsar da shi, amman da wani kunci ya wuni, wasu ranakun idan yana azumin yakan ji shi wasai, har Qur'ani yakan dauka ya karanta. Amman wasu ranakun bawai bayaso ya dauka bane, kawai wata irin kasala kan rufe shi duk idan ya yunkura sai ya kasa, haka zai hakura yaita juyi, inya gaji ya kunna sigari ya bukama cikin shi. "Ni dan Allah kabarni, wallahi nagaji, kuma na saka dogon takalmi" Layla ta furta tana shirin yin kuka, tun kafin ta fito take murnar zuwa ta gan shi, amman yanzun harya isheta, ta ina zata fara shafawa a kafa ana zaune lafiya. Zagaye suka fara "Layla..." Ya furta cike da kashedin da yasata tsayawa waje daya, yasan ko bata zagin shi a ranta, tana tunanin hanyoyin da zata jibge shi idan ta samu dama ne saboda kallon da takeyi mishi, hasken wutar lantarki ya sake ma idanuwanta launi, sai da gabanshi ya fadi daya kalle su, musamman da irin kallon da take watsa mishi, hannunta ya damqa yana janta tana tirjewa kamar karamar yarinya. Bai damu ba, cigaba yayi da janta har suka karasa wani shago, yana rike da hannunta har lokacin ya siya silipas, babu karamar lamba, dan koshi sun mishi yawa, sakinta yayi ya fito dasu daga leda yana ajiye mata "Ni ce zan saka wannan?" Ta bukata tana ware mishi ido, kamar duk ranar bataga wani abu daya daga mata hankali irin shi ba, takalman kafafuwan shi dana fata ne yan zire ya cire yana saka silipas din "Hamma..." Cikin ido ya kalleta "Kina gwada hakurina Layla, kin sani ko? Wallahi ba zan sake magana dake ba" Dogayen takalman kafarta ta cire, ta saka nashin, da kanshi ya kwashe nata ya saka a ledar daya zaro silipas din yana bata, karba tayi ta rike baqar ledar. Hannunta ya sake kamawa suna tafiya. A hankali har suka fara hango makaranta, ba hira sukeyi ba sam balle tace tafiyar tana mata dadi, amman yanayin Rayyan din ya nuna yana cikin nishadi. Musamman yanda ya kalleta yaga tana ta turo baki "Ki maida hankali, kilan bakin ki ya rigaki zuwa hostel" Ya furta yana kara sauri, yana kallon yanda take kokarin kamo shi tana kara turo baki, sai da tasa murmushi ya kusan kwace mishi, tunda dai babu yanda zatayi da shi. Har kusan kofar hostel din ya karasa da ita, inda sukaci karo da su Bilal su kuma, Aysha zata rako shi, sunyi tsaye suna hira "Hamma!" Ta kwala mishi kira tana murmushi, kallon su Bilal yakeyi da mamaki suna karasowa inda suke, hannun Layla da yake cikin na Rayyan ya kalla, bai amsa Layla ba saboda wani sanannen abu da yaji ya mishi tsaye a makoshi. Kirjin shi harya fara zafin da yakan mishi duk idan ya gansu tare haka "Ayshan Hamma" Layla ta fadi tana mata murmushi "Layla..." Aisha tace cikin gaisuwa, tana kallon Rayyan "Ina wuni" So yakeyi yayi mata murmushi koya ne, amman sam bayajin yi "Lafiya kalau. Sannu da kokari, mungode" Ya fadi, yana saka Bilal kallon shi cike da mamaki, Layla ma mamakin takeyi, shi kuma tun rannan yake so yayi mata godiya saboda tana ma Bilal kirki. Tun satin daya wuce yake hada kalaman da zai fada mata in sun hadu, sai yaune ya samu ya fada, baisan me yasa su Bilal suke kallon shi kamar sunga wani abu a fuskar shi "Bakomai" Aisha ta furta a kunyace, Layla zatayi magana Rayyan yaja hannunta sunayin gaba, ta cika surutu, baiga abinda zata fada ba kuma, bayan an gaisa. Tsayawa yayi yana sakinta hadi da fadin "Tam sai da safe" Kafin ta amsa ya juya, inda su Bilal suke tsaye ya karasa yana dan matsawa gefe hadi da jiran Bilal din, shima hakan yagani yayi sallama da Aisha din yana samun Rayyan. A hanya suka tsaya sunayin sallar isha'i sannan suka nufi gida. Sai da Rayyan ya tsaya wani shago ya siyi sigari. "Ba zaka daina sha ba ko Hamma?" Bilal yai tambayar da wani yanayi a muryar shi, sai da Rayyan ya zari kara daya ya kunna yana zuqa ya fitar da hayakin tukunna yace "Me yasa kake magana a kai?" Tunda yasan ba dainawa zaiyi ba, shima ya kamata yabar asarar bakin shi. Ba so ya daina bane bayayi, ko yanzun kamar dole ake mishi haka yake zuqar sigarin, kafin su karasa gida yasha kara hudu, yana shirin daukar ta biyar ne Bilal ya fisge kwalin daga hannun shi yana sakawa a aljihu, Rayyan baice mishi komai ba, haka da suka shiga daki ma baice mishi komai ba. Asalima kan tebir ya zauna ya fara rage tarin assignment din da yake gaban shi, yana kallon Bilal ma yayi nashi kafin ya fara danne-dannen waya da bazai wuce hira yake da Aisha ba. Nan Bilal yayi bacci yabar shi, kwayoyin shi ya sha ganin Bilal din yayi bacci, amman har karfe uku da rabi ko gyangyadi, sai wajen hudu yadan kwanta, yasan ko da babu sallar asuba, da wahala baccin ya wuce awa daya. Rufe idanuwan shi yayi, baya ganin komai sai hotunan Layla kala-kala a cikin kan shi. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:07 PM - 111: Nov 28, 2020 13 Kwance Bilal yake yana nazarin wani lissafi, saboda har an fara test tun satin daya gabata, jarabawa nata karatowa. Amman Rayyan zaune yake yana zane, wani lokacin zaka rantse da Allah hutu Rayyan yake zuwa yi Zaria ba karatu ba, saima lokacin jarabawa, idan baka gan shi yana zane ba, to zaka iya ganin shi yana kwance shiru, tunda shi dai baya hada hanya da wata kafar sada zumunta, har dan whatsapp din da akeyi ma bayayi. Asalima wayar shi da screen din ya fashe yar karamar Nokia ya siya ya saka sim din shi a ciki. Idan wani abu na makaranta ne daya kama sai an duba yanar gizo, da kwamfuta din shi kirar laptop yakanyi amfani. Kuma yana daya daga cikin mutane hudun da suke jagorantar ajin su ta fannin karatu, inda Rayyan dinne na biyu, idan da zai maida hankali ma tsaf zai zama gwarzo a ajin. "Wai ba test kace kuna da shi ba?" Bilal ya bukata, kai Rayyan ya jinjina mishi "Ba zakayi karatu ba?" Raba idanuwan shi da takarda Rayyan yayi ya kalli Bilal din, kallon da yake fassara "Da ni kake?". Kafin ya mayar da hankalin shi kan zanen da yakeyi "Lokutta irin haka kana sakani inajin kamar bani da kokari" Dan numfashi Rayyan ya fitar "Kana da kokarin ne? Tun dazun kake kallon takarda daya" Bude baki Bilal yayi, kafin ya mike zaune "Kasan wanne lissafine? Kake kira takarda daya kamar wani abu marar wahala" Fensirin hannun shi Rayyan ya ajiye, ya dan juya zaman shi yana mika hannu ya fisge takardar da take hannun Bilal, duba tambayar yayi, batare daya dago ba yace "Ina misalin? Wanda akayi?" Tashi Bilal yayi ya dauko jakar shi yana fito da littafi ya dubo wani misalin yana mikawa Rayyan daya karba, sosai ya nutsar da hankalin shi yana ganin yanda aka fitar da abin. Kafin ya fara duba wanda Bilal yake nazari, a idanuwan shi yaga yanda komai zai kasance, juyawa yayi ya ajiye akan tebir, cikin mintina kasa da sha biyar ya gama fitar da shi yana jefawa Bilal din "Ba zaka maida hankali sanda ake maka abu a aji ba, kana can kana wasu tunane-tunane..." Rayyan din ya fadi a fadace, dauka Bilal yayi yana duddubawa, murmushi yayi "Bayani zakayi mun dalla-dalla..." Hararar shi Rayyan yayi yana sake hade fuska, dariya Bilal yayi mai sauti wannan karin yana tashi ya janyo kujera ya zauna gefen Rayyan din daya ke watsa mishi wani kallo "Ni kyaleni" Ya fadi saboda surutu Bilal zai sa shi yayi, watakila sai yayi mishi bayani sau biyu ko fiye da haka, amman sai ya zaqulo wata tambayar yayi mishi. Haka kuwa akayi, har saida ya kule daya fahimci Bilal din ya gane, surutun kawai yake so ya saka shi. Ganin yayi Rayyan din yayi banza ya kyale shi yasa Bilal komawa kan gado abin shi, so yake ya sake fitar da lissafin a wata takarda daban dan yaga koya fahimta, shekarar shi ta farko ya fadi jarabawa guda daya. Rayyan yaita mishi fada kamar zai mare shi, wani lokacin ko bai niyyar karatu ba yakan dauko yayi saboda masifar Rayyan da ba karewa takeyi ba. Ranar ne karo na farko da yaji kamar yayi dissapointing din Rayyan din, yanayine da baya so ya kara faruwa. Duk da kwakwalwar su ta bambanta, yana iya kokarin shi. Rayyan zanen shi yaci gaba dayi, amman baya tafiya yanda yake so, saboda yau ya kasa rufe gabaki daya tunanin shi kamar yanda yakanyi a lokutta irin haka. Layla ce manne a ran shi, tun jiya bai ganta ba, har wayarta ya kira amman a kashe. Yanzun ma wayar da take ajiye kan tebir ya dauka ya duba ko ta turo mishi sako, amman shiru, sake gwada kiranta yayi yana jin bata shiga ba, kamar matsalar network tunda ba'a ce mishi a kashe take ba Wajen mintina sha biyar tsakani, batare daya kalli Bilal ba yace "Ka ga Layla?" Kai Bilal din ya jinjina mishi, kullum sai yaga Layla, in ya fita kafin ya wuce aji saiya biya ya kirata ta sauko yaga ya ta kwana, ko tana da wata matsala sannan ya wuce, amanar ta Abbu ya bashi, babu yanda za'ayi ba zai dubata a duk rana ba. "Ni ban ganta ba" Cewar Rayyan da wani yanayi a muryar shi da yasa Bilal dagowa "Ba tazo aji ba, bata jin dadine tun jiya da dare" Mikewa tsaye Rayyan yayi zuciyar shi na wata irin dokawa "Me yasa baka fada mun ba?" Kallon shi Bilal yayi yanda ya hargitse lokaci daya kamar yace mishi wani babban abune ya samu Layla, shi yasan lokacin al'adarta ne, badan ta gaya mishi ba, sai dan ya kula da duk wata haka take fama. Wancen watan da ciwon da komai ta zo wajen Rayyan, yana ganin yanda har fuskarta Rayyan din ya taba ko zaiji zazzabi bayan ya tambayeta me ya sameta tace mishi bakomai. Bai fada mishi ba saboda yasan idan akan Layla ne Rayyan zai dauki abin ya saka a ran shi. Amman can kasan zuciyar shi yana jin kamar akwai wani dalili bayan nan, dalilin da bayaso yasan shi saboda yana da yakinin zai saka shi yaji kamar bai kyauta ba. Jacket din shi da take can gefen gado Rayyan ya dauka yana sakawa akan kayan jikin shi da riga da wando ne, ya dauki wayar shi yana kama hanyar kofa "Ina zaka je? Takwas da rabi fa" Ko amsa bai samu ba, numfashi kawai ya iya saukewa yana bin Rayyan din da kallo harya fice daga dakin. Wani irin sauri yake ya karasa titi ya samu machine zuwa gate din makaranta, kawai so yake ya fara hango hostel din su Layla, bai daina gwada kiran lambarta ba, har lokacin bai samu ba, ya kusan mintina goma a tsaye bakin kofar hostel din kafin yayi nasarar samun wayarta "Ki daga dan Allah" Ya furta a hankali, ya kasa tsaida bugun zuciyar shi waje daya. Yankewa tayi, ya sake kira, sai gashi ta daga, muryata can kasa tace "Hamma?" Kamar tana son tabbatar da cewa shi dinne ya kirata "Layla me ya sameki? Me yasa baki fadamun baki da lafiya ba? Ina wajen hostel dinku, ki sauko in ganki" Ya karasa yana kokarin tuna ranar karshe da yayi magana cikin sauri kuma da yawa a lokaci daya irin haka. "Ni ba zan iya fitowa ba" Layla ta fadi daga dayan bangaren, tana saka zuciyar shi kara dokawa, shi fa sam bayason yaji bata da lafiya. Kuma gashi tana fada mishi ba zata iya fitowa ba, wacce irin rashin lafiya ce haka? "Ki fito ba wasa nake ba, Allah ina jira" Ya karasa yana kashe wayar, duk wata addu'a da tazo bakin shi ita yake karantawa, ya kafa idanuwan shi a kofar hostel din, har ya hango ta, dakyar take tafiya yana gani, yana kuma ji har cikin ran shi. Ta tsaya yafi sau biyar kafin ta iso inda yake tana tsugunnawa da alamar ciwon da take ji. Ta kwana biyu batayi ciwon mara irin na yau ba. Sunje clinic da Anisa an kuma bata magani, ta sha, sai taji kamar ya kara mata ciwon da take jine. Dakyar ta sauko yanzun ma "Layla" Rayyan ya kira yana tsugunnawa shima, idanuwanta da suka sauya kala zuwa wani launi da baisan ya zai fassara ba ta dago tana saukewa cikin nashi da dole ya rissina su saboda yanda ta kara ma bugun zuciyar shi gudu "Ta shi muje asibiti..." Ya furta a hankali, kai ta girgiza mishi "Munje tun jiya, na sha magani" Shima kan yake girgiza mata "Baki da lafiya har yanzun" Dakyar ta iya fadin "Zai tafi nan da kwana hudu" Da rashin fahimta yake kallon ta "Ya akayi kika sani?" Kwanciya kawai Layla take son yi saboda cikinta kamar ana shara a ciki. Kilan Allah ya taimaketa tayi bacci "Hamma..." Ta fadi a gajiye, ganin kallon da yake mata ya sata cewa "Period ne..." A hankali tana mayar da kanta ta saddar, ya dauki wasu dakika kafin ya fahimci ma'anar kalamanta. Tsintar kan shi yayi da mikewa yana kama hannunta ya taimaka mata ta mike, jin shi yayi da dumi fiye da kowanne lokaci, hakan ya saka shi taba fuskarta, zazzabine ruf a jikinta. Idan yace ya tafi gida hankalin shi ba zai taba kwanciya ba, bayan yasan babu wanda zai kula da ita idan yabarta nan hostel din "Muje gida, in kinji sauki sai ki dawo" Yanda yai maganar babu wajen gardama, kallon shi Layla takeyi, bama zata iya gardama ba a halin da take ciki, kwanciya kawai take son yi "Zan dauko abu, kuma idan na koma ba zan iya sake saukowa ba Allah... Hamma kabarni anan, zuwa gobe ma zai fara sauki in shaa Allah" Kai yake girgizawa tunda ta fara magana, sai yanzun ya kula duk tayi zuru-zuru. Idan dawowar ne gobe ta dawo, amman yau kam ba zai iya barinta ba, tunani zai mishi yawa "Layla tare zamu tafi, karki mun gardama" Yanda ya karasa maganar da wani irin sanyin murya da bata taba jiba yasa ta cewa "Ka aramun wayarka in kira Anisa to" Mika mata wayar yayi, sai da ta dan matsa sannan tayi kiran, kallonta yake duk da baya iya jin me take fadi harta gama ta dawo tana sake tsugunnawa, sun kai mintina goma da wani abu kafin Anisa ta sauko, da fara'a take kallon Rayyan "Ina wuni..." Yanayin yanda ta rage muryarta yasa Layla mikewa tsaye tana mata wani kallo "Sannun ki" Shine amsar da ta samu daga wajen Rayyan din, kyau yake yi mata tun ranar farko data fara ganin shi, amman tambayar duniya da tayiwa Layla akan shi sai ta hade rai "Bana so Anisa, bana so Allah" Takan fadi cike da kishin daya tabbatarwa da Anisa ba ciki daya Layla suka fito da Rayyan ba. Hakan dai bai hana yaci gaba da burgeta ba. Ledar da take hannun Anisa ta karba tana fadin "Nagode..." Kafin ta kalli Rayyan da alamar su tafi, ledar hannunta shikuma ya karba, yana kama hannun nata suka wuce cikin yanayin da ya burge Anisa matuqa. Ita daman saboda Anisa ne ta mike, saboda bataso ma Rayyan ya kalleta, ciwo bai hana wani irin kishi rufe ta ba. Yanda ta damqi hannun Rayyan yasan ciwo take ji, ba zaice ga yanda ciwon da take ji yake ba, amman ya san shi a karance. Shisa yanzun yaji har kasan ran shi, tsayawa yayi yana kallon yanda take runtsa idanuwanta "Sannu..." Ya furta yanajin kamar ya dauke mata ciwon da take ji, amman babu halin hakan, ganin tana shirin tsugunnawa yasa shi kama hannunta yana hanata. Juyawa yayi ya dan tsugunna, cikin tashin hankali Layla tace "Hamma..." Saboda taga yawancin mutane sun fara kallon su "Zaki hau ko saina watsa miki mari?" Rayyan ya furta, gara ya dauketa zuwa gate, watakila su sami abin hawa, tunda yaga tafiyar wahala takeyi mata. Bata taba hango kwatankwacin abinda yake faruwa yanzun ba. Rayyan ne, tana hango abubuwa da yawa da zasuyi tare, fiye da rabin abubuwan da tasan a tunaninta kawai zasu tsaya saboda shine, amman abinda yake shirin faruwa yanzun abune da bata taba hangowa ba ko a tunanin nata. Dogon wandone a jikinta da riga, da zata fito sai ta dauki hijabin da Mami ta dinka mata, dogone kusan har kasa, sallah take yi da shi. Yanzun ma shi hannunta ya fara tabawa bayan ya kirata, shisa ta saka. Ta fara tunanin yi mishi gardama, sai taga dama ce ta samu da bata san ranar kara samunta ba "Sai ka kara tsugunnawa" Ta fadi, sai da yadan juya yana harararta, murmushi take dannewa, saboda yanda yayi din kamar dole aka saka shi bashi yasa kan shi ba. Sosai ya tsugunna wannan karin tana hawa bayan shi, ta zagaya hannuwanta ta riko mishi wuya, mikewa yayi kamar bai daga komai ba "Kasheni kike son yine halan?" Ya fadi dakyar saboda yanda ta shake mishi wuya "Ba zaki sakar mun wuya ba" Ya sake maganar yana karbar ledar hannunta, sassauta rikon tayi, amman sai takejin kamar zata fado, musamman daya fara tafiya "Allah Hamma zan fado" Shiru Rayyan yayi yana kyaleta, ya zabi ya maida hankalin shi kan yanda zuciyar shi take bugawa akan Layla da take kwance a bayan shi "Da gaske nakeyi zan fado... Allah Hamma" Saboda duk tafiya idan yayi sai taji kamar ta kara sumbulowa, sosai take mamakin yanda yara suke nacewa goyo, babu wani abu mai dadi a cikin shi, ita kam har jiri-jiri take gani. Ciwon daya murda matane ma yasa ta kara saka kanta cikin wuyan shi tana makale shi sosai. Tsaye Rayyan yayi yana runtsa idanuwan shi ya sake bude su "Na kusan yaddaki kasa idan ba zaki daina motsi ba" Dago da kanta tayi "Ya zan daina motsi? Ko yara idan aka goya su baka ga suna motsi ba?" Hannuwanta Rayyan ya kama yana shirin banbaro su daga wuyan shi, ta saki kara tana dariya "Yi hakuri... Allah ya baka hakuri, na daina" Qwafa yayi yana rike hannuwanta saboda bayason zagaya su ta baya ya tallafeta. "Hamma..." Ta fara ya katseta da "Har surutu idan baki daina ba yaddoki zanyi" Shiru Layla tayi tana jin idanuwan mutane a kan su, amman ko a jikin Rayyan, tafiya kawai yakeyi kamar gabaki daya filin makarantar su kadaine a cikin shi har suka fara hango gate. "Bansan me kike ci da kike da nauyi haka ba" Dakuna fuska tayi "Ni ce nake da nauyin?" Ta tambaya "In kika kara magana saina jefar dake" Shirun ta sakeyi, daman shine yayi mata magana, tunda ai tayi shiru. A gate ma ta tsammaci ko a cikin security din wani zai musu magana. Amman meye basu saba ji ba, idan ma sun tare su ko da ba kanwar shi bace da yace musu kanwar shice zance ya kare. Sai da suka fita kofar makarantar sannan ya sauketa yana mayar da numfashi. Da gaske yayi mamakin nauyin da take da shi, wuyan shi duk ya gaji, haka bayan shi ma. Napep ya tare musu suka shiga, kusan rabin jikin Layla akan shi yake "Layla jikina zaiyi ciwo" Rayyan ya furta yana kamata ya kara gyara mata zama yanda zata kwanta a jikin shi kamar bai gama mitar zaiyi ciwo ba. A haka har suka karasa kofar gidan su. Shiya kamata ta fito ya sallami mai napep din tukunna suka shiga cikin gidan. Kana jin hayaniyar mutane, amman kowa na daki, kan shi tsaye dakin su ya wuce yana daga labulen hadi dayin sallama. Bilal da yake kwance daga shi sai singlet ya mike babu shiri ganin Layla. Riga ya dauka da sauri yana kokarin sakawa, itama Layla sadda kanta kasa tayi. Yana karasa saka rigar ya tsayar da idanuwan shi cikin na Rayyan. "Zazzabine a jikin ta, ba zan iya barin ta ba" Rayyan ya fadi, saboda ya ga tarin tambayoyin da suke cikin idanuwan Bilal din tun kafin yayi su. Har lokacin kuma kallon shi Bilal yakeyi, saboda na farko, abinda yake damun Layla din bawai na asibiti bane ba, na biyu, a hostel din tana cikin yan uwanta mata da zasu fi fahimtar matsalarta, na uku, baiga dalili kwara daya da zaisa Rayyan ya dauko ta ya taho da ita ba. Na biyu ina yake so ta kwana, gidan maza ne, idan kaga mace to wani cikin kabilun da suke hayane ya kawota, tunda ko yanzun ma akwai budurwar wani Joseph da yake gidan, kusan sati daya kenan da tazo. Amman babu wani hankali a cikin abinda Rayyan yayi tunda basu da inda zasu ajiye Layla, kuma hauka yakeyi idan yayi tunanin zasu kwana a daki daya su duka ukkun. Ko da ace ciki daya suka fito gabaki daya abune da zai zama zabin su na karshe a matsayin su na baligan musulmi, kuma hausawa. Shisa ya zabi yace "Allah ya kara sauqi" Ya juya ya dauki wayar shi, takardun da yake nazari yana karasawa ya zira takalman shi da suke gefe ya daga labule ya fice daga dakin. Irin halayyar nan na daya daga cikin halayen Bilal da bayaso. Layla takalma ta cire tana karasawa kan gado ta kwanta, dan bata da lokacin ganin jin dadi ko akasin haka a fuskar Bilal. Rayyan ledar hannun shi ya ajiye, yana bin bayan Bilal din "Bilal..." Ya kira ganin harya kusan karasawa dakin su Shehu. Juyowa Bilal yayi amman ya tsaya a wajen, sai Rayyan dinne ya taka ya same shi "Idan kana da abinda zaka fada mun ka fadamun, bana son ka dinga bani attitude..." Ya karasa da gajiya a muryar shi, cikin idanuwa yake kallon Bilal din "Me yasa zaka dauko ta? Meye zakayi mata anan da ba za ayi mata a hostel ba?" Da sauri Rayyan ya amsa da "Kulawa, zan kula da ita anan" Numfashi Bilal yake fitarwa, ran shine bayaso ya baci sam "Ka manta gidan maza ne nan Hamma? Ina dacewa ta kwana a cikin gidan nan? Me yasa baka tauna abinda zuciyarka ta raya maka kafin ka aikata? A hostel zata kwana da wasu a daki, idan tana bukatar taimako zasu fi saurin bata, anan fa? Ita kadai zata kwana..." Kai Rayyan ya girgizawa Bilal, duka a cikin abinda yayi baiga na fada ba, yaje ya dubata yaga tana zazzabi, idan ya dawo hankalin shi ba zai kwanta ba shisa ya daukota ya taho da ita. Baisan yanda zaiwa Bilal bayani ya fahimce shi ba "Zan kwana da ita" Yanda Rayyan din yai maganar yasa Bilal jinjina kan shi da ya fara alamar ciwo "Kai da ita? A daki daya?" Kai Rayyan ya daga mishi "Ni ba bacci zanyi ba, ina zane. Kuma zan duba abu haka. In tana bukatar wani abu zan sani" Idan ya tsaya zai iya fadar abinda zaizo ya dame shi, ko kadan Rayyan ba rashin dacewar su kwana daki daya da Layla yake gani ba. Tunanin shi ya tsaya a iya kula da ita ne, baisan ta yanda zai nuna mishi illar hakan ba, musamman wani abu daya tokare mishi kirji ya hana mishi tunanin komai "Sai da safe" Ya iya furtawa muryar shi na fitowa a shaqe, kai Rayyan ya jinjina, yana bin Bilal da kallo harya shiga dakin su Shehu, sannan ya koma. Layla ya samu in ta juya nan ta juya can "Kin ci abinci?" Ya bukata, kai ta girgiza mishi "In hada miki tea?" Da kai ta sake amsa shi, Bilal ya dauko musu wani flask daga gida, yakan dafa tea saiya saka musu a ciki. Yanzun ma cike yake, hada ma Layla kawai yayi yana mika mata kofin ta tashi zaune. Ya hada mata shi da kauri sanin bata ci komai ba, a hankali take kurba tana kallon shi ya natsu kan zanen da yakeyi, zaka iya rantsewa kamar baisan tana dakin ba, sanda ta gama shanye ta danji sauki-sauki. Kawai saita tsinci kanta da son ganin me yake zanawa. Dan haka ta mike tana zuwa ta gefen shi ta leqa, dago kai yayi "Bana son gulma, ki tashi daga saman kaina" Turo baki tayi "Ba aljanu ne da kai ba balle kace na tsaya a kanka zasu ta shi" Ganin ya motsa yasa ta yin tsalle daya tana matsawa, dariya takeyi ganin yanda yake kallon ta, ta san da lafiyarta kalau saiya masgeta. Shisa ta rufa ma kanta asiri ta koma ta kwanta "Meye kake zanawa Hamma?" Ta tambaya, banza yayi ya kyaleta. Kawai dan ta dame shi ne yasa ta dinga mishi tambayoyi, towel din da yake kan kofa na Bilal ya janyo ya ajiye a gefen shi, surutunta har tsakiyar kwakwalwar shi yake ji "Kaji Hamma..." Layla ta fadi, ko kadan bata ga dago towel din ba sai da ya shauda mata shi "Mayya ce ke?" Towel din ta janye tana ajiyewa gefe, juya kwanciya tayi. Ya furta kalmar daya san zata bakanta mata rai hankalin shi ya kwanta. Zanen shi yaci gaba dayi har sai da yaji shirunta yayi mishi yawa, dubawa yayi yaga tana bacci. Net din da tunda Bilal ya daura musu shi suke fada a kai ya saki yana gyara mata sosai. Kuma kawai dan ya cakar da Bilal din ne yasa shi fadin "Ni fa ba zan shiga net kamar kifi ba..." Dan murmushi ne ya kwace mishi yanzun daya tuna mitar da Bilal yai tayi har washegari. Yakan yi tunanin ko bakin Bilal na mishi ciwo wani lokacin saboda mitar tsiya. A haka su Ayya suke cewa Bilal salihi, Bilal baya magana. Bayan har tsegumi yakeyi, shi kadai kuma yake yiwa, baisan ko Aisha naganin wannan bangaren na Bilal ba. Komawa yayi ya zauna, haka kawai wannan karin saiya kasa samun natsuwa, lokaci zuwa lokaci yake tsintar kan shi da kallon Layla da take bacci. Mikewa yayi ya karasa wajen kofa yana kama labulen dakin ya daga shi sama. Fankar dakin ya kurewa gudu duk da an dan fara alamar sanyi. Ya karasa ya bude net din Layla yana rufa mata bargo. Duk da haka ya kasa samun sukuni, bai daina jin zufar rashin dalili ba duk kuwa da fankar dakin daya kure "Me yake damuna ne haka?" Ya furta a hankali. Kwayoyin shi ya tashi ya dauko ya sha yana mayar dasu ya adana. Amman har wajen awa biyu tsakani bai samu natsuwar da yake nema ba. Wata takardar ya dauka ya dora akan ta zanen da yakeyi yana rufa babban towel din daya siya domin hakan kawai ya dora kan shi akan tebir yana kwanciya. Kallon Layla yake da take bacci hankalinta a kwance, ba zai ce ga asalin abinda yake tunani ba, amman rabon da bacci ya dauke shi sha biyu saura ko da taimakon kwayoyi an dade, yau bacci mai nauyine ya dauke shi. Karfe wajen biyu da rabi hankalin Bilal ya kasa kwanciya, duk yanda yaso yayi bacci saiya kasa, kalaman Abbu na danne shi. Yana jin kamar ya kamata ace ya fadawa Rayyan bai kamata su kwana daki daya da Layla ba, amman sai yayi shiru ya bar shi. Abin kuma ya dame shi sosai da sosai. Tashi yayi ya fita. Hango fitilar dakin su yayi a kunne, kwanakin nan da wuta suke kwana. Yana mamakin yanda labulen dakin yake a dage. Yasan Rayyan, ko shara Bilal din zaiyi ya daga labule sai yaita masifa, quda zai shigo musu daki. Ya rasa hadin Rayyan da qudaje, ko kwara daya yaga gaccin shi a daki sai ya fitar dashi, ko ya kashe shi hankalin shi yake kwanciya. Balle kuma sauraye, ko jiya dariya Bilal yayi kamar zai shaqe jin Rayyan din na ma sauro masifa "Dan ubanka idan sha zakayi ba zaka sha ka wuce ba, sai kana mun ihu a kunne" Yanzun ma dariya ya tsinci kan shi dayi. Yana karasawa dakin. Bacci Rayyan yakeyi akan tebir, ko tunanin ciwon wuya bayayi. Cikin dakin sosai ya shiga, ya dauki maganin sauro na fesawa yana dan fesa musu saboda Rayyan din. Hannu ya saka cikin net din yana janyo dayan pillow din, ya mayar ya gyara. Dan bubbuga Rayyan din yayi daya bude idanuwan shi da suke cike da bacci "Ka sa pillow hamma, wuyanka zaiyi ciwo" Karbar pillow din Rayyan yayi yana ajiyewa ya mayar da kan shi ya dora, idanuwan shi ya lumshe saboda baccin da yake cikin su, sai yakejin kamar yayi kwanaki baiyi bacci ba. Wani irin numfashi Bilal ya sauke yana jinjina al'amarin su. Kafin ya fice, dan shima hamma yakeyi, idanuwan shi cike suke da bacci, hankalin shine ba'a kwance ba sai yanzun. * Zai iya cewa tunda safe yake tashi yayi wanka, wajen karfe hudu na safe wasu lokuttan. Yau ma da kan shi ya dora ruwa a kettle yaje ya sirka ya tashi Layla da ta dinga turo mishi baki kamar zatayi kuka. Duk da yasan babu mai fitowa sai da ya tsaya ta wajen hanyar bandakin har tayi wanka ta fito. Lokacin na shi ruwan yayi zafi, da duka kayan shi har wanda zai sake ya shiga bandakin. Yana fitowa ya tsoma wanda ya cire a wani bokitin yana zuwa ya wanke su. Alwala ya daura, saida ya kwankwasa dakin ganin Layla ta saki labulen, muryarta da alamar bacci ta amsa shi. Hakan yasa shi ya shiga, ya sake komawa ta kudundune cikin bargo. Kai kawai Rayyan ya girgiza. Bayason jikin shi ya bushe shisa ya shafa mai, turaruka ya fesa, yana jin shi a dai-dai. Har wani shiru yake ji cikin kan shi babu wata hayaniya saboda baccin daya dan samu. Share dakin ya karayi yaji kamar ya taka kasa. Zuwa lokacin har anyi kiran sallar farko, masallaci ya fita, kafin a tashi sallah zai samu yayi raka'a biyun da yake sunna mai karfi kafin asuba. Ko da aka idar da sallar asuba ya dade a zaune cikin masallacin, ba lazumi yakeyi ba ko wani abu, kawai lokutta da dama yakan samu natsuwa a cikin masallaci. Wani lokacin kuma kamar ana mintsinin shi haka yake so ya idar da sallah ya fita, shisa baya wasa da ranaku irin na yau. Sai da ya gaji da zaman sannan ya tashi ya fita. Dakin su ya koma, karfe takwas da rabi yake da darasi, yana nan zaune yana dan dudduba wasu abubuwan da bai fahimta ba har takwas saura, yana da biskit, da shayi ya hada yana cikin shane Hindu ta bude ido, tafi mintina biyar kafin tace "Hamma...ina kwana" Sai da ya ajiye kofin da yake hannun shi sannan ya amsa da "Ya jikin ki?" Taji sauki sosai, daman kwana biyun farko sunfi wahalar da ita "Naji sauki..." Ta furta a hankali, cigaba da shan shayin shi yayi harya gama "Ina da lecture da safen nan" Tashi zaune Layla tayi "Nima haka... Karfe tara, sai mu wuce tare" Kai Rayyan ya jinjina "Zaki iya zuwa?" Nade net din tayi tana sauko da kafafuwanta daga kan katifar "Eh mana..." Bai mata maganar taci wani abu ba, tunda yasan daga ita har Bilal basa iya cin abinci da safe haka. Shikam ko da asuba ne zaici, sai dai in bayajin yunwa. Iya abinda zai tafi dashi na ranar ya harhada ya dauko jakar shi yana kara shiryata ya saka a ciki. Ta riga da ta sake kayanta sanda ta fito, ta mayar da wancen cikin ledar da tazo da ita. Mayafin da ta ajiye akan gado ta janyo, doguwar rigace ta atamfa, mikewa Layla tayi tana duba ledar ta dauko dankwalin rigar ta ajiye. Ta karasa ta dauki ledar ruwa, fuskarta da bakinta take son daurayewa. Anan bakin kofa ta tsaya, tana jin idanuwan wani da batasan waye ba a cikin gidan yana kallonta, ko daga kai batayi ba harta karasa ta koma dakin. Dankwalin ta daura tana rataya mayafin a kafadarta "Muje?" Ta cewa Rayyan, ba kwalliya bace a fuskarta, har lokacin idanuwanta da alamar bacci, amman zuciyar shi dokawa take kamar zata fito waje. Sam ya rasa yanda zaiyi da abinda yake ji akan Layla yanzun, bayason yanda take birkita mishi lissafi haka. Tare suka fito, jan dakin kawai yayi, idan Bilal ya fito ya rufe, yana da mukulli a jakar shi. Baibi takan wasu cikin yan gidan da suke ta binsu da kallo ba har suka fice daga gidan "Hamma kana sauri" Layla ta fadi, juyawa Rayyan din yayi, ya kamo hannunta, suka taka zuwa titi, saboda ita yau zai hau abin hawa da safe zuwa makaranta, saboda kuma bata da lafiya. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:07 PM - 111: Dec 1, 2020 14 Kwance yake yana juyi. Maganganun Bilal ne suke mishi yawo, duk idan ya zauna haka kawai sai su dinga dawo mishi. Baisan me yasa Bilal din zai fada mishi su ba "Tuntuni ya kamata in maka magana Hamma, tun ranar farko da naga hannun Layla cikin naka ya kamata in tuna maka rashin dacewar haka, in tuna maka yanda tasowa gida daya a karkashin kulawar Abbu bai saka halaccin nan a tsakanin ku ba. Ka daina tabata, idan kana son ta ne kayi wani abu a kai ta zama mallakin ka, amman ka daina..." Bai amsa Bilal din ba sanda yayi mishi maganar, a cikin makaranta ne, shi yayi jarabawar safe, Bilal din kuma yana da ta azahar, haka ma Layla, baisan dalilin su na shigowa makarantar tun wajen sha biyu saura ba. Layla na karasowa wajen yaji ta riko mishi hannu ta baya, kusan rabin jikinta akan nashi, zai iya cewa ta rungume shine ta gefe "Hamma..." Ta fadi cike da wani nishadi da baisan dalilin ta nayin shi ba. Kuma a gaban Bilal din ya bambareta daga jikin shi. Ba zai manta da hawaye tabar wajen ba. Bai tuna rana daya da ya cewa Bilal shi yana son Layla ba, maganar ma wata irin dirar mikiya tayi mishi, tana hautsina wani abu a tare da shi da baisan yana a nutse ba. Yana zaman shi lafiya, yana lallaba rashin natsuwar da yake fama da ita a duk rana, Bilal yazo ya kara mishi wani tunani na daban. Ya saka shi yana neman ma'anar alakar da take tsakanin shi da Layla. Bai saba yawan magana ba, rabin da kwata na maganar da yakeyi a rayuwar shi tsakanin shi da kan shine, a iya tunanin shi maganganun suke makalewa. Kuma bai saba yiwa kan shi karya ba, yasan yanda yake jin Layla da ban da yanda yake jin su Rukayya, da sai yace ita din matsayin kanwa take a wajen shi. Duk da a ranar ne maganganun Bilal suka saka shi tantance hakan. Shi baice yana son ta ba, bai taba tunanin wata soyayya ba, bayajin yana da natsuwar janyo wata duniyar shi da take a hargitse. Me yasa ma Bilal din zai hargitsa mishi lissafi har haka, yanzun yana saka duk lokacin da jikin Layla zai hadu da nashi sai yaji wani irin tashin hankali na daban. Ya kuma rasa ta inda zai fara hanata rike shi ko da shi bai kokarin riketa ba. Musamman idan Bilal din yana wajen, sai ya kasa hada idanuwa da shi, akwai tarin abubuwa da Bilal yake nuna mishi bai kamata ba, amman yawancin su tun kafin ya fadi ya rigada ya sani, baisan yanda zai ya bari bane ba. Yawan hada jiki da Layla na daya daga cikin abin da ya kasa gano rashin dacewar shi sai da Bilal din ya tunasar da shi, sai dai kamar ko sa yaushe, ya kara kasancewa cikin jerin abinda baisan ta inda zai bari ba. Bilal ya sake mishi magana jiya, shine magana ta biyu akan abu daya "Nace maka idan son ta kakeyi kayi wani abu a kai ba zaka saurareni ba wannan karin ma ko?" Batare da ya daga kai ya kalli Bilal din ba ya amsa da "Ni bance maka son ta nake yi ba" Kai Bilal ya jinjina yana furta "Yayi kyau" Rayyan zai karya idan yace abin baya damun shi, gabaki daya komai ya kara jagule mishi. Shisa jiya yana gama jarabawar shi ya fita daga cikin makarantar bai jira Bilal ko Layla ba. Amman da tunanin ta cike da kan shi ya kwana, yau ma yana gama jarabawa ya gudo gida. Ya san za taita neman shi. Yana ma iya ganinta tazo gidan. Ko motsi yaji cikin gidan sai ya lumshe idanuwan shi yana jiran yaji shigowar ta, har bayan azahar, ko abinci ma ya kasa ci. Har zane ya fara, amman ya kasa samun natsuwa, mikewa yayi ya dauki riga ya saka a jikin shi, dan ya cire yabar singlet ne sanda ya dawo sallar azahar. Alwala yayi tun daga gida, saboda kar lokacin sallah ya kama shi a inda ba zai samu ruwan leda da zai alwala ba, ba shi bane zai saka ruwa a butar da baisan rabonta da wanki ba ya kuskura bakin shi, ya kuma wanke fuskar shi ya dauki wasu cutukan. Mikar hanyar da zata hada shi da makarantar su yayi, sanda ya shiga kuwa ana kiran sallar la'asar. Dan haka ya wuce masallaci ya gabatar da sallah yana fitowa, hanyar department din su Layla ya tsinci kan shi da nufa. Yasan ta fito daga jarabawa, tun daga nesa kuwa ya hangota da wasu riga da wando da sukayi mishi kama dana kasar indiyawa, sai dai tsakar rigar har kugunta, ya nade kanta da mayafin da ya rufe iya wuyanta. Dariya takeyi da alama, su hudune a tsaye. Ita da kawarta da har yanzun bai san sunanta ba, Anisa kawai ya sani a duk tarkacen kawayen Layla da bata rabuwa da yawo da su a cikin makaranta. Itama dan dakin su daya da Laylar, sam baka raba bakinta da kiran Anisa. Wani irin zafi yaji kirjin shi ya dauka ganin daya daga cikin samarin ya rankwafa kusan saitin kunnen Layla yayi mata maganar da tasa ta kwashewa da wata irin dariya. Daga yanayin yaron duk da bai karasa ba, yasan da wahalar gaske ya wuce sa'an Layla din. Shisa zafin kirjin shi ya karu, bai ga dalilin da zaisa ta dinga dariya da yan yara kananu haka ba. Har tuntube yake duk da babu wasu duwatsu a hanyar "Layla!" Ya kira daga nesa kafin ya karasa, muryar shi dauke da kashedi da wani irin yanayi da ba zai fassaru ba duk a tattare, ita ma Layla juyawa tayi tana hango Rayyan din, akwai wani abu tattare da fuskar shi da yake sanar mata da wahala bai dauketa da mari ba inya karaso, duk da hannun shi kan sauka jikinta da tayi laifi da batayi ba, wannan karin dai tana ganin tayi laifin ne amman bata san kona meye ba, ga kafafuwan ta kamar an dasa su a wajen. Da niyyar zuwa gidan su da sun gama labarin da sukeyi take tsaye a wajen. Saboda bata gan shi ba, jiya da ta kira wayar shi bai dauka ba, ta kira Bilal dan ya ba shi, yana karba yace "Ba kin kira ban dauka ba? Meye?" Can kasan makoshi ta amsa shi da "Bakomai" Kashe wayar yayi a kunnenta, abin ya mata zafi, ta kirane taji lafiyar shi tunda taje neman shi har ajin su bata gan shi ba. Ya hanata magana da kowa a cikin ajin, shisa bata tambaya ba, wanda suka gwada mata magana ma bata amsa su ba ta wuce abinta. Sai dai ya bata mata rai kamar ko da yaushe da yanayin yanda ya balbaleta da fada dan ta kira shi, babu kalar abinda bata fada ba kafin bacci ya dauketa, na yanda zai sani, yanda ba zata kara neman shi ba, itama tayi fushi, amman tana tashi da safe bayan tayi sallar asuba wayar shi ta fara nema taji a kashe. "Ka huta ai, kawa kanka Hamma" Ta furta tana jin babu dadi a ranta, har suka shiga jarabawa tana gwada kiran shi amman wayar a rufe take jinta. Ta kira Bilal yace mata yana makaranta, idan ya gama jarabawa shima zai zo ya dubata. Rayyan na karasowa abokanta da suke tsaye ya fara tsarewa da idanuwa yana musu wani irin kallo kamar zai rufe su da duka, yaran ko sallama basu tsaya yiwa Layla ba suka kama hanya suna wuce wa "Ina wuni..." Yarinyar da take kokarin labewa kusa da Layla ta furta cikin siririyar murya, itama idanuwan Rayyan ya kafeta dasu, tana sadda kanta kasa ta juya tabi bayan sauran "Hamma..." Layla ta kira tana son tambayar shi dalilin da duk zai kokarar mata abokai haka, amman yanayin fuskar shi ta hanata furta komai "Layla" Wani saurayi daya zo wucewa ya kira da murmushi a fuskar shi yana dorawa da "Ya jarabawar?" Murmushin karfin hali tayi mishi, zatai magana Rayyan ya damqi hannunta yana kallon saurayin "Bata son magana da kai" Ya fadi yanajin wutar da take kirjin shi tana karuwa. Murmushin shi saurayin ya fadada yana wucewa batare da yace komai ba "Uban kowa kulawa kikeyi? Bakya jin magana ko Layla?" Kai ta girgiza mishi tana kokarin kwace hannunta da take ji ya rike shi kamar zai tsage mata kashi, kamar hakan yaji ya saki hannun nata yana kamo kunnenta guda daya yana sakata fadin "Wayyoo Allah na Hamma...zaka tsigemun kunne... Hamma dan Allah" Ta karasa muryarta na karyewa, sake murda kunnen ta yayi yana mangare mata kai, dai-dai lokacin da idanuwanta suka sauka cikin nashi tun karasowar shi wajen, saboda ya dade da koyon kallon fuskar ta batare da idanuwanta sun hadu ba, kwalli ta saka da eyeliner da yasa idanuwan nata kara gudun bugun da zuciyar shi takeyi "Bar nan, mayya kawai" Ya fadi yana sauke idanuwan shi daga cikin nata, idanuwan Layla cike taf da hawaye ta raba shi, tana kasa yiwa Bilal da yake tsaye bayan Rayyan din magana saboda kukan da yake shirin kwace mata. Shima baice mata komai ba, kusan ya riga Rayyan karasowa department din su Layla din, ya tsaya gaisawa da wani abokin shine daya kwana biyu basu hadu ba, akan idanuwan shi komai kuma ya faru. Sai da tabar wajen sannan yace "Ka kori wanda suke tare, ka kuma kore ta itama" Juyawa Rayyan din yayi yana kallon Bilal "Bana son ganin ta da wasu" Yana dorawa da "Kuma ba kullum nake son ta a kusa da ni ba" Rayyan ya karasa maganar kirjin shi na zafi har lokacin, juyawa yayi yana bin bayan Layla da sauri. Bilal ya bishi da kallo yana ganin Ikon Allah, da dan gudu ya hada har ya taddo Layla da ya kama hannunta tana fisgewa, sake kamata yayi yana yin gaba ya soma janta. Zuwa wannan lokacin Bilal kuma baisan kalar tunanin daya kamata yayi ba. Abu daya yake ganewa a halin yanzun, yanda zuciyar shi take zafi kamar zata fito daga kirjin shi. Kiri-kiri yake ganin shakuwar da soyayya mai zafi ce zata haifar a tsakanin Rayyan din da Layla amman Rayyan ya karyata. Bilal ya rasa wa Rayyan yake kokarin karyatawa, kan shi, shi din, ko kuma soyayyar da take tsakanin su da alamu suka nuna basu da iko da ita. Lumshe idanuwan shi Bilal yayi yana sauke wata irin ajiyar zuciya. Yana bukatar Aisha a irin lokacin nan, idan tayi mishi hirarta zuciyar shi zatayi sanyi ya sani. Yau kanta ciwo yake yi, dan sai da ya fara rakata kofar hostel tukunna, tace mishi zata kwanta. Idan ya kirata ba zataki dagawa ba, idan kuma yace yana son suyi magana ma ba zata ki fitowa ba. Zai zamana mai son kan shi da yawa, hakan ya saka shi tafiya kawai. Motar da Abbu ya basu ta zamana kamar horo yanzun. Kiri-kiri abokai suka durfafeta, sai a tafi yawo a kone man ba za'a zuba wani ba, ga yanda Bilal yaga suna wujijjigata tunda basu san ciwonta ba, shisa ya kira Abbu yaji ko akwai inda zai iya zuwa ya ajiye motar, duk idan bukatar amfani da ita ya tashi sai yaje ya dauko. Akwai abokin Abbu din anan Zaria, kuma da yake Samaru ne, sai babu nisa. Can din ya kaita ya ajiye. Rayyan bai ko tambaye shi ina motar take ba, tunda ko kafin ya kai haka yakan shirya ya taka zuwa makaranta. Sam abin hawa bawai ya dame shi bane ba. Yanke hukunci tare machine yayi zuwa gida, ya hango kamar Rayyan tsaye ta wajen gate, karasawa Bilal yayi. "Hamma..." Ya kira, a gajiye Rayyan ya kalle shi "Ina ta jiran ka tun dazun" Ya kamata ace ya daina mamakin halayen Rayya "Ni kake jira?" Kai Rayyan ya daga mishi da ya saka shi jan numfashi "Da ban biyo ta nan ba fa? Na samu machine daga cikin makaranta? Sai kayi ta jira anan din? Me yasa baka kira wayata ba?" Kafadh Rayyan ya daga mishi kawai, bayason wata doguwar magana. Wayar shi baisan caji ya kare ba sai dazun, kuma ya ajiye a gidane. Ba wasu masu kiran shi yake da ba, amfanin wayar kalilan ne a wajen shi. Juyawa yayi ya fara tafiya, Bilal na bin shi suka jera suna fita daga cikin makarantar. Hannu ya saka a aljihu ya dauko kwalin sigarin shi "Dan girman Allah Hamma kar ka sha, idan baka kokarin ragewa ba zaka iya daina wa ba sam" Bilal ya fadi, yana kallon yanda lokaci yasa labban Rayyan har sun fara duhu saboda hayakin da yake bukama cikin shi, yau ma tunda sassafe da sigarin ya karya. Allah ne shaidar Bilal har a sallah yanzun addu'ar barin shan yake wa Rayyan. Kara daya ya zaro yana sakawa a bakin shi kafin ya mayar da kwalin aljihun shi, ya dauko lighter ya kunna. Sai da ya zuqa ya fitar da hayakin sannan yace "Ka barni Bilal, bana jin dadi" Numfashi Bilal ya fitar "Sai aka ce sigari ce jin dadin?" Kara sauri Rayyan yayi yana cigaba da zukar sigarin cike da kwarewa "Allah ya kyauta" Cewar Bilal da zuciyar shi take kara yin zafi. Kafin su kai gida sai da Rayyan din ya sha kara hudu na sigarin. Shayi suka sha da cin cin din da Layla ta kawo musu. Bilal na daukar takardun shi ya fice daga dakin dan karatu zai koma cikin makaranta yayi, tsallaken kwana daya yake da shi kafin jarabawar shi da ita kadai ta rage a zangon. Rayyan kwanciya yayi yana runtsa idanuwan shi da suka fara nauyi da alamun bacci, duk da yamma tayi. Idan baccin ya kwace mishi yasan sai dai wani ikon Allah zai samu ya runtsa da dare. Kuma kwakwalwar shi na bukatar hutun. Akwai tarin abubuwan da yake bukatar saka mata na jarabawar shi ta gaba. A hankali bacci ya dauke shi da mafarkin Layla kwance a gefen shi da baisan dalilin da yasa ta kutso mishi cikin mafarki ba. Duk da yana wata duniya daban bai hana shi furta "Mayya..." Cikin kan shi a duniyar ba. * Rayyan suka tsaya jira su dukkan su, shine karshen gama jarabawa, duk sun riga shi. Aisha ma da aka kirata a gidan su dan azo daukarta ca tayi musu zasu taho tare da su Bilal, da yake babu wanda bai san shi ba a gidan, babu kuma wanda bai aminta da shi ba sai suka amince. Ran safiyar asabar duka suka shirya. Bilal yaje ya dauko motar daga gidan abokin Abbu, dan ran juma'a yaje yakai an duba lafiyarta ya kuma zuba mai. Daga gida da suka dauki kayan su makaranta Bilal ya nufa. Yana kallon Rayyan daya bude gidan baya ya zauna, baice mishi komai ba. Dan tun jiya rabon da suyi magana, daya gaishe shi da safen nan kai kawai ya daga mishi, yan shiru-shirun sunzo fiye da kowanne lokaci, yakan dade Bilal bai gan shi a yanayin nan ba. Yasan ko me zai fada asarar bakin shi zaiyi, ba amsa zai samu ba. Abinda bai sani ba shine rabon Rayyan da ko gyangyadi kwana biyu cur, baccin ranar daya kan samu ya neme shi ya rasa. Duniyar a cunkushe yake jinta. Ga shi jiya ma bai samu ya ga Layla ba sam-sam. Ta zo ma gidan nasu da bata gan shi ba jiya batayi ba, ya sa ran zai ganta. Watakila fushi take yi mishi tun shekaranjiya, ba zai iya tuna kan me yai balbaleta da fada ba, fadan kawai yake iya tunawa. Har waya da safen nan ya dauka da niyyar kiranta yaji ko ta gama shiryawa sai kuma ya fasa. Zai ganta babu jimawa, a bakin kofar hostel kuwa suka same su ita da Aisha suna ta hira. Bilal ya fita ya saka jakunkunan su a bayan mota. Aisha tsaye tayi cikin rashin sanin inda ya kamata ta shiga ta zauna ganin Rayyan din a baya, ta dauka ita da Layla ne zasu zauna a gaba. Layla ta samar mata mafita da ta bude bayan motar tana shiga. Hakan ya sata bude gidan gaba ta zauna, Bilal ma ya shigo yaja motar. Sun gaisa dashi da safe, kara gaishe da shi Aisha tayi tana juyawa tace "Hamma ina kwana" Kai kawai Rayyan ya daga mata, da yake ta fahimci halin miskilancin shi da mutane da yawa zasu iya dauka wulakanci sai ta juya kawai. Layla kallon shi tayi, yayi kyau sosai sosai cikin farin yadi da ya saka. Yau harda hula, bawai baya saka manyan kaya bane kwata-kwata, yakan dai kwana biyu bai saka ba. Ga dinkin rigar dogon hannune mai links, ta kasa daina kallon shi, kyau yayi mata yau fiye da kowanne lokaci, zuciyarta har wani kumbura take da tarin soyayyar shi da batasan yawan ta ba. Amman inda take Rayyan bai kalla ba, asalima kan shi ya jingina da kujerar motar yana lumshe idanuwan shi. "Hamma..." Ta kira, muryarta iya kunnuwan shi, jiya fushin da ta kwana tana yi mishi bai yini ba, son ganin shi ya danne mata komai. Yanayin da har ya saka tunanin ko da gaske ne? Maitar da Mami take karyata cewa ta gada ta bangaren mahaifiyar ta, duk da zuwa yanzun shi kadai dinne yake kiranta da "Mayya..." Saboda idan har da gaske bata kasance mayya ba ya kamata ace zuciyarta ta hakure da shi, ya kamata ta sama musu sauki su duka biyun, sai dai kamar yanda batasan lokacin da ta fara son shi ba, haka bata san ta inda zata fara dai nawa ba. Idan ma yaji bai nuna mata alamar hakan ba, son jin muryar shi takeyi da dukkan zuciyarta "Hamma" Ta sake furtawa, tana dan kallon su Bilal, hira suke sosai, da alama hankulan su baya kanta. Sake kallon Rayyan da bai motsa ba har lokacin tayi, tun kiran farko da tayi mishi yaji ta, asalima tun daga nesa ya hango ta, ta saka material ruwan toka, sai farin mayafi, yau idanuwanta ya fara hangowa zuciyar shi na tsinkewa, sai dai yana dauke idanuwan shi daga kallon nata ya mayar dasu kan yanda tayi kyau sosai, sai yaji yanayin daya kwana biyu baiji ba, riketa yake so yayi, wani kusanci yake son samu da ita komin kankantar shi. A kwanakin nan biyu da yayi su a hargitse ganinta ya saka shi jin kamar daya riketa koyayane wani abu zai natsa mishi. Dakyar ya raba idanuwan shi daga kanta yana kallon Bilal da suka hada ido ta mudubin gaban motar, kai Bilal din ya girgiza mishi a hankali, kamar yana san abinda yake tunani, kamar yana son fada mishi karya fara aiwatarwa. Wani irin yanayi zuciyar shi ta shiga lokaci daya, idanuwan shi a bude suke, kuma safiya ce, baisan me yasa yake ganin duhu ba. Tana zagayo ta shigo ya zabi ya rufe idanuwan shi, har wani dumi jikin shi yake dauka da son rike ko da hannunta ne. Ya rasa kalar sabon da yayi haka da haduwar da jikin su yake yawan yi. Jin Layla tayi shiru yasa shi kara runtsa idanuwan shi yana kokarin fitar da numfashi a tsanake, ba lokaci yake gani ba, banda sautin karar mota da yake nuna alamar sun dauki hanya babu abinda yake ji, sai numfashin Layla da baisan ya akayi kunnuwan shi suka tsinto mishi shi ba, kusan yanajin bugun zuciyar ta ta hakan. Kafin yaji dumin hannunta cikin nashi da yake akan kafar shi. Kamar hannun na da ikon kan shi na budewa ta saka yatsunta a ciki tana dumtsawa, yanayin da yaji har kasan zuciyar shi "Nagode..." Ya furta a hankali yana kara dumtsa hannunta, saurin kallon fuskar shi tayi, sai taji kamar godiya yayi mata, amman bata ga alamar ya motsa komai a fuskar shi ba. Da badan wasa da yake da hannunta da ta saka a cikin na shi ba sai ta iya rantsewa da cewar bacci yakeyi. Wata irin ajiyar zuciya ta sauke, tana jin kamar yau akwai abinda yake damun shi fiye da kullum, watakila kuma tunaninta ne kawai. Aisha bacci tayi dan ita sai dai in iskar mota bata fara kadata ba. Ta mudubi Bilal yake kallon su, da alama Rayyan ma bacci yakeyi, Layla kuma ta kwanta a kujerar ne tana fuskantar shi, idanuwanta akan shi kamar a duka duniya babu wani abu da ya taba daukar hankalinta irin Rayyan din yana bacci. Yanayine da ya sa na wasu dakika Bilal ya manta da tuqi yakeyi saboda zafin da kirjin shi ya dauka. Yana kallo Layla ta daga hannunta da nufin taba fuskar Rayyan din, duk daukarta bacci yake, kamar zare ta gani a gefen fuskar tashi kan kasumbar da ta sha gyara, lokacin da yai saurin damkar hannunta da dayan hannun shi, lokacin kuma da Bilal ya taka motar yana kaucewa karawa wata mota da ta ke tahowa, B Rayyan ba hatta Aisha sai da ta bude idanuwanta tana fadin "Subhanallah..." Shima Bilal din duk wata addu'a da tazo bakin shi yi yake. Sun kusan mintina biyu kafin ya samu natsuwa dan ya rage gudun motar sosai. Rayyan kuma hannun Layla daya damqa ya saki yana kokarin saka idanuwan shi cikin nata duk da yanda zuciyar shi tayi wata irin dokawa "La hawla wala quwwata ila billah" Ya furta a cikin kan shi ganin kamar ya hada idanuwa da mage, kwayar ce kawai da ta Layla take a zagaye, ta mage kuma a tsaye. Dan runtsa idanuwan shi yayi, yana komawa cikin kujerar ya kwanta yana bata damar sauke nata, tana kula da yanda ba kullum yake kallon cikin idanuwanta ba. Kamar yasan duk idan yayi sai taji wani abu yana fisgarta a cikin su kamar igiyar ruwa. Bata da wasu kalamai da zasu fassara asalin yanda take ji duk idan ya kalleta, ta sha kallon mutane sun nitse a cikin ruwa a fina-finai daban-daban, takan kuma ji a labaran yau da kullum. Bata taba hasaso yanda yanayin yake ba sai lokacin farko da ta fara mallakar hankalinta, lokacin da Rayyan ya saka idanuwan shi a cikin nata. Sai taji ta tsundum cikin ruwan da batasan da bata ganin farkon shi balle karshen shi, take numfashi ya soma mata barazana, yau ma hakan take ji, dan har bakinta ta dan bude tana fitar da iska daga cikin shi. Zuu din wayarta ya dan taimaka mata sosai, da alama sun dan sake shiga wajen da network ya dawo, dan daga fuskar wayar tayi tana saurin mayar da ita ta kife, ta kalli Rayyan taga ya mayar da kan shi, idanuwan shi a rufe suke kuma, duk da haka zuciyarta kamar zata fito saboda bugun da ta kara, sakonnin duka daga group din "Sirrin ma'aurata zalla" Yake fitowa, group din da tun tana hangen su Nanaa da kawayenta sun tattaru a ajinsu ana shewa ana kus-kus a kai cikin yanayin da yai bala'in jan hankalinta har ta fara lekasu, ba sai an gaya mata ba, tasan su Nana sun girmeta, kamar basuyi nasarar da tayi ta samun makaranta da wuri ba. Da yake sun jima suna son yin magana da ita tana sha musu kamshi dan yanayin wayewar su baiyi dai-dai da ra'ayinta ba, har group din ya zama sanadin da take kula su. Ranar da aka sakata wuni tayi da waya a cikin aljihun wando, sai take ganin duk wani sako da yake shigowa ta manhajar WhatsApp dinta kamar wani na kallon ta, kamar wani na kallon kalar abinda take gani take kuma karantawa da bai kamata tayi ba. Rannan da Ainau Mardiyya da suke kusa da dakin su sanda ta shiga ayi mata kitso suna hirar waya sai taji kamar da ita Ainau take, kasancewarta daliba itama yar aji hudu, sauran yan dakin nasu ma duk yan aji hudune, a cikin su kuma Dina ce takan mata kitso, wata yar asalin garin Kaduna yaren bajju, taji hausa kamar bahaushiya. Hirar illar wayar da tafi amfaninta yawa a zamanin sukeyi, Ainau na fadin "Yanzun fa zamani yazo da kana iya kokarin ka akan tarbiyar yaranka, kana tsaye ba dare ba rana, da addu'a dan neman kariyar abinda baka gani wayar hannu na warware maka tufka" Dayar yar dakin su Ainau din Kamila na karbe zancen da "Wallahi, abin da tsoro, idan baka kai zuciya nesa ba, waya tsaf zata zama halakar ka, ka hana yara waya wani katon banza ya yaudare su da kwadaita musu ita a waje..." Tabe baki Dina da takewa Layla kitson tayi "Idan ka basu ma ba tsira kayi ba, kinsan wani group dana gani kwanaki kuwa? Hankalina yayi bala'in tashi, a wayar Gift kanwata nagani...nasa Maman mu ta karbe, amman naki nutsuwa" Sosai Layla ta takura, tanajin kamar da ita suke, kamar wata ta leka wayarta taga abinda yake faruwa, taga tarin labaran da bata taba cin karo da abinda ya girgiza duniyarta yana rike tunaninta irin kalar labaran ba, abinda take hasashe ne ake nuna mata yanda yake faruwa cikin yanayin da bata taba hangowa ba, ita kuma Allah yayita cikin jerin mutane masu bin kwakkwafi, dole tana sauka gida zata fadama Naana zata fita daga group din idan sun koma makaranta sai a mayar da ita, saboda Mami na da kula, Mami na kuma da bincike, kuma a karo na farko zuciyarta a tsorace take da Mami taga wannan group din. Rayyan daya kara dumtsa hannunta yana murza yatsunta ya yanke mata tunaninta dan yanayine da taji har tsakiyar kwanyarta, sai yake tuna mata daya daga cikin labaran da ake tattaunawa a kai jiya a group din, wani abu daya tsaya mata a makoshi ta hadiye tana jin wani irin yanayi da bata da fassarar shi yana saukar mata. A haka suka shiga garin Kano, tana jinta sama-sama. Aisha suka fara saukewa suna wucewa gida. Sanda suka sauka, kafafuwanta babu kwari take jinsu, Rayyan kuma bai jirata ba ya shige gida, hada idanuwa tayi da Bilal da yake binta da kallo cikin wani sanyin yanayi kamar yana son karantarta har zuci. "Ka sha maganin ciwon kai" Ta fadi tana wuce shi, launin idanuwan shi sun canza, shisa ta gane kan shine yake ciwo, barin shi tayi a tsaye kamar batayi komai ba, kamar bata taba zuciyar shi ba. Tun da ya tashi yake dan jin ciwon kan, amman ita da Rayyan ne suka kara mishi wani sabon ciwon kan, ta kula kamar ko da yaushe, ta kuma gane kan shi yana ciwo. Numfashi yaja yana fitarwa kan shi kamar zai bude, cikin gida ya shige shima, sun fitar da jakunkunan daga baya. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:07 PM - 111: Dec 2, 2020 15 Su Rayyan ne suke makaranta, sune da karatu amman Ayya ce take ramewa saboda tunani. Duk yanda Bilal yake jaddada mata cewa lafiyar su Rayyan din kalau hankalin ta ya kasa kwanciya. Asalin abinda take son ji Bilal ba zaj fada mata, balle kuma tunda suka tafin basu dawo ba sai yanzun da akayi hutun karshen zango. Da kanta ta nemi Hajiya Dije saboda ta samu a shiga tsakanin Rayyan da Layla, harma da Bilal din. Bata da natsuwar binta wani waje ma, tace taje mata ne, tashin farko dubu sittin Ayya ta tura ma Hajiya Dije. Abinda bata sani ba shine wajen shekaru hudu kenan komai ya kwance a gidan Hajiya Dije. Tunda maigidanta ya dawo da uwargidan shi, ga yara da take dana sanin cusa musu bakin hali tun suna da kankantar su, mazan kusan duk suna da sana'ar su ta kasuwanci da sukeyi. Amman basa bata kudi, idan ta tambaya sai dai suji abinda zatayi da su, idan ta kama su siya mata ne su siya. Komai ta samu kamawa takeyi ta karyar wajen dilla lai ta kai ma Malamai, to yanzun ma tunda ya kamata tana mishi barbade yai mata saki daya, dakyar aka samu aka maida auren, duk wani abu da zai fito daga bangarenta ya daina ci balle ta samo kan shi. Gani takeyi bokan uwargidan tane yafi wanda take bi. Shisa take ganin Ayya rashin godiyar Allah ne yake damunta, sam matsalarta ba matsala bace ba, kukan dadi takeyi, ta ga Laylar da Ayya take ta daga hankali a kai, yarinya ce mai kyawun gaske, yarinyar da gari banza duk kyan Rayyan din shima sai yayi gaske ya samo me kyawun Layla. Mijinta abinda duk take so shi yakeyi, kaffa-kaffa yake da bacin ranta batare da wani aikin malami ko boka ba. Amman kullum bata rasa abin mita, shisa ta samu saniyar tatse, ranar da sukaje wajen wani Malamin tare kudi ake tsulawa Ayya idan sun tafi Hajiya Dije ta koma ta karbo. Rabonta da zuwa ma Ayya wajen wani Malami na kwarai tun wanda yai mata aiki akan Haris da tambayar duniya da tayiwa Ayya akan zancen aikin sai tasan dabarar da tayi suka fada wata hirar. Watakila taji tsoro ne batayi amfani da maganij ba, duk kudin da ta kashe a kai. Tunda kwanaki ma da taje gidan ta ga Haris din ya shigo har bangaren Ayya yana gaishe da ita, harma da yar hira sukayi yana shiga Kitchen ya zuba tuwo da tayi, ba zata manta cewa Ayya "Haris dinne nan?" Saboda ita bata ga alamar lalacewa a tare da shi ko daya ba, mikewa Ayya tayi yana amsa ta da "Shine, bari in dauko miki leshin da nake magana" Murmushi kawai Hajiya Dije tayi, tasan dan karta tayar mata da zancen Haris ne. Wannan kuma duk matsalar Ayya dinne a ganinta. Yanzun dai a sama ta sami saniyar tatse. Danma kudin a wajen bin 'yan tsubbu suke tafiya itama. Duk kan mijinta da take tunanin an janye hankalin shi daga kaine. Ayya kuwa ranar wata zuciya aka kawo mata an yayyanka turbude da magani akace ta wanke ta zuba ruwan a bakin kofar dakin su Rayyan, sai ta ajiye zuciyar tayi mishi girki da ita duk idan yazo, daga shi har Bilal din a tabbata sun ci, to zai zama kamar ta kwato musu tasu zuciyar ce da Layla ta lashe. Karba Ayya tayi, da fari maganin yayi mata kama da ararrabi saboda kalar shi, kamar ta dandana da ta wanke, sai tayi saurin kauda tunanin daga ranta. Duk irin wannan was-wasin kan bata aiki wani lokacin. Yanda akace tayi haka tayi, zuciyar ta kulle a leda ta saka a fridge, take ta ajiyarta tunda su Rayyan din sunki zuwa, sai a satin da tayi waya da Bilal ya tsayar mata ranar zuwan nasu. Cous-cous ta dafa musu da ya sha hanta da zuciyar da kuma kayan hadi. Aikam ranar tas suka cinye shi da Bilal, danma Bilal ya tsaya taince albasar da take ciki. Duk da haka taki samun natsuwa, rabin rayuwar ta tun zuwan su jikin window take yinta, ko baccin rana ta daina samu tana runtsawa, dan ko ta kwanta sai taji kamar an gitta, da sauri take dirkowa daga kujera ta leqa ta ga ko Layla ce. Ga Rayyan din da ta dan fara gane kan shi kafin ya tafi ya kara hargitse mata. Ko sau daya bai tako dakin ba, itama da taje ta same su a bangaren su kan shi a kasa suka gaisa, surutun duniya da tayi baice mata uffan ba. Haka ta fita cikin kunar rai, Bilal ne ma yabi bayanta yana lallashinta "Ayya kinsan halin shi ai, kuma baya ma jin dadi kwana biyu tunda muka dawo, nima shiru-shirun ake tayi mun" Ya karashe da murmushi, ranta na suya tace "Dan uban shi dan bayajin dadi sai inta magana yanaji na yaki dagowa balle inyi tunanin zai tanka? Har yaushe zai san ina da muhimmanci mai girma a rayuwar shi Bilal? Ace yafi karfin ya taso yazo ya gaishe dani ko da sau dayane a rana? Shikenan..." Ta karashe muryarta na karyewa cikin yanayin da yasa Bilal fadin "Dan Allah kiyi hakuri....zai gyara ai..." Kai ta jinjina, dakyar ta iya cewa "Hmm...Allah ya shirya" Nan Bilal ya zauna yana ta mata labari har saida ya ga ta warware tukunna ya tafi. Shisa tayi kewar shi matuqa a watannin nan da baizo ba. Duk wata hanya da zaibi ya rage mata damuwa ya sani. Yafi kowa fahimtarta, akwai halayenta da ko Abbu baisan yanda zaiyi da su ba amman Bilal ya sani. Zata iya cewa idan da na zama amini to Bilal ne amininta, duk wata damuwarta ko ta waya idan ta kira shi ta kai karar Abbu da Mami sai ya lallaba ya bata hakuri, saiya nuna mata yanda yake goyon bayanta, cikin dabarar shi. Neman Malamanta ne kawai abu daya da Bilal bai sani ba, abu daya da ba zata iya rabawa da shi ba saboda bata so yayi mata wani kallo na daban. Mami kuwa tun da suka dawo sai ta tsinci kanta da bin Layla da ido a duk al'amurranta, tun kafin tafiyar su wayewar da yarinyar tayi ya wuce shekarunta, amman yanzun sai take ganin wata irin wayewa ta ban mamaki ta kara shigarta, kamar idanuwanta sun kara budewa. Bakinta bai daina bin Layla da addu'a ba ko a zaune take. Musamman da take makaranta, sai taita yawan tsintar kanta da faduwar gaba na rashin dalili, kuma tasan duk akan damuwar Layla ne da ta saka a ranta. Sai ta kirata sau nawa a rana, a duk karshen wayar tana jaddada mata "Dan Allah ki kula Layla, ke mace ce. Kiyi kokarin kare martabar ki a dukkan al'lamurran ki. Ba lallai sai a shigar ki ba, martabar ki na tare da abinda harshen ki zai furta, tana kuma tare da mu'amallar ki da mutane, musamman maza... Ki kula, ki rufamun asiri ki rufawa kanki asiri" Ta kan amsa da "In shaa Allah" Wani lokacin kuma ta kanyi shirun da yake karawa Mami damuwa, sai taji kamar ko Layla nayin wani abu da bai kamata ba shisa tayi shiru tana jinjina kalamanta na ranar, a lokutta irin wannan da ta sauke wayar take fadin "Allah ka taimakeni, Allah ka bani ikon sauke amanar da na dauka" Amman zuciyarta na rawa sosai. Jiya cikin dare ta farka, sabonta ne duk idan ta farka taji ba kishi bane ko wani matsi na fitsari da makamancin shi ya tasheta to fa sai tayi kokarin yin sallah ko da raka'a biyu ce tayi addu'a. Ta kanji kamar akwai dalilin da yasa Allah ya dawo mata da ruhinta a dai-dai lokacin. Watakila wani abune zai sameta, ko ahalinta shisa Allah ya bata damar sake kaddarar ta hanyar addu'a. Jiyan harta ninke dardumarta sai taji son ta duba Layla, wajen karfe biyu da rabi, tana kama kofarta da take kullewa a kwanakin nan sai tayi nasarar jinta a bude, turawa tayi taga Layla ta kife wayarta da saurin gaske. Kwan fitilar dakin ta kunna, haske na gaurayewa da yake akwai wutar lantarki "Layla?" Ta kira tana karewa Layla da take zare mata idanuwanta da ta ga sun sake launi da alamar baccin da yake cikin su da kuma wani abu daban da ba zata ce ko menene ba "Karfe nawa yanzun? Baki yi sallah ba bakiyi komai ba dan ubanki kin zauna danna waya?" Mami ta karashe a fadace, wayar nan tana ci mata tuwo a kwarya, daman da rana sanda zasu ci abinci duk sai da ta amshe a hannunta da na Jabir tukunna suka maida hankali suna cinye abinci suka sake daukar wayoyin. Yau dai a tsorace Layla take kallonta, ko kadan bata san cewa bata kulle dakin ba. Kamar sanda ta dauko ruwane wajen karfe sha biyu, hankalinta nakan labarin da take karantawa, shaf ta manta da ta kulle dakin. Hankalinta a tashe yake da yanayin labarin, ta fita daga group din. Idan an aiko wani mai zafine sai Nanaa ta mata copy ta tura mata. Makoshinta da kamar an zuba kasa saboda yanda take fitar da numfashi yasa ta tashi ta dauko ruwan, ashe bata kulle kofa ba, har zazzabi take ji na rashin dalili kafin Mami ta shigo mata daki babu tsammani, zuciyarta har cikin bakinta taji saboda yanda ta tsorata, idan Mami taga abinda take karantawa kashinta ya bushe, ita da waya har abada, a jikinta take jin haka "Bani wayar ki kwanta dan ubanki, marar hankali kawai" Wani irin bugawa zuciyar Layla tayi, muryarta na rawa tace "Dan Allah Mami kiyi hakuri, wallahi caji zan saka in kwanta yanzun daman..." Layla ta karashe tana dauko wayar daga karkashin cinyarta, hannuwanta rawa suke sanda ta fita daga WhatsApp tsabar tashin hankali. Gabaki daya wayar ta kashe ta janyo cajar ta da take makale a bango ta saka wayar ta dora kan durowar gefen gadon. Tana jin idanuwan Mami akanta "Akan wannan raba daren na kusa haramta miki wayar nan gabaki daya. Taya ba zakiyi fama da ciwon kai ba? Kullum ba zaki samawa kanki hutu ba" Ita dai Layla kwanciya ta gyara tana jan bargo ta lullube har wuya, zuciyarta banda bugawa babu abinda takeyi, duk fadan Mami bakomai yake karasawa kunnuwanta ba, yanda ba zata sake kuskuren barin kofa a bude ba take tunani. Har Mami ta kashe mata kwan dakin tana ficewa hadi da ja mata kofa. Wucewa dakinta Mami tayi, amman har yau abin yayi mata tsaye a rai. Tana tunanin ko Layla ta fara kule-kulen samarine da suke riketa da hirarraki har cikin dare haka. Duk da tana tunanin akwai wani abu da yake wanzuwa a tsakanin Layla da Rayyan da su kan su basu fahimta ba har yanzun. Tsoro ne fal a ranta, saboda a lokaci irin wannan ba yara mata bane matsalar, su daman masu rauni ne, mazan ya kamata iyaye su tsawatarwa. Allah ya sani saboda Layla take kokarin bin diddigi akan su Haris, tasan shi bashi da matsala, budurwar shi guda daya. Yar gidan Yaya Ayuba ce kuma, tasan baya kule-kule. Jabir ne damuwarta, kullum cikin mishi nasiha yake, idan wasu yake yaudara zai iya dawowa kan Layla "Dan Allah Jabir ka kula, kaga kana da kanwa, ka tayata kare martabar ta wajen mutunta yaran wasu, karka cutar da 'yar kowa..." Dariya yakan yi sosai "Malama Mami" Ya kan fadi yana dariya, har sai ta zage shi ko yaga tana shirin daukar wani abin dan ta kwada mishi tukunna yake tashi ya gudu daga dakin yana mata dariya. Tasan ba zata raba Layla da samari ba, ko dan yanda take da kyawu. Dan ta hanata raba dare tana hira abinda zasu fada din idan na banza ne har da rana ma sai su fade shi. Tana hana danna wayar daren ne dan ta kwanta ta samu wadataccen bacci, saboda yanda take yawan mitar ciwon kai. Sosai Mami na ganin wautar masu yankewa yaran da zasu gani tsakiyar dare suna chatting hukunci marar kyau. Ba lallai maganganun banza sukeyi ba, maganar banza bata bukatar lokaci, zai iya yiwuwa hira suke ta yau da kullum da abokan su, kamar yanda kake zama kayi hira sosai da naka abokan, ko idan kayi baki hira tayi muku dadi sai a raba dare ana zantawa, zai iya zamana baccine ya kauracewa idanuwansu, zamani da yai musu sabo da waya yasa suka dauka suka shiga dan duba tsofin sakkoni su rage kewa, watakila, watakila dalilai ne mabanbanta. Akwai munafunci da son kai a yanke hukuncin cewa maganar banza yaran sukeyi da tsakar dare. Saboda kai me kakeyi kenan? Me ya kaika shiga manhajar da tsakar dare? Me ya kaika bincikowa kaga ko suna online ko basa nan? Gulma? Addu'a Mami tayi sosai da ta dan sama mata natsuwa. Da yake tun dawowar Layla bata barinta yin wani aiki, ita take su girki da gyaran gidan tunda bata da kwiya. Magriba da aka kira yasa Mami kiran sunan Allah tana mikewa dan taje ta gabatar da sallah. * Tsaye yake a bakin kofar dakin su ya dawo masallaci sallar isha'i. Wayar shi yake dubawa yana ganin sakonnin Mtn da suke ta cire mishi kudi na rashin dalili, harda su wani caller tune da baisan sanda yai subscribing ba. Karamin tsaki yaja, sakonnin ma duk sun taru sun cika mishi waya, ba dubawa ya cikayi ba. Ya goge duk na Mtn din. Ya shiga na bankin shi ma yana gogewa. Na Layla ya shiga, akwai wanda ma bai bude ba ashe, shifa waya sam bata dame shi ba. Balle kuma tunda suka dawo gida, in banda Layla babu wanda ya kira da wayar, sai fa Bilal da idan ya fita yana son gaya mishi wani abin ya kira shi. Ya kara yawan kwayoyin da yake sha saboda ya daina samun bacci kwata-kwata, na ranar ma wahala yake mishi. Haushin komai da kowa yake ji, baison yin magana, ba kuma yaso ayi mishi. Surutun na kara mishi hayaniya cikin kan shi sosai da sosai. Yafi bukatar shiru akan komai yanzun. Sam baiji takun tafiyarta ba, sai hannuwanta da ta sakala cikin na shi tana fadin "Hamma..." Ba dan bata gan shi ba duk yinin ranar, ta gan shi bai dai kulata ba, inda take ma bai kalla ba, tunda suka dawo ya kara zama shiru-shiru "Kaqi fadamun abinda yake damun ka ko?" Ta furta da wani irin sanyin murya, saboda ta tabbatar akwai abinda yake damun shi, Rayyan na jinta a wajaje fiye da jikin shi, musamman da ta kara riko hannun shi tana dora kanta a damtsen hannun nashi, bai hanata ba, bai kuma daina duba sakonninta da yake dubawa ba, surutu takeyi amman tare da ita a jikin shi haka sai yake jin shirun da yake dan bukata a cikin kan shi, kamar karta raba jikin shi da nata, kamar ta zagaya duka hannuwanta ta bayan shi ta rike shi dam haka yake ji. "Hamma..." Layla ta kara kira tana jin kamar ta mayar da shi cikin ta saboda wani irin yanayi da taje ji. Da gaske tana son shi, tana kaunar shi da dukkan zuciyarta, a kwanakin nan tana hasaso rayuwa kala-kala a tare da shi. Wayar dai yake dannawa, yanda tayi luf a jikin shi da yanayin sunan shi da ta kira sun sa ya daina gane abinda yake karantawa. Su duka biyun suna wata duniya ne ta daban, har sai da suka ji muryar Mami da tace "Layla?" Cikin wani irin tashin hankali, dai-dai lokacin da Layla ta tittida kafarta tana son sumbatar gefen fuskar Rayyan din saboda yanda wata irin soyayyar shi take nuqurqusarta. Mami kuwa jikinta babu inda baya rawa, Layla din ta fito ta kira dan ta bata lambar Haris ta Etisalat din shi, wadda take ta kira taki shiga, ta tsammace ta wajen bangaren su Rayyan din daman, amman ba'a jikin shi makale ba, ba a cikin wannan mummunan yanayin da yasa numfashinta har tsaitsayawa yakeyi ba. Ga kafafuwan ta da taji suna barazanar kasa daukarta. Tun da ta shiga aji biyu sakandire ta zaunar da ita tana kara jaddada mata yanda babu halaccin wannan rirrike rirriken a tsakaninta da duka mazan gidan. Har misali tayi mata da su Rukayya, da yanda ko su basa rike hannun Rayyan. Sosai ta tsawatar mata saboda ta ganta da ta Rayyan din yazo nemanta ta rike mishi hannu. Ta dauka tun a lokacin ta bari, tunda a gabanta Rayyan din ya fisge hannun shi har duka ya kai mata, sai Mamin taji sanyi. Idan ita Layla bata da hankali Rayyan yana da shi. Amman ko da Layla tana tunanin Rayyan din Yayanta ne, wannan rikon da tayi mishi ya wuce na yan uwantaka, idan ba idanuwanta bane suka gane mata kamar sumba Layla take shirin mannawa Rayyan din "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un..." Mami ta fadi tana nufar Layla da ta raba jikinta daga na Rayyan da bayanannen tsoro a cikin idanuwanta "Ma.. Mami" Ta furta muryarta na fitowa a sarke, Mami na karasawa wani mari ta dauke Layla da shi tana kai mata dukan da Rayyan yaji har tsakiyar zuciyar shi. Lokaci daya kan shi ya sara yana daukar ciwo, bai dai motsa daga inda yake ba, idanuwan shi na kafe kan wayar da hankalin shi baya kai. "Ashe baki da hankali? Ashe baku da hankali" Cewar Mami da wani irin firgici marar misaltuwa, tana kara kaiwa Layla da take zubar da hawaye duka tana damko hannunta, Rayyan da yake tsaye Mami take kallo "Idan ita bata da hankali kai baka da shi? Baka san haramcin da yake cikin abinda kuke aikatawa ba ko? Wallahi da Abbun ku zan hada ku, ba zan iya ba, ba zaku ja mana magana ba" Mami ta karasa tana fisgar Layla zuwa bangaren Abbu, sai tirjewa takeyi saboda tsoron da yake cike da zuciyarta. Rayyan ba zaice ga abinda yake ji ba, amman jikin shi har bari yake daya kare Layla daga dukan Mami din, sosai zuciyar shi take jin ciwon dukan da tayi mata. Baice abinda tagani me kyau bane ba, har Bilal ya fada mishi ya daina baiji ba, ba laifin Layla bane ba, shine daya barta. Yaso ya bude baki yau ya gayawa Mami haka, amman baisan ta inda zai fara ba, shisa yayi shiru. Ya kasa barin wajen, yana nan tsaye har lokacin yaga Abbu yayo wajen, Mami na biye da shi, sai Layla da take biye da Mami din tana kukan da yake shigar mishi rai. Yau yasan bayason hannun kowa ya taba jikin Laylar, bayason kowa ya zama dalilin kukanta idan bashi ba. Ita yake kallo har suka karaso wajen da Abbu yana kiran "Rayyan?" Saboda shima zuciyar shi bugawa takeyi, ya zauna kenan Mami ta shiga rike da Layla tana fadin "Dan Allah kayi musu magana ko zasu jika, kayi musu magana kafin mu suja mana magana..." Yanayin muryarta da yake cike da tsoro da karaya yasa Abbu tambayar 'Su wa? Lafiya? Me yake faruwa ne Maryama? Layla me ya faru?" Ya karasa maganar yana mikewa, Layla da take kuka Abbu take kallo "Dan Allah Abbu kayi hakuri, ba zan kara ba, ba zamu kara ba" Saboda yaune karo na farko da tsoro matsananci ya cika mata zuciya haka. Kaunar da takewa Abbu mai girma ce, bataso yayi fushi da ita "Wai me ya faru?" Abbu ya sake tambaya dan duk zuciyar shi dokawa takeyi, Mami dakyar ta iya fadin "Rungume na gansu ita da Rayyan" Maganganun na fito mata da wani irin nauyi na tashin hankali. Wani sarawa Abbu yaji kan shi yayi kafin maganganun Mami su zauna mishi, ma'anar su da tashin hankalin su ya zauna mishi yana wujijjiga duk wani zaman lafiya da yake tare da shi. Marainiya, amanar da suka dauka shi da Mami, ai baisan kafafuwan shi sun taka ba sai da yaji shi a waje, kan shi tsaye bangaren su Rayyan din ya nufa yana kuwa hango shi a tsaye, suna karasawa hannun shi Abbu ya daga yana saka Rayyan lumshe idanuwan shi, saboda a karo na farko yau yayi tunanin hannun Abbu zai sauka a jikin shi. Bai bude idanuwan ba sai da yaji ya kama hannun shi. Lokacin da Ayya ta zo wajen, saboda Huda taje ta fada mata ga Mami can tana dukan Layla yanzun ta gansu wajen dakin Rayyan din, kuma ta ga Rayyan a tsaye a wajen. Shisa Ayya ta taso ta fito a bazame, ganin Abbu rike da hannun Rayyan ya sata fadin "Lafiya? Me ya faru?" Tana sauke idanuwan ta akan Mami da Layla da ta kara boyewa bayan Mami tana tsiyayar hawaye saboda kallon da Ayya ta watsa mata "Me ya faru wai?" Mami ce ta kalli Ayya tana amsawa da "Me yasa ba zaki tambayi dan ki ba?" A fadace Ayya ta kalleta "Da yai uwar me zan tambaye shi? Maryama kinga ki kiyayeni..." Sun kwana biyu basu shiga harkar juna ba, tunda Mami ba biye mata takeyi ba, amman yau ranta a bace yake matuqa, abinda duk Ayya taje ji itama tana dai-dai da ita "Idan ban kiyayeki ba me zai faru? Maimuna ki fadamun abinda zai faru yau idan ban kiyayeki ba, kuma wallahi kija ma danki kunne, ya kyalemun yarinya, domin amana ce a wajena" Da tashin hankali Ayya take kallon Mami jin maganganun ta, ta bude baki Abbu ya kalli su biyun "Maryama ki wuce ki koma ciki" Akwai wani yanayi a muryar shi da yasa Mami juyawa, Layla zata bi bayanta Abbu yace "Ke ki tsaya..." Sosai Ayya ta kalli Abbu "Ahmadi ban..." Wani irin kallo yai mata "Kema ki wuce Maimuna" Bata taba ganin shi a yanayin da take ganin shi ba yanzun shisa ta kama hanya tana wucewa cike da son sanin abinda ya faru. Sai da tabar wajen sannan Abbu ya kalli Layla da take ta tsiyayar da hawaye "Kar in sake ji, kar kuma in sake gani..." Saboda yana ganin dana sanin da yake shimfide a fuskarta, ga kuma tsoro, ko da nasiha ko fada zai mata babu wanda zata fahimta a halin da take ciki. Kai kawai take daga mishi tana share hawayenta da bayan hannun, ganin yaja Rayyan zasu wuce ya sata fadin "Dan Allah Abbu karka dake shi, baiyi komai ba shi" Numfashi Abbu ya fitar da kalaman ta yana girgiza kai kawai saboda baisan inda zai dauke su ya ajiye ba, dakin su Rayyan din yaja shi saboda gani yake kafin su koma bangaren shi kalaman da yake ta hadawa sun bace mishi, gefen gado yaja Rayyan da bai musa ba ya zauna. Tsugunnawar da yaga Abbu yayi yasa ka shi jin wani irin abu ya tsirga mishi cikin kai. Ga wajen da Abbu ya rike mishi hannu kamar an kona shi yake ji, radadi wajen yake mishi ba fitar hankali. "Rayyan..." Abbu ya kira zuciyar shi na wani irin ciwo, yau so yake yaji matsalar yaron na shi, amman yaki yarda su hada ido, gabaki daya iskar dakin tayiwa Rayyan kadan "Rayyan dan Allah yau ka kalli idanuwa ka fadamun matsalar ka, ina so in sani. Idan da yanda zan taimaka maka zanyi, wallahi zanyi komai in taimaka maka, amman hakan ba zai yiwu ba sai ka mun magana" Kan shi Rayyan ya kara sunkuyar wa kasa, kirjin shi kamar zai kama da wuta saboda iskar da bata kai mishi inda ya kamata. Baison magana da Abbu, bayason ganin shi, bayason jin muryar shi duk da yasan yana cikin jerin mutanen da ya kamata ace yana jin kusanci da su, ya kamata ace yana so "Kayi mun magana" Abbu ya sake fadi, ya kai mintina kusan goma a tsugunne yana so ko idanuwan Rayyan din ne ya saka cikin nashi amman hakan ya gagara. Numfashi Abbu ya sauke kirjin shi na mishi zafi "Idan son ta kakeyi ka fadamun, itama zan tambayeta sai in muku aure..." Sai lokacin Rayyan din ya dago yana saka idanuwan shi cikin na Abbu "Kana son ta?" Baisan dalilin shi na girgizawa Abbu kai ba, shi bai san me yasa kowa yake tsallen yanke mishi hukunci haka ba akan Layla. Baisan me yasa ba zasu barshi ya dora sunan akan alakar da take a tsakanin su ba, amman yanzun da Abbu ya tambaya sai yake ganin kamar a cikin idanuwan shi yana so amsar ta kasance eh, dalilin da yaji ya dauki Layla ya jefa can wani waje a bayan zuciyar shi, yanayin da baisan ya zai tsaida faruwar shi ba. Numfashi Abbu ya sake saukewa "Amana ce ita din a wajena, rokon ka nakeyi ka rufa mun asiri, idan baka tayani kare martabar ta ba, karka taba ta, dan Allah Rayyan a karo na farko kayi abinda nace, badan ina so ba, sai dan shine dai-dai" Shiru Rayyan yayi yana kara sadda kan shi kasa, dakyar Abbu ya iya mikewa, har jiri yakeji yana daukar shi sanda ya kai bakin kofa saboda kan shi da yake sarawa, har lokacin jin shi yake kamar yana yawo a duniyar mafarki "Abbu..." Yaji Rayyan din ya kira, da babu taimakon kofar da Abbu ya dafa tabbas da kafafuwan shi sun kasa daukar shi, rabon da yaji sunan shi a bakin Rayyan tun yana dan karami. Na rana daya ya kira shi haka bai taba ba "Yaa Rabb" Abbu ya fadi a cikin zuciyar shi, yana jin ko addu'o'in shi akan Rayyan dinne suka fara karbuwa, juyawa yayi yana kallon Rayyan da yake yawata idanuwan shi akan fuskar Abbun, akwai tarin abubuwa da yake so ya fadama Abbu amman kamar an shaqe shi haka yake ji. Idan bai fadi sauran da baisan ta inda zai fara ba, yana so ya fada mishi yanda tunanin zai taba martabar Layla yayi mishi ciwo sosai, yana kuma so ya tambaye shi ko shima a tsakanin shi da na shi mahaifin yana jin irin wannan abin da yake ji. Yau yana so ya fadama Abbu abubuwa da yawa kamar yanda yake roke shi, ya fada mishi yanda yanzun haka yake ji kamar ana zare mishi rai kallon Abbun da yake, cikin tsokar jikin shi kamar an hura wuta. Amman ya kasa, babu kalma daya da zata iya fitowa daga makoshin shi da yake ji kamar an shaqe. Saiya sadda kan shi kasa kawai, numfashi Abbu ya sauke, ya dauki kiran da Rayyan din yayi mishi a matsayin amincewa da rokon shi. "Nagode..." Abbu ya fadi da sanyin murya yana ficewa daga dakin. Yau sai yake jin kamar akwai wata matsala mai girma tattare da Rayyan, matsalar da baisan ta inda zai fara shawo kanta ba. Amman addu'a, yana da yakini a kan addu'ar shi ba zata taba tashi banza ba, zai magana ta fahimta da Ayya, zai gaya mata da ta kara tsananta addu'arta akan Rayyan din, zai kuma yi magana da Mami itama dole. Rayyan ya kalle shi yau ya girgiza mishi kai a tambayar ko yana son Layla. Amman ya rasa dalilin da yasa ya kasa yarda, haka kawai zuciyar shi na mishi rawa akan abubuwa da yawa yau din nan. "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Shine abinda yake furtawa yana karawa har ya kai daki "Allah ka musanya mun kaddarar duk da zaka dora akan yarana, Allah ka fini sanin zuciyata, amman ni inaji kamar kowacce kaddara ba zata dauku a wajena ba in har ta hada da yarana..." Shine kalaman shi a cikin sujjada, a tsorace yake da lamarin rayuwar gabaki daya. A tsorace yake da kaddarar da yake hangowa kamar tana kusanto yaran shi, kaddarar da yake son amfani da addu'a ya gina katanga a tsakaninta da yaran shi. Domin sune raunin shi, abinda zai taba su zai taba shi fiye da su. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:07 PM - 111: Dec 5, 2020 16 Kwance take a cikin hostel a kan gado, ta lumshe idanuwanta, ba dan gadon yafi nata na gida ba, amman wani irin nishadi take ji yana shigar ta, nishadin da bata da kalaman misalta shi. Ta dauka ita da Zaria sai a mafarki, yanda Mami ta dauki fushi da ita har kasan ranta ta hakura da karatu a Zaria. Ta jigata, ta sha wahala, akan gwiwoyin ta da hawaye cike taf da idanuwanta ta tsugunna tana baiwa Mamin hakuri saboda bata ga abinda tayi mai zafin da zaisa Mami ta daina mata magana ba "Ban san sau nawa zan jaddada miki MARTABAR MU a matsayin 'ya'ya mata ba kafin ki fara kare taki" Mami ta fadi tana dorawa da "Bance ki dubani ba, ki duba kanki da maraicin ki, yanzun mutunci ne ace kuna wannan rike junan ke da Rayyan?" Hawayen da suka tsiyayowa Layla ta goge da hannu "Ni dai Mami dan Allah kiyi hakuri, nace ba zan kara ba, na daina, dan Allah kiyi hakuri" Numfashi Mamin ta sauke "In zakiyi hankali dai kiyi, dan an Abbun ku ya tambayi Rayyan din yace ba son ki yake ba..." Duk wani abu da Mami ta fada bayan nan bai karasa kunnuwa Layla da suka toshe da kalaman Mamin na karshe ba, har kuma ta baro gidan bata samu wani nishadi ba sai yanzun da take a kwance. Kwananta hudu da wani irin zazzabi da ya wajigata. Mami bata taba mata karya ba tun tasowarta, amman kiri-kiri ranar ta tsinci kanta da karyata Mamin, saboda karta komawa Rayyan shisa tayi mata karyar da bakin shi yace wa Abbu baya sonta. Bata tsammaci ya sota ba, batama san da gaske ta daga burinta akan shi ba sai da Mami ta fada mata kalaman da taji kirjinta kamar an kunna wuta a ciki. Kwana tayi tana kuka, da safe fuskarta kamar kwabin alkubus saboda yanda ta kumbura, Mami bata ce mata komai ba, ko wanke-wanke tanayi tana kuka haka ta karasa shi ranar. Kuma yanzun ma da ta tuno kalaman sai da taji wani irin daci ya taso mata yayi tsaye a karkashin makoshin ta. "Mami sai dai kiyi hakuri, amman ni ba zan rabu da Hamma ba, ko ya rabu dani ni ba zan rabu da shi ba. Mayya ce, amman mayyar shi" Ta furta a hankali, kalmomin "Mayyar shi" din na zauna mata. Abin ya hade yayi mata yawa, saboda har suka bar gidan Rayyan baya mata magana, baya kiranta ya saka tayi mishi wani abu. Idan daga nesa ya hangota zai kalli wani wajen, ita kuma tsoron Mami yasa ko a waya ta kasa kiran shi. Ranar da zata koma makaranta babu kalar wa'azi da nasihar da Mami batayi mata ba, duk da batasan me Abbu ya fadawa Mami ta yarda tabarta komawa Zaria ba. Amman tana da yakinin yana da alaka da yanda watanni shidda ne kacal suka ragewa Rayyan din ya kammala karatun shi gabaki daya. A mota wannan karin gidan gaba ya zauna, daga ita har Bilal bai musu magana ba, Aisha ma da suka biya suka dauketa, da ta gaishe da shi Layla bata ga yayi alamar yaji ba ballantana ya amsa, muryar shi take son ji da dukkan zuciyarta, amman yayi shiru, cikin kujera ma ya shige yanda ko wuya ta dan leqa ba zata iya ganin shi ba har suka sauka. Bata gaji ba dan da ta sauka ta zagaya ta bangaren shi tace "Hamma..." Gilashin murfin motar ya daga yana jan shi sama ya jingina kai a jiki yanda ko fuskar shi ma ba zata gani ba. Za kuwa tayi karya idan tace abin bai mata zafi ba. Dakyar ta danne hawayen da taji suna shirin zubo mata, duk da kwakwalwar ta na son ta tirsasawa zuciyarta tuno maganar Mami, ta tauna taga ko da gaskiya a ciki taqi yarda, hakan zai iya barazana da zaman lafiyarta fiye da yanda take ciki yanzun. Ko Rayyan baya son ta bai fadawa Abbu ba, bai fada ba, tana da sauran buri akan zai kalleta da fuskar soyayya wata rana, idan ma baiyi ba ya aminta da tarin soyayyar da ita takeyi mishi, ya ishe su. Wayarta ta dauka da take ajiye a gefe jin sakonnin da suke ta shigowa. Tun a hanya an mayar da ita group daman, duk yanda taso ta daina karance-karance da takeyi sai ta tsinci kanta da kasawa, duk idan Nanaa ta turo mata sai ta karanta. Da kanta tace a mayar da ita tun tana mota, duk da wani abu a kasan zuciyar ta na son nuna mata tarin kuskuren da yake cikin hakan, yanayin da take jine ya rinjayi wancen kashedin. Gara taji da abu daya, duk da kome ta karanta din sai ta dinga hasaso Rayyan a tare da ita, cikin yanayin koma meye yake faruwa a abinda take karantawar. Mafarkai takeyi a kwanakin nan da suka kara addabarta, kallo daya zakayi mata kaga tsantsar ramar da tayi, sai idanuwan. Amman wuyanta duk kasusuwan sun kara fitowa. Sosai taji dadin shigowa Anisa da suka rungume juna kamar sun shekara basa tare "Nayi kewar ki" Cewar Anisa tana kara rungume Layla din, sai kace tunda akayi hutu basa manne a waya da chatting "Nima haka Allah...tun dazun nake duba hanya" Layla ta karasa tana sakin Anisa, suka karasa suna zama "Yunwa nake ji, su Yaya zasu kawoni suka tafiyar su yawo..." Cewar Anisa, Layla ma najin yunwa ta taso mata, tunawa tayi ko abinci bata ci ba itama, ba yanda Mami batayi ba taqi saboda tana zumudin barin gidan. "Ko mu dafa indomie? Sai mu siyo kwai?" Dan shiru Anisa tayi tana nazari kafin ta jinjina kai, Indomie din zatafi musu sauri akan duk wani abu da zasuyi tunani. Sai su dora a risho daya, dayan kuma su soya kwai a kai. Layla ta fita siyo musu kwan, Anisa kuma ta dora indomie din. * Sosai yake mamaki idan yaji mutane na hirar wani abu da ya saka su nishadi, ko suna hirar ranakun farin cikin su. Baisan ko farin ciki shine lokuttan da Bilal kan fadi wani abu da zai saka shi dariya ba, ko kuma lokuttan da Layla zata kalle shi kamar duniyar ta babu wani abu da take gani banda shi, ko da ya bata mata raine. Akwai wani yanayi mabanbanta da zuciyar shi take shiga a duka lokuttan, amman yanda ake labarin farin ciki yana saka shi tunani sosai. Watakila shi har yanzun bai san wannan yanayin ba, kullum duniyar a cunkushe yake jinta. Ko da yaushe akwai wani duhu a cikin kan shi, akwai wani kunci da ya zame mishi abokin zama. Akwai ranakun da yakan samu saukin kuncin idan yana tare da Bilal, yakan samu saukin shi sosai duk idan yana tare da Layla, musamman idan hannun shi yana cikin nata. A kwanakin nan ko zanen da yakan dan samu ya rage mishi cunkoson cikin kan shi ya kasa samun natsuwar yi. Ba karamin kokari yayi ba nakin neman Layla. Ba dan Abbu ko Mami ba, sai dan ita din da kanta, ba zai iya jure ganin Mami ta daketa saboda shi ba. Har yanzun idan ya rufe idanuwan shi yakan ga marin da Mami tayi mata, zuciyar shi kuma na zafi sosai da hakan. Saboda Layla ne yayi nisa da ita badan wani ba, in dan Abbune babu wani abu da maganganun shi suka kara mishi banda tunzura shi ya kusanci Layla din, a lokaci daya kuma wasu daga cikin maganganun suna nisanta shi da ita. Yanayine da shi kan shi ya saka shi a cikin rudani marar misaltuwa. Ba bacci yake samu ba, shisa tsakanin safiya zuwa wata safiyar yake yi mishi nisa matuka. Idan ya ga Bilal yayi bacci sai ya kwanta akan bayan shi ya kalli ceiling din dakin yana tunanin da ba zai iya cewa takaimaimai na menene ba. A kwanakin ko sallar daya kan tashi yayi sai jikin shi yayi matuqar nauyi. Bilal dai bai fasa mishi hira ba idan ya tashi, duk da baya iya ce mishi komai. Yana dai jin dadin hirar, fiye da yanda zai iya fada. Saboda ita kadai ce yake ji ta zame mishi katanga tsakanin shi da tabin hankali. Tun sanda ta shigo cikin motar yau da zasu dawo yake jinta a wajaje fiye da zuciyar shi, sai yake jin inda maganganun Abbu suka dauketa suka jefa yana budewa. Zai rantse yana jin idanuwanta na yawan neman fuskar shi kamar zasu huda kujerar da yake a kai su leqo shi. Bayan sun sauka ma haka, yana jin yanda take kokarin yi mishi magana. Sai take kara mishi wahalar da yake ciki, saboda tana yi kamar ita ka dai take azabtuwa da nisan da sukayi da junan su. Duk yanda yake daurewa sai da tayi mishi magana "Hamma..." Kawai ta furta sai da tsikar jikin shi gabaki daya ta mike, komai yana neman kwance mishi, shisa ya daga gilashin motar. Jikin shi har bari yakeyi da son fita daga motar ya riketa a jikin shi, so yake ya zagaya hannuwan shi ya riketa dam, yaji duminta ko zai nutsar da hayaniyar da take cikin kan shi. Amman babu wannan damar, zaiyi duk kokarin da zai iya na ganin damar bata samu ba. Sanda suka karasa gida har wani numfashin wahala yake saukewa. Kayan su ma Bilal ne ya shigar musu da shi. Basu huta ba suka fara share share, har wankin su labule sai da Rayyan din yayi. Yanajin Bilal na fadin "Kabari a bayar a wanke mana" Bai saurare shi ba, saboda yana son yin wani abu da zai rage mishi tunani. Sanda ya gama duk wani aiki da zai iya takalowa kan shi har azahar ta kusa, yanayin wanka ya fita yayi sallah ya dawo. Bilal ya sai musu biredi a hanya saiya dafa musu shayi, shi Bilal din yana zaune kan gado ya bude laptop din shi, Rayyan kuma yana zaune akan kujera da kofin shayin da yayi mishi zafi a hanny yana hurawa a hankali da iskar bakin shi cikin son ya huce. Wani series film ne Bilal din yake kallo tun suna gida mai suna "Suits". Shi kallo ba damun shi yayi ba, idan Bilal ya saka wata rana sunayi tare, tunda ya fara sukan kalli wasu episodes din tare. Duk dai inda ya samu Bilal din na kallo shima dorawa yakeyi. Yanzun ma idanuwan shi ya natsa kan screen din laptop din suna kallon. "Trevor din nan ba abokin Mike bane wai?" Rayyan ya tambaya yana kurbar shayin shi, juyawa Bilal yayi saboda yana son tabbatar da cewa Rayyan din magana yayi bayan satikan daya dauka yana azumin yin maganar. "Abokin shi din nan da suke daki daya" Rayyan ya sake fadi ganin kamar Bilal bai gane tambayar shi ba, idanuwa Bilal ya runtsa yana bude su akan Rayyan. Baisan yana rike da wani numfashi ba sai yanzun daya sauke shi. Sosai abinda duk yake damun Rayyan din yake ci mishi zuciya. Yayi tambayar duniya Rayyan yayi banza ya kyale shi, har fushi yayi ya gaji ya sauka da kan shi. Yakan dauki kwanaki biyu batare da yace komai ba, amman bai taba daukar wannan kwanakin shiru haka ba. "Dan Allah Hamma karka sake tsoratani haka... Ko ba zan iya taimaka maka ba, ko banda maganin damuwar ka idan ka fadamun zan saurara. Wasu lokuttan kana bukatar wanda zai saurari matsalarka ne saika sami saukin ta..." Idanuwan Rayyan din na kan laptop har lokacin yana kuma shan shayin shi a nutse, yaji duk wani abu da Bilal ya fadi "Shine, abokin shin nan ne" Ya fadi maimakon amsa Bilal din, kai Bilal ya jinjina mishi, sanin in dai ba wannan hirar da Rayyan ya fara ba, sam ba zai saurari wata daban ba. "Shine fa..." Ya tabbatar ma Rayyan da ya girgiza kai "Yasa bana son mutane, har kasan raina zan yafe komai banda cin amanar mutanen dana yadda dasu" Dariya Bilal yayi "To a duniya waye zaici amanar ka Hamma? Da wa ka yarda?" Dan jim Rayyan yayi, akwai tarin abubuwa da mutane suke da su da bayaso sam shisa yake zabar kadaici akan tarayya da su "Kuma idan wani yaji kana maganar mutane saiya dauka ba daga jinsi daya kuka fito..." Kafadu Rayyan ya dan daga "Kai..." Ya furta yana sa Bilal kallon shi "Na yarda da kai da Layla..." Rayyan yayi maganar muryar shi can kasa yana dorawa da "Sai Abbu da Ayya" Duk yanda bayajin kusanci da su, yana jin ya yarda dasu, basu taba cutar da shi ba, basu taba mishi karya ba. Shisa ya yarda dasu, bayason karya da dukkan zuciyar shi, ba kuma ya son cin amana kamar yanda ya fadi. Yanzun bashi Trevor yaci amana ba, amman har ran shi yake jin abin, mu'amala da mutane babu komai a cikinta sai wahala. "Mu din kenan ba za'a yafe mana ba?" Bilal ya tambaya yana murmushi, kai Rayyan ya girgiza mishi, yana saka idanuwan shi a cikin na Bilal din "Ba zai yafu bane..." Yanayin da yayi maganar na saka wani abu tsirgawa Bilal din. Shirune ya ziyarci dakin suna maida hankalin su kan film din da suke kallo, wannan karin kowa da abinda yake tunani a cikin kan shi. * "Hamma..." Layla ta fadi cike da farin ciki tana zagaya hannuwanta a bayan shi ta rike shi. Idanuwan shi Rayyan ya lumshe yana jin wani irin yanayi da ba zai misaltu ba, sosai a watanni shiddan sa suka wuce mishi a hankali yaso nisanta da Layla, amman ya kasa. Yana bukatar ta a kusa da shi in har zai sami natsuwar kammala jarabawar zangon. Satin farko da suka dawo makaranta ta zo wajen shi, inda ya saba zama. A gefe ta zauna batare da tace mishi komai ba. Sun kai mintina arba'in a zaune kawai. Shirune da yake cike da ma'anonin da basa bukatar kalamai. Shirune daya samar mishi da natsuwar da baiyi zato ba. Da zata tafi, jakar shi ya bude ya zaro jacket yana mika mata, babu musu ta amsa ta saka a jikinta. Ita kanta ta samu natsuwa, da gangan a ranar ta saka doguwar rigar. Tana son ko yaya ne ta ga wani kusanci da yake a tsakanin su tunda baya mata magana. Haka taci gaba da zuwa su zauna shiru kawai, a ranakun da tasan yana azumi takan kai mishi abinci har gida. Sau biyu yana hanata zama, tana ajiye kwandon da ta jera kuloli Rayyan yake mikewa alamar su tafi. Shisa ta daina sallamar mai napep ko mashin din daya kawota, tana ajiyewa itama take tafiya ba saiya koreta ba. Ranar da taji kamar zata mutu idan batayi magana da shi bane ta dauki waya ta kira shi, yana dagawa wani irin kukane ya kwace mata da yasa Rayyan din lumshe idanuwan shi, yanajin wani abu na budewa a zuciyar shi "Layla..." Ya kira da wani irin yanayi daya kara tunzura kukan da takeyi "Ban san ya zanyi ba... Ban sani ba wallahi" Ya fadi yana sauraren sautin kukanta da yake kara mishi hayaniya a cikin kan shi. Kamar katinta ne ya kare wayar ta yanke, kira ya kai biyar yayi bata dauka ba, yaso ya share, har kwanciya yayi, sai ya kasa. Idan kuka yake so tayi zai bata dalili, bayason wannan kukan nata. Mikewa ya tsinci kan shi dayi yana saka takalma, gani yake idan ya taka ba zai isa inda take da wuri ba shisa ya hau mashin. Sanda ya karasa bakin hostel din, ya mata kira yafi goma kafin ta daga tana fadin "Hello..." Muryarta na fitowa daga can kasan makoshi "Layla..." Rayyan ya furta yana lumshe idanuwan shi, abinda yake ji yaso yayi kokawa da shi ya kasa "Ki fito... Ki fito in ganki" Ya karasa hadi da sauke wayar daga kunnen shi. Sanda ta fito hula ce kawai a kanta, bai san ya zai kira abayar jikinta ba, ta dai mishi kyau saboda farar hular da ta saka. Baya son hada ido da ita bai gama karewa fuskarta kallo ba, ji yake kamar ya dade bai ganta ba, wata irin kewarta ke danne shi "Hamma..." Layla ta kira sunan shi daga kasan zuciyar ta, hannu Rayyan din ya mika mata, da sauri take takawa ta karasa tana kama hannun na shi, ta sa kafa ya hankade kashedin Mami da rokonta da yake shirin yi mata katanga da Rayyan din. Shi kam babu abinda yake ganewa, babu abinda yake gani a duk fadin wajen banda ita, babu abinda yake ji banda son hada jikin shi da nata, a hankali yake jan hannun nata da yake rike da shi harya hadata da kirjin shi inda yake jin kamar ya jima a cikin dokar daji, yanzun daya riketa ne ya iso gida. Bai taba furtawa kan shi yanda ko ina bako bane a rayuwar shi banda wannan yanayin, har Bilal wani lokacin yakan ji kamar bakone a wajen shi, amman banda Layla, tun ranar farko daya fara hada idanuwa da ita suka firgita shi yasan ita din ba bakuwa bace a yar karamar duniyar shi da take cike da tarin hargitsi, ta jima a tare da shi, tun kafin ya santa kaddara ta hada hanyar su, tun kafin ya ganta yaga halitta mai kalar idanuwanta. "Hamma" Layla tayi maganar da alamar kuka da wani shauki a muryarta tana kara shigewa jikin shi. Ita kanta abinda take ji ba zai misaltu ba, kalar duk soyayyar da take gani daban take da wadda takewa Rayyan. A jikin shi kawai taji ta yanzun, amman launin duniyar gabaki daya ya sauya mata. Idanuwanta a lumshe take, bata taba ganin kyawun duhun da yakan baibaye kwayar idanuwanta bayan ta rufe shi ba sai yanzun, saboda a cikin duhu take yawo harta isa wani waje da ya haska mata Rayyan a tsaye, tana kallon shi da zuciyarta da take cike taf da soyayyar shi "Shhh..." Rayyan ya fadi yana kara riketa a jikin shi, su duka kamar sun gaji da yawon neman juna har sun fitar da rai kafin su hadu haka suke ji. Dakyar ya iya dagota daga jikin shi yana kallon fuskarta batare da ya hada idanuwa da ita ba, duk da yau tana son ganin kwayar idabuwan na shi, ko dan taga idan yanajin wannan yanayin da take ji, a karo na farko ya sumbaci goshin ta "Nayi duk kokarin da zan iya. Ban san ya zanyi nisa da ke ba" Rayyan yayi maganar batare da yasan ko ta fahimce shi ko itama tana jinta cikin kalar rudanin da yake ji ba "Kar kayi mun nisa, dan Allah Hamma ka daina kokarin yi mun nisa" Numfashi Rayyan yaja yana fitarwa. Tare suka taka rike da hannun juna, har suka samu inda suka zauna. Sun fi awa a haka, hannunta yana cikin na shi, har sai da yaga dare na karayi tukunna. Daya rakata kuwa dakyar ya bar wajen, kamar ta bashi hannun ya tafi da shi, bai karasa gida ba ranar natsuwar daya dan samu a tare da ita na kwacewa komai yana dawo mishi sabo. Daga ranar ya sake budewa kan shi kofar da ya sha matukar wahala kafin ya kulleta. Bayan nan Bilal yayi mishi magana, yayi da lallami, yayi da fada, yayi da tashin hankali kamar zai cinye shi akan rike Layla ya rasa yanda zai ya bari. Itama Layla a nata bangaren hakane, in da tasan yanda zata daina tabashi da tayi, ko dan yanda taga hankalin Mami ya tashi, amman bata sani ba, Mami take roko da ta yafe mata, ta fahimci ba laifinta bane, soyayya ce take rinjaye akanta a kowanne lokaci, zuciyarta take riritawa fiye da martabar ta da Mami take yawan kira mata a duk wayar da zasuyi. Ta dai ji tsoro na fitar hankali randa Bilal ya sameta har hostel bayan ya kirata yana fada mata magana yake so suyi, bata kawo komai a ranta ba sai bayan sun sami wajen zama ya fara da cewa "Ban san ta ina zan fara ba, na dai san tuntuni ya kamata in miki magana, in muku magana, sai na zabi in yiwa Hamma duk da nayi a kurarren lokaci, nayi kokarin gyara kuskuren yaki..." Sai lokacin zuciyarta ta fara bugawa sosai da sosai, musamman da Bilal yaci gaba da fadin "Abbu ya bani amanar ki, Abbu yace in kula da ke, na kuma mishi wannan alkawarin. Gashi na kasa cikawa, ranar farko da na ga kin rike Rayyan ya kamata in tsawatar miki, banyi ba. Kin san illar hakan, kin san rashin kyautuwar hakan Layla...ban san ya zan miki fada ba, amman zan rokeki, idan ina da wata daraja a idanuwan ki zaki bari, zaki jini tunda shi yaki jina" Lokacin idanuwanta sun cika taf da hawaye, sai da ta saka su cikin na Bilal kafin hawayen nata su zubo "Ina son shi.. Hamma Bilal ina son shi" Ta fadi da dukkan gaskiyarta, a karo na farko tana furtawa wani soyayyar da takeyiwa Rayyan din. Cikin sonyin amfani da ita dan ta zame mata hujjar da zata isa ta bata damar rike shi, tana kallon yanda Bilal din yake fitar da numfashi a hankali kamar yana cikin tashin hankali, sai dai itama a cikin shi take "Shi sa zaki daina, saboda kina son shi. Ba zaki so yaci gaba da tarawa kan shi zunubi ba" Bilal ya fadi cike da son ta fahimce shi, kai t girgiza tana mikewa kawai tabar mishi wajen. Kuka tayi sosai ranar, da wayarta tayi kara ko bata kira ba sai gabanta ya fadi, sai tayi tunanin ko Bilal din ya kai karar su gida ne. Bata san me kuma zata cewa Mami bayan karyar da ta shirga mata na cewa Rayyan din baya kulata ba. Kuma da alama Mami ta yadda, bata dai fasa jaddada mata muhimmanci kare martabar ta ba. Kamar yanda itama bata gaji da amsa ta da "In shaa Allah" Ba, bata san ya suke so tayi ba, daga Bilal din har Mami, da alama basu san yanda soyayya take ba, basu san yanda duk lokacin da wanda kake so yake a kusa da kai baka muradin komai banda kaji ka rike shi koyaya ne, ka kara hada kusancin da kake ji. Musamman idan wanda kake so din Rayyan ne, Hammanta da emotions sukewa wahalar nunawa, Hammanta da bata da tabbacin zai furta mata wasu kalamai da suka danganci soyayya. Amman idan yana jinta a jikin shi sai take ganin a hankali zata raunana zuciyar shi, zata saka kalaman da take son ji su kubce mishi. Balle takan karanta girman tasirin mace a wajen namiji, ko sarki ne akan ce a gaban mace shi din bakomai bane. Zuwa yanzun kuma tasan kalar halittar jiki da Allah yayi mata, maza da yawa a makarantar idanuwan su a kanta suke. Bata da wani makami akan Rayyan banda jikin da shima duk baudadden halin shi taga yana so, ko hannun shi ta rike tana kallon yanda yake sauri ya dumtse shi cikin na shi kamar yana tsoron karta subuce mishi. Bilal da Mami ba zasu gane wannan bace kawai hanya daya da zata iya mallaka mata Rayyan. Tana ganin yanda Bilal ya kalleta bayan kwana biyu da rokon shi, yanda ta hada ido da shi cikin ban hakuri kafin ta rike Rayyan din. Sai mikewa yayi yana bar musu wajen "Hamma Bilal zai fadinma Abbu bamu daina ba" Layla ta furta muryarta na rawa tana dorawa da "Ya mun magana, yace in daina rike ka, Hamma ban san ya zan fada mishi ya gane ba. Dan Allah kayi mishi magana karya fada a gida. Saboda Mami" Sake riketa Rayyan yayi a jikin shi, shima din baisan ya zai fadawa Bilal ya fahimta ba, shisa bai taba amsa shi ba. In da zai iya daina rike Layla din daya bari ko dan yanda Bilal yake mishi tashin hankali a kai. Amman bai sani ba, sam baisan yanda zai fara bari ba. Hakan zaiyi dai-dai da nisa da yar natsuwar da ya samu. Yana bukatar wannan natsuwar, tana daya daga cikin katangar da take tsakanin shi da tabin hankalin da yakan ji a kurkusa wasu lokuttan. Haka suka rarrafa sukayi watanni shiddan daya kawo su inda suke tsaye yanzun. Dan Layla tafi awa biyu a tsaye gaban ajin su tana jiran Rayyan din ya rubuta jarabawar shi ta karshe a ranar ya fito. Kuma da alama bai tsammace ta ba, tana rike da shi din tace "Congratulations..." Dan murmushi yaji yana shirin kwace mishi, lokacin daya kama hannunta yana zagayo da ita, kewar shi take ji tana tunanin yanda makarantar zatayi mata fadi idan baya ciki, amman zata danne komai yau ta taya shi murnar kammala makarantar shi lafiya. Wani dan ajin su ta gani yazo wucewa da rigar da daliban da suka kammala karatun su kan saka dan a dauke su hoto, kuma ya kalleta har da dan murmushin shi "Ko zan iya aron rigar hannun ka na yan mintina dan Allah?" Murmushin shi ya fadada, yana mikawa Layla da take mishi kallo cike da godiya, tana saka Rayyan kama dayan hannunta ya rike yana ma saurayin wani irin kallo "Na san yarinyar ka ce" Saurayin ya fadi yana wuce su. Duk wanda yake a ajin su Rayyan din, koma department din yasan shi da Layla, wanda suke burgewa da yawa, wanda kuma suke zagin su ma haka. Wasu na musu kallon masu dace a soyayya, wasu na musu kallon tantiran marassa kunya. Duk da haka rayuwa take tafiya, mutane basa taba rasa abinda zasu fada a kanka. Balle kuma Rayyan da Layla da suka basu abin magana a kai, a gaban kowa suke rike juna kamar su ka daine a filin wajen, kamar ba yaran hausawa tarbiyyar musulunci ba. "Ni fa ba zan saka ba" Rayyan ya fadi yana kallon rigar hannun Layla din "Dan Allah Hamma... Dan Allah" Take furtawa tana jan hannun shi da nata yake ciki, bai musa ba yake binta, basu kai da barin wajen ba Bilal ya karaso, hannun Layla da yake cikin na Rayyan din yabi da kallo, shima a watanni shiddan nan duk yayi zuru-zuru. Abinda wasu zasu alakanta da karatu, kusan harda karatu, amman baifi kaso ashirin ba, tamanin da doriya Layla da Rayyan ne. In da zai iya bude bakin shi ya fadawa Abbu a tsawatar musu zaiyi, amman wata murya na fada mishi kishine yake saka shi wannan tunanin ba girman amanar da Abbu ya bashi ba. Sanda duk zai ga Rayyan da Layla a tare, tana mishi murmushin nan kamar zata iya tsayar da duniyar kacokan domin Rayyan idan tana da damar haka sai wani abu ya bude a kirjin shi. Amman ranar da yaji kamar kirjin nashi ya rabe gida biyu shine ranar fa ta saka idanuwan ta cikin nashi tana fada mishi yanda take son Rayyan, tana maganar kamar shine dalilinta na rike shi, dalilinta na komai. Har jiri yakeji sanda ya karasa gida, daren ranar salloli ya kusan kwana yanayi, bai san da gaske soyayyar Layla a zuciyar shi mai girma bace sai da yaga digar hawaye a cikin sujjadar shi yana neman sauki a wajen wanda ya halitta mishi zuciyar har ya darsa bugunta da soyayyar Layla. Banda wajen Aisha babu inda yake samun sauki, kamar kaddara ta san zai shiga wani halin da zai bukaci taimakon Aisha a cikin shi shiyasa ta hada hanyar su. "Hamma kace ya saka rigar nan ayi mishi hoto dan Allah" Layla ta cewa Bilal din tana katse mishi tunanin da yakeyi "Ka saka ko dan tarihi, kayi abu daya yau da zai nuna da gaske kayi makarantar nan ba siyen takardun kayi ba" Bilal ya karashe cike da tsokanar da yaso ta dan washe mishi kishin daya taso mishi, amman hakan bai faru ba. Rayyan din dai ya yarda ya saka rigar. Sun danyi hotuna, kafin suka tafi gida dan Rayyan na kiran kan shi na ciwo. Layla hostel suka rakata tukunna. Bilal na kula da kalar kallon da take yiwa Rayyan, kamar tana son daukar iya hotunan shi da zata iya a cikin makarantar kafin ya tafi, sai yaji kamar ya sama mata sauki ta hanyar fada mata plan din Rayyan din. "Ni in dai zan samu bautar kasar da zanyi anan Zaria ko Kaduna nake so" Ya fadi kamar daga sama kwanaki yana saka shi tambayar "Saboda me?" Kafadu Rayyan din ya dan daga mishi, duk da a idanuwan shi yake ganin Layla ce bayason yayi nisa da ita. Addu'a yake da dukkan zuciyar shi kar Rayyan din ya sami abinda yake so, ya kamata yayi nisa da Layla, ya taimaka mishi yayi nisa da ita ko zai saukaka mishi jin amanar Abbu da bai rike ba, ko zai daina ganin yanda yake raba zunubin duk wani abu da zasuyi shi da Layla din. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:07 PM - 111: Dec 7, 2020 17 A Zaria yai zaman shi, babu yanda Bilal baiyi da shi ba "Ka zo mu tafi gida. Idan mukayi sati daya sai mu dawo. Ko dan Ayya..." Kai Rayyan ya girgiza mishi "Sai sun ganni zan musu laifi. Ka barni Bilal, ka cikani da surutu" Shine amsar daya bashi, duk wata magana da Bilal din yayi bayan nan bai ko kalle shi ba ballantana ya amsa. Yana kokarin kare Layla ne iya yanda zai iya. Idanuwan Mami ko Abbu ba zasu hana shi riketa ba idan ya tashi. Ko dan Abbu ya nuna bayaso, akwai abinda zai tunzura shi ya rike Layla a gaban Abbu, abinda har yanzun ya kasa gane kan shi, yana fahimtar yanayin mutane tun kafin ya karanci fannin, shisa baya son su. Amman ya kasa fahimtar kan shi, ya kasa gane abinda yake damun shi. Ya sha cin karo da abinda ake kira "Depression" a turance, yanzun haka yana kan magungunan shine da basayi mishi aikin komai banda kara mishi kuncin da yake ciki. Zuwa yanzun ya hakura, ya saduda da cewa akwai wani likita da zai mishi maganin matsalar shi, ko zaima fahimceta. Ya dai san katangar da take tsakanin shi da tabin hankali bata da kauri. Shisa ya zabi zama a Zaria, shi zai dauki duk wani surutu da za'ayi. Layla ba zata dauka ba, baya son kukanta, baya son ganin hawayen da bashi bane dalilin su a idanuwanta. Sam ba zai iya zama a cikin gida daya da ita yayi mata nisa ba. Zaman shi a Zaria shine saukin su dukan su. Kuma ya ma tsaya ya karasa project din shi a satika shiddan da aka bayar ya tattara ya basu yasan ya gama. Su yake jira, ya tafi bautar kasa abin shi. Duk da Ayya ta kira shi a satin farko, sallamar da tayi ya amsa yana yin shiru "Shine baka zo ba ko Rayyan? Yaushe rabon da in gan ka? Baka tunanin idan kai baka kewata ni zanyi taka?" Akwai wani yanayi a muryarta a ranar da yasa shi fadin "Ina abune haka Ayya..." Yanda ta ce "Hmm..." Sai da yaji wani iri, kafin ta dora da "Allah ya taimaka ya tsare" Bai iya amsawa ba harta kashe wayar, daya sauke daga kunnen shi bin wayar yayi da kallo, lokutta da dama yakan nemi kusancin daya kamata ace ya kasance a tsakanin mahaifiya da danta a tsakanin shi da Ayya ya rasa. Sosai yake so yaji wannan kusancin, yakan ga Bilal na binta da kallo kamar babu macen da zata zamana da muhimmanci, kima da daraja a idanuwan shi kamarta, zai rantse murmushin da Bilal kan yiwa Ayya bai taba yi mishi irin shi ba. Akan fuskar shi zaka ga tsantsar kaunar da yake yi mata a shimfide. Ko a waya ta kira shi, kafin ya daga Rayyan ya san ita ce, saboda yanda fuskar shi take canzawa gabaki daya. Ko ran Bilal a bace yake idan Ayya ta kira shi sai yayi murmushi, karshen bacin ran kenan a wasu ranakun. A tare da Bilal yake ganin kaunar daya kamata ta kasance a tsakanin shi da mahaifiyar shi. Zai karya idan yace abin baya mishi wani iri, sosai abin yake ci mishi rai, bambancin da yake tsakanin shi da sauran mutane mai girma ne. A tsayin satikan su kanyi magana da Layla, rannan ma tace mishi "Dan Allah Hamma ka siya babbar waya" Tun kafin ta karasa maganar ma yake girgiza kan shi "Um um" Ya furta "Dan Allah, za muna chatting fa" Numfashi ya sauke yana sakw furta "Um um" Jin ta fara cika mishi kunne yasa shi fadin "Idan kika dameni zan kashe wannan in ajiye" Sallama tayi mishi da sauri tana katse kiran, sai da yayi murmushin da bai bayyana akan labban shi ba, a cikin kan shi kawai ya tsaya "Mayya... Mayya ta" Ya tsinci kan shi da furtawa. Ranar da suka dawo kuwa bata yarda Bilal ya kaita hostel ba, da yake wannan karin daga ita sai shi suka dawo. Aisha bata samu dawowa a satin ba, Mamanta tana asibiti, tafi so taga jikin ya kara warwarewa tukunna ta samu natsuwar dawowa makaranta. Bacci ma ta sha a mota har suka isa Zaria din. Shisa ta ga saurin tafiyar, kewar Rayyan takeyi har cikin kasusuwan jikinta. Ko da wasa a satikan da tayi a gida batayi maganar shi ba, Mami ta tambayeta ya yake sau daya ta amsa da "Ban sani ba Mami, Hamma Bilal zaki tambaya..." Kuma da gaske a lokacin bata sani din ba tunda kwana biyu jujun ya motsa baya daga wayarta. Kuma da alama Mamin ta karanci gaskiyarta shisa tayi shiru. Tun daga soron gidan take kiran "Hammaaa!" Harta karasa ciki inda ta ga Rayyan tsaye a bakin kofa yana kallon ta, sai ta ga kamar gashin fuskar shi ya kara cika yana kara mishi wani kwarjini da taji har a zuciyarta. "Hamma" Ta kira wannan karin da tarin kaunar shi a muryarta tana takawa ta karasa inda Rayyan yake tsaye ko motsi baiyi ba. Kallon ta yakeyi, sai ya ga kamar ta kara girma, ko kuma yanayin rashin makaranta ne, zai iya yiwuwa dadewa da yayi bai sakata a idanuwan shi bane kuma. Amman wani irin abune yake motsa mishi da ganinta. Ba zaiyi karya ba yayi kewarta sosai. Duk wani zane da yayi a satikan abune daya dangance ta, idan ba fuskarta ba, wani abu nata, wata jaka da zai iya tunawa, wani takalmi nata daya gani, ko duk wani abu da zai tuna mishi ita. Hannun shi ya mika mata da ta kama yana karasa jan ta kusa da shi, ya saka dayan yana rankwashin ta "Wayyo Hamma, me nayi maka?" Ta furta tana turo labbanta hadi da murza wajen daya rankwasa din "Kira goma saboda mayya ce ke. Ina sallah waya namun ihu a kunne" Dariya Layla tayi "Ina ta kewar ka shisa" Wani rankwashin zai sake kai mata ta kauce tana dariya. Kai kawai Rayyan ya girgiza "Ina ta so in gan ka na roki Hamma ya kawoni" Kai ya jinjina yana saka takalma a kafafuwan shi "Naji muje" Ya furta yana jan hannunta. Saboda ba karamin kokari yake ba, ba iya hannunta kawai yake son rikewa ba. "Ba kai kadai zunubin yake tararwa ba Hamma, har da ita...idan kai ka roki yafiyar Allah wanne tabbaci kake da shi tana wannan tunanin?" Sosai kalaman Bilal din sukayi mishi tsaye, suka kuma tsorata wani abu a tare da shi. Bayason wani abu ya sami Layla saboda shi. Babu kalar fadan da baiwa kan shi ba a satikan nan. Amman yana ganinta komai ya kwance mishi sai da yaji hannunta cikin na shi sannan ya dan nutsu. To a kirjin shi yake son jinta, idan tana tsaye kuma yaci gaba da ganinta abinda zai faru kenan. Shisa ya kama hannunta, gara Bilal ya mayar da ita a hostel. A soron gidan yai tsaye yana sakin hannunta "Tam. Bye" Ya fadi yana shirin juyawa. Ta gefe Layla ta rike shi a jikinta, sai da ya sauke wata siririyar ajiyar zuciya, kafin ya tureta yana fadin "Mayya..." Murmushi tayi kawai, a hankali ya korar mata ciwon da sunan yake yi mata. Ta gama yarda akan shi din da gaske mayya ce ita. Babu wani abu da zaiyi wanda zai rabata da shi kuma. Juyawa yayi, sai da ya bace ma ganinta sannan ta fice itama, inda tabar Bilal zaune a mota nan ta same shi, ta bude ta shiga ya juya yana kaita hostel. * Baisan me Bilal ya fadawa Abbu ba, bayan sunan shi ya fito a Bauchi, Wailo NYSC orientation camp din da yake a karamar hukumar Ganjuwa. Ana gobe zai tafi ne yace mishi "Ga lambar da Abbu ya turo, ka kira shi idan kaje, yasan wajen da zaka biya kudin...da duk yanda za a sauya maka waje zuwa inda kake so" Bilal din ya karasa yana daukar wayar shi ya saka lambar a ciki. Saving yayi zuwa Bappa, kamar yanda ya fada mishi sunan. Sanin halin Rayyan ya saka Bilal kiran Bappa da tashi lambar sukayi magana. Rasa yanda zaiwa Bappa bayani ya gane yayi, a daburce yace "Zan turo maka da lambar dan uwan nawa. Dan Allah sai kayi hakuri da halin shi, wani irin baudadden mutum ne" Dariya Bappa yayi sosai "Karka damu, ba matsala in shaa Allah" Bilal yaji dadin yanda daga yanayin muryar Bappa ya gane cewa yana da kirki. Duk da zai wahala Rayyan bai kure hakurin Bappan ba "Dan Allah kana shiga Bauchi ka kira shi. Ka ga da ka iya tuqi sai ka tafi da mota" Harya gama duk surutun shi in da yake Rayyan bai kalla ba. Shi babu motar da zai dauka ko da ya iya tuqi. Balle bai iya ba, ba yanda Bilal baiyi ba ya koya mishi, amman yaki mayar da hankali. Ran daren da zai tafi har cikin makaranta ya shiga wajen Layla ya ganta "Yaushe zan kara ganin ka?" Ta tambaya da wani yanayi a muryarta da yasa ka shi fadin "Idan kika mun kuka ba zan dawo ba" Runtsa idanuwanta tayi tana kokarin mayar da hawayen da suke shirin zubo mata "Zanyi kewar ka da yawa..." Shiru Rayyan yayi suna cigaba da tafiya, ganin ya fara hango gate kuma sanin ita kadai zata koma yasa shi cewa "Ki koma haka" Kai ta girgiza mishi tana kasa magana "Zan kira ki, zamuyi waya" Ya fadi, idanuwanta ta sauke cikin na Rayyan tana saka zuciyar shi wani irin dokawa, da sauri ya cire na shi yana tsayar dasu akan fuskarta "Ba zaka kirani ba, haka kake cewa ko da yaushe, ni na san ba zaka kira ba" Ta karasa muryarta na karyewa "Zan kira ki" Ya maimaita daga zuciyar shi wannan karin. Ba kiran nata bane baya sonyi wasu lokuttan, baisan abinda zaice mata bane, har yanzun bai fassara alaqar da take tsakanin su ba, bai shirya bata suna ba, yana da tarin abubuwan da yake son ya dai-daita tukunna yayi wannan tunanin. Ba yanzun ba, zuwa nan gaba "Ki wuce kafin in watsa miki mari Layla" Rayyan ya fadi yana cire hannunta daga cikin n shi. Kamar ya bata damar da zata rungume shi, matse shi tayi a kirjinta kamar tana son dibar duk wani dumi na shi da zata iya ta adana tana daukowa a lokuttan da baya nan. Hannun shi daya ya zagaya ya dan dafa bayanta. Wani abu yakeji yana kwancewa a zuciyar shi da baisan menene ba, sun kusan mintina uku, kafafuwan shi da yaji kamar suna neman yin sanyi ya saka shi dagota daga jikin na shi "Dan Allah ka kirani" Kanta ya mangare yana sata murza wajen da hannu "Ki wuce Layla" Ya fadi, labbanta ta turo gaba cikin yanayin da ya tsirga mishi yana saka shi dauke idanuwan shi daga kan fuskarta kafin yayi abinda zai dade yana juyi a kai. Juyawa Layla tayi, sai da ta dan bada taku hudu a tsakanin su, wata irin bugawa zuciyar ta takeyi kamar zata fito daga kirjin ta saboda hukuncin da taji zuciyarta ta yanke mata lokaci daya, tukunna tace "Ina son ka, karka so kowa Hamma... Ni nake son ka, na riga kowa farawa, na riga kowa fadi" Wani irin numfashi take saukewa tana dariya ganin yanayin da yake kan fuskar Rayyan din, wayarta ta daga da sauri tana shiga Camera ta dalle mishi fuska, ya dago hannu, kafin ya kare ta dauke shi, tana kara daukar wasu sun kai kala biyar da sauri "Layla..." Rayyan ya fadi tana takawa cikin kokarin hade space din da yake tsakanin su "Ina son ka Hamma Rayyan... Ina son ka da yawa" Ta fadi cike da wani irin nishadi da baisan lokacin da murmushi ya kwace mishi ba, da gudu Layla ta juya tana dariya "Mayya" Ya furta a hankali zuciyar shi na tsalle kamar zata rabo da kirjin shi, ga wani dumi da gabaki daya jikin shi ya dauka da kalamanta. "Mayya... Mayya ta" Ya sake fadi wannan karin yana dora hannun shi akan kirjin shi. Sai da ya daina ganin Layla tukunna ya juya. Murmushi yake har kumatun shi sun fara amsawa da rashin sabawa. Bai san menene asalin farin ciki ba, amman idan aka tambaye shi ko ya taba jin shi, tabbas zai ce eh, idan bai gajiya da surutun ba zai bada labarin wannan yanayin da yake ji yanzun. Zai bada labarin ranar da yaji zuciyar shi ta kumbura taf ta cika kirjin shi, ranar da murmushin shi ya fito daga wani bangare na zuciyar shi. Har yaje gida kalamanta na amsawa a cikin kunnuwan shi. Ko dan babu wanda ya taba cewa yana son shi, ko da wasa kuwa, ya sha jin ana fadawa Bilal, ba kuma Aisha ba, har su Rukayya idan suna waya ya saka a speaker yakan ji tace "Ina son ka Hamma na" Wasu lokuttan Bilal kan amsa da "Fada mun me kike so kawai Ruky" Amman ko da tana son wani abu ne da gaske take nufin kalamanta. Yaune karo na farko da yaji an ambaci "So" kuma an hada da sunan shi a ciki, sai yaji ya natsar da wani abu a cikin kirjin shi, har haske yaji a tarin duhun da yake cikin kan shi "Nagode... Nagode Layla" Ya furta a hanyar shi, har yaje gida yana jin shi sama-sama. Bilal yayi bacci sanda ya karasa, shi sai da ya watsa ruwa tukunna ya fito robar ruwan da Bilal ya shigo da ita, ko fasawa baiyi ba, shi ya fasa ya sha rabi ya qulle ya ajiye, dauka yayi, kwayoyin shi ya dibo, ya ga alama idan ya zuba su a lemo ko ruwa sunfi saka hayaniyar da yake ji yin shiru. Ya jefa a ciki ya mayar yana kullewa. Da yake ba wani sake dandanon ruwan sukeyi ba, da wahala kaji su akan harshen ka, da robar a hannun shi ya karasa ya daga net ya shiga. Ajiyeta yayi a kasa ya gyara net din yana kwanciya. Babu abinda yake dawo mishi banda kalaman Layla, baima sha ba bacci mai nauyin gaske yana dauke shi, baccin daya manta rabon da ya same shi ta dadin rai. Yayi wanka kafin su tafi masallaci daman, sanda suka dawo yawanci duk an tashi ana ta hada-hadar shirin tafiya makaranta, masu lakcar safe da masu shirin wani dan test da za'ayi, ko suna son shiga makaranta da wuri dan su kwafi assignment duk anata sauri. Bilal bai samu yayi wanka da wuri ba "Da na sauke ka tasha sai in dawo" Bilal din ya fadi ganin kamar yana batawa Rayyan din lokaci shi da yake da tafiya a ranar. Shikuma yafi son Bilal din ya shirya gabaki daya, idan ya sauke shi tasha daga can makaranta zai koma kai tsaye ba saiya wani dawo gida ya fara wani shirin ba, idan shine ba zai iya wannan ba. Wani irin sama-sama yake jin shi, ko dan hutun daya samu ne daga bacci, yana bude ido kalaman Layla ne suka dawo mishi suna saka zuciyar shi cigaba da dokawa, har zuwa yanzun kamar ana kara mata gudu, yanayine da bai taba jin irin shi ba, har sai da yai tunanin anya lafiya, kamar bugun da zuciyar shi takeyi ya wuce iya kalaman Layla, kamar tana son sanar da shi wani abu mai girma da yake shirin faruwa da shi. Lokaci zuwa lokaci yakan sauke ajiyar zuciya a hankali. Aikam sanda Bilal din ya gama shiryawa har karfe bakwai da kusan kwata. Rigace fara ya saka sai wandon jeans bula, hutun da aka dawo na karshen nan ya tara kasumba irin ta Rayyan, kalar gyaran fuskar shi da askin yayi, ya rage sumar shi kasa sosai sosai shima. Ranar da ya shiga dakin Ayya kuwa sai da tace "Oh Allah na Bilal" Dariya yayi sosai "Kema karkice kin dauka Hamma ne, yanzun Huda tace mun a waje, wai dana wuce ta dauka shine ya dawo" Murmushi Ayya tayi, to a cikin gidan nasu ma mutane da yawa sun mishi magana, daga nesa za'a dauka Rayyan ne, saiya matso kusa yanayin haske da Rayyan ya fishi da tsayi kan banbanta su, sannan shi Bilal yana fara'a. Amman tabbas idan ba farin sani kayi musu ba, ka kuma jima baka ga daya daga cikin su ba, da wahala kagane. Baiji wani iri ba sai da suka hadu da Layla, yanda ta dafe kirji tana wani irin mayar da numfashi kafin dissapointment ya lullube fuskarta ya taba zuciyar shi "Me yasa kayi irin askin Hamma?" Ta bukata tana dorawa da "Na dauka shine, wallahi na dauka shine" Ko amsar shi bata jira ba ta wuce. Zai karya idan yace abin bai mishi ciwo ba, shisa ya yanke hukunci ba zai kara tara suma ba, irin yanda Rayyan din yakeyi zaici gaba, gashi a fuska damun shi yake shisa baya ajiyewa daman, yanzun kam harya fara sabawa, yana kuma kallon yanda Layla ta kan bishi da ido kamar yayi wani abu da bai kamata ba. "Ka gama? Mu tafi?" Cewar Bilal yana daukar wayar shi ya saka a aljihu. Mikewa Rayyan yayi yana daukar jakar shi suka fice, kofar kawai Bilal yaja bai damu daya kulle ba. Mota suka shiga, ko yar jakar shi Rayyan bai saka a baya ba, anan kan cinyar shi ya ajiyeta, ya juya motar suka fice daga layin. Da mashin Layla ta hawo da ta ga motar su, amman napep ta samu, dan harta fara takowa da kafarta tunda skirt dinta ba zai hau mashin bama. Sai ga nepep ta samu, kuma kanta na kan wayar da take dannawa. Da mafarkin Rayyan ta kwana, mafarkai cikin yanayin da take fatan yin tsayin rai dan ta gani. Ji tayi tana son ganin shi kafin ya tafi, tana sauka daga cikin napep din zuciyarta tai wata irin dokawa da sai da ta lumshe idanuwanta tana budewa. Dari biyu ce ta baiwa mai napep din tana furta "Ka je kawai" Ko godiyar da yake mata bata amsa ba, zuciyarta ke bugawa kamar zata fito waje. A irin yanayin daya kamata ace tayi addu'a, harshen ta ne yayi nauyi na gaske. Wata murya ke bata shawarar ta juya, amman ta kasa, kamar wadda akewa dole haka ta taka tana shiga cikin gidan. Makoshinta harya bushe saboda bugun da zuciyarta takeyi, dakin su Rayyan ta wuce kanta tsaye tana turawa ta shiga hadi da sake tura kyauren duk da bai rufe duka ba, dakin ya mata duhu da yake kwan a kashe yake, idan akwai wutar lantarki bata kula ba, balle tayi tunanin kunna kwan. Da fitilar wayarta ta haska, robar ruwa ta gani a kasa ta karasa ta dauka ta kwance, ta sha fiye da rabi tana dorawa kan tebir din Rayyan. Gefen gadon ta zauna tana maida numfashi "Hamma tafiya kayi" Ta furta da wani yanayi a muryarta, watakila Rayyan din daya tafine yasa zuciyarta bugawa haka. Sosai ta so ganin shi, gashi tasan magana da sassafe wahala takeyi mishi fiye da kowanne lokaci, idan ta kirama ba dauka zaiyi ba shisa bata kwatanta ba. Haka kawai sai taji kanta ya fara mata nauyi, kamar wadda rashin lafiya ke son kamawa, takalmanta da ta shiga dasu cikin dakin sosai ta cire tana turawa gefe wajen tebir din. Kwanciya tayi sosai, a hankali ta zame dan mayafinta ta ajiye a gefenta. Wani irin yanayine daya hade mata da wanda ta shigo da shi da karatun wani labari a group ya taso mata da shi harya darsa mata son ko da ganin Rayyan ne. Tunda take a duniya bata taba jinta a irin yanayin nan ba, kamar wadda take yawo a wata duniya ta daban, kamar tana cikin mafarkin da idanuwanta suke a bude haka take ji, shisa ta lumshe idanuwanta tana tunanin yanda akayi su Bilal din suka saka gado a maimakon katifa kawai a dakin nasu. Tana kuma tunanin yanda suka kyauta saboda taji dadin kwanciyar sosai. Kamar a cikin mafarki haka taji shigowar Bilal da harya kusa makaranta aka kira shi aka fada mishi Malamin ba zai sami damar zuwa ba, yaji dadin hakan saboda bashi da natsuwar daukar darasin ko da anyi. Hankalin shi baya tare da shi sam, har sanda ya shiga dakin, ya kuma mayar da shi ya tura kamar babu kowa a ciki, shisa ko kadan bai hangi Layla da take kwance can karshen gadon su ba, ga kuma net da ya tattare ya kai can karshen, ga duhun dakin dan ma sun saba, kamar ta mirgina ne tana nade kanta da shi, da wahala kayi zaton akwai mutum a wajen. Balle kuma Bilal din da hankalin shi na tare da kalaman Rayyan din da suke ta fadar mishi da gaba tunda ya fade su, lafiya kalau ya sauke shi ta sha, sai dai yanata kallon shi, kallo da yake cike da tarin ma'anoni har saida ya saka shi tambayar "Hamma... Lafiya kuwa?" Da alamun damuwa da Bilal din zaice bai taba ganin kalarta ba a fuskar Rayyan din yace "Zuciyata namun wani irin Bilal" Tsoro Bilal yaji ya baibaye ta shi zuciyar, Rayyan bai cika fadar abubuwa irin hakan ba "Ko dai zaka hakura da tafiyar ne? Idan zuciyar ka bata natsu ba ka hakura" Kai Rayyan ya girgiza mishi "Bana jin ni ne" Cike da rashin fahimta da kuma son karin bayani Bilal din yake kallon Rayyan, cikin idanuwa Rayyan din ya kalle shi wannan karin "Ka kula da Layla, ka kula mun da Layla kaji Bilal, zuciyata na mun wani iri" Kai ya daga mishi, saboda yanayin shi yasa ko kishin daya sabaji sam bai taso mishi ba "Ta ce tana so na, jiya tace tana sona kamar bata san nasani ba tuntuni" Cewar Rayyan, saboda saida suna kan hanya yake tunanin babu wani bakon abu a cikin kalaman Layla, abune daya riga ya sani tuntuni,  ya riga yasan tana son shi, a cikin duk wani riko da zatayi mishi yasan hakan. A yanda take dawowa wajen shi bayan ya koreta ya karanci hakan, tana son shi duk tarin duhun da yake baibaye da shi bai hana zuciyarta doka mishi ba. Da sanyin murya Bilal yace "Ni ma ta fadamun..." Ganin kallon tashin hankalin da Rayyan yai mishi yasa shi yin murmushin da yakejin ya fito daga wani waje daya tsage a zuciyar shi yana dorawa da "Tana son ka, ta fadamun tana son ka" Kai Rayyan ya jinjina, damuwar da tabar fuskar shi tana dawowa sabuwa "Shi sa zaka kula mun da ita, ban san meye nake ji ba, dan Allah Bilal" A tsorace Bilal yace "Zan kula da ita Hamma, kai dai ka kula da kan ka dan Allah. Ni duk ka tsoratani..." Numfashi Rayyan ya sauke yana juyawa kawai. Maganganun shine suka yawaita a lokaci daya yau. Shisa suka tsorata Bilal din, sai juyawa su yake a ran shi. Yana jin kamar wani abu mai girma na shirin faruwa da su yau din nan. Shima ta shi zuciyar bugawa takeyi, ruwan daya gani a roba shiya dauka ya kwance yana kafa kai ya shanye, na karshen na sauka bakin shi da wani dandano daya kasa ganewa. Anan ya tsaya yana mayar da numfashi, wayar shi ya zaro daga aljihu ya ajiye akan tebir din, wani irin sama-sama yake jin shi, banda yanayin Rayyan babu abinda yake gani "Allah ya sauke ka lafiya Hamma" Ya furta jin zuciyar shi bata daina rawa ba. Agogon hannun shi ya kwance, kamar zazzabi yake son yi, da wahalar gaske gabaki dayan yau ya iya zuwa makaranta. Kayan jikin shi ya rage yana barin gajeran wando, shima wandon anan ya cire shi yana zare kafafuwan shi ya tsallake tunda Rayyan din da zai fada ya ajiye wando a kasa baya nan. Ya kama riga ya cire yaji kamar jiri zai dibe shi, babu shiri ya zauna a gefen gadon batare daya juya ba balle yaga Layla, kan shi ya dafe cikin hannuwan shi biyu. Da gaske duniyar shi ce take wasan kura da shi. Ya gwada mikewa yafi sau biyar yana kasawa saboda yanda jiri yake dibar shi, babu shiri ya kwanta ko zai samu sauki. Daga nan ba zai ce ga iya lokacin daya dauka baisan abinda yake faruwa a duniyar ba. Kamar a mafarki haka Layla ta bude idanuwanta tana ganin komai na rabe mata biyu "Hamma..." Ta kira a cikin kanta ganin Bilal din a kwance a gefenta, sai taga tazarar da take tsakanin su tayi mata nisa, ga yanda jikinta duka yai nauyi sanda taja shi tana matsawa sosai kusa da shi "Hamma" Ta sake kira tana jin ashe gara da tazo, ashe Rayyan bai tafi ba, watakila kuma daya daga cikin mafarkan da ta sabane na shi, saboda yanayin ta ya nuna haka, tana jinta kamar tana yawo a gajimare, hannunta ta dago tana dorawa akan fuskar shi, fuskar da take mata kyau a kowanne yanayi, duk da duhun dakin ya hana mata ganin shi sosai, sai tarin kasumbar da yake fuskar shi. Kamar yanda take jinta a mafarki hakama ya kasance a wajen Bilal, dumi yaji ta inda bai taba zato ba, dumi yake ji akan kirjin shi da wasu sassa na jikin shi inda Layla ta kwanto, sai kan fuskar shi da sam baisan meye a kai ba, har saida ya kai na shi hannun yana kama nata cikin na shi. Ya sha ganin hannuwanta, ya sha hasaso yanda zasu kasance a cikin na shi, amman yau daya jisu a cikin nashin, a duniyar da yake suna dayane yazo mishi "Aisha" Ya furta iya kan shi yana kara rikota a jikin shi, yanajin yanda bugun zuciyar shi ya karu har cikin idanuwan shi da suke a rufe, yanda ta biye shi na kara tabbatar da mafarkin da yakeyi. A cikin su babu wanda ya dawo hayyacin shi har sai da Layla taji abinda yake faruwa ya girmi duniyar da take tunani ta mafarki ce, ya kuma girmi duniyar da take ciki gabaki dayanta, a dai-dai lokacin da Bilal ya rabata da Martabar da bata san haka take ba a duk lokuttan da Mami take kira mata ita sai yau da tashin hankalin rabuwa da ita ya wujijjigata yana fisgota daga duniyar da ta fada zuwa ta mutane, lokacin da ta bude idanuwanta tana son saka duk wani karfi da zata iya tattarowa ta ture Bilal din. Tashin hankali yayi kadan a yanayin da take ciki, saboda taji muryar shi a kunnenta da wani irin yanayi yana furta "Aisha... Aisha" Muryar da yanayin bai hanata gane waye ba, sunan daya kira na sake tabbatar da firgicinta, azabar da take ratsa ruhinta ta girmi mafarki tabbas da ta fassara abinda yake faruwa din da mummunar mafarki, kuka da ihu take son tattarowa daga wani loko da tashin hankalinta yake faruwa, dakyar ta samu ta iya furta "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un..." A matuqar wahalce tana jan numfashin da ta fitar da sauran natsuwar daya rage mata kafin azaba da tashin hankali su sake rabata da hankalinta... * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:07 PM - 111: Dec 9, 2020 18 Da wani irin ciwon kai ya sauka, ga alamun zazzabi yanaji. Ya kira wayar Layla yafi sau goma bata daga ba. A ranaku da ba irin na yau ba, kira daya idan yai mata bata daga ba shikenan. Ya san in tazo zata kira shi. Amman yau din wani irin tsoro yake ji da bai san dalilin shi ba, tsoron ma bai kara yawa ba sai da ya kira Bilal shima bai daga ba. Bilal da ko karatu yake sai ya mishi magana zai ajiye waya ya natsar da hankalin shi waje daya. Idan jarabawa akeyi ma, kamar yaro haka zai ce "Ban wayar nan Bilal..." Zai saka a key ya ajiye yana fadin "Na ajiye Allah kuwa Hamma" Sanin halin shi yake saka Rayyan din kin yarda, sako na shigowa zai sake dauka, shisa yakan mike ya dauki wayar ya ajiye a gefen shi "Kayi abinda yafi danna wayar muhimmanci" Yakan fada mishi, ya rasa dadin me suke ji shi da Layla kan danne-dannen wayar nan. Ji yake kamar ya tsaya a hanya ya samu wata motar da zata juya da shi Zaria saboda rashin natsuwar da yake tare da ita. "Allah Ka san halin da nake ciki, Ka san damuwa ta, Ka san zuciyata ba zata iya daukar wani abin ba. Allah Ka sa lafiyar su" Shine abinda yake fadi yana maimaitawa, duk inda network zai dawo mishi sai ya gwada lambar Bilal da ta Layla, amman duka tana shiga basa dauka ne. Yana sauka a tashar ya tsaya ya kira Bappa da bugu daya ya daga yana sallamar da bai jira Rayyan din ya amsa ba ya dora da "Har ka karaso ne? Ka jirani a tashar in zo yanzun" Rayyan din dan dakuna fuska yayi, saboda Bappa nayi kamar sun san juna, kamar sun saba ba yau bane farkon maganar su "Eh, ok tam" Rayyan ya iya cewa yana sauke wayar daga kunnen shi, fita yayi daga tashar zuwa bakin titi. Anan yayi tsaye, masu mashin da napep na ta mishi magana, harya kawo iya wuya, ga shi gari yayi duhu tunda sai bayan Magriba suka sauka. "Alhaji tafiya ne?" Wani mai mashin ya fadi a karo na biyu, kamar bai ga ya girgizawa mutane wajen hudu kai cikin alamar a'a ba. "Sai ka daukeni ka dorani, me yasa dole sai kun sa mutane magana ne?" Jinjina kai mai mashin din yayi "Allah ya baka hakuri, daga tambaya" Wani irin kallo Rayyan ya watsa mishi, dai-dai lokacin da wata mota baqa, kirar Honda Accord DC V6 ta tsaya a gaban shi. Gilashin aka sauke daga bangaren da yake, kafin aka kunna fitilar cikin motar haske na gaurayewa "Rayyan?" Bappa ya fadi daga cikin motar, Rayyan din na jinjina mishi kai "Muje..." Cewar Bappa, hannu Rayyan yasa yana bude murfin motar ya shiga, batare da yace komai ba ya rufe. Bappa ma baice mishi komai ba yaja motar, hankalin shi sam ba'a kan titi yake ba, shi dai yana garin Bauchi, zaune a cikin motar Bappa da sai kamshi takeyi. Amman hankali da natsuwar shi suna garin Zaria. Baisan anyi parking ba sai da Bappa yace mishi "Mun zo" Budewa yayi yana fita, in da duk Bappa ya sa kafar shi nan Rayyan yake mayarwa, ko sunan Hotel din bai duba ba, daga yanayin shi bayan sun shiga ya dan gane ko ina ne, ciki suke shiga sosai har suka karasa daki mai lamba 19, inda Bappa ya zaro mukulli daga aljihun shi yana bude dakin. Da sallama ya shiga, Rayyan na biye da shi, ya mayar da dakin ya rufe, akwai haske gauraye da dakin, babba ne da tanqamemen gado sai tv da take ta aiki, amman babu magana, anyi kasa da ita. Har da kujera doguwa a cikin dakin. Yayi kyau sosai da sosai. Ko ina a gyare tsaf, da alama zaiyi tsada "Na san ka kwaso gajiya, ga sallah kuma da wahala kun tsaya..." Bappa ya fadi yana saka Rayyan kallon shi, dogone dan da wahala idan bai mafi Rayyan din tsayi ba, sai dai shi siririne, da kasumba a fuskar shi, akwai abin sallah a goshin shi, wata natsuwa Rayyan yake gani a tattare da Bappa, duk da kananun kayane a jikin shi yayiwa Rayyan din kwarjini. Mutanen da suke mishi kwarjini basu da yawa, duk izzar da kake tare da ita kuwa. Da hannu Bappa ya nuna mishi bandaki "Ga toilet din nan" Jakar da take rataye a kafadar shi Rayyan ya sauke akan kujera, bandakin ya karasa yana zira takalman da suke ajiye a bakin kofa ya shiga sosai yana rufewa. Har ruwa ya watsa, sannan ya daura alwala. Sanda ya fito sai yake jin shi ya samu yar natsuwa. Sai kan shi da yake ciwo kamar ganga ake bugawa a ciki. Baiga Bappa ba a dakin ya dai shimfida mishi darduma, sun tsaya sukayi azahar inda akaci abinci, shi banda nutri-milk da biscuit babu abinda ya sakawa cikin shi, shima dan yana bukatar wani dan karfi ko ya yake kafin zullumi ya saka shi faduwa. Sallolin shi yayi a nutse yana zaro wayar shi ya duba, ganin lokacin isha'i yayi ya saka shi gabatar da ita. Zaune yake akan kafet din yau ya rasa kalar addu'ar daya kamata yayi bayan rokon Allah da yasa daga Bilal har Layla lafiyar su kalau. Lambar Layla ya sake kira "Dan Allah ki daga" Ya fadi a hankali, amman bata daga din ba, haka Bilal. Rasa abinda yake mishi dadi yayi a duniya, saboda zuwa yanzun ya aminta da zuciyar shi, tabbas wani abu ya faru, babu yanda za'ayi yayi tafiya haka ace ko sau daya Bilal bai neme shi ba. Lakca zai tafi yayi yamma, in har bai fada mishi zaiyi yamma ba ya dinga kira kenan har sai ya mishi text cewar yana aji "Wai ni karamin yaro ne Bilal?" Ya taba tambayar shi wani lokaci da yayi mishi kira goma akan shidda tayi ina ya tsaya bai koma gida ba "Ni dai ka dinga fadamun in ka san zaka biya wani waje" Bilal din ya amsa cike da damuwa a muryar shi, amman yau ya tafi wani waje mai nisa haka ace ko sau daya Bilal bai neme shi ba, da gaske ba lafiya ba, wani abu ya faru, ko da shi ko Layla. Saboda tunanin Rayyan din sam bai kai gida ba, kallon wayar shi yake kamar yana so ta taimaka mishi da wata maslaha. Amman shiru "Ayya..." Zuciyar shi ta ambata, a karo na farko a tsayin rayuwar shi da yaji yana son ya kirata da kan shi, yana kuma bukatar taimakonta, watakila ita tayi magana da Bilal a tsayin ranar. Ko Bilal baiyi magana da kowa ba, tabbas zaiyi da Ayya, lambarta ya lalubo ya kira, zuciyar shi banda dokawa babu abinda takeyi mishi, tana dagawa bai jira ta gama sallamar ba yace "Ayya kinyi magana da Bilal?" Dan jim da tayi ya sa Rayyan din kiran "Ayya" Yana jin numfashin da ta sauke "Rayyan?" Ta kira sunan shi kamar tana shakkun cewa da gaske ya kirata, da gaske tana magana da shi "Kunyi magana? Bilal..." Ya sake maimaitawa "Ina ta kira bai dauka ba, tun da safe da yace mun ya kaika ta sha, yace yana da lakca da safen da, amman ba za'ayi ba zaije gida ya kwanta yayi bacci, har yanzun bai kirani ba, na kira shi yafi sau hamsin bai daga ba. Na kasa samun natsuwa" Runtsa idanuwan shi Rayyan yayi yanajin kamar bangwayen dakin na hadewa da shi a ciki saboda wani irin tsoro daya taso mishi "Kai ma bai neme ka ba?" Ayya ta tambaya da wani irin yanayi a muryarta, kai Rayyan yake girgiza mata, tashin hankali bakon abune a wajen shi, ya san kunci, ya san rashin natsuwa, yasan bacin rai, har tsoro ya sani saboda yana jin shi idan ya ga mage, yana kuma jin shi duk idan ya sauke idanuwan shi akan Layla, ya san abubuwa da dama, tashin hankali bakon shine, musamman mai hade da firgici irin wannan. Kafin wasu dakika ya fara kokawa da numfashin shi "Rayyan!" Yaji muryar Ayya kamar a wata duniya kafin wani haske ya gilma ta cikin idanuwan shi yana saka shi runtsa su ya sake budewa, ji yake kamar an kama kafafuwan shi an sadda kan shi kasa ana jijjiga shi, idan wani abu ya sami Layla, baisan ya zaiyi ba, amman bai kara sanin asalin firgici ba sai da yai tunanin wani abu ya sami Bilal "Gabana sai faduwa yake tun safe" Ya tuna maganar Bilal jiya da daddare "Kayi addu'a" Ya amsa shi, yana kallon yanda ya danyi jim kamar mai nazarin wani abu sai kuma yaci gaba da danna wayar da yakeyi, sai yau din yaga kamar akwai rama a cikin idanuwan Bilal din da baigani ba sai yanzun yake tunawa "Ka kwantar da hankalin ka, watakila ko ya ajiye wayar wani waje bai ganta ba, ka san Bilal" Wani irin numfashi Rayyan ya sauke "Ni da ke mun san Bilal baya ajiye abu ya rasa in da ya ajiye Ayya" Cewar Rayyan yana sauke wayar daga kunnen shi ya kashe kiran, a gefe ya ajiyeta yana dafe kan shi da hannuwa biyu, tabbas da ace zai sami motar da zata juya Zaria ba zai kwana a garin nan ba yau, bashi da wata natsuwa idan bai sami Bilal ba. Bappa ne ya shigo da leda a hannun shi yanayin sallamar da Rayyan ya amsa ya dora da "Zan iya samun motar da zata koma Zaria yau?" Da mamaki Bappa ya kalle shi "Da daren nan? Amman ka san hanyar ba aminci gareta ba ko? Kuma me yasa kake tambayar motar Zaria" Cike da damuwa Rayyan yace "Zan koma ne" Sai da Bappa ya karasa ya ajiye ledar hannun shi ya zauna sannan ya fuskanci Rayyan sosai "Lafiya dai ko?" Bai san me yasa yaji kamar zai iya yadda da Bappa ba, bayan shi din baya yarda da mutane.  Amman yana cikin damuwa kalar da bai taba sani ba, taimako yake bukata ko daga wajen waye "Ina ta kiran kanina baya dagawa" Kai Bappa ya jinjina "Watakila baya kusa da wayar, ko kuma ya yarda ba'a kai da tsinta an kashe ba. Ko wani ya dauke, akwai dalilai irin haka" Kai Rayyan ya girgiza mishi, yau kalamai yake nema da zai misalta abinda yakeji Bappa ya fahimta "Banda kanina, Bilal ba haka yake ba. Zai kirani ko da wayar wani ne ya fadamun. Yaune na farko da muka yini bamuyi magana da juna ba" Numfashi Bappa ya sauke "In shaa Allah komai lafiya. Ka kwantar da hankalin ka, ba kada lambar ko abokin shi haka? Sai ka kira a duba shi?" Kai Rayyan ya girgiza, a karo na farko yana dana sanin halayen shi, da ace ko lambar mutum daya a cikin gidan nasu yana da ita yau zatayi mishi rana "Mutum yana da ranar shi Hamma, duk yanda kake tunanin baka bukatar wani bayan ni da Layla ba fata nai maka ba, Allah kar ya nuna maka ranar da zata karyata tunanin ka..." Ga ranar ta zo yau, ranar da Bilal yayi mishi addu'a karya gani "Allah bai amshi addu'ar ka ba Bilal" Rayyan ya fadi a zuciyar shi "In shaa Allah komai lafiya. Na san zai kira" Numfashi kawai Rayyan yaja yana mikewa dakyar, kamar abinda ake kira "anxiety attack" ne yake shirin kamashi saboda tashin hankalin da yake ciki. Inda jakar shi take ya karasa ya dauka yana budewa, jikin shi babu inda baya bari sanda ya dauko kwalin sigarin shi, ya dauki kara daya ya saka a baki ya lalubo lighter din saiya tsinci kan shi da juyawa, yau abubuwan da suke baqi a wajen shi yake tayi "In ba zaka damu ba" Ya cewa Bappa da yayi dan murmushi yana girgiza mishi kai. Kunna sigarin yayi yana shanyeta cikin yan dakika ya sake kunna wata, sai da ya sha kara biyar, amman jikin shi bai daina kyarmar da yake yi ba. Karshen daya rage ya karasa bakin kofa inda ya hango kwandon shara ya zuba, harda kwalin daya tara toka a ciki. Dawowa yayi yana kara saka hannun shi cikin jakar shi ya laluba, kafin zuciyar shi tayi wata irin dokawa da bata da alaka da su Bilal, ya manta magungunan shi, jiya bai saka a jakar shi ba "No.. No... Please no" Yake fadi cikin tashin hankali yana kara dubawa ko watakila bai manta din ba, amman babu su, har kayan ya fito da su yana duddubawa, kafin ya sake mayarwa yana runtsa idanuwan shi, ji yake kamar wani abune a cikin kan shi yau da yake jiran cikar lokaci kafin ya tarwatse. Juyawa yayi ya nufi kan gadon, bai karasa ba yaji muryar Bappa da shaf ya manta yana dakin ta daki kunnuwan shi "Ka ci abinci sai ka kwanta" Kai Rayyan yake girgiza mishi yana zama a gefen gadon saboda yanda jikin shi yake bari, sosai yanzun yake bukatar magungunan shi, badan bacci ba, sai dan mugun sabon da jikin shi yayi, jiya bai sha ba in zai tuna, yini biyu kenan bai sha ba, shisa jikin shi yake sanar da shi babu lafiya. "Kana bukatar ka sa wani abu a cikin ka" Cewar Bappa da ya bude ledar take away din da yayo musu a cikin hotel din, shinkafa ce dafaduka ta sha nama da kayan hadi, harda hadin salad a gefe. Yana kallon Rayyan din ya sake girgiza mishi kai "Yunwa da withdrawal effect ba hadi bane me kyau" Bappa ya karasa maganar yana saukowa kasa kan kafet din dakin ya ja abincin shi daya saka cokali a ciki ya fara ci. Shi din ya karanci Psychology ne a kasar amurka, zai koma yaci gaba, saboda yana son zama abinda ake kira Profiler, akwai graduate degree da zaiyi akan forensic psychology kafin ya fara aiki da hukumar tsaro ta yan sanda da yake a can kasar, yana da kokarin da yasan da wahala idan bai samu ba. Shi din dan gidan Sheikh Abdullah Bappa ne, sunan kakan shi yaci wato Muhammad sai suke kiran shi da Bappa kamar yanda ake kiran kakan na shi, baban shi sanannen Malami ne, duk kuwa da tarin arziqin da suke da shi. Suna da dattako, ana kuma ganin girman su a garin Kano, da wahala ka kira sunan Baban shi ace an samu mutane biyar a waje babu wanda ya san shi ko yaji labarin shi. Tun da ya dauko Rayyan yaga alamun damuwa a tare da shi, karantar shi yake tayi har zuwa yanzun. Yanayin dabi'un shi, yanda jikin shi yake kyarma da idanuwan shi da sukayi wani irin haske duk kuwa da doguwar hanyar daya sha yasa Bappa gane cewa yana ta'ammali da miyagun kwayoyi. Watakila shima Rayyan kamar sauran mutane ne masu fama da depression, daga shan magungunan da zasu taimaka sai su dinga kara daya akan ka'idar da likita ya rubuta, a hankali a haka sai abin ya zame maka shaye-shaye batare da ka kula ba. Ka kara wa kanka matsala da kanka. Rayyan kuwa shiru yayi yana tauna maganganun da Bappa yayi kafin ya kwanta yana juyawa, Bappa bai san shi ba, dan ya gane daya daga cikin matsalar shi baya nufin ya gane gabaki daya. Amman jikin shi kyarma yake, makoshin shi yakeji kamar an zuba yashi saboda bushewar da yayi, harshen shi babu miyau ko daya a ciki. Numfashi Bappa ya sauke yana mikewa, Rayyan baiga me yakeyi ba saboda ya rufe idanuwan shi har sai da ya karaso in da yake kwance yana fadin "Ungo" Bude idanuwa yayi, yaga robar ruwa sai irin maganin shi guda biyu a dayan hannun Bappa, jikin shi na kara sabon bari ya mike yana karbar maganin ya watsa a cikin bakin shi hadi da lumshe idanuwan shi, kafin ya sake bude su yana karbar robar ruwan ya kora "Ka kara mun guda biyu" Kai Bappa ya girgiza mishi "Zai rikeka zuwa safe" Ya fadi yana wucewa ya koma inda ya tashi, abincin shi yaci gaba daci, Rayyan kuwa ya kai mintina talatin kafin maganin ya fara nutsar da shi, rawar jikin da yake ya bari, ya sake gwada kiran su Bilal amman shiru. Wannan karin Bappa da yake kwance akan kujerar cikin dakin yana danna waya ya kalla, a saman damuwar shi tunanin waye Bappa ya darsar mishi, haka kawai ya tsinci kan shi da son sanin waye Bappa? * Sama-sama yake jin shi, iskar da yake shaka da fitarwa ma kamar an daureta da zaruruwa haka take shiga kofofin hancin shi. Jin shi yake kamar a cikin wani mugun mafarki da zai farka daga shi ko yaushe. Sai dai kamar ya farka kusan awa daya da ta wuce ko fiye da haka, babu agogo a hannun shi balle ya duba lokaci, ba shi da natsuwar kiyastawa kuma. Amman tabbas ya farka daga abinda ya tabbata ba mafarki bane ba, dumin jikinta ya fara tabbatar mishi da ba mafarki yake ba, kafin ya kara ware idanuwan shi akan fuskarta, wani irin mikewa yayi yana hankadeta gefe tare da fadin "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un..." A matuqar razane, kan shi ya kalla da yanayinta itama kafin komai ya dawo mishi, ba Aisha bace ba, Layla ce, Layla ce. Wata murya a cikin kan shi take fadi tana maimaitawa. A matuqar gigice ya suturta kan shi, baisan abinda ya kamata yayi ba banda kokarin ganin ta tashi, dabarar ya shafa mata ruwa bata zo mishi ba, haka yaci gaba da jijjigata a gigice har Allah ya dawo mata da hankalinta ta bude idanuwanta akan shi "Layla ki tashi, dan Allah ki tashi ki karyata mun abin nan, ki ce mun karya ne, ki ce mun ko a mummunan mafarki ba zai faru ba..." Bilal din yake fadi a gigice, yana girgiza ta, sai da ta kama hannun shi ta ture, jinta take kamar tana yawo a saman gajimare, dakyar taja jikinta tana mikewa, numfashi dakyar take fitarwa lokacin da ta kama skirt dinta tana saukewa, idan tace ga abinda take ji karyane, a fadin duniya babu wasu kalamai a cikin kowanne yare da zasu taba yiwa halin da take cikin adalci wajen fassara shi. Kafafuwanta ta sauko daga kan gadon, tana mikewa taji wani irin abu ya tsirga mata, amman bata da lokacin ririta kowanne ciwone yake taso mata, dakin kawai take son bari "Layla..." Bilal ya kira, amman bata kula shi ba, dankwalinta ta dauka tana daurawa. Ta dauki jakarta da mayafi "Layla..." Ya sake kira ganin tana shirin nufar kofa a halin da take ciki. Shirun tashin hankalinta yake karanta da yake kara bugun zuciyar shi. Bashi da karfin motsawa balle ya hanata ficewa daga dakin. Tun fitarta bai motsa daga inda yake ba, sai yanzun daya samu yaja jikin shi yana dora kan shi a jikin katifar, idanuwan shi ya lumshe kamar hakan komai daya faru yake jira ya dawo mishi "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Ya furta daga wani lungu na zuciyar shi jikin shi na wani irin bari "Me zan cewa Abbu? Me zan cewa Abbu..." Yake fadi kamar wanda ya sami tabin hankali, har lokacin so yake ya tuna lokacin da Layla ta shigo dakin, so yake ya tuna yanda akayi ta hau kan gadon shi, yanda akayi wannan kaddarar ta same su, ko tabin hankali ya fara bai sani ba, tunda ance in kana hauka baka sanin abinda yake faruwa. Saboda in ba hauka yake ba babu yanda za ayi ace wani abu ya faru a tsakanin shi da wata mace daban da igiyar aure bata kulla su ba, balle kuma Layla. Yana da yakinin ko mazinaci ne shi ba zai bi Layla ba, yana mata son da ba zai yarda su kasance a irin wannan yanayin ba. Hannun shi daya dora kan katifa yaji kamar ya taba wata lema-lema, ba shiri ya dago kan shi yana kallon wajen da hannun shi, abinda yagani na kara gudun zuciyar shi, baisan yanda ciwon bugun zuciya yake ba, amman tabbas yana gab da kama shi, saboda abinda yake gani na kara tabbatar da ko ciwon hauka yake, to tabbas a cikin wannan ciwon ya kasance tare da Layla. Wannan gaskiya ne ko da hankalin shi yabar jikin shi. Wata irin mikewa yayi yana kama zanin gadon ya yaye shi daga kai, fita yayi daga dakin kamar sabon mahaukaci. Bokitin daya fara cin karo da shi ya saka zanin fadon a ciki ya koma daki ya dauko omo, ya nufi bokitin da sukan tara ruwa ya bude ya diba, kallo daya zakayi mishi da yanda yake wanke zanin gadon kasan ba a cikin hayyacin shi yake ba, yayi mishi wanki yafi biyar kafin ya shanya. Ruwan ya kara diba ya shiga wanka, sai dai ya kai awa daya tsaye a cikin bandakin ko kayan shi bai cire ba, kalar wankan da zaiyi yake tunani, idan ya saka sabulu ya fito tabbas zai fito da daudar da yake ji har cikin ruhin shi. Idan kuma yayi wankan da zai tsarkake daudar wajen shi baisan yanda zaiyi da ta ciki ba, kuma wankan zai tabbatar mishi da abinda yake so ko yayane tunanin shi ya karyata mishi. Bashi da wani zabi daya wuce yin wankan tsarki ya daura alwala ya fito zuwa daki, kaya ya sake yana fita da wanda ya cire kamar suna tare da wata dauda da ta girmi idanuwa ya saka su a bokiti, dakin dai ya sake komawa ya dauki darduma ya shimfida, har ya kabbara sallar azahar da yake tunanin ta wuce shi, saboda sanda ya fita yaga kamar yamma tayi sosai, komai bai kwance mishi ba sai da yayi sujjada, sai da ya dora goshin shi a kasa ya kara jin yanda bashida wata hijabi tsakanin shi da Ubangiji sannan sauran nutsuwar da yake tare da ita ta kwance. Maimakon karatun sujjada sai "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Da yake fadi muryar shi can kasan makoshi yana maimaitawa ko Allah zai tausaya mishi ya sake mishi wata kaddara da zai iya dauka ba wannan da ta faru ba, tun yana yi muryar shi na fitowa harta daina ya koma yi a zuciya, tun kafafuwan shi na da sauran karfin durkuson sujjadar harya kife gabaki dayan shi, Ayya kance "Ko rigimar yarinya bakayi ba Bilal, zan iya kirga lokuttan da naga hawaye a fuskar ka" Amman yanzun kukane mai gunji ya kwace mishi, kuka yake daga zuciyar shi, rurin shi na fitowa da sauti kafin wasu irin hawaye masu zafi su zubo mishi, hade jikin shi yayi yana wani irin kuka yau da yake neman mai lallashin shi, saboda a labarai ma bai taba cin karo da kalar kaddarar su ba, bai taba jin labarin tashin hankali makamancin wannan da yake ciki ba, bayani yake nema yayiwa kan shi ya kasa, idan ya kasa gane abinda ya faru ko ya akayi ya faru taya zai ma wani bayani ya gane, wanne irin uzuri zai bayar "Abbu..." Ya kira sunan na fitowa da gunjin kuka, ta ina zai fara yiwa Abbu bayani, me zaice mishi, me zai cewa Abbu, ya dade yana jin bai cika mishi alkawarin daya rike ba, ya dade nauyin amana na bibiyar shi, amman yau yake jin duniyar shi ta tsaya cak, kuka yake na yanda lokaci daya kaddara ta bude mishi shafin da baisan ya zai karanta shi ba balle yayi tunanin wucewa, saboda an kashe fitilar da take haske da rayuwar shi, duhu ya baibaye ko ina. Yau kuka yake da dukkan zuciyar shi, kukan maraicin da bai taba shi ba shekarun da suka wuce sai yanzun. Ji yake kamar wani abu na ruri banda zuciyar shi, kafin kwakwalwar shi ta sanar da shi wayace, wayar shi ce take ihu, dakyar ya iya daga jikin shi ya rarrafa inda wayar take kan tebir ya mika hannu ya dauka, zuciyar shi nayo tsalle zuwa cikin makoshin shi ganin "Hamma" Rubuce a jikin screen din wayar da ta subuce daga hannun shi tana faduwa kasa, baiko matsawa yayi kamar wayar na dauke da wani abu da zai iya cutar da shi, sam a lissafin da yakeyi na mutanen da zasu tuhume shi Rayyan ya bace mishi, komai ya bace mishi banda Abbu har wayar ta yanke bai iya motsawa ba, tana sake daukar ruri wasu hawayen na kara zubo mishi "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Yake fadi yana maimaitawa, yanzun kam ya tabbatar da wannan shafin da kaddara ta bude mishi shine shafin karshe, babu yanda zai ayi yai tsahon ran ganin wucewar shi, zuciyar shi bata da karfin daukar wannan tashin hankalin "Ka kula da Layla, ka kula mun da Layla kaji Bilal, zuciyata na mun wani iri" Maganganun Rayyan suka dawo mishi, sake durkushewa yayi, da yawan mutane in suka shigo su kaga Bilal din zasuyi mamakin ganin namiji kamar shi yana kuka haka, abin zai zame musu baqo, saboda an san namiji da juriya, shi da kan shi in da wani yace zai kuka kamar dan shekara biyu zai karyata, saboda bai taba hango rayuwa zata bashi wannan dalilin ba, amman yau kuka yake "Me zan ce musu?" Ya furta a zuciyar shi, ashe akwai wani abu da ba zai fassaru ba, ashe akwai kalar kaddarar da babu kalaman da zasu misaltata, ya akayi Layla ta zo dakin su? Yaushe Layla ta shigo dakin su? "Sai kayita bacci kamar ba namiji ba, ka dinga rufe daki idan ba kowa a gida..." Rayyan kan ce mishi, saboda kar a shigo a illata shi yana bacci, amman bai taba bacci irin wannan ba, bai taba baccin da za'ace Layla ta shigo har tahau kan gadon shi bai sani ba, har wani abu ya shiga tsakanin su haka "Ko mafarki nake? Ko da gaske mafarki ne?" Ya furta yana tashi zaune, fuskar shi harta kumbura saboda kukan da yakeyi, wayar shi ce take ci gaba da ruri, dakyar ya iya mika hannu ya dauka "Layla" Ya gani, cikin sauri ya daga yana karawa a kunnen shi, watakila da gaske mafarki yake, muryar shi a dakushe yace "Layla..." Sai dai yanayin tata muryar ya tarwatsa wani abu a cikin tashi zuciyar da ba yajin zai taba komawa dai-dai "Hamma ba mafarki bane ba, ba mafarki bane Hamma..." Wayar ce ta sake subucewa daga hannun shi a karo na biyu, sosai yake kokawa da numfashin shi, sai dai wannan karin a juye ta fadi, yana ganin screen din, baisan iya mintinan da ya dauka ba kafin ya ga kiran Aisha ya shigo, dariya yayi wannan karin, saboda abin ya fara fin karfin shi, nata kiran na yankewa na Ayya ya shigo "Ayya..." Ya kira wata dariya da ta fito da sautin kuka na kwace mishi, da gaske karshen duniyar shine yazo, sosai yake tabbatar da hakan lokacin da idanuwan shi da suke wani irin radadi suke kafe akan screen din wayar da kararta ta daina zuwa kunnen shi, yana kallonta in wani kiran ya yanke sai wani ya sake shigowa, kiran mutanen da kamar sun san abinda ya faru, kamar suna jira ya daga ne su fara jeho mishi tambayoyin da yasan bashi da amsar su...! * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:07 PM - 111: Dec 12, 2020 19 Har ta sauka daga cikin napep din jinta take kamar a wata duniya ta daban. Tayi gaba yayi mata magana "Hajiya kudin" Jakarta ta bude, bata san nawa bace ta dauko ta miqa mishi, tayi juya ya sake cewa "Ga canjin, ko kin barmun?" Hannu tasa ta karba tana zuba su cikin jakar da ko zageta batayi ba. Ta sha jin kalmar tsiraici, ta dauka tasan ma'anar kalmar, a da ta dauka tsiraici shine ka rabu da tufafin jikin ka, sai yau ta fahimci akwai tsiraicin daya girmi rabuwa da tufafi. Akwai suttura da ba kaya bane kawai yake saka jinta a ranka, haduwa take da mutane a hanyar hostel din, musamman da ta shiga, sai ta tsinci kanta da jan mayafinta tana kara gyara shi, babu inda yake bude a jikinta, amman jinta take kamar bata saka komai ba, kamar kowa na ganin duk wani tsiraici da yake tare da ita. A daddafe ta karasa dakin su, babu kowa sai Anisa da take zaune akan gadon Layla din, da yake nata saman na Layla ne, in ba lokacin baccinta yayi ba anan suke zaman su, wasu ranakun ma in tayi bacci Layla bata tashin ta. Yau ita batayi lakca ba sai karfe sha biyu na rana. Tana dawowa ruwa ta kara watsawa ta samu waje ta kame ta dauki waya tana dannawa, da yake taci abinci a restaurant, yayarta ta turo mata banner din Zahra Tabiu. Su kan siyi Donut dinta sosai, matar karshe ce, taje gidan Yayar tata ne ta samu Donut, duk a tunaninta na Zahra Tabiu ne, ko da ta fada mata ita tayi sam bata yarda ba, sai da ta kwana taga tayi a gabanta "Inalillahi... Anty yaushe kika koya? Ina kika koya?" Murmushi Antyn tayi "Zahra Tabiu dince fa ta koya kwanaki, kin san nayi saving lambarta saboda siyen Donut, to shine naga tana talla zata koya yanda akeyi online, dubu biyar" Ware idanuwa Anisa tayi, zatayi abubuwa da yawa da dubu biyar "Kuma har kika iya haka?" Tayi maganar cikin rashin yarda, dariya Antyn tayi mata "Akwai videos haka, sosai ake ganewa, dan su Ammar sun fasa mun screen din waccen wayar dana nuna miki, kiyi joining in zata sakeyi" Batayin ba ko da Anty ta turo mata, amman duk wani Donut da zata siya sai taji kamar bai kai na Zahra Tabiu ba, shine da safe da ta tashi taga Anty ta turo mata banner din, ta zabtare rabin kudin koyarwar daga dubu biyar zuwa dubu biyu da dari biyar. Gara dai ta koya ta huta, in ta koma gida ta dinga cin kudin Yayyenta, tana da kwalayen Donut Fairy data siya, in sun ce tayi musu order sai ta karbe kudin tayi a gida ta saka a kwalin, in sun cinye tabi ta kwashe. Lambar wayar take dubawa ko iri daya ce da wadda take da ita +234 806 515 6303. Ta gama dubawa kenan ta ga ita din dai ce, sai ga Layla ta shigo dakin kamar an korota. Kallo daya Anisa tayi mata tace "Layla?" Tana sauko da kafafuwanta daga kan gadon, tsaye Layla tayi bakin kofar, so take wani abu da zai nuna mata mafarki takeyi ya faru, kamar ace Anisa ta girgizata tana tashinta yanda ta saba da fadin "Ke banza takwas saura" A ranakun da suke komawa sallar asuba bayan sun makara. Amman kallon da Anisa takeyi mata ya tabbatar mata da cewa ba mafarki takeyi ba, idonta biyu. Ta dai kasa karasawa cikin dakin ne, kafafuwanta take ji sunyi wani irin sanyi. Ganin haka yasa Anisa ajiye wayar tana saukowa daga kan gadon tazo ta kamata "Layla? Lafiya?" Kai ta girgiza ma Anisa da ta kamata tana janta zuwa kan gadon, sai da ta zauna sannan jikinta ya fara bari "Dan Allah menene? Me ya faru? Ko wani ne ya rasu?" Anisa ta karasa muryarta na karyewa. Gabaki daya yanayin Layla ya gama daga mata hankali, ta san yanda mutuwa take, Yayanta ya taba rasuwa, ta kuma ga kalar hargitsin da kowa ya shiga, yanayin Layla ya nuna cewa tana cikin matsananci shock da ba labari bane me kyau yake haifarwa. Shisa gabaki daya hankalinta ya tashi "Ki saka mun ruwa inyi wanka" Layla ta fadi daga kasan makoshinta, watakila ruwa da sabulu su fitar mata da daudar da takeji, kila kuma idan ta saka ruwa a fuskarta zata farka. Babu musu Anisa ta tashi, sukan ajiye ruwan zafi a flask ko dan shan shayi, shi ta juye mata a bokiti tana sirkawa, da kanta ta kai mata komai bandaki ta dawo tana fadin "Ki tashi ga ruwan can" Mayafi kawai Layla ta cire, ko towel bata dauka ba ta fice daga dakin. Da yake sukan dibo ruwa da bokatan wankan nasu, da sun fito bandaki sukan saka omo su wanke shi har bayan. Shisa tasan ruwan ciki mai tsarkine, karkatawa tayi ta fara wanke hannayenta, a karo na farko da takejin sauqi irin na addinin musulunci, niyyarka a zuciya idan ka daurata tayi, ba saika fadeta a fili ba, bata da kwarin gwiwar motsa labbanta da daura niyyar wannan wankan da take tunanin ya zame mata dole. Tashin hankalinta bai fara ba sai da ta wanke fuskarta tana sake bude idanuwanta a cikin bandakin. A daddafe ta karasa wankan, kayanta ta mayar tana fitowa, can ta baro bokitin, sai Anisa ce ta koma ta dauko, doguwar riga ta dauka ta sake kayan jikinta da take da tabbacin ta gama saka su har abada. Wayarta ta bude jaka tana dauka, tana kallon yanda hannunta yake bari, a kasa ta zauna. Tambayoyin Bilal ne suke dawo mata, amman yanda ta kula ya kasa gane yanda akayi abinda ya faru ya faru, haka itama take cikin wannan rudanin. Ta san sanda ta shiga dakin su, ta tuna sanda ta zauna harta sha ruwa, amman daga nan babu abinda zata iya tunawa banda tashin hankali da wani irin firgici marar misaltuwa. Dakyar ta iya lalubo lambar Bilal tana kiran shi, bugu biyu ya daga "Hamma ba mafarki bane ba, ba mafarki bane Hamma..." Ta furta da wata irin nisantacciyar murya, girman kalaman na zauna mata da wani yanayi daya birkita mata komai, wayar ta sauke daga kunnenta tana ajiyewa a gefe, kafin ta janyo kafafuwanta ta hade su da jikinta. Har lokacin jinta takeyi kamar bata da kaya "Martabar ki darajar ki Layla, martabar ki sutturar ki..." Kalaman Mami suka dawo mata. Kalaman na tuna mata da Mami "Mami... Mami" Ta ke kira cikin wani irin tashin hankali, duk wata nasiha da ta tabayi mata tana dawo mata. Da gaske martabarta suttura ce a wajenta, sutturar da bata gane muhimmanci ta ba sai yanzun da take jin bata tare da ita. Kuka take nema amman sam yaki zuwa, banda wani irin numfashi da take ja tana fitarwa kamar mai ciwon asma babu abinda take iyayi, batsan shigowar Anisa dakin ba sai da taji ta kamota "Dan Allah kiyi mun magana Layla" Cewar Anisa da hawaye cike taf a idanuwanta, dan ita bata son tashin hankali sam, sai lokacin wani irin kuka ya fito tun daga kasan zuciyarta tana sakin shi cikin shesheka, ko ina na jikinta bari yakeyi "Kiyi hakuri, banma san me ya sameki ba, ko me ya faru, dan Allah kiyi hakuri..." Anisa tace tana kara rike Layla a jikinta, yanayin yanda take kuka ne yake ba Anisa tsoro, saboda bata taba ganinta cikin yanayi irin wannan ba, wayarta da ta fara ringing Anisa ta dauka tana dubawa, an rubuta "Mami ❤" A jiki, gyarama Layla kwanciya tayi a jikinta "Dan Allah kiyi shiru, kinga ga Mami tana kiran ki" Wata irin mikewa Layla tayi tana jin kamar an watsa mata ruwan zafi, fisge wayar tayi daga hannun Anisa, tana kifeta akan cinyarta, kamar hakan zai hanata rurin da takeyi, jikinta kara bari yakeyi cike da sabon tashin hankali, ji takeyi kamar Mami ta gane, kamar tasan me ya faru shisa take kiranta, tana yankewa wani kiran na sake shigowa, amman ta kasa dubawa, sau biyar ana kira tana yankewa, kukanta ke kara tsananta saboda tashin hankalin da take ciki, saboda tasan duniyarta ce gabaki daya tazo karshe shisa Mami ta gane, shisa take kiranta. Bata da abinda zata fada mata "Fyade" Shine kalmar farko da ta dace a yanayi irin wannan, ita kuma ce kalma guda daya da zata iya labewa bayanta dan samun sauki. Amman zuwan kalmar tunanin ta, alakanta Bilal da wannan kalmar kawai barazana take karawa shige da ficen iskarta. Ko kwaya Bilal yasha ba zai taba mata fyade ba ita tasani, ita zata bada shaidar waye Bilal. Shisa bata da kalmar da zata fassara abinda ya faru din, bata da shi, da duk dakika da yanda rudani da tashin hankalinta suke karuwa. Wanne irin mugun abune wannan yake faruwa dasu? Kamar wanda akayiwa asiri, asiri ne kawai abu daya da take da shi da zai fassara mata abin nan ta yarda, sai kuma iskokai, amman a iya saninta bata da iska, haka ma Bilal. Sai dai akwai iskar da bata bayyana sai daga baya, watakila abinda ya faru da su kenan. Amman wa zatayiwa wannan bayanin ya gane? "Ke yanzun kina tunanin shi Rayyan din da kike biyewa idan tsautsayi ya gifta a tsakanin ku zai aure ki?" Kalaman Mami suka dawo mata, suna kuma tuna mata da Rayyan daya fice daga kanta na wucin gadi "Na shiga uku, Anisa na shiga uku na" Ta ce cikin firgici "Ki daina Layla, babu kyau fadar haka, ki daina dan Allah. Kiyi addu'a koma menene zai zo da sauki" Kai Layla take girgiza mata wasu irin hawaye masu dumi na zubo mata, jiya ta ga yanayin da bata taba gani ba a cikin idanuwan Rayyan, a karo na farko jiya yayi mata kalar murmushin da bata taba gani ba, zata rantse daga zuciyar shi yayi mata murmushin bayan ta fada mishi tana son shi, kamar yana son gaya mata ita da shi din zasu iya faru, a cikin murmushin shi ta ga possibility din zaman su a karkashin inuwa daya a matsayin masoya da zai iya kaisu da aure wata rana, ta hangi cikar burinta a kwayar idanuwan shi. Da yace ta tafi sai taga kamar akwai rokon da yake mata, kamar yana bata amanar kanta ne kafin ya dawo. "Bana son kowa a kusa da ke Layla" Ya sha fada mata, a wasu lokuttan takan gane zai fadi kalaman tun kafin ya furta su. Da wanne ido zata kalle shi? Ya zatayi mishi bayani ya gane? Zai fahimceta? Zai fahimce su ita da Bilal idan sukayi mishi rantsuwa da su kan su har yanzun basu san ya akayi abinda ya faru din ya faru ba. Wayarta da ta sake daukar ruri ta katse mata tunanin da takeyi, wannan karin da wani irin bugun zuciya tasa hannu ta birkita wayar tana ganin "Hamma Na" A rubuce, bakinta da matuqar nauyi ta iya furta "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Wani irin yanayi take ji da batasan ya zata fassara shi ba, ashe haka tashin hankali yake bata sani ba? Ashe haka asalin firgici yake, ko ranar da ta fita bandaki cikin dare taga gicci tayi tunanin aljani ne bata firgita irin wannan da take ciki yanzun ba. Tashin hankaline da babu wanda zai taba fahimtarta sai wanda ya taba shiga cikin irin yanayin da take yanzun. Wayarta da ke ruri ta ga Anisa ta mika hannu ta dauka, da sauri ta rike hannunta "Ba dagawa zanyi ba, zan saka a silent ne" Tayi maganar cikin wani irin yanayi, a silent din ta saka mata wayar tana mikewa ta ajiyeta gefe. Fita tayi daga dakin, ruwan sanyi ta siyo ta dawo. Guda daya ta dauka ta tsiyaye a kofi ta zo tana ba Layla din da ta girgiza mata kai "Ki sha dan Allah, watakila kidan ji dama-dama" Hannu biyu ta saka ta karbi kofin saboda yanda jikinta yake bari, shan ruwan tayi sosai, Anisa ta karbi kofin tana ajiyewa a gefe. Mikewa tayi ta fita ta daura alwalar la'asar tana tunawa Layla yanda itama batayi sallar ba. Dakyar ta iya mikewa tana dauro alwala, a karo na farko ta tsinci kanta da kunyar tsayawa a gaban Ubangiji, sai take jin kamar ita din bata cancanci tsayawar ba, kamar tana da tarin laifukan da batasan yanda zata fassarasu ba, har Anisa ta idar ita tana ta rakubewa a gefen gado "Kinsan la'asar da saurin wucewa, ki samu kiyi sallah sai ki sha panadol ki dan kwanta. Sannu" Kai ta jinjina, ko da ta gabatar da azahar ta sake mikewa ta gabatar da la'asar ta idar Anisa batace mata komai ba. Hannuwanta ta daga tana rasa abinda ya kamata ta roka, gabaki daya addu'o'inta basayin tsayi ko da can, idan tayiwa iyayenta da suka rasu, sai Mami da Abbu, sauran ta fatan samun Rayyan ce, sai kuma Bilal, shima bata taba mantawa da shi a cikin addu'o'inta, in tayi tama sauran yan uwanta shikenan. Lokutta da dama sai tayi niyyar mikewa sai taji kamar bata kyauta ba, kamar saboda Rayyan da Bilal ya kamata tayiwa Ayya itama, a ranakun da abin yake ci mata rai, takan koma tace "Allah ya raya miki duka yaranki cikin aminci Ayya, Allah ya yafe miki, nima na yafe miki duk ce mun mayya da kikayi" Wasu ranakun kuma turo labba takeyi ta mike abinta, yanda Ayya bata sonta, itama hakan take ji. Amman yau ta rasa abinda zata roka, a karo na farko ta rasa. Tana tsakanin rokon sauki, ko kasancewar abin da yake faruwa mafarkin da tasan ba haka bane ba. "Mami.. Mamina... Allah ka dauke duka saukin a kaina ka bata....Allah Mami...Mamina" Shi take fada hawaye masu zafin gaske na zubar mata. Nan take zaune kan dardumar, tun tana iya fadar kalamai har suka bace mata, banda Mami da take kira tana wani irin kuka babu abinda take iyawa. Anan Magriba ta sameta ta tashi tayi, isha'i ma haka. Duk yanda Anisa taso ko ruwan shayine ta kurba kiyawa tayi. Zuwa goman dare sanda ta kwanta zazzabi ya rufeta kuwa. Tun Anisa na mata sannu, har ta daina amsawa, tana jinta ta tabata, tayi luf dan Anisa ta samu bacci, sannan kuwa ta hau sama tana kwanciya. Bude idanuwanta takeyi, dan duk idan ta rufe bata ganin komai sai ita da Bila a abinda take tunanin mafarki ne, tambayoyin da take da su idan ta fito dasu fili zai iya barazana da imaninta, shisa ta zabi taci gaba da fadin "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Ko zata samin saukin da kalmomin sukan samar a yayin tashin hankali. * Tun da ta sauke wayar daga kunnenta take cikin tashin hankali, har ciwon kai ya taso mata. Tunda akayi wayar hannu, ko tace tunda Bilal ya mallaki tashi wayar, ko suna gari daya sai yayi mata kira fiye da hudu a rana. Duk a cikin yaranta Bilal ne zai fita fiye da awa biyu ya kirata ya tabbatar mata da cewa yana lafiya, ko da kuwa ya sanar da ita cewa zai wuce awa biyun. Shakuwar da take tsakaninta da yaranta, gabaki dayan su Rayyan ne kawai bata kira a waya, sai ta jima bata kira shi ba saboda ranta kan baci idan bai daga ba, gara ta kira Bilal taki ya yake. Amman ita ko su Rukayya sukaje makaranta tana iya musu kira goma-goma kafin su dawo. Ko muryoyin su taji sun sauya sai ta gane. Shisa tun da safe da bataji Bilal ba ta kasa samun natsuwa, ko da yana lakca zai mata text ya fada mata, yana kuma fitowa zai kirata. Ko Abbu bata waya dashi yanda takeyi da Bilal, wani sim Bilal din ya siyo musu ya bata guda daya, duk wata yake tura mata kudi sai su dauke, haka zasuyita labari ba kama hannun yaro. Kwanaki Khalifa daya sameta sunata waya bayan sun gama yake cewa "Hajiya Ayya da Danta" Dariya tayi "Ko katin ku ma bakwaji, ni da nake saka katin ma ba'a kirana haka" Dariyar ta sakeyi sosai "To dan ubanka kafin ka samun kati sau daya mijina ya sakamun sau hamsin... Kuma wannan layin Bilal ne ya siyo mana shi, ba'a daukar kudi, duk wata ake saka ko dari shida ne" Khalifa yayi dariyar, takan ga mamaki a fuskar yaran nata kan kalar shakuwar da take tsakanin ta da Bilal, har tsoro takan ji wata rana kar abin ya darsa kishin Bilal a ransu, amman ko na rana daya bata taba gani ba, suna kaunar shi kamar daga cikinta ya fito, ko dan Bilal dinta haka yake. Da wahala ka zauna da shi baka kaunace shi ba, ko dan yanda zai dinga kaffa-kaffa da bacin ranka, a duk gidan daga shi sai Haris zata yiwa wannan shaidar, dan ko yanzun duk a cikin yaran Maryama babu wanda take ji a ranta kamar Haris. Shi ka daine yake kiranta kullum su gaisa harma suyi labari, ko yanzun da akayi maganar auren shi da yar wajen Yaya Ayuba, kudi na nan tana warewa da zata bashi gudummuwar ta, so take tayi hidimar auren yaron kamar yanda zatayi ta su Bilal. Yanzun wayarta tabi da kallo da ta sake kiran Bilal amman wannan karin a kashe ma taji wayar tashi, abinda ya kara daga mata hankali matuqa. Ta kara kiran Rayyan har sau hudu bai daga ba, tasan yana Bauchi. Yanzun take tunanin yanda in har Bilal ya daga waya zata saka ya tura mata lambar abokan shi guda uku ko fiye da haka yanda zata kira su duk idan bata same shi ba a duba mata a gani ko lafiya. Tayi tunanin kiran Abbu, amman bata son daga mishi hankali, gara ta bari ya dawo, tunda ya kai wannan lokacin bai dawo ba tasan wani abin mai muhimmanci ne ya tsayar da shi. Nata hankalin dai yaki kwanciya, ga yaran duk suna gidan Yaya Ayuba, shiru sai ita kadai a falonta. Ta saka wannan ta kwance, sallama taji, sallamar da sai bayan ta amsa sannan muryar ta karasa kwakwalwar ta da wani yanayi da ya sata daga kai ta kalli kofar inda Mami take tsaye a tsorace. A nata bangaren ita tun cikin daren jiya ta farka da faduwar gaba, haka ta karasa daren cikin salloli, to tunda gari ya waye kuma jikinta yake a sanyaye, rabonta da yanayi irin wannan tun rasuwar mahaifiyarta. Addu'a ta dingayi, sam hankalinta bai kai kan Layla ba sai da tayi mata kira ya kai goma da safe bata daga ba. A yinin ranar in ba wayarta aka duba ba, ko ta Layla babu yanda za'ayi a gane yawan kiran da tayi mata. Har dubawa tayi ko ta ajiye lambar Anisa da Layla ta taba kiranta da ita, tana fada mata dakin su daya da Anisar, amman bata ajiye ba. Kusan duk wata baquwar lamba da ta iya gani a wayar saida tabi ta kira cikin son gano lambar Anisa, amman bata samu nasara ba. Idan ta kira wani cikin yaran tabbas hankalin su zai tashi, shisa ta kira Bilal, shima sau hudu bai daga ba, kuma tasan in dai yagani to zai kirata, haka kawai ta kasa samun natsuwa. Musamman ba jimawar nan da ta kira Bilal din taji wayar shi a kashe, haka ta Layla. Sosai zargin ko lafiya da takeyi ya tabbata, tasan ba shiri sukeyi da Ayya ba, na rana daya basu taba shiri ba, duk kuwa yanda taso hakan ya faru, amman akwai lokutta da dama da suka ajiye rashin jituwar da yake tsakanin su sukayi maganar fahimta, musamman lokuttan daya kasance ya shafi wani a cikin yaran su. Ko kwanakin baya da Haris ya sami hatsari, Ayya ce kiran shi na karshe, dan haka ita aka kira da wayar shi, bata ma kira Mami ba sai da taje asibitin wajen Haris, sannan tunanin yazo mata, shima Haris ya bata lambar Mami, dan bata taba sanin yanda lambar take ba. Kuma sai Mamin bataje ba, tabar Ayya da Haris din da yake tace mata ba wasu ciwuka yaji ba, ya bugune harya suma, kuma ya dawo hayyacin shi ana mai dinkine, ana gamawa aka basu magunguna suka tafi gida. Shine karo na farko da Ayya ta dinga jera kwanaki tana shiga bangaren ta tunda can Haris yake wuni, ba kulata takeyi ba, zata duba jikin shine, ta dan zauna suyi hira, da aka kwana hudu ma sai Haris din ya dinga wuni a falon Ayya din. Shisa yau take da yaqinin Ayya zata kulata indai zancen yarane, duk kuwa yanda tasan bata kaunar Layla, duk a cikin gidan ita da Layla ta dauki tsanar duniya ta dora musu. "Maryama?" Ayya ta kira cike da alamar tambaya, saboda sai da taji kanta ya kara sarawa, tasan akwai dalili babba da zai shigo da Mami bangaren ta, cikin rawar murya Mami tace "Bansan ko kinyi magana da su Bilal ba, dan Allah zanji ko Layla tana lafiya ne, tun safe nake kiran wayarta ba'a dagawa, yanzun kuma a rufe, Bilal ma na kira shi bai dauka ba, yanzun da na sake gwadawa shima tashi wayar a kashe..." Mami ta karashe maganar muryarta na karyewa, cikin tashin hankali Ayya tace "Nima inata kira ba'a daga din ba, yanzun nake so Abbun su ya shigo... Bana so in kira in daga mishi hankali" Kai Mami ta jinjina "Allah ya sa dai lafiya. Na kasa samun natsuwa wallahi..." Numfashi Ayya ta sauke, sam Mami ba zata gane yanda take ji ba, saboda watakila ita Layla kan yini basuyi magana ba, saboda haka rashin wayar su yau ba abin da zai daga hankali bane ba. Amman tasan ko a cikin yaranta ta fadawa wani duk yau tun safe batayi magana da Bilal ba hankalin su zai tashi, zasu san ba lafiya ba. Suna nan tsaye Rukayya ta karaso ita kanta mamakin ganin Mami tsaye a bakin kofar su tayi "Mami... Lafiya dai ko?" Cewar Rukayya, Mami din na matsa mata ta shiga cikin dakin, Ayya ta kalla "Me yake faruwa?" Ta sake tambaya gabanta na faduwa "Babu komai" Mami da Ayya suka amsa a tare, suna saka Rukayya kallon su cike da rashin yarda "Me yasa zaku amsani a tare idan babu komai? Me ya faru? Ina Abbu? Abbu bai dawo ba?" Rukayya tayi maganar da wani irin tashin hankali da yasa Ayya fadin "Dan ubanki karya zamuyi miki to?" Idanuwan Rukayya har sun fara tara hawaye, saboda tasan abinda duk zai hada Ayya da Mami waje daya haka, suna tsaye hayaniya bata tashi to mai girmane, kuma tafi kawowa ranta cewa Abbu ne, ganin yanda hankalinta ya tashi shisa Mami tace "Ke ba wani abu bane bafa, Layla ce ban samu a waya ba tun safe, shine nazo amsar dayar lambar Bilal in kira dan ya duba ta" Numfashi Rukayya ta sauke wani abu yana natsawa a zuciyarta jin ba Abbu bane ba "Nima na kira bata daga ba, ta saka hoton wasu takalma jiya sai nayi mata magana tace kawarta take siyarwa, to ina so in tura kudin, na dauka ko tana lakca shisa... Nasan lafiya in shaa Allah... Watakila wayar ta fadi ko ta ajiye wani waje" Kai Mami ta jinjina, ita sam batayi wannan tunanin na cewa zai iya zamana wayar Layla bace ta fadi, ko aka sace, sai taji ta dan samu natsuwa "Allah yasa lafiya dai... Sai anjiman ku, zanci gaba da kara gwadawa" Cewar Mami tana juyawa, har tayi taku biyu Ayya tace "Maryama..." Juyowa Mami tayi "Idan na same su zan aiko Rukayya ta fada miki" Kai Mami ta jinjina, haka kawai kwalla na cika idanuwanta. Shisa ta kasa cewa komai ta tafi kawai, akwai wani abu a cikin idanuwanta da yasa taba zuciyar Ayya din, tasan yanda tashin hankalin tararrabi akan ko yaronka yana lafiya yake. Shisa ma ta ajiye kishi da tsanar da tayiwa Mami din a gefe yau. Suna nan zaune tana dan amsa Rukayya dai-dai cikin tsegumin malaman makarantar su da kuma rashin mutuncin su da takeyi mata dan ta dan rage damuwa Abbu ya shigo, suna gaisawa da Rukayya ta tashi tana barin dakin, da yake girkin Mami dinne. Ta so yaci abinci tukunna ta fada mishi, amman yasan ta, ya karanci damuwa a fuskarta "Lafiya dai Maimuna?" Kai ta girgiza a hankali "Duk yau tun da safe banyi magana da Bilal ba, inata kiran wayar shi ba'a dauka, sai babu jimawa kuma Rayyan ya kirani yana tambayar ko nayi magana da Bilal din, kaga kenan shima basuyi magana ba..." Cikin tashin hankali Abbu yake kallonta tunda ta fara maganar, shima yau aiki kawai yakeyi, amman tunanin yaran nashi ya addabe shi, musamman da Bilal din bai kira shi ba, ko da suna wani meeting da yammaci, lokaci zuwa lokaci ya dinga duba wayar shi ko, dan yasan zai kira shi, cikin hira zai fada mishi Rayyan ya sauka Bauchi lafiya tunda yasan shi Rayyan din ba zai taba kira ba. Ta hanyar Bilal yakan san Rayyan yana lafiya. To kuma hidimar da yayi yau tana da yawa, amman yanata tunanin su, har Layla ba suyi magana ba, garama ita Layla ya kira bayan azahar bata daga ba. "Kuma yanzun Maryama tabar nan, tace bata samu Layla a waya ba" Wannan karin da kallon da yake mata hade yake da mamaki, duk da batun yanzun yasan akan yaran su Ayya zata iya ajiye duk wani tashin hankali a gefe ba, yaji dadi, sosai yaji dadi har cikin ran shi "Ki kwantar da hankali, in shaa Allah nasan lafiya. Yanzun haka wayoyin suka kai wani waje... Idan har zuwa anjima ba'a samu ba, gobe da safe sai in kira aje a duba su, kinga yanzun ba zaka kure mutane cikin daren nan ba dan suna jin kunyar ka" Kai Ayya ta jinjina mishi, duk da haka sai da ya kara zama a wajen nata ya tabbata ya ga murmushi a fuskarta sannan. Yana fita daga dakin nata wayar shi ya zaro yana kiran abokin shi da yake Zaria, amman bai daga ba, bayason ya karasa rikita Ayya, amman akan yaran shi ya fisu rauni, sosai zuciyar shi take bugawa, yunwar da ya yini da ita ta dauke daf, dakin shi ya nufa inda ya sami Mami ta shirya mishi abinci, shigowar da tayi yasa shi daukar plate, da kanta ta karasa ta zuba mishi abincin, yasan bataci ba shisa ya saka cokulla biyu, batayi mishi gardama ba, haka suka dinga tura abincin ba dan yana musu dadi ba. "In shaa Allah babu wani abu, da yardar Allah lafiyar su kalau" Kai kawai Mami ta iya daga mishi, amman yanayin jikinta yana kara tabbatar mata da babu lafiya, kawai addu'a takeyi a zuciyarta. Abbu ma haka, daren duka ukkun cikin wani irin yanayi sukayi shi, kowa da abinda yake tunani. * Tabbas yara raunin iyaye Yara karfin gwiwar iyaye Yara kwanciyar hankali da natsuwar iyaye Yara tashin hankali da firgicin iyaye. Allah ya bawa dukkan iyaye karfin zuciyar kaddarar da zata gifta ta kan yaran su. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:07 PM - 111: 13 Dec, 2020 (An kirkiri Airport a Zaria domin tafiyar labari badan akwai ba) 20 Lokaci zuwa lokaci wanda yake kujerar kusa da shi a cikin jirgin yakan ja karamin tsaki saboda yanda Rayyan din yake bubbuga kafar shi a kasa cikin kosawa. Gani yake kamar jirgin baya sauri, baisan menene a nannade tare da harshen Bappa da kalaman shi ba, amman sunyi tasirin da suka saka shi daukar shawarar shi na tsayawa yayi abinda ya kaishi Bauchi ya wuce wajen, sai su duba idan akwai jirgin da zai tashi daga Bauchi zuwa Zaria, da yake a yar jakar shi duka katikan shaidar shi suna ciki, na makaranta, katin zabe da kuma katin shaidar dan kasa. Bappa na dubawa kuwa yayi nasarar ganin akwai jirgin da zai tashi karfe biyar da rabi na ranar. Har suka gama abinda sukeyi a camp wajen azahar suka dawo hotel room din Rayyan bai daina mamakin yanda akayi Bappa ya saka shi zama a Bauchi har wannan lokacin ba, saboda gabaki daya hankalin shi yayi Zaria. Bai sake gwada kiran lambobin su Bilal ba duk ranar, wayar shi dai tana hannun shi, yana gudun kar ya sakata ko da a aljihune wani a cikin su ya kira ya zamana bai samu ba. Har airport din ma Bappa ne ya raka shi, a hanya ya tsaya ya sai mishi strawberry yoghurt, da yake yana da sauran biskit a jaka saiya hada ya dan sakama cikin shi, jiri har dibar shi yake idan ya mike, kuma yasan yunwa ce. Bappa ya zauna da shi har sai da lokacin tantancewa yayi sannan suka mike a tare "Nagode... Nagode sosai" Rayyan ya tsinci kan shi da furtawa, saboda shine kalaman da zai iya fitowa da su da kalar karamcin da Bappa yayi mishi. Kai kawai ya jinjina ya furta "Sai munyi waya" Shima na shi kan ya jinjinawa Bappa, bai tabayin aboki ba balle ya san yanda yake. Amman yanajin da rayuwa ta hada shi da Bappa da wuri, watakila da sun zama abokai. Bayason mutane, amman Bappa yana mishi daban, ba shi da lokacin tunani akan abin saboda su Bilal da suka kara taso mishi suna danne duk wani kwanciyar hankali da yake tare da ita. Da su a manne cikin kan shi suka sauka garin Zaria. Kafafuwan shi kamar basa mishi saurin da ya kamata yau haka yake ji lokacin daya karasa bakin titi da yake da yar tafiya daga cikin airport din. Mashin ya samu zuwa gida "Dari biyar" Mai mashin din ya fadi, kai kawai ya daga mishi yana hawa "Kayi sauri dan Allah" Rayyan yayi maganar da wani irin yanayi a muryar shi, har sai da mai mashin din ya dan duba ta mudubi ko zai ga Rayyan din da kyau, ko a cikin abokai lokacin daya fara koyon tuqin mashin din "Dan asabe ganganci" ne lakabin shi, yanzun ma sunan Dan Asabe ya bace sai ganganci din, yanda yake jan mashin idan yana tuqi kowa mamakin samun kwastomas din shi yakeyi. Musamman idan ya busa hayaqin wiwi din shi, bakin shi babu hakora wajen biyar saboda hatsarin da yakan yawaita samu. Tabbas yau ko labari yaje ya bayar na cewa wani ya nemi ya kara gudu da shi a mashin babu wanda zai yarda. Daman ance in da ranka zaka sha kallo, yau ya dauko mahaukaci. Sai yake jin shi a tsorace da Rayyan din, wani mahaukacin tas zaka gan shi, saika saki jiki kaji saukar duka. Haka suka lallaba harya sauke shi. Kafafuwan Rayyan din yaji suna mishi rawa, kamar suna son ce mishi ba zasu iya karasawa da shi cikin gidan ba. Zuciyar shi bata kara gudu ba sai da ya karasa tsakar gidan, har wani numfashin tashin hankali yake fitarwa, dakyar ya karasa dakin su yana ganin kofar a ture, daga hannu yayi cikin tunanin ya kwankwasa ko ya tura, ko kuma ya gwada saka mukulli. Karshe ya tsaya kan shawarar turawa, yaga dakin ya bude, duk da gidan akwai hasken wutar lantarki, dan ga mutanen cikin gidan nan sunata shige da fice, dan ko sun mishi magana ma bai kula da su ba. Yana tura dakin ya ga duhu, makoshin shi ya bushe kamar an zuba ya shi, switch ya laluba ya kunna, duk yanda ya sha cin karo da tsayuwar bugun zuciya a karance da kuma a videos bai taba tunanin haka abin yake ba sai yanzun da ganin Bilal a kwance a kasa kamar gawa ya saka tashi zuciyar tsaya na dakika kafin ta soma aiki tana wata irin bugawa, wannan karin kafafuwan shi duka sunyi sanyi, gwiwoyin shi kamar an buge su da guduma haka yake ji, kasa yayi gabaki dayan shi. Da rarrafe ya karasa inda Bilal din yake yana dora hannun shi a jikin Bilal din "Bi.. Bilal..." Rayyan ya kira cikin rawar murya, tashin hankalin shi na karuwa, dan gani yayi kamar Bilal din ya rabe mishi gida biyu, idan zuciyar shi bata daina gudu ba yana gab da sumewa, dakyar ya iya birkito Bilal yana dora hannun shi kan kirjin Bilal din inda yaji zuciyar shi na dokawa a hankali a hankali cikin yanayin daya fara nutsar da na shi bugun zuciyar. "Bilal..." Ya sake kira can kasan makoshi, Bilal din da yake jin shi a wata duniya yana bude idanuwan shi dakyar kafin ya sake mayar da su ya rufe. Tun jiya yake nan kwance, dakyar yaja jikin shi da safiyar yau din ya shiga bandaki, daya fito ma jiri ya dinga dibar shi har ya karasa daki, towel din shi na wanka ya ajiye a kasa ya dauki ruwa yai alwalar asuba a kai, dakyar yayi sallah sabo da ciwon kan da yake fama da shi ko numfashi dakyar yake fitarwa, sanyi yakeji, amman ya mika hannu ya janyo bargo ya kasa, anan yake kwance tun safiyar yana jiran ikon Allah ya cika a kan shi. Saboda tun jiya ya rigada yasan karshen duniyar shi yazo, baisan har rayuwar tashi gabaki daya tazo karshe ba sai yau. Akan kunnen shi aka kira azahar aka idar, amman ya kasa motsin kirki balle ya gabatar da sallah ko da daga zaune ne. Babu tunanin da baiyi ba, Ayya ita ce tafi kowa tsaya mishi a rai, yana tunanin wanda zai kula mishi da Ayyar shi a lokuttan da shi ka dai yake gane tana bukatar kulawa, wa zai kirata yayi mata hira, zai so ace ya samu dama, har addu'a yayi ya samu damar da zai roki Rayyan daya canza in zai iya, ya kula mishi da Ayya, ya kuma yafe mishi. Ko yanzun zuwan Rayyan din sai yake mishi kamar a mafarki, labban shi sunyi nauyine balle yayi magana, daya bude idanuwan shi ma hasken dakin kara mishi ciwon kai yayi, sai yaji kamar an soka mishi allurai ta cikin idanuwan, shisa ya mayar da su yana rufewa babu shiri "Bilal..." Rayyan ya sake kira, amman yaki yin wani kwakkwaran motsi, bawai ciwo bane Bilal bayayi, har yini sun tabayi a asibitin makaranta aka kara mishi ruwa, amman zuwa tara na dare kamar ma baiyi jinya ba, haka yake hidimar shi, bai taba ganin shi cikin hali irin wannan ba. Tunanin zuwa asibitine yazo ran shi, amman bai taba raina karfin shi ba sai da ya daga Bilal dan ya dauke shi yaji kafafuwan shi banda rawa babu abinda sukeyi, a hankali ya mayar da Bilal din ya kwantar, dakyar ya karasa mikewa yana fita daga dakin, ba zaice ga sanda ya cire takalman shi ba, sai da ya taka tsakar gidan su yabi takan ruwan da yaji har tsakiyar kan shi sannan ya gane babu takalma a kafafuwan shi. Abinda ko a daki da wahala ka same shi babu su, akwai wanda yake ajiyewa dan yawo a cikin daki kawai. Yakan ce Bilal din na tako kasa ya shigo musu da ita, ko idan wani a cikin abokan shi yazo neman shi yana shigowa da kasa, shikuma bayaso ya taka kafar shi yaji kasa a cikinta ko ya take "Kai da za'a saka a cikin kasa Hamma wanne gudunta kakeyi kuma?" Bilal ya taba fada mishi, ya saka shi kwanaki maganar na mishi yawo, shisa ya daina cewa komai kan shigowa da kasar, amman zai iya sharewa sau goma, kuma da takalma a kafar shi in yana zaune, ko safa wasu lokuttan. Amman yau bashida wannan lokacin, Abdul kamar yanda yaji Bilal din na kira yaci karo da shi "Rayyan" Abdul din ya fadi cikin gaisuwa "Ka taimaka mun, Bilal bashi da lafiya" Rayyan ya fadi cikin wani yanayi yana dorawa da "Zan kai shi asibiti..." Cikin tashin hankali Abdul yace "Subhanallah... Bilal din? Yana ina?" Dan dazun nan suke maganar sun ga motar shi yayi parking, amman har daki Sulaiman yace ya kwankwasa yaji shiru ba ayi magana ba, kuma sun nemi wayar Bilal din a kashe, sunata mamakin inda ya shiga tun safiyar jiya, saboda shi din na mutane ne, kuma anyi wasan kwallo mai zafi, an lashe club din Barcelona da Bilal din yake bi, sunata neman shi ayi adawa. Amman shiru bai leqo su ba, har Abdul din yake cewa "Su fa yan Barca haka suke, in su suka ci su addabi kowa, amman basa daukar dabi duk idan aka cinye su" Anata dariya da fadin yanda Bilal ya san bambanci dabi irin na kwallon, da kuma yanda baya taba bari gardamar tayi nisan da zai zamana wani yaji babu dadi, in an matsa mishi da yawa yakan ce "Ai shikenan, ku bani panadol in watsa ko zanji dama-dama" Shikenan gardamar sai tazo karshe a kama dariya kuma. Kaf gidan babu wanda zaice ga rana daya da Bilal yayi mishi wani abu. Yanzun ma hanyar dakin su Rayyan ya nunawa Abdul da hannu yana juyawa. Har ya fara bin shi yayi tunanin kiran sauran yan gidan, in har yau Rayyan ya tsaya yayi magana mai tsayi da shi Bilal din na cikin yanayi sosai. Kafin kace me, kusan duk wanda yake gidan a lokacin ya fito sun nufi dakin su Bilal din har babu wajen da wasu zasu tsaya, Abdul da Rayyan ne suka kama shi, baima san duniyar da yake ba, daya daga cikin su ya dauki mukullin motar daya gani ajiye kan tebir suka fita da shi, sai dai su shidda suka iya tafiya asibitin duk kuwa tarin mutanen da suke son binsu. Motar babu waje, mutum biyune a baya, sai Bilal na ukku da suka saka a tsakiya. Har Rayyan daya shiga gaba zai kulle kofar yaga wani da zai iya kirga ranakun da magana ta taba hadasu ya kutso, dole ya matsa mishi ya shiga ya rufo suka tafi. Babu fadan da ba'ayi musu ba a asibitin, da yake na kudi kawai suka nufa a maimakon na makaranta. Nan da nan aka fara bawa Bilal din taimakon gaggawa, Rayyan yaso tsayawa cikin dakin, amman bayason yin gardama da likitocin a bata lokaci wajen bawa Bilal taimako. Daga shi sai Sulaiman aka bari dan sauran da suka tabbatar Bilal din ya samu taimako duk sai suka tafi, da zasu barwa Rayyan motar ya girgiza musu kai "Ban iya tuqi ba, ku tafi da ita kawai..." Yana kula da kallon mamakin da sukeyi mishi, babu dai wanda ya furta komai. Da gaske yau yaga ranar mutane da Bilal kan fada mishi, wajen dubu sha biyar aka bukata tashin farko, shi kuma dubu uku da dari biyune a jikin shi tunda jirgi ya biyo, sai dai jakar shi na goye a bayan shi har lokacin. Akwai kuma ATM din shi a ciki, kudin duk ya kwashe ya biya jirgi, sauran dubu takwas a ciki. Kafin yayi wani yunkuri ma su Abdul sun harhada kudin hannun shi, shima saiya kara da dubu ukkun aka bayar. Zaune suke a dakin shiru daga shi har Sulaiman din suna kallon Bilal, har sai wajen karfe tara na dare, Abdul shi kadai ya dawo, ya kawo musu darduma da kaya guda biyu dan su ya fara gani baisan kona waye a ciki ba. Harda brush ya dauko musu da McLean ya taho da shi. Tare suka mike da Sulaiman suna fadin "Allah ya kara sauqi yasa kaffara ne, zamu dawo da safe in shaa Allah" Kai Rayyan ya jinjina "Mungode...nagode sosai. Nagode" Murmushi Abdul yayi "Haba maza ai ana tare" Ya fadi suna danyin dariya, sosai Rayyan yaso yayi murmushi amman baya cikin yanayin. Kai kawai ya iya jinjina musu, suna ficewa daga dakin. Mikewa yayi shima ya shiga bandaki ya dauro alwala, magariba da isha'i yayi, yau Bilal kawai yaiwa addu'a ya tashi ya dawo yana jan kujerar sosai ya matsa kusa da gadon Bilal din "Me ya same ka haka Bilal?" Yayi tambayar a zuciyar shi yana sauke numfashi, saboda likita yace mishi jinin Bilal din yayi wani irin hawa. Har sai da yaji tsoro da yaga takardar. Kwata-kwata Layla ta makale a wani waje cikin kan shi saboda Bilal ya danneta, sai yanzun ne ta fado mishi, wani sabon tashin hankalin na dirar masa, watakila itama bata da lafiyar. Ya laluba wayar shi baiji ta ba, saiya kula cikin kayan da Abdul ya kawo harda wayoyin su shi da Bilal da cajar waya ya hado. Shikam zuwa yanzun baisan kalar godiyar da zai musu ba, sai dai in Bilal ya tashi shi zaifi sanin abinda ya kamata. Wayar Bilal ya tashi ya saka a caji dan yaganta a kashe, aikam cajin ne babu. Sai da yaga ta dauka sannan ya dawo ya zauna. Gwada lambar Layla yayi inda yai nasara ta shiga, har ta kusa yankewa sannan aka daga, wani irin numfashi ya sauke "Layla..." Ya kira daga lungun zuciyar shi, yanajin kamar yabi ta cikin wayar ya leqa inda take yaga lafiyar ta. "Layla..." Ya sake kira, muryarta can kasa ta amsa "Hamma" Lumshe idanuwan shi yayi yanajin yanda zuciyar shi ke rawa, nutsuwar da ta kwace mishi yake nema koya take, iya wadda zai samu karfin yi mata magana yaji inda ta shiga haka. Amman ya kasa samu "Hamma ban da lafiya" Layla ta fadi ta dayan bangaren, cikin wani mawuyacin yanayi da ya saka Rayyan din mikewa, sai dai ya kasa kara yin motsi saboda Bilal da yake gani a kwance shima, tunani yake ko akwai hanyar da zaibi ya raba kan shi gida biyu yabar daya anan asibitin dayan kuma yaje wajen Layla, dan sai yake jin kamar kuka take kokarin dannewa, zuciyar shi ciwo takeyi, ciwon daya kama ta nan take, dakyar ya iya cewa "Kina ina? Me ya same ki? Waye a wajen ki?" Ya kusa dakika biyar kafin ta amsa shi "Bani da lafiya Hamma..." Ta sake maimaitawa kamar bataji tambayoyin da yayi mata ba, wannan karin yaji sautin kukanta da ya kara mishi ciwon da zuciyar shi takeyi, dan baisan yanda zaiyi ba, baisan wa zai kira ya taimaka mishi ba. Ya bude baki zai sake yin magana ta riga shi da fadin "Anisa...muna asibiti tun da safe. Hamma kana ina?" Numfashi Rayyan ya sauke, a muryarta yake jin yanda take bukatar shi "Ina asibiti, Bilal ba shi da lafiya. Me yasa zaku min haka Layla? Ya kuke so inyi? Ya zakuyi rashin lafiya lokaci daya?" Ya karasa maganar yana bi da rokon yafiyar Allah dan yaji kamar yayi sabo, kamar yana kokarin dora ayar tambaya akan abinda basu da zabi a kai. Amman da gaske baisan yanda zaiyi ba "Ki ba Anisa waya..." Ya fadi muryar shi na fitowa da gajiyar da yake ji har cikin zuciyar shi "Hello..." Yaji muryar Anisa cikin kunnen shi "Anisa ya jikin nata? Me suka ce yana damun ta?" A nutse Anisa ta ce "Zazzabi ne mai zafi, sai sunce tana bukatar samun hutu saboda jininta ya hau, sun mata allurar baccine tun da safe, sai yanzun ba dadewa ta tashi, gashi na hada mata shayi zata sha, likita yace za'a karayin wata allurar dan ta kara samun bacci... Da sauki ba kamar yanda muka zo ba" Tunda ta fara magana yake saurarenta da dukkan nutsuwar shi, amman ya kasa gane yanda za ayi ace yarinya karama kamar Layla da yanzun ne zata cika shekara ashirin a duniya tana da hawan jini, ina ta samo shi? Tunanin me takeyi? Ko yace tunanin me sukeyi daga ita har Bilal da za ace suna da hawan jini haka. Lafiya kalau ya tafi yabar su duka, amman yanzun ya dawo lokaci daya duk sun kwanta. Gara Layla yaji muryarta, ta tashi, amman Bilal har yanzun ko motsi baiyi ba. A ina zasu sami hawan jini? "Nagode Anisa.. Dan Allah ki zauna da ita kafin gobe, ina asibiti wajen Bilal, shima bashi da lafiya" Ya karasa yana jin kirjin shi na zafi "In shaa Allah...Allah ya basu lafiya" Amsawa yayi da "Amin" Kafin ta mikawa Layla wayar "Hamma..." Ta kira shi tana saka shi jin kamar yayi fuka fuki zuwa inda take "Kiyi hakuri Layla, Bilal ko motsi baiyi ba har yanzun... Ba zan iya barin shi ba, ba zan iya barin shi inzo wajen ki ba, dan Allah ki kula da kanki, ki sha tea din idan Anisa ta hada, ki kwanta ki huta kinji" Muryarta da yake ji can kasa na kara taba shi, kamar bataji duk abinda ya fada ba, dan ta zabi amsa shine da "Ina son ka, wallahi ina son ka da yawa. Dan Allah karka barni, Hamma ina son ka" Ta karasa da kukan da ya saka shi fadin "Ina zanje Layla?" Dan tun daga dan yatsan kafar shi yake jin babu inda zashi yabarta. Baima san itace mutum na biyu mai matuqar muhimmanci a rayuwar shi ba sai yau, Bilal ne na farko, yau yasan matsayin Bilal ba zai taba haduwa dana kowa ba. Yana jin yanda zuciyar shi take zafi da rashin ganin Layla, amman awannin da suka wuce Bilal ya danneta a zuciyar shi da kan shi gabaki daya. "Ina son ka" Ta sake fadi, muryarta na isowa kunnen shi cike da firgici, baisan tsoron da take ji ba, amman ya taba zuciyar shi "Ina son ki Layla, watakila yaune rana ta farko kuma ta karshe da zan fada miki, saboda nayi magana mai yawa yau, ina tayi har yanzun. Amman ina son ki, ko da bazan fada ba, zan nuna miki, ina nuna miki, ke ce bakya gani" Ajiyar zuciyar da tayi na nutsar da wani abu a cikin kan shi "Mafarki nakeyi ko Hamma? Daya daga cikin mafarkina ne yau ma" Kai Rayyan ya girgiza mata, baisan soyayyarta na da yawa a tare da shi ba sai yanzun da yake jin kamar zata danne shi "Zan sake fadi a karo na biyu, sai ina ganin ki, kafin lokacin ki kula mun da kanki" Jin tayi shiru ya sa shi dorawa da "Zan iya yarda dake? Zan iya yarda zaki kula mun da kanki?" Shirun ta sakeyi sai sautin numfashin ta da yake tabbatar mishi da kuka take "Kasheni kike son yi Layla? Idan banji zaki kula da kanki ba abin zai mun yawa, dan Allah kiyi mun magana" Ya karasa yana kai hannu ya murza kirjin shi, inda zuciyar shi ke ciwo har kaikayi takeyi, amman murzawar baisa yaji kamar ya sosata ba "Eh" Ta fadi, kai ya jinjina ba sai ta tsawaita maganar ta ba "Idan kin kasa bacci sai ki kirani muyi labari, ki sha tea din yanzun kinji ko?" Bata amsa ba, amman yasan kai ta daga mishi, dakyar ya raba wayar da kunnen shi yana sauke ajiyar zuciya. Inda wayar Bilal take ya karasa ya kunna, yasan password din shi dan haka ya shigar, ya jira wayar ta gama kawowa, saboda Aisha ta fado mishi a rai. Yasan hankalinta ba'a kwance yake ba, kuma ba zata taba iya tako kafafuwanta gidan su ba, in dai yanda Bilal yake labarinta ne, yana da wannan tabbacin. Missed calls ya gani har guda sittin da bakwai, baibi ta kan su ba, lambar Aisha ya dubo, yana tura mata text "Rayyan ne, muna asibiti da Bilal bashi da lafiya. Amman da sauki. Idan ya tashi zai kira ki" Karantawa yayi yaga ko yayi sannan ya tura mata, kamar tana jira dan yana shiga tana dawo da amsa "Subhanallah, Allah ya bashi lafiya. Dan Allah daya tashi ya kirani, da safe zan kira sai in zo in gan shi" Har zai ajiye wayar saiya kula da tarin sakonnin da ta turo babu amsa, guda daya ya karanta "Dan girman Allah Nawan ka rufa mun asiri, dan Allah be ok be fine, dan girman Allah" Sai ta bashi tausayi, saboda yasan yanda firgicin nan yake "In shaa Allah daya tashi zan kiraki sai kuyi magana. Da sauki fa, kiyi bacci" Ya sake tura mata, wannan karin yana saka wayar a key, har zai ajiye kira ya shigo. Ya ga Ayya ce, zareta yayi daga jikin cajin yana dagawa "Bilal!" Muryar Ayya ta daki kunnen shi da wani yanayi "Ayya nine" Ya furta a gajiye, bakin shi harya gaji, tunda yake bazai tuna ranar karshe da yayi surutu mai yawan na yau ba, ya gaji da komai, so yake ko dan kwanciya yayi ko zai samu sauki. "Rayyan.. Ina Bilal? Me ya faru tun jiya nake kira ba'a dagawa? Gobe da sassafe in shaa Allah zamu taho Zaria... Yau babu hali, Abbun mu yace mu jira shi mu taho gabaki daya, saboda akwai taron da sukeyi da ba zasu bar shi ba a wajen aiki" Sai da ya bari ta gama yi mishi bayani, ya bude baki yaji tana fadin "Maryama! Maryama... Ga Rayyan na samu" Kamar zata fasa mishi dodon kunne, sannan tayi kasa da muryarta tana sake fadin "Ina Bilal din?" Numfashi Rayyan ya sauke "Gashi nan muna tare, bashi da lafiya. Muna asibiti, Layla ma bata da lafiya tana asibiti, amman waje daban daban" Yana jin salatin da Ayya takeyi tana kara wani "In shaa Allah gobe da sassafe zamu taho... Allah ya basu lafiya" Amin din a zuciyar shi ya amsa wannan karin yana sauke wayar daga kunnen shi hadi da kashewa. Ya jima anan tsugunne kafin ya iya mikewa yana komawa kan kujerar, jakar shi da take gefe ya dauka yana dubawa, ba shi da sigari ko daya, ya zuqe ta tas kuma bai samu damar siyan wata ba. Yana bukatar wani abu da zai dan nutsar da shi. Cikin magungunan Bilal da aka siyo ya duba, tunda duk yasan su, akwai sedative a cikin su kuwa. Budewa yayi yana ballar guda shida ya dauki ruwan da su Abdul suka kawo ya fasa ya shanye. Sauran maganin ya saka a cikin jakar shi, da safe yaje ya siyo wani yayi replacing da wanda ya dauka din. Badan yana jin bacci ba, ya dai dora kan shine a jikin gadon Bilal din dan yadan huta. Wayar shima a gefe ya ajiye. Yana son Layla ta huta, a lokaci daya kuma yana son ta kasa samun baccin dan ta kira shi ya kara jin muryarta, tunda ba zai iya kiranta ba gara yaji muryarta. Baisan iya lokacin daya dauka a haka ba, amman lokaci zuwa lokaci yakan tashi ya dora hannun shi a kirjin Bilal din yaji ko zuciyar shi na bugawa, sannan kuma ya kara duba wayar shi ko Layla ta kira baiji ba. Kan kunnen shi aka kira sallar asuba, kan shi yake ji yayi nauyi kamar an dora mishi dutse saboda kwanaki biyu kenan rabon shi da samun bacci, sosai ya so ya tambayi Bappa yanda yayi ya samu bacci, saboda magani guda daya yaga ya sha, kuma bacci yayi har asuba. Amman ya adana abinne a bayan zuciyar shi, duk idan ya samu wata dama zai san yanda zaiyi ya tambayi Bappa, ko a asibiti wajen karbar magani bai taba cin karo da wani ba, Bappa ne mutum na farko da ya gani akan Anti-depressant, duk da yasan akwai dubban mutane da matsalar depression, shi din dai ya fara cin karo da shi. Da tunani barkatai a kan shi ya daura alwalar asuba, dakyar ya iya tattara natsuwa ya kabbara sallah. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:07 PM - 111: 14 Dec, 2020 21 Su Ayya basu isa Zaria ba sai wajen bakwai da rabi, dan ma yau a karo na farko ta ga Abbu ya taka mota sosai. Wajen su Rayyan suka fara biyawa saboda Ayya, maganar farko da Abba ya fara bayan sun shiga dakin shine "Me yasa zaku kawo shi wannan asibitin? Baku san na makaranta yafi kowanne kyau a Zaria ba? Kuma sai yafi samun kulawa fiye da ko Ina" Kallon shi Rayyan yayi kafin ya sauke kan shi, saboda shi dai asibiti yasan Bilal yana bukata, ko da asibitin kauye aka kaisu a daren jiya in dai zasu iya bawa Bilal din wani taimako a halin da yake ciki zai barsu. Bai iya magana ba saboda kan shi da yayi bala'in nauyi, ga ganin Abbu ya kara mishi nauyin kan da yake ji ba kadan ba. Ayya kam bata bi takan Rayyan ba, kujera ta ja ta zauna kusa da Bilal tana tunanin a fadin duniya wanne ciwone zai kwantar mata da yaro haka "Bilal..." Ta kira da wani irin yanayi a muryarta dan tun suna hanya take tarbe hawaye, Abbu na kallon yanda lokaci zuwa lokaci take kai hannu tana goge gefen idanuwanta, gabaki daya hankalinta a tashe yake "Me suka ce yana damun shi?" Abbu ya sake fadi zuciyar shi na kara shiga cikin wani hali, dan shima bai taba ganin Bilal din ya kwanta ba "Bashi da lafiya Abbu" Rayyan ya furta dakyar, kyale shi Abbu yayi, duk da shikam daya ga Bilal din a zaune, zaije yayi magana a basu sallama su tafi asibitin makaranta gabaki dayan su. Amman a kwance yake da alamar bacci yakeyi. Mami ba damuwa da Bilal bane batayi ba, amman sun gan shi, ya kamata su karasa su duba Layla itama tunda tasan da wahalar gaske daga Rayyan har Ayya subar gefen Bilal din "Bacci yake?" Ayya ta tambaya tana kallon Rayyan da ya dan daga mata kai kawai. Gabaki daya zaman Abbu a dakin ya takura mishi, kan shi harya fara dawowa da ciwo. Wani abu yake tsikarin shi daya fita yabar dakin har sai Abbu ya tafi, amman saboda Bilal ba zai iya matsawa ko nan da can ba. Mami bata ce komai ba, saboda duk wata tambaya da zatayi su Ayya sun rigada sunyi. Rayyan din ba gaishe da su yake ba sai ta kama, zata iya haduwa da shi ya sadda kan shi kasa, ko yayi tsaye in da yake kan nashi a kasa har saita wuce sannan ya tafi inda zaije shima. Kuma tun ranar da ta gansu da Layla sai ta kula kamar ya kara nisanta da ita. Ba abin bane ya dameta, amman batason kowa ya kullace ta, Ayya ma dan babu yanda zatayi ne shisa suke wannan zaman doya da manjan. Amman iya soyayyar da zata iya nuna musu a lokacin shine a tsawatar musu. Idan basu fahimceta yanzun ba, wata rana zasu fahimce ta. "Maimuna kina nan ne? Mu dubo Layla?" Dan juyawa Ayya tayi ta kalli Abbu, sannan ta sake mayar da dubanta kan Bilal. Bata zaton akwai wani abu da zai faru wanda zai saka zuciyarta taso Layla, yarinyar batayi mata ba tun daga ranar farko da ta dora idanuwanta a kanta. Ta kara girmama tsanar da take mata daga lokacin da Bilal ya fara raba lokuttan shi tare da yarinyar da kuma Mami, har yana shiga bangaren su. Sai kuma take kara ganin yanda Rayyan yake bata lokacin shi cikin yanayin da ko ita bata samun shi. Babu wani abu da zai sa taji yarinyar a ranta, bata sonta, in zata iya nisantata da duka yaranta zatayi. Amman rashin lafiya ce, batama san dan ance Layla bata da lafiya zataji wani abu ba. Ganin yanda take tunani yasa Abbu fadin "Ki zauna tare da Bilal din muje mu dawo" Kai ta jinjina ma Abbu da ya saka hannu a aljihun shi, dubu hamsin ce ya cire ya taho da ita ko da zasu bukaci wani abin, talatin ya kirga ya bawa Ayya da fadin "Ko da za'a bukaci wani abu" Zuciyar shi a jagule take, ba zai kara jagula yanayinta ba ta hanyar bawa Rayyan kudin da yasan da wahala ya motsa daga inda yake ballantana ya saka hannu ya karba, sai yaga Rayyan yake tuna yanda yake son sakawa a tayashi a addu'a akan matsalar Rayyan din, ko da Nasiru ne yayiwa zancen, amman kamar wanda ake shafarwa kwakwalwa sai ya shirirance, sai ya sake ganin Rayyan din tunanin maganar ya dawo mishi, numfashi mai nauyi ya sauke yana juyawa, Mami na fadin "Allah ya kara sauqi ya bashi lafiya" Kafin ta juya tabi bayan Abbu suka fice daga dakin. Ayya kuwa Rayyan ta kalla, idanuwan shi duk sun shige ciki, bata ga sunyi ja ba balle ta alakanta abinda take gani a cikin su da rashin bacci, amman yayi duhu ya kuma fada da alamun rama "Yaushe rabon da kaci abinci?" Numfashi ya sauke "Na ci abu jiya da rana..." Mikewa Ayya tayi, bai tambayeta in da zataje ba, ya gaji, a gajiye yake jin shi. Kan shi da kirjin shi kamar akwai wani a cikin su daya danne. Ga son ganin Layla da kewarta da suke nukurkusar shi. Ba zaice ga mintina nawa Ayya tayi a waje ba, amman da leda ta dawo, lemukane ta siyo na robobi sai kuma biskit. "Ka zo ka dauka" Tace mishi, tsaye yayi yana kallon lemukan, kafin ya kalli Ayya, kamar yana son sanin lokacin da ta kula, ko ya akayi ta sani "Ka zo ka dauka Rayyan, na san bakacin abinda baka san inda ya fito ba, Bilal ya fadamun" Ta karasa maganar da wani yanayi a muryarta, duk wani kusanci da yake tsakaninta da Rayyan, wanda ya kamata ace yana tsakanin uwa da danta, ta same shine a sandin Bilal. A cikin labaran shi yakan fada mata abubuwan da Rayyan yake so da wanda bayaso, yanayin shi da duk wani babba da karamin abu da yake tunanin zata bukaci ta sani, ko kuma zata so ta sani din. Ko waya sukayi saiya fara bata labarin yanda ranar Rayyan din ta kasance, sannan zai bata labarin ta shi ranar "Rayyan ma yau yayi lakca..." Ya kan fara fadi bayan sun gaisa ko yace "Sai da muka tsaya wani shago yau da muka fita da Rayyan ya siyi biskit, kin san halin shi ba cin wani abu yake a waje ba" Ya kan karasa maganganu irin wannan da dariyar da kan sakata yin dariya itama. A fadin duniyar ta Bilal daban ne, Bilal ya kan fahimci damuwarta a lokuttan da Abbu bai gane ba. Shisa hankalinta ya tashi, ta kasa samun natsuwa duk yinin jiya har zuwa safiyar yau, bacci ma sai dai tace barawo, da kuma ya fisgeta take farkawa saboda mugayen mafarkan da bata tunawa da suke addabarta suna sake sakata jin kamar wani abu mai girma ya sami yaranta. Rayyan daya karaso ya saka hannu ya dauki coke tabi da kallo, biskit din kwara daya ya dauka. Bata ce mishi don me ba. Tana ji da Bilal ba zata biye Rayyan ba, yana da girman da yasan cikin shi na bukatar abinci ko da bakin shi bayaso. Batayi mishi magana ya zauna ba, tana kallo yaja kujera ya zauna. Suna nan su Abdul suka biyo, sosai Ayya ta jinjina karamcin su, sun siyo su Maltina da ruwa sun taho da shi. Ta kuma yi mamakin ganin Rayyan ya gaishe su, yana kula da kallon da takeyi mishi, ko da yabar Zaria su Abdul na cikin jerin mutanen da ba zasu taba mantuwa a zuciyar shi ba, sun mishi kirkin da bai taba tsammani ba a lokacin da yake cikin tsananin bukatar taimako "Ka gaisa da kowa a mutunce ko baka so Hamma, ko mutuwa kayi kafin a kira su Ayya su din nan da muke waje daya zasu fara sani" Bilal kan fadi amman bayajin shi, saboda yana ganin gaisuwar kanta a matsayin takurar sosai, gashi sai su dinga gaisawa da kai da sassafe hannun su duk ruwan da baisan kona menene ba. Yanzun kam in sun gaishe shi zai amsa ko da bayaso din, in yaso ya wanke hannun shi da sabulu kamar yanda yakan yi. Sai bayan sun tafi Ayya tace "Abokan ku suna da kirki" Kai Rayyan ya girgiza mata "Abokan Bilal ne, gida daya muke..." Saboda shi yasan ba abokan shi bane ba, ya san ko da suka taimaka mishin dan Bilal sukayi. Kai kawai Ayya ta jinjina, ta dan gyara zamanta kenan taga Bilal ya motsa. Sake motsin yayi yana jin shi kamar wanda yayi tafiya mai nisan gaske zuwa wani waje, aka kuma dauke shi aka cillo da karfin gaske. Idanuwan shi da sukayi nauyi yake kokarin budewa a hankali saboda haske yayi mishi yawa. Yayi kokarin bude su yakai sau biyar kafin ya samu ya bude su gabaki daya "Bilal..." Yaji an kira cikin muryar da ta saka shi juyar da kan shi a hankali ya kalli Ayya, bakin shi yayi nauyi balle ya kira sunanta "Bilal" Ta sake fadi tana sauke numfashin da batasan tana rike da shi ba. Idanuwan shi ya mayar ya runtse, komai na dawo mishi cikin yanayin da y saka yan hanjin shi yamutsawa cike da sabon tashin hankalin daya dirar mishi. Ko su Ayya har sun sani ne shisa suka zo, da wanne ido zai kalle su, ta ina zai fara amsa tambayoyin su, dakyar ya iya sake bude idanuwan shi yana bin hannun shi da kallo, yaga karin ruwan da saura kadan ya kare, sosai yake karewa dakin kallo yana gane tabbas a asibiti yake, kamar sama-sama yaji muryar Rayyan, da ido ya lalubo Rayyan din da yake zaune kan kujera yana kallon shi "Hamma" Ya furta muryar shi a hankali, amman Rayyan din yaji, fuskar shi ya saka cikin hannuwan shi yana wani irin sauke numfashi. Allah kadai yasan halin da yake ciki tun shekaranjiya, musamman jiya kuma zuwa safiyar yau. Komai karfin hali yake, sanin Bilal na da rai baya nufin hankalin shi ya kwanta tunda bai ga ya motsa ba. Wata natsuwa ce take dawo mishi, ya kai dakika biyar kafin ya bude fuskar shi yana mikewa ya karasa in da Bilal din yake "Bilal?" Ya kira cike da alamar tambaya, duk da idanuwan shi a bude suke, yana son ya kara tabbatar da cewa da ya tashin "Hamma" Cewar Bilal, wani numfashin Rayyan ya sake fitarwa, da wani yanayi a fuskar shi ya ke kallon Bilal "Karka sake tsoratani haka, Bilal karka sake tsoratani haka..." Ya karashe maganar yana sake sauke numfashi, sai da yaga Bilal din ya dan daga mishi kai tukunna ya juya, hanyar kofa ya nufa yana budewa ya fita, hadi da ja musu kofar ya rufe. Anan bakin kofar ya tsugunna yana wani irin mayar da numfashi kamar yayi gudu. Godiya yakewa Allah da duk wani yare da yake fahimta, da zai iya kuka tabbas zaiyi na saukin da ya samu lokaci daya haka. Ya kusa mintina  biyar anan tsugunne kafin ya iya mikewa, kujerar da take ajiye irin na karfen nan ya zauna kan guda daya. Hutawa yakeyi yasan Ayya da Bilal labari zasu fara, yanda kan shi yayi nauyi sosai zai takura. Yana nan zaune Abbu ya dawo "Ya mai jikin? Har ya tashi?" Abbu ya fadi, kai Rayyan ya jinjina mishi, harya karasa ya murza kofar Rayyan yace "Ya Layla? Abbu ya take?" Dan juyowa Abbu yayi "Taji sauki, na barta da Maminta ma, abinci take ci sanda na fito" Kai Rayyan din ya jinjina zafin da kirjin shi yakeyi yana yin sauki. Da Mami ta biyo Abbu sun dawo zaije wajen Layla. Amman yasan Mami batason shi a kusa da Layla, saboda haka zai jira sai ta tafi, zaiyi wannan hakuri. Wayar shi dai ya zaro daga aljihu yana tura mata sako "Baki kirani ba da kika ta shi" Yana shiga tana dawo mishi da amsa "Sai da su Mami suka zo na tashi Hamma, naji sauki. Ya Hamma Bilal?" Numfashi ya sauke "Ya tashi yanzun shima. Allah ya baku lafiya. Ki kula da kanki, zan zo in ganki anjima" Har yana shirin mayar da wayar aljihun shi yaji sako ya shigo "Ina son ka Hamma" Murmushi yayi, abinda ya kwana uku rabon da yaji ko alamun shi, sosai murmushi yayi har hakoran shi suka bayyana, a hankali wani sanyi yake sauka cikin kirjin shi, sake karanta sakon da ya zauna a kwakwalwar shi yayi saboda yana jin muryarta a cikin kan shi inya karanta daga wayar. Ya jima kafin ya iya mayar da wayar aljihun shi, ya kasa daina murmushi. Yanayin da yake ciki bayason ya bar shi, zaiso ace kullum yana cikin yanayin, kafin yayi mata magana tunanin fita ya nemi sigarin da zai sha yakeyi ko zuciyar shi zata kara rage zafi. Amman yanzun yaji baya bukata, dutsen da yake danne da kirjin shi ya daga da kalaman Layla. Hamma yayi alamar baccin da yanzun yake jin alamun shi, amman bashi da halin kwanciya. Natsuwa ce ya samu shisa ma har baccin ya samu zuwar mishi. * Bacci ta sake komawa bayan tayi sallah, babu ciwon kan, sai zazzabi kadan da kuma duniyar da batajin dadin ta. Ta so ta dan watsa ruwa amman batajin karfin jikinta. Sai kuma lokacin Anisa tace zataje ta dawo, sanda ta dawo ta soyo mata kwai ta taho da ruwan zafi da kayan shayi data kullo su a ledoji. Sai kofi da cokali. Layla ta san tana da lakca shisa ta matsa mata ta tafi "Baki ga naji sauki ba, kinga an fara test, ana iya yin wani babu tsammani, kuma idan akwai wani abin zan kira wayar ki ai" Bataso tafiya ba "Dan Allah ki tafi, ni bacci ma zan koma" Sai da ta ga Layla din ta juya kwanciya da yake tun wajen karfe hudu da aka cire mata ruwan daya kare sai suka barta ta huta. Tafiya Anisa tayi don tayi shirin tafiya aji. Lokacin ne wayarta ta soma ruri, ganin Abbu a rubuce yasa cikinta hautsinawa, sabon zazzabi na dirar mata, amman idan taci gaba dakin daukar kiran su hankalin su zai tashi fiye da yanda tasan ya tashi. Batayi magana da Bilal ba, amman idan yaji zabinta na barin komai daya faru a tsakanin su tasan zai amince. Ta san boye komai shine saukin su, in ma sunce zasu fada ta ina zasu fara? Kuma jiya Rayyan yace yana son ta, shi ya saukar da zazzabinta ya rage ciwon kan da takeji, ya rage kusan rabin damuwarta, shi ya bata kwarin gwiwar daga wayar Abbu har tana amsa sallamar shi "Layla... Ya jikin naki?" Numfashi ta sauke, kenan sun san bata da lafiya, tana da tabbacin Rayyan ne ya fada musu "Da sauki Abbu, ina Mami?" Ta tambaya "Gata nan tana jinki, yanzun zamu karaso ma, muna Zaria" Mikewa zaune tayi wata irin zufa na karyo mata, kanta take kallo tana neman alamun da zasu iya nunawa Mami wani abu ya faru da kuma yanda zatayi ta boye "Hello..." Abbu ya fadi jin tayi shiru "Sai kun karaso Abbu" Tayi maganar tana mamakin yanda akayi muryarta bata rawa. Sauke wayar tayi daga kunnenta, tabbas idan bata saita nutsuwarta ba Mami zata gane akwai wani abu, karyar da zatayi take nema amman gabaki daya kanta ya kulle, tana nan zaune tana tunani sai ganin su tayi sun shigo. Wani kukane yake neman taso mata da ta hango Mami, saboda a tsayin rayuwarta Mami ce komai nata, duk da Abbu ya zame mata mahaifin da ta rasa, Mami daban take, ko da tana cikin damuwar da bata taka kara ta karya ba haka takan shige jikin Mami tana mata sangarta, Mamin kuma zata biyeta ta lallasheta a wasu lokuttan in ta kula da gaske akwai damuwa a tattare da ita. Yanzun ma kasa daurewa tayi, suna karasowa ta zagaya hannuwanta tana rike Mami, hawaye masu dumi na zubo mata, numfashi sosai Mami ta sauke tana samun natsuwa da taga Layla din, dagota tayi daga jikinta tana zama gefen gadon "Menene na kukan kuma? Ai gamu mun zo" Mami ta fadi muryarta na rawa, har cikin ranta take godewa Allah da yasa babu abinda ya sami yarinyarta. Jikinta ta taba tanajin da zazzabi "Kin ci abinci?" Kai Layla ta girgiza tana share hawayen da yake fuskarta "Gashi Anisa ta kawomun shayi" Abbu ta kalla "Abbu" Murmushi yayi "Sai yanzun kika ganni?" Dariyar karfin hali Layla tayi, amman tanajin yanda wani abu yake budewa a cikin kirjinta. A lokutta da dama na rayuwarta ta saka kafa tayi fatali da duk wata tarbiya da suke dorata a kai, saboda tana ganin a kasan kaunar su akwai rashin wayewa, akwai dogon bambancin da take gani tsakanin yanda sukayi tasu rayuwar a baya da kuma yanda rayuwa take tafiya yanzun. "Babu wani abu zamani Jabir, duniya bata canzawa, mutanen cikinta ne kawai suke canzawa, bambancin yanda mukayi tamu rayuwar da yanda ku kukeyin taku yanzun shine zabi..." Mami ta taba cewa Jabir sanda yake mata maganar cewa zamanin su da kuma na yanzun daban ne, sun jima suna dariya bayan Mami din ta tashi, a ganinsu ba zata taba fahimta ba, ashe sune basu fahimceta ba, akwai tarin ma'anoni a kalamanta, ko kan maganar kaya da take yawan yiwa Layla din, ta dauki shekaru tana mata fada da nasiha a kai sai yanzun take kallon abin da kalar idanuwan da Mami ta ke taso ta duba. Abubuwa da damane suke ta mata yawo. A cikin abinda ya faru a kwanakin nan biyu ta daina kokarin gane ya akayi abinda ya faru ya faru, saboda bata da wannan amsar, ta dai san babu tirsasawa a al'amarin saboda rudanin da take ciki shi Bilal yake ciki. Abu biyu zuwa ukku ta sani a yanzun, kafafuwanta ta dauka taje gidan su Bilal, da ta tura taga basa nan zata iya juyawa kamar yanda Rayyan ya taba balbaleta da fadan shi harda rankwashi da ta kai musu abinci taga basa nan ta zauna tana jiran su. Yana shiga ya ganta ya rankwasheta yana kama hannunta, dakyar ya bari ta saka takalma "Idan kika ga bama nan karki kara zama, baki da hankali ke kam sam ko? Baki san maza bane kawai a gidan? Karki kara zuwa ki zauna idan ni ko Bilal bama nan, dakin tura dakin ki juya ki tafi gida, kina jina?" Harya rakata bai daina fada ba, da tabi maganar shi, tunda ko suna nan din baya bari ta zauna. Tana shiga zai mike, shisa ta daina sallamar masu abin hawa. Ko a ranar dan tana tsammamin zata same sune, shisa ta sallami mai napep din. Tunda tana son taga tafiyar Rayyan din in yaso ita da Bilal sai su koma makaranta. Amman da ta juya da taga basa nan, da ta janyo dakin ta juya, sai ta zabi ta shiga ciki harta zauna. Idan Mami taji tana da yakinin tambayar farko da zatayi mata shine "Me kikaje yi gidan su Rayyan?" Kuma bata da amsar wannan tambayar, uzurin duk da zata bayar a cikin kanta ma bamai karbuwa bane ba. Akwai abubuwa da yawa da ta fahimta yanzun, abubuwan da take dauka a matsayin takura da batasan kariya bane a wajenta. Tun jiya take daukar alkawurra kala-kala, ciki harda sauraren duk wani abu sa Mami zata fadi da kuma yin aiki da shi, dan taga alama maganganun na da karfin kareta daga abubuwa da dama. Da ta saurare su da bata zo inda take yanzun ba, amman tana jin kamar lokaci bai kure mata ba. Ganin Mami din ya sa duk ta kara jin karfin ta ya karasa karewa. Ita ta taimaka mata taje bandaki ta kara kuskure bakinta suka dawo, likita ne ya shigo yin round da yake dakin su hudune a ciki, akwai dai yar tazara tsakanin wani gadon zuwa wani, kuma akwai wasu gadajen da babu kowa, su Abbu fita sukayi sai da aka gama sannan suka dawo. "Wai idan naci abinci sai a kara sakamun ruwa yace, zan kara kwana sannan su sallameni" Kai Mami ta jinjina mata, tana daukar kofin da yake cikin kwandon da Anisa ta kawo. Shayin ta hada mata tana dauko yar kular ta bude mata wainar kwan, ta fara cine Abbu yace "Bari in koma wajen su Bilal in kara ganin ya nashi jikin tun da ita ta samu" Kai Mami ta jinjina "Kayi mishi sannu" Dubu sha biyar ya kirga ya bata yana barin biyar a jikin shi, karba tayi hadi da yin godiya, ita da Layla suna mishi addu'a da bada sakon yiwa Bilal din sannu da jiki. Daurewa Layla tayi ta shanye shayin tas, wainar kwance ta kasa cinyewa, karfin hali takeyi kar Mami ta fahimci wani abu, hira sukeyi a hankali, har akazo aka kara mayar ma da Layla ruwan, da yake an saka allurai a ciki, baccine ya dauketa. Mami na nan zaune Anisa ta dawo, gaisawa sukayi ta wuce da fadin zata dora girki "Kina ta shan hidima, idan akwai waje me kyau ki siyo kawai Anisa" Mami ta fadi tana bata dubu uku, tasan duk tsadar abincin dai nasu su uku ba zai wuce dubu dai-dai ba. Karba Anisa tayi dan kuwa da gasken a gajiye take jinta. Saida tayi sallar azahar sannan ta dawo, tana kawo musu nasu sallama ta kara yiwa Mami saboda tana da wata lakca har karfe hudu. Har tana saka Mami yin tunanin ya za'ayi yara ba zasuyi rashin lafiya ba da wannan zirga-zirgar da sukeyi. Ga shi saika dawo daga daukar darasi zaka fara neman abinda zakaci "Kullum daman sai kun dawo sannan kuyi girki?" Ta tambayi Layla cike da damuwa bayan ta tashi, dariya Layla tayi "Muna ci a cikin makaranta, mun mafi yin abincin dare dai, ko da safe mu girka kafin mu fita idan babu lakcar safe" Numfashi Mami ta sauke, babu wani abu a karatu nesa da gida banda wahala a nata ganin, saboda idan a gidane zakaje ka koma kuma ka sami abinci a girke, shisa duk in suka dawo sai taga sunyi zuru-zuru. Ayita maganar wahalar karatu ce, nan kuwa harda kujuba kujuba da rashin samun abinci akan lokaci "Kinga da kinyi zamanki BUK kikaqi" Murmushin Layla tayi mai ciwo, saboda a karo na farko maganganun Mami din sun zauna mata, da ta zauna a BUK din abin nan da bai faru ba, saboda ina taga Bilal din ma in ba hutu ya dawo ba? Batason tsaurara tunani a kai har mami ta fahimci akwai wani abu "Kai Mami, baki ga su Hamma ba har sun gama, sauran fa sati uku a fara jarabawa...da an dawo an karayin wata nima aji uku zan shiga" Kallonta Mami tayi "Babu in shaa Allah kamar kece da rayuwar" Dan murmushi ta sakeyi "In shaa Allah" Ta fadi tana saka Mami fadin "Hmm..." Kawai saboda ganin Layla ya nutsar da ita, amman akwai wani yanayi da zuciyarta take ciki wanda ta kasa fahimtar shi, watakila yana da alaka da kalar rashin tarbiyar da ta dinga cin karo da shi tunda ta shigo makarantar, yarane kala-kala, wasu matan kallo daya zakayi musu daga fuskar su ka gane yaran hausawa ne kuma musulmi, amman shigarsu tayi hannun riga da wannan, ga shi sai rike juna suke da maza kamar hakan bakomai bane ba, ga gungun dalibai duk an jera an taho tare anata hada kafadu da sunan za'a tafi aji. Addu'ar duk da tazo bakinta yinta takeyi, bataje jami'a ba, tana jin labari kala-kala da yake tattare da jami'a dai. Amman taga yaran da suka shiga cikinta suka fita kalau, yaran da suka tsallaka kasar ketare sukayo karatun su batare da tarbiyar su ta sami tangarda ba, hakan baya nufin kowa ma zai kasance a haka, idan babu rashin ji kacokan na yaro, akwai mugayen abokai da tasirinsu mai girma ne. Illar jami'a zatayi dai-dai da rashin illarta idan ma illar batayi rinjaye ba kenan. "Allah ya shirya mana, Allah ya tsare mana" Shine abinda taita furtawa sanda suke hanya. Kusan har karfe shidda suna garin Zaria. Sosai Mami taso tafiya da Layla, amman taqi "Nafa ji sauki Mami, kuma mun kusa fara jarabawa mu dawo gida hutu gabaki daya" Abbu kuma ya goya mata baya da fadin "Nan da kwana biyu sai mu kara dawowa mu kara duba su" Zuciyar Mami ta kasa nutsuwa, Ayya ma dakyar Abbu ya rabota da asibitin bayan sunje daukarta. Can ma suka sami Aisha da wata kawarta sun zo duba Bilal din sunyo abinci sun kawo. Abbu najin labarin Aisha a wajen Ayya, amman yaune ya fara ganinta, yarinya ba dai kunya ba, dan dakyar ta gaishe da su, ko sallama batayi ma su Bilal ba suka fice suka tafi. Sai da suka jira ta karbi lambobin abokan Bilal din, tana tunawa Mami da cewa itama zata saka Layla ta tura mata lambar Anisa. Haka suka bar garin Zaria da rashin nutsuwa daban da wanda suka shigo garin da shi. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:07 PM - 111: Dec 17, 2020 22 "Shiru-shiru halina ne Bilal, shisa naka yake mun yawa a kwanakin nan" Rayyan ya fada mishi, yasan baiyi maganar dan yana jiran amsa ba, ya fadane kawai saboda abinda yake ran shine. In da ya tsammaci amsa ne Bilal din bashi da abin cewa, shiru-shirun da yakeyi ba zabi bane ba, dole ce ta saka mishi. Ya kanji mutane sunyi maganar tsoro, sunyi maganar kwana cikin firgici, yanzun ya gane ma'anonin kalaman su, baccin kirki baya samu sosai. A tsorace yake al'amuran shi, ko kallon shi yaga Rayyan ya cikayi sai yaga kamar yana zargin akwai abu mai girma da yake boye mishi, kamar yana so ya gane cewa yaci amanar shine. Sanda duk zaiyi waya da Abbu sai zuciyar shi ta doka, muryar Abbu yanzun batayi mishi komai sai kara gigita mishi lissafi. Hirar su da Abbu batayin tsayi, saboda a kagauce yake daya sauke wayar kafin ya fadi abinda baiyi niyya ba. Yana fadama kan shi maganar da Malamai da yawa sukayi a kaine na boye zunubi irin wannan, saboda bayayin komai sai yada rikici da haifar da shakku a zukatan mutane, in dai har ranka zaka tuba saboda Allah, zaka kiyaye sharuddan tuban, to kayi shiru shine mafi alkhairi, Allah ya sirranta zunubinka ne saboda dalilai da dama. Har wa'azin ya lalubo ya saka a wayar shi ko zai saukaka mishi jin nauyin amanar daya ha'inta da yakeyi. Kwanan shi biyu a asibiti aka sallame shi, duk yanda Rayyan yayi mishi maganar ya huta kafin ya koma makaranta sai ya kasa. In ya zauna baya komai sai tunani, zuwa makarantar na rage mishi tunani, yakan yi kokari sosai wajen mayar da hankalin shi kan lissafin da akeyi. Sai da aka hada sati daya a hakan, kafin ya dauki wayar shi yaga shigowar saqo, ya dauka Aisha ce, dan itace comfort din shi a wannan lokacin, har tausayin damuwar da yakan gani a cikin idanuwanta yakeyi, damuwar da yake da yakinin shine silarta "Nawan wani abu na damun ka, nasan zaka fada mun inda zaka iya. Amman bana so wallahi, ko menene yake damun ka yana mun ciwo a zuciyata saboda bansan me ya kamata inyi in taimaka maka ba" Murmushi ya iya yi mata, duk wani abu da zatayi domin shi tana comforting din shine, a lokaci daya kuma tana saka shi jin yanda da duk dakika bai kyauta mata ba itama. Kamar yaci amanar duk tarin kaunar da takeyi mishi. Shisa yake ta wasa da wayar a hannun shi, bai bude ba, jiya ya kasa zuwa ya ganta, ta kira shi da daddare bai daga ba, kuma baibi kiran ba da safiyar ranar, sai ya dauka itace tayi mishi sakon a lokacin, ya fi mintina goma yana tararrabin budewa, sai daya duba yaga sunan Layla sannan wani abu ya tsirga mishi. Tun da akayi abin bai yarda ya sakata a idanuwan shi ba, baisan ta inda zai fara ba. Jikin shi na rawa ya bude "Bansan me zance ba Hamma, bansan me zan fada maka ba, har raina ina so in dora laifin komai a kanka ko zan samu sauki, amman na kasa, saboda kana daya daga cikin mazan da suke a rayuwata da nake da tabbacin ba zasu taba cutar dani ba. Har yanzun ina cikin rudani, ban san ko abinda zan fada ya kamata ba, ina so in roke ka, dan Allah karka fada idan kayi niyya, sirrin mu ne mu biyu, kowa zai iya zabar abinda zaiyi da na shi nasani, amman shirun ka shine kariyar karshe da zaka bani. Martabata ce akan layi idan kayi magana, mu manta idan zamu iya, dan Allah ina rokon ka. Ka goge idan ka karanta" Ya karanta yafi sau goma, yana shirin gogewa ne wani sakon nata ya shigo "Zamu raba laifin abinda ya faru Hamma, karka dauka duka kai kadai" Wata irin ajiyar zuciya ya sauke da baisan daga inda ta fito ba, duk da bata sauke nauyin da yake ji a kirjin shi ba, ta bude wasu hanyoyi da suka toshe mishi. Ya kasa bata amsa daga lokacin har zuwa yanzun, ya dai goge sakonnin kamar yanda ta bukata. Bashida kwarin gwiwar hada idanuwa da ita, har yanzun idan ya kwanta bai daina addu'ar farkawa ya ga komai ya kasance mafarki ba. Sai dai da duk ranar da zata wuce da yanda gaskiyar komai da ya faru yake kara zauna mishi. Babu abinda yake kara mishi nauyi sai kallon Rayyan a duk rana, musamman yanda yake ganin damuwa a idanuwan Rayyan din, sosai yake son ya koma dai-dai, ya manta abinda ya faru, amman ta ina zai fara idan yanajin amanar mutanen daya kamata ya roka gafara tana danne shi? Idan yana jin kamar yana yawo da hakkin da zai iya mutuwa da shi rataye a kai a kowanne lokaci? Gabaki daya dan karfin da ya rage mishi ne ya tattara akan karatun shi ko zai sami sauki. Musamman yanzun da aka fara jarabawa, sosai karatun yake zamar mishi wata hanyar da zaiyi amfani da ita wajen kaucewa wasu tunane-tunane. Yau dai tazo mishi daban, bashi da jarabawa, shisa yace zai kai Rayyan din Kaduna inda aka kaishi don fara bautar kasa. Tunda yake shiri sai ranar take ta dawo mishi da abubuwa da dama, kamar ranar da Rayyan zai tafi Bauchi haka yake jin shi. In da duk yayi nan Rayyan da yake zaune yake bin shi da kallo. Tun suna asibiti yake kula da Bilal din, kamar akwai abinda yake damun shi fiye da jinyar da yakeyi "Tunanin me kakeyi? Menene? Bilal jinin ka ya hau... Me ka sa a ranka da ban sani ba" Ya tambaye shi, amman shiru Bilal yayi yana kasa hada idanuwa da shi "Aisha ce?" Ya sake tambaya, kai Bilal ya girgiza mishi, ganin kamar a takure yake sai ya kyale shi. Saboda yana ganin bashi da lafiya, bai kamata ya takura shi da yawa ba. Ya yarda da Bilal, ya kuma san halayen shi, idan har ya kamata ya sani zai fada mishi. Sai dai kwanaki sunata tafiya, damuwar Bilal din kuma gani yake tana kara yawa, har makaranta ya shiga yaje department din su Bilal yayi tsaye a bakin ajin su, da yaga ya fito sai da dariya mai sauti ta kwace mishi "Me nake tunani?" Ya furta yana girgiza kai, nan ba sakandire bace ko ma yace firamari da zaiyi tunanin ko wani ne yake takurama Bilal din harya shiga damuwa. Amman ya rasa me ya kamata yayi tunani, abin na damun shi. Haka suka jera tare suka koma gida, kowa da tunanin da yakeyi a ran shi. Yana kallon Bilal, kusan shi kan shi a darare yake da Bilal din, ko abinci ya karbo musu wajen Aisha, ko shi Layla ta kira shi yaje ya karba in ya kawo sai ya taba Bilal sau goma kafin su gama ci saboda yanda yake tafiya duniyar tunani, kamar yakan manta cewa yana cin abinci ne sai ya tuna mishi. Layla ma yana ganin kamar akwai abinda yake damun ta, baya jure kallon idanuwanta ne, a yan lokuttan daya kalla din, a kasa tsoron da suke bashi akwai damuwa shimfide a cikin su, sai yake ganin kamar harda tsoro da wani abu da ya kasa fahimta. Randa yaje ganin ta, sosai zuciyar shi take cike da soyayyar ta, haka yasa shi kai hannu don ya taba fuskarta, ba dan yana son tabata din ba, so yake yaji ko da sauran zazzabi su koma asibiti, amman yanda ta janye jikinta tana kallon shi da wani irin firgici shi kan shi ya tsorata "Ina so inji ko da zazzabi ne a jikin ki har yanzun" Ya fadi da sauri, amman zai rantse jikinta bari yakeyi, yaso ya rike ko da hannunta ne ko zata natsu, amman kai take dinga girgiza mishi "Naji sauki, babu zazzabin Hamma, babu" Ta furta, kai ya jinjina yana kallon ta, har sai da yaga ta dan nutsu tukunna "Menene?" Ya tambaya can kasan makoshi "Bakomai" Ta amsa cikin sanyin murya "Layla..." Dago kanta tayi, amman ta kasa hada idanuwa da shi "Ban san me yake damun Bilal ba, ba zan iya hadawa da taki damuwar ba, ki fadamun idan akwai wani abu..." Kai ta sake girgiza mishi. Bai matsa mata ba, haka suka cigaba da zama shiru, saboda yana bukatar zama a kusa da ita. Amman ita ba kamar Bilal ba, tana dariya, tana mishi hira kamar ko da yaushe, amman yana kula da yanda take barin space a tsakanin su duk idan zasu zauna, yanda take tabbatar akwai wani abu a hannunta idan suna tafiya, dan kar ya kama hannunta, yana kula da duk kananun canjin da yake tunanin kalmar son daya furta mata ce ta saka shi a tsakanin su. Bai damu ba, yana son ta ya sani, ya riga da ya fada yana son ta. Tun kafin ya fada mata yasan ita din tashi ce, idan bata rike hannun shi yanzun ba, zata rike nan gaba. Abu daya ya sani, hannun shine na farko kuma na karshe da zata taba rikewa a rayuwarta. Yana da wani irin kishi da akanta ne ya fahimci hakan, musamman yanzun, ko ganinta yaje yi duk idan zai tafi sai yace mata "Bana son kowa a kusa da ke kin sani ko?" Dariya takan yi ta daga mishi kai, haka kawai saboda ita yakan shiga cikin makaranta, murmushi yakan bata a matsayin tukwici saboda yanayin shigar da takeyi yanzun, abaya take dorawa akan kayanta, wasu ranakun ma hijabi take sakawa, tana mishi kyau naban mamaki, hakan dai bai hana shi jin wani zafi a kirjin shi ba, duk idan yaga tana magana da wani dan ajin su, bayason ganin kowa a kusa da ita. Har ran shi baya so, ya fara kirga kwanakin da suke cikin shekara biyu da kusan rabi daya rage mata a ABU. Jiyama tun da akayi Magriba yana wajenta sun sami waje sun zauna, ba wani hira suke ba tunda ta bashi labarin jarabawarta, da wani yaro da aka kama yana satar amsa. Da akayi isha'i dai ita ta koma cikin hostel shikuma yaje masallacin yayi sallah. Suka kara dawowa, shine ma yace mata "Gobe da safe zan tafi In shaa Allah...Bilal zai kaini" Shiru ta danyi na wasu dakika "Sai yaushe zan gan ka?" Numfasawa yayi, goben zai kama lahadi "Zan shigo nan da sati daya in shaa Allah..." Kallon shi Layla tayi, ya girgiza mata kai "Kar kimun kuka Layla, idan zan iya zuwa a wasu ranakun da ba karshen mako ba zan zo" Muryarta a shagwabe tace "Ba zan gan ka ba, mun gama jarabawa, na tafi gida sannan" Ta karasa maganar da wani irin yanayi "Zan zo gida... Bance nan da satin ba, amman zan zo in gan ki" Numfashi ta sauke "Ka siyi waya Hamma" Zuciyar shi yaji ta doka, kamar ya dora hannun shi a kirji karta fito waje, saboda sai da ta saka idanuwanta cikin na shi tukunna tayi maganar "Ina da waya" Ya amsa yana dauke idanuwan shi daga cikin nata "Wannan ba waya bace ba, calculator ce kake da Hamma" Ta karasa tana dariya, rankwashinta yaje yi ta kauce tana sakeyin dariya "Waya nake nufi, waya irin ta kowa da kowa" Kafadu yadan daga "Ni ki barni" Gyara zamanta tayi tana fuskantar shi "Dan Allah Hamma, zamu dinga chatting, ko bamuyi ba zan kiraka video call in gan ka idan baka zo ba" Shiru yayi yana jinta "Kaji... Dan Allah" Shirun dai ya sakeyi yana kauda kan shi gefe, bata gaji ba ta tashi ta same shi ta dayan gefen tana fadin "Ka siyi babbar waya Hamma" Numfashi Rayyan ya sauke "Ni ki barni, bani da kudi" Da sauri ta amsa "Ni ina da kudi sai in baka" Murmushi yayi yana mikewa saboda dare ya fara yi, kuma yanzun Bilal na ran shi ko da yaushe, basu ci abinci ba ya fito, bayaso ya koma ya samu Bilal yayi bacci, ba zai iya tashin shi ba, ba kuma yaso ya kwanta baici abinci ba. "Allah ina da kudi, Abbu ya sake turamun, kuma kaga bamuci abinci a waje ba sosai, dafawa mukeyi ni da Anisa. Ka bani account number dinka sai in maka transfer" Wannan karin ya rankwasheta, ta dafe wajen tana murzawa "Na fasa baka Hamma" Tace tana murza wajen sosai, murmushin ya sakeyi "Dan Allah ka siya" Numfashi ya sauke yana furta "Mayya..." Dariya kawai tayi, harya rakata tana mishi magiyar ya siyi waya. Kuma da tunanin ya tashi yau da safe, har yana gama shirin shi. Baima san wacce zai siya ba idan ya tashi, ko kuma nawa kudaden su suke, da gaske bashi da kudi, Abbu yana tura mishi duk wata, ko da ya gama makaranta, Abbu kuma ya sani bai daina tura mishi kudin ba, ya dai rage yawan su, rabin abinda yake bashi ne da yana makaranta. Yana so ma yace daga watan nan kar Abbun ya sake turawa saboda shima zai fara samun kudi, ga na bautar kasa da za'a fara bashi, ga kuma Bappa da yayi mishi text ya fada mishi in da zaiyi bautar kasar suna biyan kudi suma. Bai dai san yanda zai fadama Abbu haka ba, ko yayi mishi text yake tunani, abinda zai fada din ma yana mishi wahala gabaki daya "Na wa waya?" Ya tambaya, yana saka Bilal da yake shiryawa kallon shi "Waya irin taka, ko ta Layla haka, waya dai da akeyin chatting, nawa?" Murmushi Bilal yayi, saboda yanayin yanda Rayyan din yayi tambayar, ya kwana biyu baiyi murmushin daya fito tun daga zuciyar shi ba haka "Wacce iri?" Kai Rayyan ya rausayar "Shisa nake tambayar ka, ban sani ba" Maballin rigar shi Bilal ya karasa ballewa "Akwai har ta dubu tamanin" Wani irin kallo Rayyan yayi mishi da ya sa shi kwashewa da dariya, sai yake jin kamar wani abu da yayi duhu a cikin kirjin shi ya dan washe da dariyar da yayi "Baka da hankali ashe Bilal? Dubu tamanin ka sa ka siyi waya? Ai kam saina fadama Ayyar ka" Sosai Bilal yake dariya, a tsayin zaman su da Rayyan, yaune karo na farko da yayi barazanar kai karar shi. Yanda yayi maganar kuma kamar har ran shi zai fadama Ayya cewa ya saka dubu tamanin ya siyi waya "Ina ma ka sami kudi?" Rayyan ya sake tambaya, dariyar da Bilal yake na son saka murmushi kwace mishi, yayi kewar ganin yanayin a tare da Bilal, yayi kewar ganin shi cikin raha, cikin farin ciki, da dariyar nan tashi da take hayaqa shi a lokutta da dama, saboda Bilal baisan sanda ya kamata ya daina dariya ba idan ya fara, amman yau idan zai wuni yana dariyar nan hakan zai so. Haka yake fata ya kasance, addu'ar shi kenan, yana kuma sake dora wata cikin rokon Allah ya sa damuwar Bilal din ta yaye kenan. Bai san me zai cigaba da fada ba, amman bayason wannan yanayin ya wuce "Da gaske Ayya zan fadama tunda kai baka da hankali" Jakar shi Bilal ya dauka yana saka cajar waya a ciki da dan abinda zai bukata, saboda yace zai kwana sai washegari ya dawo tunda har Monday din bashi da jarabawa. Watakila idan ya dan dagama Zaria yayi numfashi batare da nauyin da yake danne da kirjin shi ba "Waye yace maka wayata dubu tamanin take? Tecno ce fa, waccen na bayar saina cika dubu sha biyu na dauki wannan" Kai Rayyan ya jinjina "Kamar irinta nawa?" Dan jin Bilal yayi yana hada kudin da wayar ta tasar mishi a cikin kan shi, ko watanni biyu batayi ba "Dubu talatin ko da biyar haka, ba zata wuce da takwas ba dai" Hannu biyu Rayyan ya saka ya dafe duka kuncin shi, ba dariya yake so ya saka Bilal ba, har ran shi ya girgiza, mamaki yake yana kuma hasaso abinda zaiyi da dubu talatin da yafi siyan wata waya muhimmanci, ta hannun shi dubu biyar da dari ko biyune ya siyeta sabuwa fil a kwali. Kuma yana ganin abinda wayar su Bilal takeyi shima tashi zatayi "La hawla wala quwwata ila billah..." Dariya Bilal yakeyi daya kwana biyu baiyi irinta ba, idan kaga fuskar Rayyan din zaka rantse da Allah wani abune mai girma ya faru "Allah ya shiryaka Bilal" Rayyan ya iya kara furtawa, har lokacin yana jinjina yanda zaka mika wannan kudin ka dauko wata waya. Karasa daukar abinda duk zai bukata Bilal yayi suna fitowa, shiya kulle dakin, Rayyan kuma ya kama hanya yana ficewa daga dakin. Sai da zage zip din jakar shi daya goya ta gaba ya kara saka hannun shi ciki ya laluba yaji magungunan shi suna nan, kafin ya sake kuskuren barin su. Bai san inda zai samu ba a Kaduna, chemist ba zasu siyar mishi babu rubutun likita ba, kuma rabon shi da wani likita kusan shekara daya da wani abu yanzun. A hanya Bilal ya tsaya ya sai musu ruwa kafin su kama hanyar Kaduna. Hira suke danyi kadan-kadan, Rayyan na sauke wata ajiyar zuciya marar sauti da baisan yana rike da ita ba. Sai yake jin duk surutun Bilal kamar wani sauti daya saba da shi shekara da shekaru sai lokaci daya yaji yayi mishi shiru. Akwai hayaniya a cikin kan shi ko da yaushe. Amman surutun Bilal bai taba zama hayaniya ba, da babu shi a cikin kan nashi sai yake jin shiru a bangaren Bilal din, sai yanzun yaji ya samu wani dai-dai to. Gyara zaman shi yayi a cikin kujerar yana kwantar da kan shi hadi da lumshe idanuwan shi, bacci ne ya dauke shi, baccin da ya kwana biyu bai samu ba ko da rana, saboda yana kula da yanayin Bilal. * Zuciyar shi a makoshi yake jinta lokacin da yayi parking din motar, kan shi ya dora a jikin abin tuqin yana wani irin mayar da numfashi, ji yake kamar zai sume. Ga zufa da take tsatsafo mishi ta ko ina, tunda akayi abin nan rabon shi da ya saka ta a idanuwan shi, ko yanzun ma text yayi mata da ta fito yana bakin hostel din su. "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Yake iya furtawa, ga shi Aisha ta riga su gama jarabawa, anzo an dauketa tun shekaranjiya, saboda za'ayi bikin yayarta a cikin satin. Daga shi sai ita zasu tafi, bai san mintinan daya dauka a zaune cikin motar ba. Layla ma tun da taga text din shi cewar yana kofar hostel din su wani abu ya kulle a cikinta, a tsorace take, ita tace mishi su manta da komai, amman ta karanta text din yafi sau hamsin kafin ta iya goge shi, ko itama sakon zai isar mata, ko zata iya mantawa da abinda ya faru. Amman har yanzun tana jinta kamar babu suttura a jikinta, ko da ita kadai ce a kwance. Sam a aji bataso wani ya zauna kusa da ita, kamar abinda ya faru ya saka mata tsoron maza gabaki dayan su, tayi jimla ne saboda yanda har kanta sarawa yayi ranar farko da Rayyan ya daga hannun shi da niyyar ya kai shi jikinta, wani irin matsananci tsoro taji ya shigeta, sai take ganin duk idan tayi kuskuren yin kusanci da wani namiji abinda ya faru tsakaninta da Bilal zai iya sake faruwa, ta kara shiga wani sabon rudanin. Tana son Rayyan, wata irin soyayya da har tashin ta take da tsakar dare, rokonta karya taba ganewa ko sanin wani abu ya taba faruwa a tsakanin ta da Bilal, group din su ma fita tayi, dan tafi sati tama manta da shi, sai ranar da ta dan samu natsuwa taga sakonnin su, fita tayi tana goge komai, babu wanda ya tambayeta dalili, a aji ma basu ga fuska ba, ta daina musu dariya, ta koma hade fuska kamar yanda takeyi daga farko, da yake babu wanda baisan ta iya masifa ba duk sai suka kiyayeta. Duk da suna mamakin canzawar ta lokaci daya haka. Sosai ta kan dauki waya ta gwada kiran Bilal, ko gaisawa suyi kamar yanda suka saba, amman sai ta tsinci kanta da kasawa, bata san me zatace mishi ba, saboda kafin ma ta kira din take jin zufa na karyo mata. Tashin hankalin da take ciki daban yake, dakyar ta iya janyo akwatinta ta sauko da shi, amman ta dade bayan ta sauko kafin ta sami kafafuwan ta su motsa ta fita waje, tana ganin motar shi ta hango shi a ciki ya hada kan shi da gaban motar sai da zuciyar ta tayi wata irin dokawa, kamar ta koma ciki da gudu haka take ji. Bakinta ko yawu babu sanda ta karasa wajen motar, hannuwanta duk sunyi gumi saboda tashin hankali, ta kama baya ta bude saita kasa, hakan yasa ta kama gaban motar tana budewa, cikin yanayin da ya sanar da Bilal ta karaso. A firgice ya dago yana juya kai ya kalleta, sai ya bude nashi bangaren ya fita kamar tana shirin shigowa da bomb, itama yanda kafafuwanta suke rawa yasa ta shiga cikin motar ta zauna tana mayarwa ta rufe "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Kawai yake furtawa bayan ya fita daga motar, jikin shi babu inda baya bari saboda tashin hankali. Dakyar ya zagaya ya dauki akwatin Layla ya saka a bayan motar, amman ya kasa shiga, ya rasa ta inda zai zagaya ya shiga cikin motar. Ya kusan mintina goma kafin ya samu ya karasa, ya bude ya zauna. Jikin shi ko ina bari yake sanda ya tayar da motar, babu kowa, babu komai a bayan shi, amman sai yaji kamar yana kara motar da wani abu, dakyar yayi kwana, ya runtsa idanuwan shi ya bude su yafi sau biyar yaki daina ganin kamar akwai yana a cikin su. Sai da suka fita titi, taga yanda yake gefe da gefe, motar na yawo, in suka kara mintina goma akan titin tabbas zai bugawa wani, ko ya giftawa wani su a buga musu "Hamma..." Layla ta kira tana jin hawaye sun cika mata ido, mutane zasu ce Rayyan na abubuwa a nutse, amman har gobe ba zata ga mutum da yake komai da natsuwa kamar Bilal ba, shisa take gane idan ran shi a bace yake, ko Haris baya abu da natsuwar da Bilal yakeyi. Ba sanyin jiki gare shi ba, wata irin nutsuwa yake da ita, kamar komai a lissafe yake yin shi. Shisa yau da karara take ganin natsuwa ta kwace mishi abin yake kara tabata "Hamma kayi parking dan girman Allah" Ta karasa maganar muryarta na karyewa. Parking din Bilal yayi, zuciyar shi zafi takeyi, baisan da wanne ido zai kalleta ba, baisan me take ji ba idan har shi yana jin kamar duniyar shi tazo karshe. Kan shi ya sake hadewa da jikin steering wheel din, baisan hawayen shi na zuba ba, sai da yaji digar su akan cinyar shi. Kuka yake saboda baisan yanda zaiyi ba, baisan inda zai saka ran shi yaji sanyi ba, yanayin kafadar shi tagani tasan kuka yake marar sauti. Nata hawayen zuba sukeyi itama. Batajin kowa zai fahimci kunci na zuciya sai ka farka cikin dare, jikinka ko ina yana bari da tashin hankalin da ba zaka iya sanar da mutanen da kasan zasu sama maka sauki ba, mutanen da suka fi kusanci da kai akan kowa, saboda kana tsoron tashin hankalin da kake ciki zai hargitsa tasu duniyar, a lokacin hawayen zasu fara zubar maka, kukan da kake tsoron fitar sautin shi dan kar wani yaji yai maka tambayar da ba zaka taba iya amsa shi ba. Shine halin da suke ciki ita da Bilal, kuka sukeyi, kukan abinda ya faru da su da basu da kalaman misalta shi, kukan yanda rayuwa ba zata taba zamar musu dai-dai ba, karshe kuka suke na alakar da take tsakanin su da ta samu tangardar da basu da tabbacin zata taba komawa dai-dai, dakyar ta iya dago da kanta tana share hawayenta, bata san me yasa take jin kamar ta fi shi karfin zuciya ba "Hamma... " Ta kira da wani irin yanayi da ya saka Bilal kara shigewa cikin abin tuqin kamar yana so ya bace daga motar gabaki daya "Ba laifin ka bane, na fada maka ba laifin ka bane ba, ba zan taba ganin laifin ka ba... Karka taba tunanin zan ga laifin ka, kaddarar mu ce tazo a haka" Kai Bilal yake girgiza mata, ya kasa dagowa, idan tana fada mishi ba laifin shi bane tana kara saka kirjin shi yin nauyi, tana tuna mishi da tarin mutanen da suka bashi amanar ta, tana tuna mishi da cewa abinda take tunani bashi da wani muhimmanci in har su din ba haka suke tunani ba, a duk yanda ya hasko su, baiga zasuyi mishi uzuri ba, saboda ya kasa yima kan shi uzuri. "Dan Allah ka daina... Ka daina kuka" Dakyar ya iya dagowa, ya kasa kallonta, fuskar shi ya goge, ta gefen idanuwan shi yaga ta bude jakarta ta zaro hankici ta dora mishi akan cinyar shi, dauka yayi yana goge fuskar shi sosai, yayi gyaran muryar da yakejin ko da yayi magana ba zata fito ba. Layla ba zata taba gane tashin hankalin shi ba, su Ayya ka dai yake da a fadin duniyar shi, tana da wasu yan uwan bayan Mami, akwai wanda suke uba daya, bashi da kowa daya rage mishi a duniyar shi banda Ayya. Ba hulda takeyi da daginta ba sosai, balle ya san sauran dangin shi na bangarenta. Su da Abbu ne kadai makusantan da yake da su sai Rayyan da ita, sune kuma mutanen da ya kasa rikewa amana. Aisha ma da yake jin tashi ce, yake jin ba zata bar shi ba, bayajin zata zauna da shi bayan tasan abinda ya faru, sai da ya kunna motar tukunna yace "Kaddara, ita ce kalmar da kika zaba Layla?" Ya karasa tambayar yana juyawa ya kalleta, sai take ganin idanuwan shi sun mata wayam, kamar babu emotions ko daya a cikin su, wani irin murmushi yayi mai ciwo daya karya wani abu a cikin zuciyarta "Kaddarar nan zata iya rabani da mutanen da su kadai nake dasu a fadin duniyata... Idan kin mun uzuri baya nufin su din zasuyi mun" Shiru tayi, tana jujjuya maganar shi badan bata da amsar bashi ba, in ta bude bakinta sautin kukane zai fito, har saida ya hau titi, wannan karin a nutse yake tuqin, sai da ta tabbatar zata iya magana batare da ta fashe da kuka ba sannan tace "Shisa ba zamu taba fada musu ba" Titi Bilal yake kallo, yaji me tace, ya zabi yin shiru ne kawai, saboda zuciyar shi na cikin wani hali. Taya zai kalli idanuwan Abbu bakin shi yayi shiru? Ta ina zai hada idanuwa da Abbu kamar bai ci amanar daya bashi ba? Ana mutuwa sau daya, shine yardar kowa, amman a tsayin satikan nan, ya mutu a duk ranar da zai tashi daki daya da Rayyan, ya ga Rayyan yayi mishi murmushi, numfashin shi daukewa yake yi Ba zai iya kallon Mami kamar bai taba amanar da ta dauko ba Wannan karin bayajin mutuwar da zata dauke shi ta wasa ce Bashi da tabbacin idan numfashin shi ya tsaya zai dawo. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:08 PM - 111: Dec 20, 2020. 23 "Layla ta dawo ko?" Naadir ya tambaya yana shigowa dakin, murmushi Mami tayi "Bata dawo ba" Ta amsa shi, kallon ta yakeyi da murmushi a tashi fuskar kafin ya wuce kitchen, bude-bude ya fara yana ganin wake da shinkafa, sai sauce din manja da ta sha kifi, yana zubawa yake fadin "Layla ta dawo Allah Mami...ni na sani" Dariya tayi wannan karin, da yake nan BUK Naadir din yakeyi, kuma duk a cikin yaranta shine makaranta take wahalar wa, saboda kokarin shi bai kai nasu ba, yana cikin gari amman ba kullum yake kwana a gida ba, musamman lokacin jarabawa irin haka, a makaranta yake kwana suna dan taba karatu, wani lokacin har tausayin shi take ji, akan Naadir ta yarda kokari halitta ne, amman babu wanda zaice baya fahimta, idan harka sakawa zuciyarka hakuri da juriyar bibiyar abu, hatta da Marwan tana kallon shi ya ajiye islamiyya, gashi da kokarin amman karatun bawai ya dame shi bane can-can. Yafi gane harkar kasuwan ci da yakan bi Yaya Ayuba. Amman Naadir na zuwa islamiyya har yanzun, idan zaibi abu sau hamsin kafin ya fahimta baya gajiyawa. Yanda ake yaran suna gane Layla ta dawo har mamaki yake bawa Mami, shisa Naadir na fitowa daga kitchen din tace "Wai ya ake kuna gane ta dawo ko baku ganta ba?" Dariyar shi Naadir yayi "Kamshi Mami, kamshin turare" Dariyar tayi "Wato ni bana saka turare kuke nufi ko menene?" Kai Naadir ya girgiza, yana ficewa, Mamin su na kokari matuka wajen tsafta, amman turarukan da Layla take amfani da su daban ne, duk idan ka shigo zakaji su. Su suke fara sanar da kai tana cikin gidan. Sai kuma abinci da manja yawanci, su duka yaran suna so, ita kuma Mami bai dameta ba, kuma ba zata iya wahalar girki kala biyu kamar yanda Laylar takeyi ba, idan miya ce tana iya yiwa Mamin tata daban da babu manja, su kuma tayi musu mai manja. Kuma tana iya binsu a waya tana tambayar me suke marmarin ci, Mami abinda taga damar dafawa shi takeyi, ko Abbu baya mata zaben girki balle su. Layla ma daga dakinta ta fito dan yunwa ta korota, tunda tayi azahar ta kwanta tana bacci, bata tashi ba sai da la'asar din, jikinta da yayi nauyi yasa ta watsa ruwa bayan ta idar da sallah "Wai ina kike siyen turaren wutar da kike zuwa da shi? Yafi na nan da mukan siya dadewa a dakuna" Mami ta tambaya "Wajen wata Kamshi by Saffad, Anisa ce take zuwa da shi tana saka mana a daki, kamshin yana mun dadi, shine ta bani lambarta duk idan zan dawo nake siyo mana fa, kuma babu tsada Mami" Layla ta karasa tana shigewa kitchen, sai da ta zuba abinci ta kai daki sannan ta daukowa Mami kwalbar turaren wutar tana dawowa ta kawo mata. 07010137848 Lambar wayar Mami ta duba, Layla kam yunwa takeji shisa ta koma cikin daki abinta, yau da ta tashi ji take a duniya idan bata ci miyar kifi da manja ba komai zai iya faruwa, shisa ta kira Jabir a waya tace ya siyo musu kifi. Da yake yafita kwadayi ko awa daya ba'a hada ba ya shigo dakin da kifi mai yawa, sai da ta saka wani a fridge ma. Abincin take ci tana duba text tsofin texts din su ita da Rayyan, ba sosai suke waya ba tunda ta dawo saboda Mami. Shisa kusan wuni sukeyi suna musayar text, baya gajiya da saka mata kati ko da tace mishi tana da saura, yi yake kamar baijita ba, ta dai rasa ya zatayi da shi akan waya. Duk idan tayi mishi zancen waya sai yace ta kyale shi, ba zai barnar kudi ba akan waya. Kewar shi na danneta, in da ya siyi babbar waya zata saka shi ya dauko manhajar IMO dan su dinga video call ta nan, ta ga fuskar shi, ko hotunan shi basu kai goma ba wanda take da su, na ranar da ya gama jarabawa, sai kuma ranakun da yazo wajenta ta daga camera bai fisge wayar daga hannunta yana hada mata da rankwashi ba saboda zata dauke shi hoto. "Ko aljanu sukan rabo a dauki hoto da su wani lokaci Hamma, amman ace kai baka da hotuna saboda Allah" Ta taba ce mishi, murmushi yayi kawai yana girgiza mata kai, akwai hoton su ita da shi da take so, saboda ranar tayi sa'a ya tsaya sosai, kuma manyan kayane a jikin shi harda hula. Har ranta take jin Rayyan, kamar yanda har a zuciyarta take jin shine cikon farin cikin ta. Abincin ta karasa cinyewa ta dauki plate din ta mayar kitchen ta koma ta kwanta abinta. Idanuwanta take ji suna mata nauyi da alamun bacci, ba dan bata kwanciya ba, amman a yan kwanakin nan sai take ganin kamar baccin da takeyi yayi yawa. Shisa da ta idar da sallar asuba take shiga kitchen tayi abinda zatayi, saboda Mami bata tashin ta, idan tayi aiki shikenan, idan kuma bata fito ba ita zatayi da kanta. Shekaranjiya wata irin kasala ta dinga ji har cikin kasusuwan ta, shisa ta kasa fita tayi kwanciyar ta, sanda ta tashi karfe goma na safe "Mami baki tasheni ba, shine kikayi aikin ke kadai" Murmushi kawai Mamin tayi mata "Rai na son hutu Layla, kuma motsa jiki na da kyau, tunda kika zo bana wani aikin komai, sai kin shagwabani ki koma makaranta abinki" Dariya tayi, ko da babu makaranta tasan Mami ba zata tasheta ba. Wayarta da harta fara subucewa daga hannunta saboda bacci ta dago, haka kawai sai idanuwan ta suka sauka kwanan wata, period biyu kenan batayi ba, wannan karin ma har wajen kwana takwas kenan ta kara. Farkon da sukaje makaranta, daga ita har Anisa sun sha wahala saboda infection da suka kwasa na amfani da bandakin makaranta, gara ma ita ciwon mara ya kara mata sai kuma period daya dinga mata wasa, dakyar Anisa ta samu ta sakata taje asibiti "Ni fa in zan shekara banga period ba zaifi mun, Allah ya kawomun saukin wahala ne" Har duka Anisa ta kai mata tana fadin "Ke daman ai baki da hankali" Amman da gaske takeyi, babu wani ciwo da yake bata wahala banda period, har zullumi takeyi idan taga tsakiyar wata ya kusa, tana hasaso kalar wahalar da zata sha. Shisa yanzun ma bata damu ba, daman Anisa na mata fadan ta dinga tafiya da tsintsiya bandaki, ta wanke wajen kafin ta tsugunna, shisa rashin period din bai wani dameta ba, tasan ba zai wuce infection din da har a asibiti aka fada mata idan bata kiyaye ba zai iya dawowa, saboda babu matsalar da take damun mata irin wannan, babu kuma abinda yake da wahalar sha'ani kamar shi. Idan ta koma makaranta sai ta sake zuwa asibiti, zuwa yanzun kam zata shana abinta. * Fitowa tayi daga bangaren ta, tana jin Intisar na fadin "Ayya ko ina ne fa babu network din glo, ga nawa ma ya dauke" Bata bi ta kanta ba, cigaba tayi da tafiya tana daga wayarta, sai kuwa ga tsinke daya ya kawo ya sake daukewa, a ranta take fadin "Ga shi na fara zuko sji, amman yaran nan sai suce maka ai ko ina ne babu network" Bilal take ta kokarin kira tunda ya fita, sai take ganin kamar ya koyi yawo yanzun, duk da yakan ce mata wajen tirenin din kwallon kafa yake tafiya, ko wajen Aisha. Fitar tashi tana mata yawa, sam baya son zama a gida kamar yanda sukan yi, ta kira MTN din shi bai daga ba, tasan karamar wayar na tare dashi, nan ne kuma glo din su yake, dabarar ta gwada kiran shi da wata lambar bata zo mata ba sam. Intisar da taso fada mata zagi ta sha, sai tayi shiru tana dariya. Harabar gidan ta fita sosai, kamar daga sama taga giccin Layla, yanayin da ya sata raba idanuwanta da wayarta tana kallon yarinyar. Ba cika kallonta tayi ba saboda yanda bata cikin yan kayanta, amman yau wani irin bugawa taji zuciyarta nayi, fara ce dan fara, Layla na da hasken fata kamar su Rayyan, amman sai taga ta kara yi mata wani sanannen haske, hasken da bata fata ya kasance tare da budurwa kamar Layla. Sosai zuciyarta take bugawa, musamman yanda Layla ta dawo ta wuce cikin wani irin rashin kuzari da ba nata bane, ita din mai kazar-kazar ce, bata san kiyayyar da takewa Maryama bata mamaye dukkan zuciyarta ba sai yau, sai yanzun da ta tsinci kanta da furta "La hawla wala quwwata ila billah" Tana saurin kauda zargin da yake son darsuwa a cikin zuciyarta. Kafin ta dora da addu'ar neman tsari daga shaidan da kan jefa zato kala-kala a zuciyar dan adam. Tsoron da taji ne ya mantar da ita neman Network din da ta fito yi tana komawa ciki. Duk surutun da Intisar takeyi mata bata jiba balle tabi ta kanta, sam zuciyarta ta kasa samun natsuwa, ko dan kacokan rayuwarta akan yaranta ne? Takan san basu da lafiya kafin ma su farga da basu da lafiya, ko jikin Rukayya ya taba nata takan gane idan zafin jikin dai-dai yake ko akasin haka "Ayya lafiyata kalau fa, ina ga gajiyar makaranta ce" Rukayya kan fadi wasu lokuttan idan tace mata ta sha ko panadol ne, sai ta barta, karshe da safe zaka ji tana cewa "Kinga zazzabi ya dameni ko Ayya?" Harararta takan yi ta share, sai ta fara dariya, a cikin yaranta kaf Rayyan ne kadai bata gane wani abu a kan shi. Shisa yanzun tasan akwai abinda yake damun Bilal da yake boye mata "Akwai wanda zai san damuwar ka idan ban sani ba Bilal?" Ta bukata bayan ya dawo da kwana biyu, amman murmushi yayi mata "Bakomai Ayya, idan akwai zan fada miki kinsani" Kai ta jinjina, bai saba mata karya ba, a yanda sautin muryar shi ta fito tasan karya yakeyi. Bata ja maganar bane saboda batason ta saka shi sake yi mata wata karyar akan wadda yayi mata. Fatanta matsalar kar ace daga wajen Aisha ne yake fuskantar ta, saboda damuwa ba abokiyar Bilal bace ba, banda ita Rayyan ne kawai take tunanin zai san damuwar Bilal, shikuma ba zai taba fada mata ba. Addu'a kawai takeyi Allah yasa ba wata damuwa bace mai girma. Shisa take son yakice Layla da ta tokare mata makoshi daga ranta, saboda bata bukatar wata damuwa ta rashin dalili a kwanakin nan. Har dare ma bayan tayi isha'i taci abinci nan falon tayi zamanta tana kallon wata dirama a tashar Dadin Kowa. Amman hankalinta rabi ne a kai, rabin na wajen kofa tana jiran ta inda zata ga bullowar Bilal, har Abbu ya riga shi dawowa yau. Bai shigo ba sai wajen tara na dare, sallamar shi ta amsa a hankali tana kallon shi ya wuce kitchen ya zubo wani abinci da ko Huda yayiwa kadan ya dawo falon ya samu kujera ya zauna "Me ake kallo ne Ayya?" Numfashi ta sauke tana nazarin yanayin shi, gashin daya ajiye a fuskar shi bai hanata ganin ramewar da yayi ba, yau sai take ganin kamannin da akan ce yanayi da ita sun fito sosai, saboda ramar ta kara fito da hancin shi "Wata dirama ce fa, kamar ma kullum sukeyi" Tv din Bilal ya dan kalla, yana mayar da hankalin shi kan abincin da yake ci, yasan jikin shi na bukata, amman tunda yazo gidan ba gane kan abinci yakeyi ba. Texts din Rayyan suke tuna mishi wasu lokuttan "Kaci abinci Bilal" Shine abinda yake rubutowa da safe, da rana, da kuma dare, bai taba kara wani abu a kai ba, ko ya rage, in sukayi waya kuma baya tambayar shi yaga sakon ko me yasa bai bashi amsa ba, ko da bai tuna mishi ba yana kokarin ganin ya saka wani abu a cikin shi ko da sau daya ne a rana. Duniyar ce yakeji ta hade mishi waje daya. Idan zaka tambaye shi ya yake kwanciya ya tashi da safe ba zai iya fada maka ba, wata rana akan darduma in da yakan yi salloli nan bacci yake dauke shi, ya fara sallolin ne saboda tunanin neman wani abu ya sha dan ya taimaka mishi wajen bacci ya fara damun shi "Muryar ka na mun kama da wanda depression yake shirin kamawa Bilal, idan ba zaka iya mun magana a dan uwan ka ba, kai mun magana a matsayin likitan da zai iya taimaka maka..." Rayyan yace mishi jiya da safe, yana kara saka shi jin babu dadi, saboda ya saka shi cikin damuwa, bayan abinda yakejin yayi mishi "Ban san me zance maka ba... Idan na kara ce maka babu abinda yake damuna zai zamana wata karyar akan wadda nake tayi a kwanakin nan, saboda haka zan fada maka gaskiya Hamma, wani abu na damuna, amman bana son inyi magana a kai, dan Allah ka daina tambaya, kana karamun nauyi da tambayoyin ka" Yanajin numfashin da Rayyan ya sauke ta dayan bangaren, runtsa idanuwan shi Bilal yayi yana bude su "Ba zan sake tambaya ba, in kayi mun alkawarin ko da kaje asibiti sun baka wani abu karka sha sai naga menene" Dan murmushi Bilal yayi, shi me zai ma kaishi asibiti. Har yanzun duk yanda ake magana kan mental health bai shiga zuciyar shi ta yanda zai dauki kafafuwan shi yaje asibiti a kai ba. "In shaa Allah. Lafiyata kalau da gaske, damuwa ce kuma kowa na tare da ita yanzun..." Ya karasa da yar dariya dan ya saukaka musu yanayin daga shi har Rayyan din "Zan zo karshen wata In shaa Allah... Zan zo in gan ka" Kai Bilal yake girgizawa "Kar ka baro hidimar ka nace maka lafiyata kalau Hamma" Wayar Rayyan ya kashe a kunnen shi alamar ya rigada ya gama yanke hukuncin zuwa, babu kuma abinda zai sake hakan. Tun jiyan yake lissafa kwanakin da suka rage a cikin watan, yana ganin saura kwana tara, tabbas nauyin da kan shi yayi zai karu idan Rayyan da Abbu suka kasance waje daya yana ganin su a duk rana. Tunda yazo ya kasa bari idanuwan shi su shiga cikin na Abbu sam, ko hira mai tsayi ya kasa zama suyi, kullum cikin uzuri yake dan yabar dakin Abbu din. Ga Aisha yanzun da fada suke na rashin dalili, ko yau sai da sukayi kafin ya taho "Damuwar ka na damuna duk da ban santa ba, amman baka mun adalci ka sani..." Ta fadi tana tashi tabar shi a wajen, ya rasa yanda zai ya dinga bata hankalin shi kamar da, ko waya suke yakan shiga wani tunani sai taita magana bai san tanayi ba, haka idan suna chatting yakan manta ya ajiye wayar, wasu lokuttan sai ta kira sannan yake tunawa, banda hakuri babu abinda yake da shi da zai bata, amman yana bukatar duk wasu kalamai na hakuri da zai iya adanawa, saboda yanajin yanda shine kawai abinda ya rage a tsakanin shi da mutanen da suka fi kowa kusanci da shi. * Ganin karfe sha biyu saura yasa Mami sake tashi dan taje ta duba taga ko lafiyar Layla. Bataji motsin ta ba da asuba sai da ta tasheta, wajen tara na safe ma ta sake tashin ta dan ta karya. Tana tura dakin kuwa taga bacci takeyi, karasawa tayi tana dan bubbugata "Layla..." Mami ta kira a dan tsorace, dakyar Layla ta bude idanuwanta, da zazzabi ta kwana ga kasala, jikinta kamar ta aro takeji, da tana sallah da asuba sai takejin jiri na dibarta, raka'a ta biyu a zaune ta karasa ta dakyar "Lafiyar ki kuwa?" Mami ta tambaya tana taba jikin Layla da taji kamar wuta "Subhanallah..." Ta furta tana kama Layla ta dago ta "Mami bani da lafiya" Cewar Layla tana sake komawa ta kwanta saboda yanda take jinta, tana zazzabi kala-kala, amman wannan daban yake, tunda take a duniya bata taba jinta a irin yanayin da take jinta yanzun ba, ko dazun da Mami ta shigo ba bacci takeyi ba, maganar ce take mata wahala da ta fada mata bata da lafiya. Gabaki daya Mami ta gama rikicewa, tashi tayi tana wucewa ta dauko hijabi ta saka a jikinta tana dawowa dakin Layla da take jin wani sanyi na ratsa sassan jikinta, lokaci daya tunanin mutuwa na gifta mata, yana sakata jin ko dai ciwon ajali ne ya kamata "Ko mutuwa zanyi Mami? Jikina baya mun dadi" Zuciyarta Mami taji tayo wani tsalle tana dawowa makoshinta "Wacce irin magana ce wannan? Jiba shirme" Ta karasa tana daukar wayarta da take kan gadon Layla tana rasa waya kamata ta fara kira, Haris dai baya garin ma, sunje wani Seminar a Katsina. Idan ta kira Jabir da wahala yana kusa, lambar Bilal ta lalubo tana kiran shi, sai da tayi tunanin ba zai dauka ba sannan taji sallamar shi cikin kunnenta "Dan Allah Bilal idan kana kusa kazo ka kaimu asibiti, Layla bata da lafiya..." Da sauri ya amsa da "Gani nan... Bari in shigo" Sauke wayar tayi daga kunnenta tana mikewa, hijabi ta samo ta kama Layla ta dago ta tana saka mata, duk ta langabe a jikin Mami, ga amai da yake tukarta amman yaki fitowa, tunda asuba take jin shi. Gabaki daya sama-sama take ji, kamar rabinta a duniya rabinta a wani waje da bata san ina bane ba. Ko minti goma ba ayi ba sai ga Bilal din ya shigo bangaren Mami da sallamar shi, dan a kwance yake sanda kiran Mami ya shigo, da kamar ba zai daga ba, baisan me zaice mata ba, tunda ya dawo sau biyu ya ganta, yana duk kokarin shi wajen ganin basu hadu ba, sai dai Mami ba zata taba kiran shi babu wani dalili mai karfi ba. Yana dagawa kuwa yaji dalilin ne mai karfi, motar su ta sami matsala tun shekaranjiya daya ajiyeta wajen gyara bai waiwayeta ba sam. Kuma yaji muryar Mami kamar hankalinta a tashe yake, shisa yana fitowa ya wuce dakin Ayya, a Kitchen ma ya sameta "Bilal... Lafiya?" Ayya ta tambaya, ganin yana balle maballan rigar shi kamar a hanya ya sakata "Mukullin mota zaki bani Ayya, yanzun Mami ta kirani inzo in kaisu asibiti Layla bata da lafiya" Wani irin kallo Ayya takeyi mishi, duk yaran Maryama din sai ta kira Bilal saboda gulma da neman dalili, Haris baya nan tasani tunda ko da safe sunyi waya. Amman Jabir aikin me yakeyi "Ina Jabir? Sai kaine zaka kaisu asibiti? Ita ina motar hannun ta?" Numfashi Bilal ya sauke "Ayya dan Allah, tun da kikaga ta kirani watakila basa nan ne shisa" Karamin tsaki Ayya taja "Kinibibi ne dai da neman magana irin nata, sai kaje ka dauka yana kan drawer din gefen gado, in ka kaisu ka dawo mun da motata zan fita" Wucewar yayi ya dauko, yanajin Ayya na fadin "Kabi a hankali kaketa rawar jiki..." Baiko juya ba harya fice ya na nufar dakin Mami. Aikam yanayin da ya ga Layla din ya daga mishi hankali "Ki taso Mami" Ya fadi, kama Layla tayi suna fitowa, sunzo harabar gidan dan ya dauki motar Ayya, sai ga Jabir ya shigo shima da motar Mami din da Ayya take magana a kai "Bilal ga Jabir nan ma ya dawo, bari sai mu tafi kawai" Kai ya jinjina mata "Bari in maidawa Ayya mukullin dan zata fita sai in zo mu tafi" Wannan karin kai Mami ta girgiza mishi, daman saboda tana tunanin idan ta tsaya jiran Jabir za'a bata lokaci shisa. Tasan halin Ayya, zata iya fadar maganganu idan Bilal din ya bisu asibiti, kwana biyu basuyi ba, bata neman tashin hankali "Nasan muma ba jimawa zamuyi ba In shaa Allah...ka koma kawai dan Allah" Dan juya zancen yayi, kafin ya jinjina kai "In dai sun rike ku dan Allah a kirani" Ya fadi yana rakasu har wajen motar, sai da yaga sun shiga har sun juya sannan ya koma ciki. Kai tsaye Aminu Kano Jabir ya nufa da su, in da ba'a bata lokaci ba, basu ma samu layi ba, Jabir ya sai musu kati, mutum daya aka gani sai su da suka shiga, Mami ta zaunar da Layla da take jin kamar zata shide akan kujera ita tana tsayawa, tambayoyi likitan ya fara yi kamar yanda sukan yi "Tun yaushe kike zazzabin?" Ya tambaya, dan jim Layla tayi, takan kwana da shi tun dawowar ta, amman baya damun ta, tun da sai ta farka ko fitsari taji shi, in ta samu ta koma bacci kuma da safe ya tafi, yaune kawai ya kwantar da ita haka, cikin rawar murya ta amsa shi "Na kai sati, amman da dare ne kawai. Yaune har yanzun bai tafi ba" Sosai yaci gaba da mata tambayoyi kala-kala, jin ance za ayi awon jini dana fitsari yasa Mami fadin "Bata da aure fa" Murmushi kawai likitan yayi "Za'a duba komai ne Hajiya, babu wata matsala" Haka kawai sai ta tsinci kanta da shiga damuwa, tare da Jabir sukaje aka dibi jini da su biyan kudi, zuwa duk wani abu da ake bukata suka dawo suka zauna suna jiran results din "Ko zaki sha wani abu in siyo miki?" Kai Layla ta jinjina "Ka siyomun Sprite" Da mamaki Jabir yake kallonta "Yaushe kika fara shan sprite?" A shagwabe ta kalli Mami "Ka wuce ka siyo mata bata da lafiya karku sakani surutu" Dan tasan halin Jabir baya gajiya da tsokanarta, kawai dan yaga tana mitarta da kai kara. Wucewar yayi, bai jima ba ya dawo. Mami yasan ba sha zatayi ba, ruwa ya siyo mata, shi ya siyowa kan shi coke. Suna zaune aka ce musu result din ya fito "Mami kiji me zaice, jiri nakeji Allah" Kai Mami ta daga mata, nan ta ajiye robar ruwan da ta fasa ta dan sha, sai Layla take jin ta dan samu, ba kamar sanda suka fito daga gida ba, har ranta ta dauka ciwon ajaline ya kamata. Zaune sukayi abinsu ita da Jabir yana mata hirar wani film da suke kalla su dukan su mai suna Blind spot "Hamma banyi nisa ba, kabarni, bana son jin me zai faru..." Dariya yayi, ya bude baki yayi magana ya hango Mami, yanayin ta na saka shi mayar da bakin shi ya rufe, saboda a hargitse take, a hargitse kuma ta karaso inda suke "Ki bude bakin ki Layla, ki fadamun karyane, ki ce mun likitoci da kan su nayin kuskure, na'urar su na samun tangarda..." Cike da rashin fahimta suke kallon Mami da take magana kamar ta sami tabin hankali "Mami..." Jabir ya fara magana Mamin ta katse shi ta hanyar daga mishi hannu, idanuwanta kafe suke cikin na Layla "Ki tashi muje ki fada mishi ke din budurwa ce, ki kalli idanuwan shi ki fada mishi babu yanda za ayi ki samu ciki!" Wannan karin har mutanen da suke wajen sai da hankulan su ya tattaru ya dawo kan su, robar lemon da take hannun Jabir tana subuce mishi "Ciki? Mami ciki? Bashi da hankali? Wanne irin ciki kuma?" Layla tun daga kalmar "ciki" komai ya daina karasawa kwakwalwar ta, in dai ciki likita ya gano mata tasan inda ta same shi, in dai da gaske akwai wani abu a cikin ta tasan ya akayi, ba karya yayi ba, na'urar su bata da matsalar komai, kwakwalwar ta ce ta samu tangarda, tunaninta ne ya yaudareta da alamomin duk da ta dinga gani amman ta kasa fahimta, ba infection bane ya dauke mata al'ada, shigar cikine. "Layla..." Mami tayi maganar tana girgizata cikin yanayin da ya sata daga ido ta kalli Mami din "Ciki Mami... Ciki ne da ni" Ta karasa cikin wata irin murya da yasa wani abu kullewa a cikin Jabir, yaune ya fara sanin tashin hankalin, Mami kuma da ta yanke jiki ta fadi tana kara mishi wani sabon tashin hankalin, ya sha ganin yanda duniya take birkicewa mutane a fina-finai. Yau a gaske yake ganin yanda duniyar ta karkata ta juya da shi a ciki, kamar film haka wani gefe na kwakwalwar shi yake daukar hoton komai, kafin ya tsugunna a kasa cikin lemon daya zubar yana kama Mami, magana yake amman sautin muryar shi baya fita saboda tashin hankali. Cikin Nurses din wajen ne wasu suka rugo dan su taimaka mishi, har aka dauke Mami yana tsugunne a wajen, Layla na zaune ko motsi ta kasa, tun tasowar shi duk wata damuwa tashi kafin Mami ta sani Abbu ya sani, ya saba abu koya kai ko bai kai ba ya nemi Abbu, shine babban abokin da yake da shi saboda mutum ne shi da yarda da mutane takewa wahala, shisa yanzun ma wayar shi ya laluba yana kiran Abbu "Abbu kazo Aminu Kano, Layla bata da lafiya" Ya iya fadi saboda kirjin shi da yayi nauyi, bayason fadama Abbu cewar Mami ta yanke jiki ta fadi, baima ji me Abbu yake fadi ba ya sauke wayar daga kunnen shi yana sakata a aljihun shi. Yana wani irin sauke numfashi yake kallon Layla "Ciki gare ki Layla?" Ya bukata yanajin maganar ta fito mishi kamar da wani irin yare, saboda kalamai ne da baisan yanda za ayi ace sun gifta tsakanin shi da kanwar shi ba, tsakanin shi da Layla, sai da ta dago kanta tana kallon idanuwan shi da suke rokonta da ta karyata maganar, ko da ta zamana da gaskene ta saukaka mishi tashin hankalin da yake ciki ta karyata. Amman bata san ta inda zata fara ba itama, ta dauka ta gama fahimtar menene shock, sai yau tasan da gaske komai zai iya tsaya maka cak, ciki harda emotions dinka "Ciki ne da ni Hamma" Ta karasa maganar da dariyar da batasan ta inda ta fito ba, duk da kuwa tana jin idanuwanta cike suke taf da hawaye "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Jabir ya furta yana zama a kasa, cikin asibiti, batare daya damu da cewa cikin lemar lemon daya zube bane, balle kuma ya damu da cewa fararen kayane a jikin shi. Tarin tashin hankalin daya kunno musu yake hasasowa, MARTABAR SU da ta samu gurbata ta fannonin da ba zasu misaltu ba ke mishi yawo, rayuwar kanwar shi da ta canza har mutuwarta yake dubawa. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:09 PM - 111: Dec 26, 2020. 24 Can nesa Layla take jin duk wata magana da sukeyi, ba zata ce ga abinda ya dinga faruwa ba, daga asibiti, zuwan Abbu, dawowar su gida, banda sautin kukan Mami babu abinda take ji, dan yanzun haka da suke a tsakar gidan ta samu wajene ta zauna a kasa, gefen Mami da ta kasa shiga daki ta durkushe a wajen. Kuka takeyi kamar ranta zai fita, dan har yanzun ta rasa ta inda zata fara yiwa Abbu bayani, sanda yazo asibitin ta farfado, dan haka suka dawo gida, ita da shi a mota daya, sai Jabir daya kama hannun Layla yana sakata a motar da suka zo suka taho. "Wai dan Allah wani a cikin ku ya bude baki yayi mun magana, tun dazun na tambaye ku abinda ya faru" Abbu yake maganar da wani yanayi a muryar shi, hankalin shi a tashe ya same su asibiti, sai dai lokacin harma sun fito, tun daga can kuma Mami take kuka, sau daya ya tambayeta abinda ya faru, da bata amsa ba sai yayi shiru saboda bayason su fada mishi abinda zai saka shi kasa yin tuqin su iso gida. "Layla me ya faru? Wani abin suka ce ya same ki?" Ya karasa tambayar yana kallon Layla da ta dago idanuwanta tana saka su cikin na shi, bata san me zata ce mishi ba, saboda har yanzun wani irin shiru take ji cikin kanta. Kafin jikinta gabaki daya ya dauki bari, zuciyarta na soma dokawa, girman abinda yake faruwa da ita yana danneta, so take ta bude bakinta, ba ta dan ta bawa Abbu amsa ba, sai dan ta kira sunan Allah, ta furta kalmar "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Ko zata samu sauki, ko Allah zai kawo mata dauki abinda yake faruwa ya zama mafarki, amman ta kasa, Abbu kallon shi ya mayar kan Jabir da karo na farko a duniya yake son kasancewa ko ma ina ne da cikin gidan, banda fuskantar abin nan da yake faruwa da su "Abbu karka tambayeni, dan Allah karka sa in fara fada maka" Ya karasa maganar muryar shi na karyewa, zuciyar shi zafi takeyi, so yake yabar wajen, amman ya kasa, ba kukan Mami bane baya ci mishi rai, tunanin halin da Abbu zai shiga ne yake hautsina mishi lissafi. "Ciki gare ta, cikine a jikin Layla... Ahmadi ciki" Mami ta karasa tana jin kamar ana zare mata rai, ya kusan mintina biyu maganganunta na yawata mishi, runtsa idanuwan shi yayi yana sake bude su, so yake ya ga shin shi kadai ne yake ganin wani duhu-duhu ko kuma garin ne gabaki daya ranar da ake kwallawa ta lumshe, amman da ya bude wannan karin ma duhun ya sake gani, kamar a cikin duhun wani abu na jujjuya mishi. Ba dan Bilal daya fito daga bangaren Ayya da kofi a hannun shi ba, ya hango su ya fara karasowa in da yake ganin kamar Abbu na shirin faduwa, yanayin da ya saka shi yin jifa da kofin zobon da yake rike da shi ya karasa ya tallafe shi yana taimaka mishi ya tsaya kan kafafuwan shi, tabbas da zancen ya bambanta "Subhanallah, Abbu..." Bilal ya kira zuciyar shi na wani tsalle cike da tashin hankali, Abbu kuwa kafadar Bilal ya dafa yana samu ya tsugunna saboda kafafuwan shi da suke rawa, kokawa yake da numfashin shi saboda tashin hankali, baiga ta yanda Mami zata ce mishi Layla na dauke da ciki ba. Kirjin shi na zafi yake kallon Mami "Maryama ki fadamun abinda zuciyata zata iya dauka... Dan girman Allah, rokon ki nakeyi" Hannu ta saka tana share hawayen da suke sake zubo mata, ta bude bakinta yafi sau biyar tana rasa kalaman fadi, haka kawai Bilal ya tsinci kan shi da shiga tashin hankali, bai san me yake faruwa ba, amman zuciyar shi duk ta gama birkicewa, hannun shi yaji Abbu ya kamo "Bilal kaji me tace? Wai Layla ce take dauke da ciki, yata Bilal, yarinyata, amana ta" Runtsa idanuwan shi Bilal yayi, ya bude su a cikin na Layla da take kallon shi, duniyar na karasa hautsine musu a lokaci daya. Kai ta girgiza mishi a hankali tana neman hawayen da zasu sama mata sauki ko yayane. Amman ta rasa su, sunki fitowa. Tsaye Bilal yake a waje daya, amman duniyar duka juyawa takeyi da shi, kamar wanda aka dauka ana zagayen cikar shekara haka yake jin shi, so yake wani ya taba shi ko zai daina jujjuyawa haka, kamar an amsa rokon shi yaji hannuwan Ayya akan kafadar shi, hannun da yake da yakinin zai gane shi a cikin dubban hannaye. Hannun daya kama nashi a lokacin daya rasa kowa, hannun daya taimaka mishi tun kafin ya budi bakin rokon hakan. Ayyar shi, juyawa yayi yana ganin damuwar da take kan fuskarta "Ayya" Ya kira da wani yanayi da ya sata fadin "Menene? Me akayi maka? Me akace kayi?" Saboda ta san yaranta, tasan Bilal ba zai hargitse haka ba idan ba wani laifin akace yayi ba, ganin yana kallonta kamar duniyar shi na shirin zuwa karshe ya sa Ayya kallon su Abbu sa suma a hargitsen suke, ba zatace ga abinda ya fito da ita ba, zuciyarta ce taki samun natsuwa sam. Ashe yaranta aka saka a gaba haka shisa hankalinta yaki kwanciya "Me yayi muku?" Ta watsa tambayar, tana saka Mami share hawaye kafin ta kalli Ayya "Ba shi bane ba, Rayyan ne" Ta amsa muryarta na fitowa a dakushe, yanayin da yasa Abbu fadin "Maryama!" Juyawa tayi ta kalle shi "Karka ce mun baka san in har cikine a jikin Layla to na Rayyan bane ba..." Cike da rashin fahimtar in da zancen su ya dosa Ayya take binsu da kallo, saboda maganar ce ta daketa a haggunce. "Ciki? Laylar ce da ciki? Ciki naji kince Maryama. Kin san me kike fada kuwa?" Saboda duk yanda ta tsane su, duk yanda bata son ganin su, ciki na daya daga cikin abu na karshe da zata so kowacce yarinyar da bata kasance karkashin inuwar aure ba da shi, ko da bata santa ba, balle Layla da suke cikin gida daya. Yarinyar da ta girma a gaban idanuwanta, bugun zuciyarta da yake kara hauhawa na tabbatar mata da tashin hankalin nan bana Mami bane ita kadai, kafin wani bangare na kwakwalwar ta ya juya kalaman Mami din "Mami..." Wannan karin Layla ce ta kirata, wani irin kuka na kwace mata, kukan da take ta nema tun shigowar su gidan "Uban waye? Ki fadamun cikin waye a jikin ki idan bana Rayyan ba Layla? Ki fad..." Bata karasa zancen ba Ayya ta katse ta "Rayyan ya fita daga bakin ki Maryama, nasan kina cikin tashin hankali, wannan karin zan miki uzuri. Amman karki sake alakanta cikin jikin ta da yarona. Wallahi zamuyi tashin hankalin da bamu taba yin irin shi ba" Wata dariya Mami tayi duk kuwa da sabon kukan da yake gab da kwace mata "Akwai wani tashin hankali da kike tunanin zai girgiza ni bayan wannan da nake ciki? Babu, yau dai kece zaki girgiza saboda ina dai-dai dake" Kallon su Abbu yakeyi, tun kafin Mami ta shigo gidan yake fuskantar tashin hankali kan zuwanta a wajen Maryama, tun da tazo duk tsayin shekarun nan da addu'a yake shigowa cikin gidan shi kar yaji wani tashin hankalin. "Idan har ba zaku iya ajiye haukan nan ku san muna cikin matsalar da ta fishi girma ba ku fitar mun daga gida, dan Allah ku duka ku fitar mun daga gida inji da abu daya" Daga zuciyar shi yayi maganar, ba zasu kara daga mishi hankali fiye da wanda yake ciki ba, saboda a duniya baisan akwai irin wannan tashin hankalin ba, duk yanda yake dauka labaran kalar shi na taba shi, bai kai yanzun ba sam, ta ina zai fara? Yar shi da rayuwarta gabaki daya ta sauya? Amanar daya kasa rikewa? Ko kuma Rayyan da Mami take alakantawa da wannan barnar? Dan mutane basu dame shi ba, abinda zasuce bashi bane a gaban shi a yanzun. Yanda zai fara daukar wannan matsalar balle ya nemi mafitarta. Wasu hawaye masu zafi Mami taji sun zubo mata. Ayya ma ji tayi kafafuwanta sun kasa daukarta, har ranta taji zafin abinda Mami ta fadi akan Rayyan, badan tasan halayen shi ba, amman zuciyarta ba zata taba yarda shi yayi wannan barnar ba. Kallon Layla tayi da ta saka fuskarta cikin hannuwanta tana wani irin kuka. Abinda duka yara suka kasa ganewa kenan, abinda in da yanda zatayi zata bi yara wanda suka kai Layla, wanda basu kaita ba, wanda suka girmeta daya bayan daya ta hasko musu wannan ranar, ta nuna musu tashin hankalin da zai biyo bayan kuskure kwara daya. Abinda duk suke dauka wayewa aikin banza ce in har ta kasance ba'a karkashin inuwar aure ba. Jin dadin wani lokaci zai iya zama barazana da sauran zaman lafiyar da ya rage musu a duniya. Kuskure daya zai jefa wasu wasi a zukatan mutane kan Martabar su, da ta duk wani ahali nasu, kuskuren su zasu aikata, amman zunuban zasu raba da duk wani daya damu dasu ne. Sai da tsikar jikin Ayya ta mike gabaki daya da ta hasaso faruwar abin nan akan Rukayya, wani irin tsoro marar misaltuwa na dirar mata. Kafin ta tuna ta kula da Layla, sai taji kamar ba huruminta bane bincike saboda Layla ce, saboda ta tsane ta, ta kuma tsani Mami, ga shi yanzun abin ya samu wajen zama a kirjinta yana sakata jin daukar wani bangare a kason tashin hankalin da suke ciki. "Ta fadi komai Ahmadi, komai banda dorawa Rayyan laifin nan" Ayya tayi maganar cike da roko, kirjinta kamar ana hura wuta. Saboda batasan ya zatayi ba idan akace dan daya fito daga cikinta ne yayi wannan aikin "Baki san na gansu rungume da juna ba? Ya zaki ce mun bashi bane ba?" Mami ta tambaya tana kallon Ayya da take mata wani irin kallo itama "Rayyan da Layla kika gani rungume da juna?" Cewar Ayya, Mami na jinjina mata kai "Saboda baki da mafadi ko rashin hankali shine kika sake barin ta kusa da shi? Maryama sai kika barta a kusa dashi in har kin gansu da idanuwan ki kamar yanda kika fada... Baki da hankali ashe? Auren mijin mutane ne kawai abinda kika iya, baki iya kula da tilon yarinyar da kike da ita ba?" Ayya take maganar yau tana jin da tana kusa da Mami din sai ta dauketa da mari, tana jin yanda komai ya koma gefe sai kalaman Mami din, tana jin yanda har zuciyarta ta shafe mata matsayin Rayyan, so take taji me abinda ya kwance akan Mami tabar Layla ta sake komawa Zaria in har da gaske ta ga Rayyan rungume da ita. Saboda daga ranar da ta ga maganar banza a wayar Rukayya tsakaninta da wani a makaranta, ko duniyar zata hade waje daya tabar makarantar kenan, saboda bata da iko da yaron balle ta hana mishi bibiyar mata yarinya, amman zatayi ikon da Allah ya saka a karkashinta ta nisanta yarinyarta da shi. "Ya ma za ayi ace tana da ciki baki kula ba? Ki kwana daki daya da ita ki tashi daki daya da ita kice mun baki kula wani abu ya canza a tare da ita ba? Sakarar ina ce ke?" Daga Mami har Abbu sun kasa cewa komai, maganganunta ne suke shigar su, musamman Mami da take jin Ayya na zakulo kasawarta a matsayinta na uwa, yau matar da take dauka ta tsaneta, bata kaunar ta ganta ce take fada mata gaskiyar da bata da mai gaya mata ita, duk da gaskiyar tazo a kurarren lokaci. "Kasan ta gansu rungume da juna? Ahmadi ka sani?" Ayya ta tambaya tana kallon Abbu daya kara sadda kan shi kasa, bayason hada ido da ita, so yake dai labban shi su motsa ya roketa da tayi shiru, karta saka zakulo mishi nashi laifin, amman lokaci ya kure musu gabaki daya "Ka sani kenan..." Ayya ta fadi, shirun shi na tabbatar mata da ya sani, mikewa tayi tana wani irin maida numfashi, yau da yaranta ne sai ta hadasu ta zane su gabaki daya. "Sai kaima kabarta ta koma ko? Saboda ba yarku bace ba" Su duka suka kalleta lokaci daya "Maimuna..." Cewar Abbu, kai ta girgiza mishi "Baka son ji nasani, amman ka duba zuciyarka Ahmadi, idan Rukayya ce zaka bari ta koma? Me yasa kabar Layla? Ni me yasa baku fadamun kun gan su tare da juna ba?" Saboda tana da tabbacin zatayi tashin hankalin da ba zasu bar Layla ta koma ba, ko dan ta nisanta yarinyar da Rayyan. Amman sai suka barta, saboda suna ganin ita din marainiya ce, kamar komawar ne gatan da zasuyi mata, barinta da zabinta shine cikar soyayyar su. Juyawa Ayya tayi da nufin barin wajen ta hango Rayyan da jaka a kafadar shi, har ya kama hannun kofar dakin su, hayaniyar da yake ji ta rinjaye shi zuwa cikin gidan saboda muryar Ayya yake jiyowa. Tana ganin shi kuwa ta karasa ta kamo hannun shi "Zo ka fada musu Rayyan, suji da kunnuwan su" Binta yakeyi, amman idanuwan shi na kafe kan hannunta da yake rike da nashi, so yake yaji yanayin nan da yake ji duk idan tayi kusa da shi haka, amman babu, bayajin komai sai Ayya, sai yanda kusanci da ita bai saka zuciyar shi ciwo ba. Kamar mai yawo a duniyar mafarki haka yake jin shi, lokacin daya dauke idanuwan shi daga nata yana mayarwa kan Abbu da yake zaune "Abbu..." Rayyan ya kira a cikin sauki, a karo na farko a tsayin rayuwar shi. Wani murmushi mai sauti ya kwace mishi, ya sake kallon Abbu yana jiran sanannen yanayin nan ya taso mishi, yaji iskar wajen gabaki daya tayi mishi kadan, amman babu, sam bayajin kamar zai mutu idan ya kalli Abbu, ko sun kasance a waje daya kamar haka, shisa bai ga tashin hankalin da suke ba, yau baya ma ganin komai banda iyayen shi. Waje daya Bappa ya samar musu inda suke bautar kasar "Akwai gidan Uncle dina, Autan su da yake karatune a ciki da abokin shi, daki ukune amman, akwai extra daki da zamu iya rabawa da kai..." Cikin ido ya kalli Bappa ba zai manta ba "Ban tuna na fada maka ina son zama waje daya da kai ba" Ya amsa yana saka dariya kwacewa Bappa "Allah ya bada sa'ar neman gidan haya a garin Kaduna, zama dani ne saukin ka, kuma ina da mota" Wani irin kallo Rayyan yake mishi, banda Bilal bai taba kwana daki daya da wani ba, sai dai Ayya lokacin da yana yaro. Amman da hankalin shi ko na rana daya, sai ranar daya kwana a Bauchi da Bappa din, yanzun kuma ba zai zamana kwana daya ba. "Nawa ne zamu dinga biya?" Yayi tambayar saboda har ran shi bayason takurawa Bappa din, bashi kadai ba har sauran mutane. "Zan iya kiran Uncle dina in tambaye shi, amman ba ma shiri" Numfashi Rayyan ya sauke, ya kula Bappa na da son maida magana da yawa wasa, kamar Bilal haka yake wani lokacin "Da gaske bana son imposing..." Kai Bappa ya girgiza mishi "Karka damu, babu wata matsala, ka yarda dani shine saukin mu, idan ina da wani wajen ba zan zauna a gidan mutimin nan ba" Cewar Bappa, kallon da Rayyan yake mishi yana saka shi karawa da "Karka ce mun a cikin Uncles dinka babu wanda baka so" Kai Rayyan ya girgiza mishi, bawai yasan sauran bane ba, zai iya kirga lokuttan da ya taba ganin su har suka gaisa. Cikin su Yaya Ayuba ne kawai ya sani sosai sosai. Kuma karyane kace akwai wani abu da zaka ki so a halayen shi. Mutum ne mai saukin kai, kusan zai iya cewa duka yan gidan su Abbu ne da sanyin hali, har matan daya gani kuwa. "No way" Bappa yai maganar cikin rashin yarda yana saka murmushi kusan kwacewa Rayyan din, bayason mutane, amman Bappa na da wani abu a tattare da shi da yaja shi hira haka har maganar ta tsawaita "Ba kamar kai ba, ni ina son kowa" Yayi maganar cikin sigar wasa, sosai Rayyan yayi dariya "Karka manta karantar mutane ne fanni na" Murmushi Rayyan yayi yana fadin "Bana son mutane, ko kadan" Kusan zaice ranar ne ya san menene aboki, menene magana da wani da bai hada jini da shi ba. Duk da cikin satin farko na zama da Bappa ya saka shi jin kamar zai dinga tsigar gashin kan shi saboda yanda Bappa yake tura shi bango, kuma dariya yakan yi "Bafa zan zauna bana magana bakina yayi tsami ba" Tunda sassafe zai fara bashi labari, wani lokaci saiya nemi wani abu ya jefa mishi, saboda sai da safen yake samu yadan runtsa bayan ya gama shiryawa, wajen karfe tara suke fita, amman surutun Bappa ba zai barshi ba "Bacci kakeyi?" Zai tambaya, ko yayi shiru ya kyale shi zai fara mishi surutu yana bashi labarai "Wai akan me zaka dinga bani labarin da ban tambayeka bane ba Bappa?" Ya tambaye shi wani lokaci, sai yaci gaba da kurbar shayin shi yana bashi labarin kamar ma baiyi magana ba, juyawa Rayyan yayi yana daukar dayan Pillow din ya rufo daga kunnen shi zuwa fuskar shi, kafin yayi amfani da shi yana jifan Bappa daya addabe shi, ko Layla bata takura mishi yanda Bappa yakeyi a yan kwanakin daya san shi. Sosai yake shigar mishi hanci, musamman ma akan magungunan da baisan me yasa yake sha a gaban shi ba, tunda ko Bilal baisan yana shan su ba. Ranar da ya saka shi a gaba yana fada mishi illar kwayoyin da bukatar sake ganin likita tunda ba damar ya ga kan shi yana abusing magunguna haka kamar bai sani ba ya tura Rayyan din bango, sosai yake jin ya gaji da yanke mishi hukunci da Bappa yake dan yana shan kalar magungunan da yake sha, duk da ba kullum ba, kuma guda daya yakan sha. "Me yasa kake tunanin ka sanni ne Bappa? Dan kana shan Anti-depressant baya nufin ka fahimci matsalata" Cikin ido Bappa yake kallon shi "Ka fahimtar da ni" Numfashi Rayyan ya sauke, watakila idan ya fito da abin a fili yayi mishi saukin dauka, watakila idan ya fadama Bappa ya daina damun shi, ba zaice ga dalili daya da ya saka shi bude bakin shi da yake rufe da matsalolin shi duk shekarun nan ba, dan ko likitocin da ya dinga gani bai fada musu ba, har wanda sukayi tunanin bayan depression yana tare da post traumatic disorder wato PTSD, da sauran tarkacen ciwuka da suka shafi mental health. "Bana son ganin Babana, ko kadan bana son ganin shi, bana son magana da shi, bana son duk wani abu da shi yake so. Koma menene idan ya nuna yana so zuciyata kamar wani na turata ta nisanta da abin... Idan ya matso kusa dani kamar zan mutu nake ji. Bappa babana fa, Abbu, bana son komai yana hadamu kamar ba daga jikin shi na fito ba..." Rayyan ya karasa yana numfasawa da nauyin da abin yake mishi a zuciya "Kowa na dariya da shi, suna magana, suna hira. Kowa nayi da baban shi, ni ban samu wannan ba. Ban kuma san dalilin da yasa na kasa samu ba, karka tambayeni. Ina tuna lokuttan da nake zama tare da shi, amman lokuttane masu nisa, bansan me ya faru ba lokaci daya..." Ganin Bappa yayi shiru yana sauraren shi da dukkan hankalin shi yasa Rayyan cigaba da magana, a wannan bigiren baima jin zai iya yin shiru ko da yaso, duk da abu da yawa da yake damun shi din baisan yanda zai misalta ba. Kirjin shi ya dafa "Kaman akwai duhu a zuciyata da kaina haka nake ji, duniyar duka bata mun dadin zama, ko karatun Qur'ani da nake samun sauki bana iyayi wata rana, jikina namun nauyi in tashi, ban san ya zan fada ka gane ba, amman bana jin dadi, na zabi Psychology dan in fahimci matsalata, amman babu abinda nagane, nawa ba depression bane ba, ya wuce haka" Ya karasa da wata irin karamar murya, kafin shiru ya ziyarci dakin, siririn numfashi Rayyan ya sauke, akwai tarin maganganu da yake sonyi amman ya gaji, ba da surutun ba, da yanda zai hada abinda yake cikin kan shi ya zama kalamai. Gyara zama yayi da nufin ya koma ya kwanta, muryar Bappa ta daki kunnuwan shi "Mu biyar mukai accident, Mamana, Yayyena guda biyu sai Kanwata, ni ka dai na fita..." Kallon shi Rayyan yayi "Ban san me yake damun ka ba, ba kuma ina kokarin nuna maka matsalata tafi taka bane ba, ina so ka fahimci komai zaiyi dai-dai, kowacce matsala tana da lokaci... Bana jin taka na da alaka da asibiti. Baba zai zo Kaduna nan da kwana biyu, sai muje mu fada mishi, kila zai iya taimaka maka" Kai Rayyan yake girgiza mishi tunda ya fara maganar, shima baisan ya akayi ya fada mishi ba, bayajin bakin shi zai sake budewa a karo na biyu ya fadama Baba kamar yanda Bappa ya kira shi. Kallon Bappa din yake da wani yanayi na daban "Allah ya jikan su" Ya furta a hankali, kan da Bappa ya jinjina yana amsawa da "Amin Ya Rabbi" Shi yasa Rayyan sanin yaji me yace, saboda a hankali yaji muryar shi ta fito. Hidimar su sukaci gaba dayi bayan nan kamar kowa baisan ciwon kowa ba. Har kwanaki biyu suka cika, Bappa baice mishi komai ba, bai sake daga mishi maganar zuwa ganin Baba ba, duk da yaji sunyi waya sun gaisa. Jikin shi na mishi wani iri, musamman da ranar tazo asabar, su kadaine a gidan, sauran yaran da suke nan sai da ya gansu duk basu shige sa'annin Layla ba. Gashi suna da hankali, basa wani hayaniya suna damun su, ko falo suka zauna suna kallo da wahala kaji hayaniyar su, kuma zasuyi kasa da maganar tv din. Har yamma suna gida a zaune, Bappa ya dafa musu taliya, kamar Haris, ya iya dafa abubuwa da yawa. Kuma mai dadi yakeyi musu ba irin girkin Bilal ba. Dan haka babu inda suka fita, yanzun ma yana zaune yana kallon wani film a laptop din Bappa, Chinese ne ma, amman yana mishi dadi, yaga Bappa ya mike, gyara zama yayi yana cigaba da kallon shi, har saida ya dawo yana fadin "Ka fito ga Baba nan" Bai bashi damar amsawa ba ya sake ficewa, wani irin bugawa Rayyan yaji zuciyar shi nayi, tabbas zai saukema Bappa, saboda ba suyi haka da shi ba, sai ya tsinci kan shi da jin wani irin nauyi, saboda idan har Bappa na mishi kwarjini haka, baisan yanda baban shi zai kasance ba. Tunda yake bai taba sake kayan da suke jikin shi bai kara wanka ba, amman yau manyan kaya ya dauka ya saka, yana nemar hula ya dora a kan shi sannan ya fita. Aikam baiyi mamakin ganin kwarjinin da yake tattare da Sheikh Abdullah ba. A mutunce suka gaisa, Baba na dorawa da "Bappa yamun bayanin komai, In shaa Allah babu abinda yafi karfin addu'a. Anjima da daddare sai kuzo ku karbi sako, akwai addu'o'in da zan baka kuma, saika daure ka dingayi kullum da safe muga abinda Allah zaiyi nan da kwana bakwai" Kai Rayyan ya jinjina, sai da Baba yayi musu addu'a sannan ya mike, har bakin kofa suka raka shi, Rayyan ya dawo ya jira Bappa anan falon harya raka Baba waje ya dawo "Baka da hankali ashe? Me yasa zaka saka Baba yazo?" Murmushi Bappa yayi "Ba zan iya daukarka ba, balle in sakaka a mota in kaika, shisa. Kuma karka damu Baba bashi da wata matsala bai dauki hakan komai ba" Numfashi Rayyan ya sauke, shi ya dauki hakan wani abu, saboda Baba mutum ne Babba, ko bai girmi Abbu ba zasu zo sa'anni. Haka yayita jin wani iri har sanda suka je gidan da Baba ya sauka. Ruwan zam zam ne ya basu roba biyu, daya yace Rayyan din ya samu waje mai tsaf sai ya shafe duka jikin shi, kullum da dare har kwana bakwai, dayan kuma ya dinga zubawa a cikin kofi, ya saka garin habba, sai Ayat as shifa da zai karanta kullum. Sosai ya tsinci kan shi da yiwa Baba godiya, bai barsu sun tafi ba sai da suka ci abincin dare tare da shi, yanda yake ta musu hira na saka Rayyan jin wani iri. Saboda shine karo na farko da ya zauna da wani babba suna cin abinci. Ko Yaya Ayuba basu taba yin wannan da shi ba, da suka koma gida ma ya kalli Bappa da nufin yi mishi godiyar da baisan ta inda zai fara ba katse shi yayi "Karka cemun ka gode, get better, shine godiya da zakayi mun, nasan depression Rayyan, na san duhun da yake cikin shi. Kayi kokari dan Allah, sai muje asibiti daga baya kan kwayoyin nan, yanzun ka fito daga duhun da kake ciki" Kai ya jinjina, ranar kuwa yayi amfani da duka ruwan zam-zam din biyu kamar yanda Baba yace tunda a hanya suka tsaya suka siyi garin Habba din me kyau. Baiji komai ba saida ya kwanta, kamar ana zare mishi rai haka ya dinga ji, jikin shi ya dauki zafi sai kace yana cikin gidan biredi. Zuwa karfe sha daya na dare ya fara galabaita da tuqar amai da take taso mishi, aman daya dinga kwarawa kamar zai fitar da kayan cikin shi. Haka suka kwana, Bappa yaki yin bacci saboda yanata fama da Rayyan suje asibiti amman yaki. Da safe kasa fita masallaci yayi, sai a gida suka tsaya Bappa yaja musu sallah. Har wajen tara yana jin gabaki daya jikin shi ko karfin kirki babu. Da Bappa ya taba shi ture mishi hannu yayi "Rayyan kaji jikin ka kuwa? Tsaf zan soya kwai akan goshin ka, ka tashi muje asibiti" Banza yayi ya kyale shi, amman halin da yake ciki yasa Bappa ya kira Baba yana fada mishi "Alhamdulillah, abinda nake tunani ne ya tabbata, ka barshi, aman shine saukin shi. Yaci gaba da sha, har Allah ya taimaka ya fitar da abinda yayi karfi a jikin shi" Cike da tsoro Bappa yace "Sihiri ne ko Baba?" Murmushi kawai Baba yayi ta dayan bangaren "Allah ya bashi lafiya. Allah ya kare mana imanin mu ya nisanta mu da dukkan abin ki" Numfashi Bappa ya sauke, yana amsawa da "Amin" Kafin yayiwa Baba sallamar. Kwanakin da suka biyo bayan ranar ba masu sauki bane ba, dan duk yanda Rayyan din yaki saida Bappa ya kira likita cikin gida aka daura mishi karin ruwa. Kamar ana zuko wani abu a cikin jijiyoyin da suke jikin shi suna hade da zuciyar shi haka yake ji. Bai taba ciwo irin wannan ba, cikin kwanaki bakwai kamar bashi ba, duk ya fita hayyacin shi, wajen aiki ma randa yaje ca sukayi ya koma ya kara hutawa na sati daya sannan. Yayi wata irin ramewa. Baba sai da ya kara aiko mishi da wasu robobin biyu, yace karya daina sha saiya sha sau biyu yaga baiyi amai a cikin kwanakin ba tukunna. Ba abinda ya dinga bama Rayyan mamaki sai baccin da yake kusan kwana ya wuni yanayi, saiya alakanta hakan da rashin karfin da bashi da shi. Amman a cikin sati na biyu ranar ya tashi da safe yaji shi kamar yana lilo saman iska, kan shi wasai, sai kace an kwashe wani datti daya jima yana taruwa a cikin kan nashi haka yake ji. Da sukayi waya da Layla dariya yaga yanayi, zuciyar shi na dokawa da wani bakon yanayi da bai taba sani ba, kwana wajen hudu yana tashi a tsorace, saboda gani yake kamar yanayin ba mai zama bane ba. Sam baiwa Bappa gaddama ba sukaje asibiti, wasu magungunan aka dora shi a kai. Yana sha kuma, yana samun bacci, ashe haka baccin dare yake tattare da Rahma, duk da ba duka daren bane tunda ya samu sauki, amman zaiyi bacci wajen sha biyu har safe, sai yake jin shi duk wani sakayau. Ga Bappa baya barin shi ya zauna shi kadai, kullum suna yawon zaga gari, har gidan ball yake jan shi suje kallo, duk da yakan dawo da ciwon kai. Yanzun yake sanin halayen shi akwai wanda basu da alaka da komai, sam bayason mutane, wannan halin shine. Baba bai daina aiko mishi da robobin zam zam ba, a cewar Baba har yanzun yana bukatar su. Saboda hutun rashin lafiya da suka bashi shisa basu zo Kano ba, sai yau, Bappa ya sauke shi ya wuce, yanata sauri shisa bai karaso da shi ba, yace zaiyi zuwa na musamman idan ya tashi. Da wata irin kewar Layla da Bilal din ya sauka garin Kano, da ita kuma ya shigo gidan har yake tsaye inda yake yana juya kasancewa waje daya da Abbu batare da yaji kamar iskar wajen tayi mishi kadan ba. Yana kuma jin zuciyar shi sakat "Ka fada musu cikin jikin Layla ba naka bane ba" Muryar Ayya ta katse mishi tunanin da yakeyi tana dawo da hankalin shi kanta cike da son fahimtar inda zancen ta ya dosa... * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:09 PM - 111: Dec 26, 2020. 25 Maganganun Ayya ne suke mishi yawo, kafin ya zare hannun shi daga cikin nata, yana kallon Layla da jin an kira sunan shi ya sakata bude fuskarta, idanuwanta har sun kumbura saboda kukan da takeyi. Tana jin su, bata san kalar tunanin da ya kamata tayi ba, duniyar duka take ji ta hade mata waje daya. Ta rasa da wanne zata fara, tashin hankalin abinda yake faruwa da ita karon kanta, halin da su Mami suke ciki, Abbu da take ganin ba zuciyar shi kawai ta taba ba, harda Martabar shi, ko kuwa Rayyan da take ji suna lakabama laifin da ba nashi ba? Ko yanzun da yazo yake kallon ta, yake neman amsa a cikin idanuwanta, a hankali take ganin yanda komai yake shirin canzawa a tsakanin su. Duk a cikin abinda yake faruwa shi tafi ji, shi tafi tunani, in zai rike hannunta, ya kasance da ita, hargitsin zai mata sauki, amman tana ganin yanda wasu katangu suke fara ginuwa a tsakanin su, wasu hawaye ne masu dumi suka zubo mata, tana runtsa idanuwanta ta bude su a kan Rayyan. Dan kallon ta yakeyi, wannan karin ta cikin idanuwanta yake son tabbatar da gaskiyar abinda kunnuwan shi suka jiye mishi kafin yasan matsayin kalaman a zuciyar shi, kamar ciki yaji ance tana da shi, kamar ji yayi ana kiran cikin da yake jikinta da nashi. "Hamma..." Labbanta suka motsa, muryarta sam bata fito ba, amman shi yajita a cikin kan shi, yaji ta a cikin zuciyar shi inda wani abu yake bubbudewa da ciwo na gaske "Rayyan..." Yaji muryar Ayya da take kallon shi cikin tashin hankali, saboda shirun shi yana nufin abubuwa da dama, shirun shi yana nufin daukar laifin da ake so a makala mishi, bata san lokacin da ta kama hannun shi tana jijjigashi ba "Kana da matsala kala-kala tun tasowar ka. Rayyan ka bude bakin ka kace mun ba kayi ba, ka fada kowa yaji wannan matsalar ba taka bace ba" Wani abu yake ji tokare da makoshin shi, amman baisan ta yanda zaiyi ya hadiye shi ba, bakin shi ya kafe kamar ya kwana biyu bai sha ruwa ba. Baisan yanda akayi jikin shi baya rawa ba, saboda gabaki daya zuciyar shi jijjiga takeyi tana rarrabuwa sashi-sashi. "Ciki aka ce... Rayyan ciki. Ciki ake magana a kai ba abu na wasa ba" Ayya ta karasa muryarta na karyewa, idanuwanta sun fara cikowa da hawaye saboda tashin hankali. Dan daya fito daga cikinta ba zaiyi wannan barnar ba "Rayyan" Ta kira cike da roko wannan karin, hawayenta na zubowa, kallonta yayi cikin ido, abinda yakan dade baiyi ba, kafin ya kama hannunta da yake damke da nashi ya sauke. Kan Layla ya sake sauke idanuwan shi da suke cike da tarin tambayoyin da baisan ta inda zai fara yi mata su ba, guda daya yake so tayi duk yanda zatayi ta amsa mishi duk da bai furta a fili ba, da dukkan muryar zuciyar shi yake tambayar "Ciki gare ki? Cikine a jikin shi?" Bata san ya akayi ba, amman ta fahimci neman tabbaci Rayyan yakeyi, kai ta dan daga mishi a hankali, wasu hawaye na zubo mata. Hawayen da suka hana ta fara ganin wani yanayi da bata da kalmar fassara shi cikin idanuwan Rayyan din, kafin ya dauke idanuwan shi daga cikin nata. Numfashi yake fitarwa a hankali a hankali saboda yanda yake ji kamar baya shiga inda ya kamata, kamar yau akwai abubuwan da suke cunkushe mishi hanyar shiga da ficen iska. Juyawa yayi da nufin barin wajen ko zai samu maganar ta natsa mishi da kyau, ko zai tattara hankalin shi wajen gane girman da maganar take da shi, karfin da yake tare da maganganun da yake barazana da dan zaman lafiyar daya fara samu a duniyar shi. "Rayyan..." Wannan karin muryar Abbu ta tsayar da shi cak, tana kuma saka shi juyowa ya kalli Abbu din ido cikin ido "Ka ce baka taba mun amana ta ba, ka bude bakin ka kayi mun magana" Wani numfashi Rayyan yaja a wahalce, bashi bane ba, ko zai taba Layla, ba zai taba zama ta wannan fannin ba. Ko kwayoyi yasha ba zai taba ta haka ba. Saboda tunanin abinda yake faruwa yanzun, saboda yanda mutanen da suka fi komai muhimmanci a rayuwarta ne zasu fara dora ayar tambaya akan ta, kafin mutanen da basu taba bada gudummuwar komai wajen tarbiya, ci, sha da sutturarta ba su fara zagayawa da maganganu kala-kala akanta, akan Martabar gidan su. Shisa bayason mutane, wannan halin shine, ko kadan baya son su. Mutanen da yake so basu da yawa, saboda matsalolin da suke tattare da mutane yawa gare su. "Bani bane Abbu" Ya furta kalaman cikin kan shi, dama ta farko daya samu tsaye a gaban Abbu, yayi magana da shi kamar yanda kowanne da yake magana da mahaifin shi tazo mishi a haggunce. Martabar Layla zata fi karuwa idan suna tunanin cikin jikinta nashi ne, ba za'a fara mata dukan da yaga ana yiwa wata a film din Hausa da Bilal yake kallo wani lokaci ba, kan sai ta fadi uban cikin da yake jikinta. Idan sun karbi abin, tashin hankalin su ya sauka zasuji a bakin Layla, shikam yanzun ba zasuji komai banda shiru ba. Numfashin daya sauke mai nauyine, kafin yakai hannu yana dan murza goshin shi, kan shi kamar zai tarwatse haka yake jin shi. "Rayyan rokon ka nakeyi..." Cewar Abbu, kirjin shi zafi yakeyi, zuciyar shi ciwo takeyi har ko ina na jikin shi yana amsawa. Gara ace wani ne a waje, wanda zai iya shari'a dashi daga filin duniya har zuwa na lahira inda ba zai taba yafe mishi wannan laifin ba. Idan ya zaman Rayyan ne baisan yanda zaiyi ba, bai sani ba kam. Amman tabbas komai zai iya faruwa "Idan kaci gaba dayin shiru zan dauka da gaske laifin naka ne" Shirun dai Rayyan ya sakeyi, yana sadda kan shi kasa, kirjin shi Abbu ya dafe, ya dauka hawaye sun mishi kaura a shekarun shi, sai yanzun da yake jin taruwar su a cikin idanuwan shi "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Ya furta yana dafe fuskar shi da duka hannuwan shi, wani irin numfashi yake ja yana fitarwa kafin ya bude fuskar shi ya kalli Rayyan da yake tsaye a gaban shi, daga yanzun zuwa wani lokaci da bai hango shi nan kusa ba idan yana ganin Rayyan din zai mishi baki, sosai yake danna zuciyar shi da kalaman da take son furtawa "Ka fitar mun daga gida Rayyan, ka tafi kawai" Ba Rayyan bane kawai ya dago da kai yana kallon Abbu, hatta da Mami sai da ta dago. Ayya ma kallon shi takeyi tana son jin ya sake furta kalaman ko zata yarda da taji su daga farko, Rayyan daya fara magana ne ya sata kallon shi "Ka nuna mun wani uban, Abbu a yanzun nan idan ka nuna mun wani uban ko jakar da take kafadata ba zan sauke ba, zan fita in bar maka gidan ka, zanyi nisa da gidan ka, zanyi nisan da ko nemana kayi ba zaka ganni ba..." Numfashi Abbu ya sauke yana kallon kasa, kafin ya sake dagowa, baisan lokacin da ya daga hannu ya dauke Rayyan da mari ba, karar na amsawa a ko ina na wajen kafin Bilal ya motsa kafafuwan shi yana karasawa ya shiga tsakanin Abbu da Rayyan din, dan harya sake daga hannu zai kara dauke Rayyan da yake kallon shi ido cikin ido har lokacin da mari "Abbu... Dan Allah Abbu" Bilal ya fadi a wahalce, wani nishin wahala na kwace mishi, tunda suka fara magana yake so kasar wajen ta bude ya fada ciki ta rufe da shi, rufewa na har abada ko zai gujema fuskantar kowa da kowa. Amman yaki faruwa, tunda suka kira sunan Rayyan komai ya karasa kwance mishi, kalaman Abbu suke mishi yawo har lokacin, babu tunanin komai a ran shi sai na yanda idan mutuwa ba tazo mishi ba, tabbas karshen zaman shi tare da su yazo. Idan Abbu yace Rayyan ya fita yabar mishi gida a haka, tabbas shi zai saka a rakashi waje ne. A tsorace yake, tsoron da ya saka shi tunanin akwai sauki mai girman gaske a tattare da mutuwa, wani tsoron na daban yana kara bugar shi, saboda hango kwanciyar kabarin shi da yake cike da kokwanto da yayi, a da laifukan shi yana jin tsakanin shi da Allah ne, yanajin suna da sauki mai girma saboda Allah Mai Rahma ne. Amman yanzun laifin shi nacin amana ne, kuma bayason fara tunanin makomar masu cin amana. Bayaso sam, gabaki daya jin shi yakeyi a gigice kamar zai shide "Matsa mun Bilal..." Abbu yayi maganar da wani yanayi da Bilal bai taba ganin shi a ciki ba, kai Bilal yake girgizawa "Abbu ni ne, ni ne Abbu" Ya furta a razane, saboda ba zai tuna ranar karshe daya ga Abbu ya dagama wani daga cikin su hannu ba, amman a idanuwan shi yake ganin inda abun duka a kusa da shi yau zai saka shi ya jibgi Rayyan din, ba zai kara wani laifi ba, bayan cin amana ba zai shiga tsakanin mahaifi da dan shi ba, ba zai iya kara daukar wani tashin hankalin ba, kamar zai fashe da kuka yake kara fadin "Ni ne Abbu" Kai Ayya ya dafe, hawaye masu zafi na zubo mata, Mami ta kalla, duk ita ta shigo rayuwar su, ta shigo musu da Layla har suka zo inda suke din nan yanzun. Bilal take kallo da gabaki daya ya rikice, tun tasowar su, ko Rayyan zata daka haka yake shiga tsakani, ko da zata rufe ido taci gaba da kai duka ba zai matsa ba, zai amfani da jikin shi ya kare na Rayyan din yana kuka yana bata hakuri. Akwai tarin lokutta da tasan Rayyan ne yayi laifi amman Bilal din zai dauka. Shine yake faruwa a gaban idanuwanta yau, amman ba zata bar shi ba, ba zata kyale shi daukar wannan laifin ba "Karya yake, ya saba Ahmadi, ya saba daukar laifin Rayyan" Ayya ta karasa da wani yanayi, kanta sarawa yake ta kowanne bangare, tana tunanin rashin amfani na Malaman duk da tayita asarar kudinta a kansu, duban su da bugun kasar su ya tashi a banza da suka kasa hango mata wannan tashin hankalin, da basu fada mata ko da bata iya kauce mishi ba tasan yanda zata karbe shi tunda wuri, hawan jinin da bata da shine yake son kamata lokaci daya "Bilal ka matsa kafin in wanke ka da mari kaima" Cewar Abbu, jiri yake gani sosai zuwa yanzun, amman so yake Bilal ya matsa ya kara ganin Rayyan "Abbu wallahi ni ne" Wani murmushi mai ciwo Abbu yayi "Karyar ce kake bi da rantsuwa Bilal? So kake in yarda da kai haka?" Kan shi Bilal ya sadda kasa yana rasa inda zai saka ran shi yaji sauki-sauki. Komai ya cunkushe mishi, yana ganin Abbu ya juya ya fara takawa, sai dai ko taku biyu baiyi ba ya yanke jiki ya fadi. Kan shi sukayi gabaki dayan su cikin karaji banda Rayyan da Layla, shi yana nan tsaye inda yake, yana rasa kalar tunanin da yakeyi ko ya kamata yayi. Layla kuma tashin hankali ne ya sake dirar mata, shikenan ta kashe mutum daya da ya karbeta a lokacin da kowa yakita, mutumin da bai taba sakawa taji maraicin da take tare da shi ba. Kuskure daya ya canza mata komai. Bilal da Jabir ne suka kama shi suna yin dadin Ayya da shi, dan tunanin asibiti baizo musu ba. Jabir ne yayi tunanin samo ruwa ya shafama Abbu a fuska kafin ya bude idanuwan shi yana kokarin mikewa "Abbu faduwa kayi fa, ka kwanta dan Allah" Jabir yayi maganar kamar zai saka kuka, baisan tashin hankali ba duk tsayin rayuwar shi sai yau. Ko abokai ne in ka nemi daga mishi hankali zaka neme shi ka rasa ne. Sam baya zama, shisa abin yake tabashi sosai da sosai. "Idan na kwanta ba zai canza komai ba Jabir, kabar ni in tashi in fuskanci matsalar nan" Mikewa Bilal yayi, ba zai iya dauka ba, zuciyar shi ba zata iya dauka ba sam. Ficewa yayi daga dakin zuwa nasu. Rayyan kuwa yana inda suka bar shi, Layla yake kallo har su Mami suka bi bayan su Bilal suna barin su kadai a wajen "Hamma" Layla ta kira tana son ya taimaka mata, ko da zai zama lokaci na karshe a tsakanin su, ya taimaka ya fahimce ta, saboda tasan babu wanda zai taba fahimtarta. Yanzun a kan idonta taga rashin yarda a idanuwan kowa kan cewa cikin na Bilal ne, kowa yaki yarda, tana kuma ganin katanagar da Rayyan yake ginawa a tsakanin su, idan ta bude bakinta, idan ta fada musu cikin na Bilal ne duka zasu yarda, dole zasu yarda. Amman idan suka ce ta auri Bilal fa? Tunanin kawai ya girgiza duka ilahirin zuciyarta balle ya kasance ya tabbata, da gaske mutuwa zatayi idan ta rasa Rayyan. Watakila tana da sauran rabon zama da Rayyan shisa yaki musa cikin jikinta ba nashi bane ba, so take ya bude bakin shi yayi mata magana "Hamma" Ta sake kira, dafe kan fuskar shi Rayyan yayi da hannuwan shi duka biyun, yakai mintina biyu a haka kafin ya bude su akanta, a karo na farko yana tsintar kan shi da kin son ganinta. Har a zuciyar shi bayason ganinta "Dan Allah Hamma..." Ta fadi cikin kuka, kai Rayyan yake girgiza mata "Bana son ji, koma menene, ba zai canza komai ba Layla" Ya karasa yana juyawa, baisan yana cikin tashin hankali ba saida ya karya kwanar da zata kai shi dakin su yaji kafafuwan shi sun kasa daukar shi, a wajen ya tsugunna ya dafe kirjin shi yana jin kamar zai rabe gida biyu. Bude bakin shi yayi yana fitar da numfashi saboda ta hancin kofofin sun toshe mishi, cikine a jikin Layla. Yaron wani ne yake rayuwa a jikinta, yaron da ba na shi ba. Layla, Laylar shi ake magana a kai ba wata ba. Waye zai musu wannan abin? Waye zai taba mishi ita haka, runtsa idanuwan shi yayi yana kuwa bude su babu shiri saboda kazantar hoton daya hasaso cikin kan shi. Koma wanene tare da Layla suka ci amanar shi. Abin da yafi tsana a rayuwar shi, ya bude baki ya fada mata yana son ta, Layla da ya dawo da burin fuskantar kowa da sunan soyayyarta ce da dan wani a cikinta. Bangon wajen ya dafa ya samu yana mikewa, so yake ya karasa daki ya kwanta, jiri yake gani a tsugunnen ma. Dakyar ya iya mikewa yana shiga dakin su inda ya samu Bilal a tsaye "Zuciyata zata fashe Bilal, kirjina ciwo yakeyi" Rayyan ya fadi, in bai gayawa wani ba da gaske zuciyar shi fashewa takeyi. Bakin shi ba zai iya shiru a gaban Bilal ba, wannan abin ya mishi girma ya dauka shi kadai, so yake a lallashe shi, kamar karamin yaron da yayi mummunar rauni haka yake ji, a hankali Bilal ya juyo yana sauke idanuwan shi akan Rayyan da yake fitar da numfashi kamar mai ciwon asthma. Shima yana gab da fara fitar da numfashi ta wannan sigar idan wani bai yarda dashi ba, idan bai fadama wani laifin shi bane, saboda shi kowa yake cikin rudani, tashin hankalin zai mishi yawa. "Hamma..." Bilal ya kira da wani yanayi a muryar shi da yasa Rayyan kallon shi, abinda yake kan fuskar shi na saka zuciyar Rayyan wani irin dokawa, tun kafin ya bude bakin shi Rayyan yake girgiza mishi kai yana rokon shi, baisan kafafuwan shi sun gaji ba sai da yaji gwiwoyin shi a kasa "Dan Allah Bilal..." Ya furta a hankali, na shi kan Bilal yake girgiza ma Rayyan din shima, dole ya fada mishi, idan yai shiru bashi da hope akan Rayyan din zai yafe mishi, idan ya fada musu, idan kowa ya sani wata rana zasu ji rokon gafarar shi "Ni ne Hamma, cikina ne a jikin Layla" Kan shi Rayyan ya durkusar kasa sosai yana wani irin maida numfashi, watakila haka ake ji yayin fitar rai, saboda wani abu ke fisgar shi da kalaman Bilal. Dakyar bakin shi ya iya furta "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Yana dagowa ya dafe fuskar shi da hannuwan shi ko inya bude zai farka daga wannan mummunan mafarkin. Bilal ma kasa yayi "Hamma idan nace kuskure ne zaka yarda?" Bude fuskar shi Rayyan yayi "Kuskure? Cikin ne zaka dauka ka dora akan kuskure? Layla fa... Bilal ba wata bace Layla" Rayyan ya fadi yana kallon Bilal, har lokacin yana son ya san me ma yake ji gabaki daya "Kuskure n..." Mikewar da Rayyan yayi na katse ma Bilal maganar daya fara. Hannu ya mike mishi "Bani mukullin mota..." Da wani yanayi Bilal yake kallon shi "Baka iya tuqi ba Hamma, me zakayi da shi?" Yanda Rayyan din yake kallon shi ya saka shi mikewa "Ni ya kamata in bar maka dakin" Ya karasa yana ficewa, ko takalmi babu a kafar shi, komawa Rayyan yayi ya zauna, kan shi ya dora jikin gadon dakin yana jin kamar zai mutu. Kwanan shi biyar yau rabon da ya busa hayaki, saboda yana son ya bari, baima yi tunanin akwai wahala sosai a barin shan tababa sai da yake son bari. Jakar shi da sai lokacin ya sauketa daga kafadar shi ya bude, jikin shi har rawa yake lokacin daya dauko kwalin tabar, a yanda yake jin shi zabi biyu yake da shi, ko tabar ko kwayoyin da yayi ma Bappa alkawarin zai sha su kan ka'ida a kowanne yanayi "Abu daya zai iya sa ka koma Rayyan, dan Allah ka kula, kaga su da taba ne kawai matsalar ka yanzun" Ya kan ga Bappa din ya dauki robar maganin na shi yana lekawa, kamar yana son kirga su batare daya fito da su gabaki daya ba, ba zai iya surutun maimaita magana daya ba saiya kyale shi. Shisa yanzun ya zabi tabar, kunnawa yayi kuwa, sai da yaja kara goma amman a banza, banda zafin da kirjin shi ya kara har tari yake kamar sabon shiga a shan sigarin. Ko dan yana kokawa da numfashin shine bai sani ba. Amman ya kasa samun sauki ko yaya. Yanda duk yaso ya hango Layla da Bilal ya kasa, idan wani ne daban zai iya lakaba mishi kowanne sigar laifi. Zai iya cewa tursasa Layla yayi, zai iya cewa ya bata wani abune ta sha. Zai iya cewa komai, amman Bilal ba zaiyi abu daya daga cikin duka tunanin shi ba, gabaki daya Bilal bashi da wani dalili da zai iya tunawa nayin abinda yayi. Shisa baiga dalilin da zai saurari komai ba, iya abinda yaji ya ishe shi har karshen rayuwar shi. Kirjin shi zafi yake kamar ana hura wuta a ciki. Shisa ya sulale ya kwanta, babu abinda yake mishi yawo sai Bilal da Layla da ya kasa haskowa saboda tabbas zuciyar shi tarwatsewa zatayi. Mutum biyun da yafi yarda dasu akan kowa, mutum biyu da suka fi kowa kusanci a rayuwar shi. Bilal yana fita a bakin kofa ya zauna, hawaye yake nema ko zai samu sauki amman ya rasa su yau "Kaina kamar zai bude nake ji" Muryar Jabir ta daki kunnuwan Bilal din, gefen shi ya samu shima ya zauna. Kowa da abinda yake ji, kowa da abinda yake tunani. Yanayi ne da babu wanda zai iya lallashin wani "Na kasa yarda Hamma Rayyan zai mana haka, zuciyata ta kasa yarda..." Numfashi Bilal yaja yana saukewa "Bashi bane ba, ni ne" Murmushi mai kunar rai Jabir yayi "Idan kace kaine sai kake tunanin abin zai mana saukin dauka? Ka daina dan Allah Hamma, kabari muji da abu daya" Jabir ya karasa yana mikewa, gara ko ruwa yaje ya dauka ya sha, koya watsama jikin shi. Koma me da zai dan saukaka mishi abinda yake ji, bin shi da kallo Bilal yayi, wato babu wanda yake son sauraren shi, haka girman yardar da sukayi mishi yake daman? Haka suke ganin ba zai taba cin amanar su ba. Kamar an dora dutse a kirjin shi haka yaji. Kafafuwan shi ya kara ja yana hade su da kirjin nashi ko zai ji dama-dama. Kan shi ya dora a jikin gwiwar shi yana sauke numfashi a hankali. * Zaune Ayya take akan kafet, sai yanzun komai yake tabata, yanzun girman abin yake yawo a kwanyarta. Layla da Rayyan, kaddarar su mai girma ce haka ashe? Duk yanda taso ta shiga tsakanin su alkalami ya gama rubutun shi akan su, sai kawai tunanin farraqun da tayi musu ya fado mata. Zuciyarta na wani irin tsalle ta koma cikin makoshinta, daman ance wani rabon har kisa yakeyi. Ko nasu ne yazo a haka? Raba sun da tayine da rabo a tsakanin su shisa ya kullu ta wannan gurbatanciyyar hanyar da take jin gara mata auren, komin yanda zuciyarta bata so zata koyi jure ganin su a tare kamar yanda take ganin Mami da Abbu. Batason laifin ya zagayo ya dawo kanta, bataso saboda hakan na sakata jin kamar an tsomata a ruwan kankara. Zuciyarta ta tsinke daga inda take a kulle lokacin da taga Abbu a kasa, dan tana jin yanda zuciyar ke mata barazanar daina bugawa a mintunan da Abbu yayi bai tashi ba, yaran da take karewa da kominta, yaran da take jin zata iya komai dan nisanta su da juna, sune hanya irin wannan ta hada har suna neman kashe mata mijin da take so fiye da su, mijin da take kauna fiye da yanda take son kanta. Yanzun ma kallon shi takeyi, yanda yake durkushe kan gwiwoyin shi yana sharar kwalla, zuciyarta kamar zata fito waje "Dan Allah Ahmadi kayi hakuri, kar wani ciwon ya shigeka lokaci daya, bansan ya zanyi ba... Kayi hakuri dan Allah, komai zai zo da sauki" Take fadi tana kokarin tarbe nata hawayen, tasan mijinta, ta san shi din mai rauni ne akan lamurran duniya. Sau nawa ita take nakuda amman take samun karfin halin bashi hakuri duk idan ciwo ya kwanta mata, kuka riris haka Ahmadi yakeyi duk idan ta fara nakuda, balle takan yi mai dogon zangon da sai an fara fidda rai da ita. Yana da raunin da batasan ya zata misalta a fahimta ba, shisa tasan da wahala ya iya daukar wannan kaddarar salin alin. Bata su Rayyan ko Layla takeyi ba yanzun, ta mijinta takeyi, ta tunanin halin da yake ciki da wanda zai shiga anan gaba. Watakila da batayi katsalandan a cikin al'amarin ba da haka bata faru. Akwai abinda ya girmi tsanar da tayiwa Mami, akwai abinda zai iya tabata fiye da kaddarar da ta hada Mami da Abbu waje daya. Yanzun take gani, abubuwa ne masu tarin yawa suke mata yawo, lokuttan da tayi kokarin shiga hurumin da ba nata ba, canza lamurran da bata da iko a kan su. Zuciyarta da tsoro take bugawa, da kokwanto mai girman gaske kan makomar ayyukanta, kan inda kaddarar da tayi komai dan ta canza take son ta kai ta "Idan mutuwa ta daukeni yanzun fa Maimuna? Ni ya zanyi? Me zan fadi akan amanar da ban rike da kyau ba? Ke da kanki kin gano mun matsala a rikon da nayiwa Layla, Allah da yake ganin komai fa?" Sai Ayya taji kamar da ita yake, kamar ya watsa mata ruwan gishiri a ciwukan ta haka taji. Idan ita tata mutuwar ta dauketa kafin ta mike fa? Ya zatayi ita? Me zata fada akan katsalandan da tayi ma kaddara? Wanne hujjoji zata labe a bayan su? Hawayen da suka zubo mata masu zafi ne na gaske. "Ba kai bane baka da abin fadi, nice. Wallahi nice ban da abinda zance, ya zan kalli yan uwana? Me zance musu ya faru?" Mami da ta samu bakin magana tayi jero tambayoyin wani sabon tashin hankalin yana dirar mata, tunda suka shigo dakin ta jujjuya maganganun da Ayya ta fada mata. Idan tace ga dalili daya da ya saka ta barin Layla komawa Zaria zatayi karya. Bata san ya akayi ta yarda ta koma ba, a wannan halin ma ba zata iya dorawa kaddara ba, ba kuma ta son yin amfani da kalmar sakaci da take ta mata yawo. Gani tayi kamar akan tarbiyar duka yaran tana iya yinta. Yaune take gane baka taba yin iya yinka a tarbiya, saboda ba abu bane na lokaci daya, ba kuma abu bane iri daya. Tarbiyar jiya takan banbanta da ta yau, saboda a duk rana halaye kan canza, yanayi mai girma ko karami, bakon yanayi kan samu wajen zama da dan adam. Shisa tarbiya zata zamana yau da kullum. In kayi jiya, yau ma ka kara, saika hada da addu'ar samun karfin yin fiye da ta yau a goben da zaka samu aronta. "Nayi iya yi na" Da iyaye da yawa kan fadi ba uzuri bane ba, ba kuma lallai ya zama hujja ba a gaban Allah, su yaran amana ne. Mutum ma ya baka amana kaci ya kake karewa, balle Allah da kan shi da ya zabeka a cikin mutane da dama ya baka amanar yara, ya baka aron lokaci, lafiya, da wadatar kula da su. Soyayyar Layla ta rufe mata ido "Rikon maraya da wahala" Shine kalaman da mutane kan furta a duk lokacin da tarbiyar marayun da suka dauki amanar kula dasu ta sami matsala. Kusan shine hujjar da suke kafawa, har wanda basa rike da maraya ma suna hasaso wahalar da take cikin rikon maraya. Yau ta canza mata tunani gabaki daya, babu wani riko na yaro da yake da sauki, babu kuma wani kalar yaro da baya bukatar tarbiya. Maraya ko mai iyaye, musamman maraya da tausayin rashin iyaye kan saka iyayen rikon sakaci kan tarbiyar shi. Bata san me yasa duk wannan tunanin yazo mata a kurarren lokaci ba, babu wanda zai mata uzuri kamar yanda ta kasa yiwa kanta yanzun "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Ta furta a fili wani kukan na kwace mata. Ayya ma duk yanda take saka hannu tana share hawayenta basu daina zuba ba. Na Abbu sun tsaya daga idanuwan shi, a zuciyar shi suke zuba da ciwo na gaske, da kuma tunanin ta inda zai fara bullowa abinda yake faruwa dan bai sani ba, yaran shine karfin zuciyar shi, sune kuma raunin shi. * Iyaye Iyayen riko Jinjina da lokuttan da baccin ku baya tsawaita saboda tunanin tashin hankalin da yake tare da amanar da take karkashin kulawar ku Fatan alkhairi da tarin sadaukarwar ku Addu'ar karfin gwiwar ci gaba da kular da kuke Ta yau tafi ta jiya Ta gobe ta dara ta Kuna kokari mun sani Idan bamu yaba yau ba zamu yaba gobe, kar tunanin rashin jin dadin mu na kankanin lokaci ya rufe idanuwan ku da hango gaba Rabbi ya tayaku, Ubangijin da ya baku amana ya tayaku rike ta. Amin thumma amin * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:09 PM - 111: Dec 30, 2020. 26 Ba idanuwan shi ba, har fuskar shi a kumbure take, yayi kuka har wani yaji-yaji idanuwan shi sukeyi. Duka sallolin shi yau a gida yayi su, abinda ya manta ranar karshe da yayi. Ko bashi da lafiya saiya fita masallaci, ruwa kam banda yanzun da Yaya Ayuba ya tsare shi bai shiga cikin shi ba. Duk yanda Ayya tayi fama da shi kuwa, kai kawai ya dinga girgiza mata, da yake tasan halin shi, ta kuma san bashida wani abokin shawara a wannan yanayin daya wuce Yaya Ayuba shisa ta kira mishi shi, dan tana tunanin ko bai san damuwar su ba, zai ma Abbun fada yasa shi yaci wani abu kar ciwo ya hadar mishi biyu. Fuskar Yaya Ayuba yake kallo dan tun da ya gama magana Yaya Ayuban yayi shiru baice komai ba. Ji yake kamar Abbu ya watsa mishi ruwan kankara, ya rasa mamaki zaiyi, bacin rai ko tashin hankali. Saboda maganar yake ji tana amsawa a cikin kunnuwan shi har yanzun "Layla ciki gareta, cikin Rayyan" Lokutta da dama har ran shi yana mantawa Layla da Bilal ba daga jikin Abbu suka fito ba. Shisa maganar ta dake shi ba kadan ba, tana tuna mishi da cewar Layla yar amana ce a hannun Abbu, yar riko ce, marainiya gaba da baya. Baisan wacce irin kwamacala bace wannan da yanda zasu fara bullowa lamarin. "Kayi shiru..." Abbu ya fadi zuciyar shi na tafasa "Hmm" Yaya Ayuba ya iya furtawa yana sake gyara zaman shi, sosai maganar ke yawata mishi, amman duk yanda ta kai cikin kan shi sai yaji wani irin tashin hankali ya tsirga mishi "Nayi shiru ne ina so kace mun abinda naji ba dai-dai bane Ahmadi" Numfashi mai nauyi Abbu ya sauke, shima tun dazun yake jira, tunda ya dawo dakin shi yake so wani ya same shi yace mishi komai daya faru wasa ne, an gwada shine kawai kuma anga yanda yaran shine raunin shi, amman shiru. Duk dakika da zai wuce saiya kara tabbatar mishi da cewa komai da ya faru da gaske ne. "Ban san ya zanyi ba, wallahi ban sani ba" Cewar Abbu, Yaya Ayuba na jinjina mishi kai "Zubar da cikin ba mafita bane ba" Wani bugawa zuciyar Abbu tayi, aiko mafita ne ma bai hango za ayi wannan danyen aikin da shi ba, zunuban zasuyi mishi yawa. Laifukan zasuyi mishi nauyin dauka matuqa, yana jin kuma da muryar da Yaya Ayuba yayi magana, bamai kwari bace ba, kamar yana son Abbu ya duba yiwuwar lamarin ne. Kuma hakanne a zuciyar Yaya Ayuba, so yake ya duba in zai yiwu a zubar da cikin, zai saukaka musu abubuwa da yawa, musamman maganganu da surutun mutane idan zancen ya fita, amman a fuskar Abbu yaga yanda babu wannan tsarin a cikin jerin mashalar da yake nema. "Ina tsoron fitar maganar nan Ahmadi, wallahi ina tsoron ta, mutane zasu fadi komai, zasuyi surutai kala-kala... Ba akan Layla kawai zasu dora ayar tambaya ba, gabaki daya Martabar ahalin Dikko sai ta sami tangarda..." Kai Abbu ya dafe da duka hannayen shi, a tarihin ahalin su gabaki daya, makamancin wannan bai taba faruwa ba. Ya fahimci tsoron Yaya Ayuba, sai dai maganar mutane mai wucewa ce, tunda gabaki daya rayuwar ma ba mai dorewa bace ba, komai zaizo karshe wata rana. Surutun zai taba zuciyar shine idan akayi shi akan Layla, idan aka dora ayar tambaya kan rikon da suke mata, sosai zuciyar shi take ciwo yanzun da tunanin hakan. Mutane zasu ce bai riketa da kyau ba, zasu ce yayi sakaci da tarbiyar ta, Ayya ma bata fito fili tace haka ba, amman ta fada mishi akwai raunin shi a cikin abinda ya faru. Idan duk tarin kaunar da take mishi bai hanata fadin abinda ta fada ba, bashi da tabbas akan abinda mutanen da suke jiran kuskuren shi zasu fada, cike da matsananci tsoro Abbu yake kallon Yaya Ayuba "Ya zanyi? Me zanyi?" Dan jim Yaya Ayuba yayi, a cikin abin duka baiga wani zabi mai sauki ba, in dai cikin yana nan basu da tabbas akan tsayawar maganar a tsakanin su kawai. Amman yanzun bayason fadin wani abu da zai kara firgici da fargabar dan uwan nashi, shisa ya zabi fadin "Shi Rayyan din ya kamata ya aure ta" Kai Abbu ya jinjina cikin aminta da maganar da Yaya Ayuba yayi. Wayar shi da take kan kujera ya dauka yana kiran Ayya "Ki kira Rayyan sai kuzo tare" Ya fadi tana dagawa, bai jira amsarta ba ya kashe. Mami ma kiranta yayi yace ta taho da Layla "Gara su san da maganar" Ya fadi yana kallon Yaya Ayuba da baice komai ba, bayason ya tuna ma Abbu ko da za'ayi auren sai bayan ta haihu dole. Sosai yake kara jinjina lamarin. Ayya ce ta fara shigowa dakin da sallama, duk da gefe ta samu ta zauna. Ta kasan idanuwanta Abbu take kallo, yanda fuskar shi take a kumbure na taba zuciyar ta, zata dauke mishi duka wannan tashin hankalin in zata iya. Saida ta koma daki ta zauna ita kadai sannan tasan babu yanda za'ayi ta taba son Mami da Layla, saboda da bata dauko musu yarinyar ba da yanzun suna zaman su lafiya, da bata shigo musu da ita cikin gida ba, da mijinta bai shiga wannan yanayin ba. Da ta dauko ta din, data riketa yanda ya kamata, da bata barta tabi mata yaro har Zaria ba duk wannan abin da sun kauce mishi. Sai dai in tayi magana yanzun za'a ce ita din bata san kaddara ba, kuma ba haka bane ba, tasan kaddara, ta dai san akwai wadda take tafiya da son zuciya, akwai kuma wadda take hade da sakaci irin wanda Mami tayi kuma Abbu na kallo ya biye mata. Da sun fada mata ita da tasan yanda zata nisanta yaronta daga Layla, watakila da duk basu zo nan ba. Yanzun da taje ta kirawo Rayyan din, zaune ta same shi ya hada kan shi da gwiwa, Bilal ma yana bakin kofar dakin a zaune ya hade na shi kan da gwiwa. Sai bayan ta fito ne ta dafa shi ya dago mata fuskar shi da take a kumbure kamar wanda yaci kuka "Ka tashi daga nan Bilal, ko dakina ka koma" Numfashi ya sauke, da wani yanayi yake kallonta "Ki barni anan Ayya, dan Allah ki barni" Bata da zuciyar tursasa shi, shisa ta kyale shi din tana tafiya. Yanzun ne tayi mamakin ganin shi ya biyo bayan Rayyan daya juya yana mishi wani irin kallo, yanda yayi tsaye na sanyaya wani abu a zuciyar Ayya, bata san meye take gani a tsakanin yaran nata ba, amman bata son shi, koma menene yana kara ma wutar tashin hankalinta fetur. Gefe Rayyan ya karasa yana tsayuwa, Bilal ne ma ya zauna a kasa kusa da Abbu. Yaji me Ayya tace, yaji tana fadama Rayyan din Abbu na kiran shi, sai da ya fito sannan shima ya mike da nufin rufa mishi baya "Ina zaka je?" Rayyan din ya tambaya, ya gwada shiga dakin bayan ya dawo sallar la'asar, ya sake yin magana da Rayyan, ko baice komai ba ya zauna a tare, amman yana daga labulen ya dago yayi mishi wani kallo da ya saka shi mayarwa ya saki. Bayason ganin shi, kamar yanda kowa na gidan yake gab da fara ji a kan shi ya sani, har karshen rayuwar shi zai kasance mai godiya da karamcin su, yanda suka karbe shi suka darajta shi. Ba kuma zai ga laifin su ba, yaci amanar sune shisa, yayi musu kuskuren da ko bakin da zai basu hakuri baida shi. "Ba zaka dauki laifin da bakayi ba, ba zan bari ba Hamma" Sai da Rayyan din ya dan dafe kan shi sannan ya saki yana kallon Bilal din "Karka biyoni Bilal, karka fara biyoni..." Kamar baiji kashedin Rayyan din ba, yana juyawa, inda ya saka kafar shi nan Bilal ya mayar da tashi, yana tsayawa shima ya tsaya, batare da ya juyo ba wannan karin yace "Nace karka biyoni bakaji ko?" Sun kusan minti daya a tsaye kafin Rayyan din ya sake cigaba da tafiya, wannan karin sai da ya sha kwana sannan Bilal yabi bayan shi. Ba zai zauna ya sake hada Rayyan din da su Abbu ba, bayan abinda yayi, ba zai bari ya kara wani ba. Ko yanzun da Rayyan din ya bishi da wani irin kallo, kan shi kawai ya sadda kasa, ya zauna kusa da Abbu ne saboda ya san damar yin hakan na gab da kwace mishi, zuciyar shi yake ji zaune cikin kirjin shi tana dokawa a hankali a hankali, kamar wadataccen jini baya zagaya mata, suna zaune Mami ta shigo, Layla na bin bayanta, har yanzun tun kayan dazun ne na jikinta, ko hijabin ma bata cire ba. Inda suka barta bata tashi ba, anan rana ta sameta, anan kuma tabarta, ko sallah batayi ba sai da Magriba da Jabir yazo ya sameta tana zaune anan, shima har zai wuce saiya kasa, ya dawo baya "Ki tashi daga nan" Taji shi, ko karfin kirki bata da shi balle tayi motsi, hannunta ya kama yana dagata, batayi musu ba ta mike. Janta ya farayi, suka wuce Mami da take zaune a kasa kan kafet, sai da ya kaita dakinta sannan yace "Kinyi sallah?" Kai ta girgiza mishi batare da ta kalle shi ba "Tun dazun kina waje Layla? Baki tashi ba? Anan kika zauna rana ta kare akan ki? Baki da hankali ko?" Idanuwanta taji sun kara cika da hawayen da ta dauka sun kare mata da fadan Jabir din "Ki wuce kiyi sallah" Batayi mishi musu ba ta shiga bandakin ta dauro alwala ta fito, tana cikin sallah taji shigowar Jabir din kafin ya ajiye kofi yana sake ficewa. Sai da ta gama gabatar da sallolinta duka, zuwa lokacin an kira isha'i shisa tayi, bakinta yayi nauyi, bata san kalar addu'ar da zatayi ba. Dan sallar ma sai take ganin kamar ta makale ne a wani waje, kamar ba zata isa inda za'a karba ba, saboda cikin da yake jikinta, saboda daudar da take ji a tattare da komai nata. Kofin da Jabir ya ajiye ta dauka, shayine mai kauri ya hada mata, sai taji cikinta yayi wani qugi da yunwar da take tattare da ita, ga zazzabi ya sake saukar mata. Tana kurbar shayin hawaye na zubar mata, batama gama sha ba taji muryar Mami a saman kanta "Abbun ku yana kira" Mami ta furta tana juyawa, dan shayin da ta samu ya shiga cikinta taji yana barazanar dawowa saboda tashin hankali. Shisa ta dade a zaune kafin ta iya mikewa. Kara hautsinawa cikinta yayi da taga Rayyan din, gefen Mami ta zauna, tana kokarin ganin idanuwan Rayyan ko yayane, amman a tsaye yake ya jingina bayan shi da bango, kan shi a kasa. Wani irin shiru ne a cikin daki da kowa yake ji a jikin shi kamar bargo, ganin Yaya Ayuba bashi da niyyar cewa komai yasa Abbu yanke hukuncin yin magana, ya dauka zai saukaka mishi komai ta hanyar yi ma su Mami bayanin shawarar da suka yanke. Ya bude bakin shi ya kai sau biyu yana rasa ta inda zai fara ko abinda zai fada din "Rayyan zai auri Layla" Ya furta, maganar na zuwa kunnen shi da wani irin yanayi. Sai lokacin Rayyan ya dago ya kalli Layla, zuciyar shi ciwo take cikin yanayin da bai taba tunanin zatayi ba, ita ma so yake taji abinda yake ji, musamman da ta dago tana sauke nata idanuwan cikin na shi, yau tashin hankali ya korar mishi tsoron idanuwanta da yake ji. So yake taji ciwon da yake ji, taji rabin abinda ta saka yake ji, batare daya dauke idanuwan shi daga cikin nata ba yace "Ba zan aure ta ba Abbu" Karar rushewar wani abu Layla taji cikin kunnuwanta, amman ta rasa daga inda take fitowa, tashin hankalin da take ciki yanzun yafi duk wani tashin hankali da ta taba cin karo da shi a baya. Dan bata san lokacin da ta kai hannuwanta tana jijjiga Mami da take zaune kusa da ita ba, hawaye ne masu zafi wani nabin wani suke zubar mata "Mami ba zai aure ni ba... Hamma ba zai aure ni ba Mami" Layla take fadi tashin hankalin duniya yana tarar mata waje daya, yanayin yanda take fadar maganar tana fitar da numfashin da take kokawa da shi da yanda take jijjiga Mami shi Ayya take kallo, kafin ta dubi Rayyan da idanuwan shi suke kafe akan Layla kamar kukan ta baya taba zuciyar shi. Namiji kenan, daga randa Abbu ya hada soyayyarta da ta Mami tasan da gaske baka shaidar namiji, shikenan fa, ya gama da Layla, yana da damar da zaici gaba da rayuwar shi kamar komai bai faru ba, surutun da mutane zasuyi ma da wahala ya bi takan shi. Zai dauki lefin yin cikin da yake jikinta ne kawai. Abinda Ayya take da yakinin ba zai hana shi auren yarinya kimtsatsiyya ba, amman ita Layla zai hanata auren namiji kamili, ko da ta samu, surutan dangin shi zasuci gaba da binta har karshen rayuwar ta, yaji mata ciwon da samun saukin daukar tabon shi na tare da auren shi ne kawai. Duk da shima din babu tabbacin ba zata fuskanci wulakanci a wajen shi ba, musamman yanzun daya furta ba zai aureta ba. Bata son yarinyar har yanzun, tunaninta a tare da Rayyan na saka cikinta kullewa, amman bai hanata tausaya mata ba, bai kuma hanata tsanar son kan da Rayyan yake sonyi ba. "Wacce magana kakeyi Rayyan?" Kawu Ayuba ya tambaya yana kallon Rayyan din, shima kallon shi yayi "Ba zan aure ta ba, bana son ta Kawu" Ya karasa yana jin zuciyar shi na ihun karyata kalaman, a hade da hakan yana jin ciwon da takeyi mishi "Bana son yi maka baki Rayyan... Bana..." Abbu ya fara, Bilal yana katse shi da fadin "Abbu..." Ganin kamar baiji ba yasa shi kara fadin "Abbu..." Cikin yanayin da yasa hankalin kowa ya koma kan Bilal, wannan abin da yake faruwa yanzun ne yasa ba zai bari Rayyan ya dauki wannan laifin ba, ba zai bari su Abbu su fadi maganar da zasuyi dana sani akanta ba kan laifin da baiji ba bai gani ba. Ga kukan da Layla takeyi ya kara daga mishi hankali, shi ya sakata a cikin wannan tashin hankalin, shi ya shiga tsakiyar su ita da Rayyan, abinda bai kamata yayi ba tun daga farko, ko zuciyar shi data doka mata ya dade da sanin bai kamata tayi mishi wannan rashin adalcin ba. Amman cikin watanni kalilan ya fahimci rayuwa bata san wani abu adalci ba, da basu zo inda suke ba yau. "Ba shi bane Abbu, dan Allah ku saurareni... Layla kiyi magana ke zasu jiki, ki fada musu ba Hamma bane, ki fada musu bashi bane" Bilal ya karasa yana kallon Layla da kukanta ya tsananta, kai take girgiza mishi, tana rokon shi a zuciyarta da karya karasa datse sauran igiyar da ta rage a tsakaninta da Rayyan din, shima rokonta yakeyi "Shirun mu ba zai canza komai ba, dan Allah ki saukaka mana, ki fada musu bashi bane ba" Zaninta Ayya ta tattaro tana goge fuskarta da take jin kamar alamun zufa, saboda yanayin maganar Bilal din bata nuna alamar wasa ko son daukar laifi ba. Abbu ma kallon Bilal yake da sabon tashin hankali, kafin daga kasan makoshin shi yace "Bilal" Abbu ya kalla yana riko hannun shi "Ni ne Abbu, ba Hamma bane ba... Ni ne" Ya karasa wasu hawaye masu zafi na zubo mishi, komai na jikin Abbu bayason yarda da maganaganun Bilal din, shisa ya kalli Layla duk kuwa da kukan da takeyi tana girgiza mishi kai "Layla ki mun magana dan Allah, ku fadamun abinda zan iya dauka" Kuka takeyi kamar zata shide, bata roki Bilal komai ba sai shirun shi, bayan duk abinda ya faru. Ya kawota inda ba zata iya juyawa ba, Abbu da kan shine yake rokon ta, a hankali ta daga mishi kai "Ba Hamma Rayyan bane" Ta iya furtawa dakyar tana kwantar da kanta a jikin Mami hadi da sakin wani kuka da ko sautin shi baya fita "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Yaya Ayuba ya furta, ba zaice maganar bata dake shi ba tun daga farko. Amman yanzun jijjiga shi tayi tana dagawa ta buga da kasa. Yasan Bilal, ko a yaran shi babu mai natsuwa da hankalin Bilal, babu mai sanin ya kamatan shi. Ya sha aiken Bilal kan abubuwa masu muhimmanci saboda ya aminta da nutsuwar shi. A mafarki idan aka fada mishi Bilal zaiyi abinda yake cewa da kan shi yayi zai karyata, idan ya tashi kuma zaiyi addu'a harma da sadaka. Abbu ya kasa cewa komai, kan shi yayi wani shiru na ban mamaki. Akan Rayyan ya yarda da zancen Ayya, akwai sakacin shi a ciki, akan Bilal fa? Me zaice? Me zata ce ita ma? Kallon ta yayi, hargitsi ne bayyane akan fuskarta, yaronta take kallo, Bilal dinta take kallo tana yarda da akwai kaddarar da bata da kalaman misaltawa, yanda yake saka hannu yana share hawayen da sunki daina zubar mishi yana saka nata idanuwan cika da hawaye. Abinda yake damun shi kenan, damuwar da yake ta boye mata a watannin nan kenan ashe, bata taba daukar zata yiwa wani uzuri kan lamari irin haka ba sai yau. A tare da Bilal bata bukatar wani bayani, koma meye ya faru kaddara ce, ko menene ya gifta tsakanin shi da Layla tsautsayi ne. "Bilal" Mami da ko kukan ita ta kasayi ta kira, so take ya kalleta dan ta tabbatar da shi dinne, kallon ta yayi, ta kasa tambayar shi, duk da tana son jin bayanin shi kafin ta yanke mishi hukunci, saboda Bilal ne, idan za'a tambayeta shaida akan shi zata fadi cewa duk yanda tasan Ayya tayi kokarin ganin yaran bai kulla alaka da ita ba ya tsallake, baya shakkar dukan da zai sha a hannun Ayya a gabanta yake gaishe da ita, a lokutta da dama ta sha ganin Bilal din ya mata murmushin ban hakuri duk idan Ayya ta sauke mata wata masifar da bata san dalilinta ba. Da yayi hankali har daki yakan bita yana fadin "Dan Allah Mami kiyi hakuri, karki sa abin a ranki. Ayya bata nufin duka abinda ta fada, kinsan idan ranta ya baci" Ba dan Abbu ba, saboda Bilal ma ta sha kauda kai kan abubuwa da yawa da Ayya zatayi mata. Shisa take son jin bayani daga bakin shi, take son sanin me ya faru, sai dai kafin yayi magana Ayya ta riga shi "Karku dora mishi laifi, dan Allah kar kuce wani abu, kuskure ne, Bilal ka fada musu kuskure ne, ni nasan kuskure ne, in dai da gaske ne kuskure ne" Hawayen da suka zubo mishi Bilal ya share yana jin kalaman Ayya na saukar mishi, suna ratsa wajaje da yawa a cikin jikin shi, suna kuma sanyaya zuciyar shi da take matukar ciwo. Ayya kenan, Ayyar shi, uzuri take son mishi tun kafin taji bayanin shi, bata da wata tambaya, saboda a idanuwanta ba zaiyi laifi mai girma haka ba, wannan ce girman kaunar da takeyi mishi, kaunar da yake jin ya ha'inta yau, saboda kuka takeyi, shine sanadin kukan da takeyi. A muryarta yaji shisa ya kasa kallonta, Abbu yake kallo da baice komai ba "Abbu..." Bilal ya kira muryar shi na karyewa, Abbu ya kasa kallon shi, ya rasa abinda yake ji, amman so yake kowa yabar shi, ya dan zauna shi kadai, shisa yace "Shikenan kai sai ka aure ta... Ku fita dan Allah, ku dan barni" Rayyan da yake tsaye yana jin shigi da ficen duk maganganun su batare da sun taba zuciyar shi ba yaji maganganun Abbu sun shiga wajen da suka zauna daram suna kasa fitar mishi. Ya dauka babu wani abu da zasu fada da zai taba shi, ya gama jin su duka daga bakinta da na Bilal. Sai yanzun da yaji Abbu na kiran Bilal ya auri Layla, bayan cikin da yake jikinta da ba nashi ba, yanzun ita din ma ake so ace ba tashi bace ba. "Abbu" Rayyan ya kira sauran kalaman na makale mishi "Dan Allah ku fita ku barni" Abbu ya sake rokon su, saboda muryar Rayyan da yaji na kara saukar mishi da wani yanayi daban. Ganin duk suna mikewa yasa Rayyan sake kallon Abbu cikin tashin hankali, so yake ya fada mishi shifa baice ba zai auri Layla saboda wani abu ba, ya fadane dan shine hanya daya kawai da yake da ita da yasan zataji kalar ciwon da yake ji. Da yace baya son ta ya dauka su duka kamar zuciyar shi sunji karyar da yake yi. Mami ita ta fara barin dakin da Layla a jikinta tana wani irin kuka da yake ji a kasan zuciyar shi. "Ahmadi" Yaji Ayya ta kira, tana saka shi kallonta, da zuciyar shi yake rokonta da ta fadama Abbu ya janye kalaman da yayi, amman sai yaji tana fadin "Dan Allah kar kaga laifin shi, ka tsaya yayi maka bayani... Bilal kayi mishi bayani kaji" Kafin yayi magana Abbu ya kalli Ayya "Dan Allah Maimuna, naji iya abinda zai tsaya dani har karshen rayuwata, dan Allah ku barni, kuje ku barni dan girman Allah" Hawayenta Ayya ta goge tana mikewa, harta yi taku daya Bilal daya fara magana yana sakata taja ta tsaya cak "Ban da uzurin da zan baka Abbu, bani da shi... Nayi laifi na sani. Ko bakin da zance ka yafe mun bani da shi" Karasawa tayi ta kama hannun Bilal din tana jan shi, dole ya mike. Zasu dawo ita da Bilal suyiwa Abbu bayani yanda zai fahimta. Suna ficewa Yaya Ayuba ma ya mike, su duka suna bukatar yin bacci kan maganar, gobe ya dawo su kara sanin yanda zasuyi. Ko bankwana baiyi wa Abbu ba ya fice daga dakin. Rayyan ne yayi tsaye, ya kasa tafiya, yana kallon Abbu ya kai hannu ya share kwallar da ta zubo mishi "Rayyan bakaji nace ka tafi ba?" Kai Rayyan ya jinjina mishi, yaji shi, yaji me yace tun da farko, ya kasa tafiya ne saboda akwai tarin maganganu da yake son yi da Abbu, watakila yau ba ita bace ranar daya kamata, amman ya kasa tafiya "Abbu baka mamakin ya akayi nake daki daya da kai?" Dagowa Abbu yayi yana kallon Rayyan din, yau duka bashida wajen mamaki kuma "Karka ce in tafi. Abbu karka koreni yau kawai da nake jin zan iya zama daki daya da kai na lokaci mai tsayi batare da iskar wajen ta mun kadan ba" Kai Abbu ya jinjina ma Rayyan din. Shi kam zaman ma bashi da karfin yin shi, shisa ya kwanta, duniyar duka na mishi lilo, ya rasa kalar tunanin daya kamata yayi, ya kuma rasa abinda yake faruwa da su haka, abinda yake faruwa da yaran shi. Kafin kalaman Bilal su fara mishi yawo suna saukar mishi da zazzabi. Kuskure shine abinda Ayya ta kira komai da akalar lamarin ta juya kan Bilal, shima bashi da wasu kalamai da zaiyi amfani da su, kalmar iri daya ce da ta Ayya, kuskure. Idanuwan shi ya rufe yana son ya hada ya rufe tare da duk wani tunani amman abin ya faskara. Ya kasa rufe tunanin da yayi mishi cunkus. Rayyan kam ba zaice ga lokacin daya dauka a tsaye ba, yasan dai kafafuwan shi da kansu suka gaji suna kaishi kasa, da yake akwai kafet cike da dakin nan ya kwanta shima. Ciwo yake ji, ciwon da yake bukatar lallashi ko ya yake, kuka yake nema watakila idan yayi irin wanda Layla takeyi zai samu sauki. Abu daya ne yake mishi yawo, dan yace ba zai auri Layla ba baya nufin yana son ta kusa da wani, balle ace wanin ya kasance Bilal, mutuwa kawai zaiyi ya tabbatar yanzun. Dan kirjin shi kamar an zauna a kai haka yake ji. Me yasa Bilal zai mishi haka? Ya kasa samun wannan amsar, idan kuskure zaiyi me yasa sai akan Layla? Duk da dazun yana jin surutun da yake yi a bakin kofa, ya zabi yin kamar baiji shi bane ba. Shisa bayason juya kalaman, baya son yin wani tunani da zai hada da yiwa Bilal uzuri, abinda yayi mishi ba zai yafu ba, ba zai iya yafe musu ba daga shi har Layla. Har cikin kasusuwan jikin shi yake jin hakan, yana so suji ciwo kalar wanda shima yake ji. Amman hakan baya nufin yana son ganin Layla a tare da Bilal, yama Abbu zai fara cewa Bilal ya auri Layla. Yana tunanin baccine ya fara fisgar shi, dan kiran sallar farko da akayine ya saka shi bude idanuwan shi dakyar yana tunanin inda yake. Kafin komai ya dawo mishi yana saka shi dafe kirjin shi da yake ciwo. Dakyar ya iya mikewa, ko ina na jikin shi ma ciwo yakeyi. Abbu da yake kwance ya kalla, sai da yaga ya juya kwanciya sannan ya fice daga dakin. Fitilun gidan duka a kunne suke yau. Dakin su ya nufa, yana shiga zuciyar shi tayi wata irin dokawa da yanayin yanda yaga an fiffido kaya, tun bai karasa cikin dakin ba kafafuwan shi suke rawa, kan tebir din shi yaga takarda a ajiye, ya dauka yana budewa, da daya daga cikin fensiran zanen shi akayi rubutun da yake ganin yana rabe mishi biyu, saida ya runtsa idanuwan shi ya bude su tukunna ya iya karantawa da muryar Bilal a zuciyar shi "Nayi kuskure na sani, ba zan kara shiga tsakanin ka da Layla fiye da yanda nayi ba Hamma, ba saika yafe mun ba, dan Allah ita ka duba zuciyarka, nasan akwai wajen da zai iya yafe mata, ka yafe mata. Ka dora duka laifin a kaina. Nagode da tarin kaunar ka, ka kula da kan ka, ka kula da Ayya" Ya karanta wasikar yafi sau ashirin kafin asalin ma'anar ta ya zauna mishi, cikin wani irin tashin hankali ya fito daga dakin, tun daga bakin kofar yake fadin "Ayya!" Yana kara kwala mata kira harya karasa bakin kofar dakinta inda suka hade saboda daman ba bacci takeyi ba, kiran shi ne ya sata mikewa tana tahowa da sauri, ko da yana yaro kome yake bukata bai taba mata irin wannan kiran ba, yana ganinta kafafuwan shi na kasa daukar shi "Ayya ya tafi... Ayya tafiya yayi... Bilal tafiya yayi ya bar ni... Dan ba zan yafe mishi ba sai nace ya tafi? Me yasa zai tafi? Ina ya tafi Ayya?" Duka zancen shi a baibai take jin shi, jijjigata Rayyan ya fara yi, saboda yasan babu inda Bilal zaice bai fada mata ba, gara ta gaya mishi ya bishi ya dawo da shi. "Ki fadamun inda ya tafi Ayya... Kinga ni me yace mun..." Wasikar Ayya ta karanta, fahimtarta ne yake mata wahala saboda babu yanda Bilal zai tafi wani waje bata sani ba, balle ace irin wannan tafiyar, ture Rayyan tayi tana nufar dakin su ya rufa mata baya, kayan Bilal ne tagani a zube, batayi magana ba ta sake fitowa tana jin Rayyan na biye da ita har cikin dakinta inda ta dauki wayarta, tana mamakin yanda komai yayi mata shiru, lambar Bilal ta kira a kashe, duka lambobin shi a kashe, Rayyan ta kalla da shima yaji a kashe ne, kai dai kawai yake girgiza mata, duniyar na kara hargitse mishi, runtsa idanuwan shi yayi yana sake bude su da wani irin matsananincin tsoro daya ziyarce shi "Ayya dan Allah..." Cewar Rayyan yana dafa bango ya sulale kasa, a cikin daki yake, amman duniyar duka yake ji tayi mishi fili, babu kowa a cikinta sai shi kadai, bai san inda zai nufa batare da Bilal ba "Ayya ki ce mun bai tafi ba, dan Allah kice ya dawo" Rayyan yake fadi yana jin iska ta daina kaiwa cikin kan shi, kafin wani irin duhu ya rufe mishi idanuwa ruf, yana saka Ayya tsugunnawa ta riko shi kafin ya karasa kaiwa kasa, kan shi a jikinta yake da wani nauyi da batayi zato ba, nata kan ta dora a na shi, tunda take bata san akwai tashin hankali makamancin wannan ba, a wahalce ta dago, muryar da zatayi amfani da ita wajen neman taimako take nema ta rasa yau. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:09 PM - 111: Jan 1, 2021. 27 Ko sallamar Abbu daya dawo daga masallaci kan shi tsaye ya nufo bangaren ta bataji ba. Zuciyar shi na wata irin dokawa ganin ta rike da Rayyan din "Rayyan..." Ya kira muryar shi na fitowa yar karama saboda tsoron da yake ciki. "Me ya same shi? Me ya faru?" Saboda ya ga fitar Rayyan din daga dakin shi, kuma lafiya kalau ya gan shi. Baisan me yake a kwance haka kamar gawa ba. Ayya da sai lokacin hawaye masu zafin gaske suka zubo mata ta dago tana kallon Abbu, bakinta take so ta bude tayi magana amman ta kasa, saboda zafin da zuciyarta takeyi. Ta dauka raba soyayyar Abbu shine abu mafi daci da zata dandana a zaman duniyarta gabaki daya. Saboda Abbu ne komai nata, sai yanzun da take tunanin inda Bilal ya nufa a cikin duniyar da babu aminci, a rayuwar da naka ma da wahala ya taimaka maka balle wanda baka sani ba. Kafafuwan Abbu har rawa yake sanda ya kara bandaki ya dibo ruwa ya dawo. Da kan shi ya tsugunna yana dibar ruwan a hannun shi ya shafama Rayyan a fuskar shi, sai da yayi hakan kusan sau biyar sannan Rayyan din yaja wani irin numfashi mai nauyi yana mikewa gabaki daya "Bilal" Ya kira daga lungun zuciyar shi yana kallon Abbu "Abbu tafiya yayi... Bilal tafiya yayi" Cike da rashin fahimta Abbu yake kallon Rayyan din, kafin ya maida duban shi kan Ayya da ta saka fuskarta cikin tafukan hannunta tana wani irin kuka marar sauti, bayani yake so wani yayi mishi yanda zai fahimta. Dube-dube Rayyan yayi yana dauko takardar da Bilal ya bar mishi da take can gefe ya mikawa Abbu, sai da ya karanta babu adadi kafin kalaman su zauna mishi. Baiyi magana ba ya mike tsaye, aljihun shi ya laluba yana zaro wayar shi da sabo ya saka shi daukarta ya zira bayan yayi alwala zai fita masallaci. Jikin shi babu inda baya bari, dakyar ya iya saka lambobin sirri ya bude wayar. Sakkoni ya gani da hannun shi ya dangwalo batare da yayi niyya ba. Ganin sakon Bilal a sama ya saka shi saurin budewa: "Kayi hakuri Abbu, ka yafe mun dan Allah, watakila zan samu sauki a duk inda rayuwa zata jefani. Ka yafe mun ban rike amanar da ka bani ba, ban kula da Layla yanda nai maka alkawari ba. Nagode da karbata da kayi,  nagode da yanda ban taba jin maraici a karkashin kulawar ka ba. Ina fatan nisan da zanyi ya saukaka muku komai" Sosai Abbu yake jin kan shi na sarawa "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Ya furta yana saka Rayyan saurin fadin "Menene Abbu? Ya fada maka inda yaje?" Ya karasa yana mika hannu ya karbi wayar da Abbu ya miko mishi, karanta sakon yakeyi wani abu na tattarowa yayi mishi tsaye a kirjin shi, dago idanuwa yayi yana kallon Abbu cike da wani yanayi "Amana ka bashi Abbu? Me yasa?" Saboda bai ga dalilin da zai sa Abbu yace ya bashi amanar Layla ba, sun san yanda Bilal yake, su dukan su kowa yasan raunin Bilal,yanda bashi da wani aiki sai kula da kowa, furta kalaman ba zaiyi komai ba sai dora ma Bilal din wani nauyi da Rayyan bayajin Abbu ya fahimta "Abbu ko bakace ba, ko baka furta da bakin ka ba Bilal zai kula da ita da duka zuciyar shi, me yasa ka dora mishi nauyin nan? Kaga ya tafi, saboda yana tunanin ya kasa sauke nauyin amanar daka bashi ya tafi... Kasa ya barni" Yanda Rayyan din yake magana kamar ba a cikin hayyacin shi yake ba, wanda zai dora ma alhakin tafiyar Bilal yake nema, bai sami kowa ba sai Abbu a yanzun. Dube-dube yakeyi ganin Abbu ya sadda kan shi kasa ya kasa cewa komai, har saida ya hango wayar Ayya sannan. Idan Bilal ya turoma Abbu sako, tabbas itama yasan ya tura mata, watakila ya fada mata inda zashi ita. Yana dauka yaga ko password babu ita, dan haka kanshi tsaye wajen sakkoni ya shiga, ya kuwa ga Bilal din ya turo mata itama: "Ki yafe mun Ayya, zanyi kewar ki da yawa" Dariya Rayyan yayi da bata da alaka da nishadi, saboda ko shi zai fita duk yanda magana mai tsayi bata hadasu da Ayya, iya abinda zai tura mata kenan. Bai taba sanin Bilal bashi da hankali ba sai yau. Wayar ya ajiye gefe yana samu ya mike "Ina zaka je?" Abbu ya bukata, amman Rayyan din bai kula shi ba ya wuce. Tsintar kafafuwan shi yayi da bin Rayyan din, kafin shima ya tafi, jin takun Abbu a bayan shi ya saka shi juyawa "Abbu ba inda zanje, ka koma dan Allah... Ba inda zani" Ba don ya yarda da kalaman Rayyan din ba, ya dai yi tsaye ne har sai da ya daina ganin Rayyan din da ya nufi dakin su. Kayan da Bilal ya baza ya fara harhadawa, watakila yabar wani abu da ko yane zai nuna alamar inda ya nufa, amman harya gama hadasu baiga komai ba. Gefen gadon ya zauna yana rasa kalar tunanin da ya kamata yayi, kafin wani abu cikin kan shi ya fada mishi baiyi sallar asuba ba. Alwala kam dan sabo ne shisa ya cikata dai-dai. Lokacin daya idar da sallah, bai san ta inda zai fara addu'a ba ko abinda zai roka, kawai yana rokon Allah Ya duba halin da yake ciki ya karbi sallar da yasan bashi da wadatacciyar nutsuwa a lokacin daya gabatar da ita. Baisan iya lokacin daya dauka a zaune ba, rurin da wayar shi takeyi ce ta dawo da shi daga duniyar tunanin da yakeyi. A hargitse ya mike yana rasa inda zai gano wayar, har ta yanke tana sake daukar ruri "Dan Allah ina dubawa ne Bilal, nasani, ni nasan babu inda zaka tafi ka barni" Rayyan yake fadi yana cigaba da neman wayar kafin ya juyo ihunta cikin jakar shi da ko budeta baiyi ba. Lalubo wayar yayi, kafin ya daga ta sake yankewa, budewa yayi yana kallon lambar hadi da nazarin inda ya taba ganin ta, ko ma a ina ne yasan lambar, kafin a sake kira, bai tsaya jira ba ya daga wayar yana karawa a kunnen shi "Hamma..." Muryar Aisha ta daki kunnen shi tana saka zuciyar shi matsewa a cikin kirjin shi, kafin ya amsa ta dora da fadin "Hamma ina Nawan? Sakon shi nagani yanzun, bansan ko ya yarda wayar bane, saboda na kasa fahimtar duka zantukan da yakeyi" Runtsa idanuwan shi Rayyan yayi, akwai wani yanayi tattare da muryar Aisha da yake kara bude bangarori da dama a cikin zuciyar shi "Dan Allah ka fadamun...kai mun magana" Sai da ya bude idanuwan shi sannan ya iya cewa "Ina kike tunanin idan Bilal ya bar gida zai je?" Ta kusan mintina uku kafin ta amsa shi, muryarta na fitowa a karye "A watan nan yana yawan maganar kasancewa a wajen da kowa bai san shi ba, yana fadin Lagos ne kawai zakaje ka bace bat... Ban sani ba, ban san me yake faruwa ba, me yake faruwa Hamma? Me yasa zai tafi?" Ta karasa maganar ne da alamar kukan da ya kwace mata, ba shi da amsar da zai bata, ba kuma shi da wasu kalamai da zai tausheta dasu, shima yana bukatar lallashine "Ina zai tafi ya barni? Ta ina zan fara?" Wani irin numfashi take saukewa kamar wadda aka shaqe "Zan kiraki" Rayyan ya fadi yana sauke wayar daga kunnen shi, dan yaji alamar zata kara hargitsa mishi lissafi ne. Yana da abubuwa da yawa a gaban shi. Mikewa yayi yana saka wayar a aljihun shi, sai da ya karasa bakin kofa sannan yayi tunanin saka takalma a kafafuwan shi, tashin hankali bai barshi yaji kasar da yake ta takawa ba yau. Yana fitowa daga daki yaci karo da Abbu "Abbu zan duba a tasha, ina motocin Lagos suke lodi? Aisha tace Bilal yana maganar zuwa can ne" Kai Abbu yake jinjina ma Rayyan, gabaki daya ya rasa abinda zaiyi tunani. Duniyar ta birkice mishi, yaran da yake tunanin yana duk wani kokari da yake karkashin ikon shi dan kare sune yake kallo yau kaddara na aikinta a kan su babu abinda zai iya. Bilal ne ya dauki kafar shi yabar gida yau, Bilal da gabaki daya rayuwar shi zagaye take da tasu, shine yau ya nufi inda baisan kowa ba, ya ture komai ya tafi saboda yana tunanin yayi musu wani laifi. Wani irin tsoro Abbu yake ji yana shigar shi, Rayyan yake kallo, yana tuna kalaman da yayi mishi jiya na yabar gida "Ko da zan taba ce maka kabar mun gidana, karka tafi ko ina, kalaman ba zasu taba fitowa daga zuciyata ba" Abbu ya fadi yana dorawa da "Bari in dauko mukullin mota sai mu tafi" Anan inda yabar Rayyan ya dawo ya same shi, sun karasa wajen motar ne Yaya Ayuba ya shigo, ko gaisawa ba suyi ba ya fara da tambayar "Lafiya? Ina zaku je da sanyin safiyar nan?" Abbu na bude murfin mota ya amsa shi "Bilal ne ya bar gida, Rayyan yace kamar Lagos ya nufa. Shine zamu duba a tasha mugani" Karasawa Yaya Ayuba yayi yana karbar mukullan motar daga hannun Abbu batare da yace komai ba. Shiga sukayi, Rayyan na bude gidan baya ya shiga. Da yake Yaya Ayuba yasan duk tashoshin da motocin Lagos suke lodi. Tunda kafin ya samu budin hawa jirgi idan tafiya kudu ta kama shi motar hayar yake bi. Rayyan ba tuqi ya iya ba, amman gani yake kamar Yaya Ayuba baya taka motar da sauri, saboda so yake kawai su karasa yaga Bilal din yaji dalilin da zai sa ya fara tunanin barin su. Kudi Kawu Ayuba ya bama cikin yan kamasho na tashar, kafin kace wani abu an dauko musu wani babban littafi da jerin sunayen mutanen da suka hau motocin Lagos daga daren jiya zuwa wayewar gari, motocin safe. Amman ko daya babu sunan Bilal a ciki, duk da Rayyan yaki aminta, wanda ba shi ya duba ba da kan shi sai da ya karba ya sake dubawa, tashoshi suka dinga bi har wajen karfe tara na safe, saboda duk inda sukaje sai sun tsaya an duba list sannan suke barin wajen. Suna hanyar nufar wata tashar da akayi musu kwatance, wayar Rayyan ta fara ihu, bai bi ta kanta ba harta yanke, saboda wani abu na fada mishi ba Bilal bane ba. Sake kira akayi, ko waye ma bai hakura ba a karo na biyu, ya sake kiran a karo na uku "Rayyan ba wayar ka bace take kara?" Yaya Ayuba da yake tuqi ya tambaya, Rayyan din bai amsa shi ba, dan daga jikin shi yayi yana zaro wayar daga aljihun shi, dubawa yayi yaga ko Aisha ce, dan bashi da wata magana da zai fada mata, da akwai daya kirata kamar yanda yai mata alkawari. Wata lamba ce yagani daban, karamin tsaki yayi yana shirin saka wayar a silent kar a dame shi aka sake kira, dagawa yayi ya kara a kunnen shi yana fadin "Waye?" A hasale, ta dayan bangaren aka furta "Daga tashar Mass ne, mun dauki lambar cikin lambobin da daya daga cikin fasinjan da motar su ta tashi karfe hudu na safiyar yau daga nan Kano zuwa Lagos ne mai suna Bilal Abdullahi Dikko..." Zaman shi Rayyan ya kara gyarawa yana kai hannu yana wuyan rigar shi da haka kawai yaji kamar ya shaqe shi "Ni ne, ina Bilal din?" Ya furta a kagauce, dan jim yaji anyi cikin yanayin da ya saka shi fadin "Hello, ina Bilal din? Wacce unguwa tashar taku take?" Yana kallon Abbu ya juyo da jikin shi gabaki daya daga gaban motar yana fuskantar shi "Bilal ne ya bada lambata a tashar shine suka kira ni" Ya tsinci kan shi da fadama Abbu daya sauke wani numfashi da baisan yana rike da shi ba, Rayyan kuwa hankalin shi ya mayar kan wayar jin har lokacin ba'a kara cewa komai ba, ya bude baki zai magana yaji muryar mutumin ta daki kunnen shi da wata iska mai karfin gaske "Sun sami hatsari ne..." Cikin wata irin murya da Rayyan baisan daga inda ta fito ba ko yanda akayi ya iya motsa labban shi yace "Hatsari? A ina? A ina? Suna ina yanzun?" Wannan karin iskar yake ji tana kadawa a ko ina na jikin shi da yayi wani irin sanyi na ban mamaki, baya tunanin ya fahimci abinda aka fada din, saboda kunnen shi yaji daga wajen "...Babu wanda ya fita a motar, da tankar mai suka hade..." Abinda aka fada kafin nan da bayan nan duk bai jisu ba, iya inda yaji din ma bai fahimta ba shisa ya mikawa Abbu wayar "Ban gane me yake fada ba Abbu, kaji me yace" Abinda mutumin ya fadama Bilal shi ya sake maimaitawa Abbu da wayar ta subuce daga hannun shi yana furta "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Yana sake maimaitawa ko ina na jikin shi na bari, duniyar gabaki daya tana hargitse mishi "Menene? Me ya faru?" Yaya Ayuba yake tambaya saboda yanayin Abbu din duk ya hargitsa shi, shisa ya sauka daga kan titi yana yin parking din motar, wayar Rayyan da take jikin Abbu ya dauka, kiran ya yanke. Bai bi takan su Abbu ba ya sake duba lambar da yake itace kan kiran karshe da ya shigo, sau hudu yana kira duk ana ce mishi busy alamar ana kira da layin, sai ana biyar tukunna ta shiga "Ina kira akan Bilal Abdullahi Dikko ne, bamu fahimci me kake cewa ba" A nutse yayiwa kawu bayanin hatsarin da motar ta samu a hanyar Zaria, hatsarin da aka dade ba'a ga irin shi ba, saboda doguwar motar gabaki daya babu wanda aka fitar a ciki, wasu ma sun zama toka, iya gawarwakin da aka samu fitarwa basu fi goma ba idan aka hada jimillarsu, suma wasu duk sun hade da yan uwan su, yanayin da bai bar ma mutanen da suka kawo musu dauki wani zabi daya wuce hade su gabaki daya aka yayyafa musu ruwa aka sallace su hadi da haqa kabari daya aka hade su ba. Shi kan shi kawu babu inda jikin shi baya kyarma, saboda a tunanin shi ma ya kasa hasaso yanda lamarin ya kasance "Bilal ya rasu" Ya furta a hankali yana dorawa da "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Abbu ma abinda yake fadi kenan yana maimaitawa, bayason bama kwakwalwar shi wani space nayin tunanin komai. Sun kai mintina goma a wajen kafin ya iya samun karfin jan motar suna nufar gida. Da suka karasa ma aka bude musu ya shiga yayi parking, duka yan gidan babu wanda bai tashi ba. Sun zo harabar da ake ajiye motocin sunyi tsaitsaye ne kamar suna jiran dawowar su Abbu din. Shi kan shi Yaya Ayuba da ya fito yana ganin su tsaitsaye yaji kamar ya koma cikin motar, amman daga Abbu har Rayyan babu wanda ya iya ko motsawa balle yayi tunanin ko zasu fito. Ayya ce ta karaso wajen da sauri, kallo daya zakayi mata kaga yanda idanuwanta suka kankance suka sake launi saboda kukan da tayi, kukan da yanzun ne zata soma shi. "Kun gan shi?" Ta tambaya, Yaya Ayuba na girgiza mata kai hadi da dauke idanuwan shi daga kanta. Ya daiyi mamakin ganin harsu Khalifa a cikin gidan. Suna hada idanuwa da Khalifa ya tako ya karaso inda Yaya Ayuba da yaji shi gefe yake "Khalifa ya rasu... Bilal ya rasu" Yaya Ayuba ya furta girman kalaman na dukan shi, cikin tashin hankali Khalifa yake kallon shi, da hankalin shi, a tsayin rayuwar shi baisan wani abu rashi ba, wani daya taba shakuwa da shi bai taba rasuwa ba, yaune rana ta farko da aka fara sanar da shi labarin mutuwar da ya saka gwiwoyin kafafuwan shi yin sanyi gabaki daya, da Yaya Ayuba bai riko shi ba sai yakai kasa "Subhanallahi, Khalifa" Yaya Ayuba ya fadi, a zaton shi tunda Khalifan ne Babba a gidan, zaifi sauki shiya fara sani kafin a san yanda za'a sanar da Ayya da ta karaso wajen tana kallon Yaya Ayuba "Me ya faru? Me akayi?" Kan shi Khalifa ya dafe yana saki, numfashi yake fitarwa ta baki ko zai samu saukin abinda yake ji, amman komai kara hade mishi waje daya yake. Gurin motar Ayya ta karasa tana bude bangaren da Abbu yake, kan shi taga ya hade da gaban motar, a tsorace ta dafa shi, ya kasa dagowa "Ahmadi" Ta kira, amman bai ko motsa ba, mantawa tayi da yaranta na wajen, mantawa tayi akwai kowa banda ita da shi, ta saka hannuwanta tana dago da shi "Ahmadi..." Ta sake kira, idanuwan shi Abbu ya saka cikin nata, kafin ya dago nashi hannuwan ya kama nata da yake jikin shi, kamar yana so ta taimaka mishi ya fito daga motar, hakan kuwa tayi, duk da yana fitowa sai ya kasa yin komai banda jingina bayan shi da motar yana zamewa a hankali ya zauna, har lokacin yana rike da hannuwan Ayya shisa itama ta bishi kasan tana tsugunnawa, da wani yanayin tashin hankali yake kallonta "Ya rasu Maimuna... Bilal ya rasu" Ba wannan bace mutuwa ta farko da aka fada mata, ance baka san daci na mutuwa ba sai ranar daka rasa mahaifa, miji ko da. Ta dandani mutuwa kala-kala, bata san ciwon rashin da daban yake ba sai yau, dan wani abune ya tsirga mata daga dan yatsan kafarta zuwa tsakiyar kanta, kafin komai ya tattaro ya dawo yana tokare mata kahon zuciya, kukan kowa da wani yanayi yake isa kunnuwanta, musamman Rukayya da ta karaso inda take tana jijjigata "Ayya me suke cewa? Ayya kice mun karya ne, ki ce mun Hamma Bilal bai rasu ba" Bata ko iya juyawa ba, hannuwa Abbu da yake rike da nata ne kawai abinda tasan yana rike da sauran hankalin da take tare da shi, haka Rukayya ta dinga bin duk wanda ta samu tana jijjiga shi, har ta karasa inda Mami take tsaye hawaye na zubar mata, wani nabin wani. Tun jiya Ayya ta fada musu abinda yake faruwa, tun jiyan kuma Rukayya take tunanin rayuwa da yanda komai zai iya canzawa cikin kankanin lokaci. Tun da ta taso Ayya ke fadin laifukan Mami, duk da sanda ta fara hankali ta gane rabin mitar Ayya din na tare da kishin da yake dawainiya da ita. Mami bata taba ko da mata kallon banza ba, gaisuwar mutunci tana hadasu, wasu lokuttan ma har su danyi hira. Duk yanda Ayya taso ta ga laifin Mami bata taba gani ba, sai yau da ta karasa tana kama hannun Mami "Kingani ko Mami? Muna zaman mu ki dauko mana Layla, da bata shigo rayuwar mu ba da yanzun bamu san tashin hankalin nan ba, da Hamma bai bar gida ba, da labarin mutuwar shi baizo mana ba... Wallahi ba zan yafe miki ba, Mami ba zan yafe miki ba..." Rukayya take fadi tana durkushewa wani irin gunjin kuka na kwace mata. Duk abinda akeyi Rayyan na cikin motar, ba jinsu bane bayayi, kan shi yake ji kamar a wata duniya ta daban. Komai ne yake karasawa cikin kunnuwan shi kamar saukar ruwan saman da babu hadari, yana zaune ciki yaji muryar Haris na fadin "Bilal ya rasu? Yaushe? Garin yaya?" Kafin ya dora da "Ina Rayyan?" Baiji wani ya amsa shi ba, ya dai ji lokacin da Haris din ya bude murfin motar a bangaren da yake. Ya kuma ji hannun Haris ya kama na shi yana janyo shi ya fito da shi daga motar "Rayyan... Rayyan" Haris yake kira, amman baya ganin komai, ba shi da kalma ta hausa da zai misalta ganin shi da ita, abinda bature ke kira da "Blank" shine abinda yake faruwa da ganin shi. Yasan akwai mutane a zagaye da shi, amman baya ganin su, jin su kawai yakeyi. Da duk dakika kara jinsu yake, kukan su da maganganun su da yake tabbatar mishi da kalaman da yaji dai-dai ne, Bilal ya rasu, Bilal ya bar shi, ya mishi nisan da bashi da tabbas akan ranar da zai kamo shi "Rayyan..." Ya sake jin muryar Haris wannan karin yana jijjiga shi, iska yake nema, ko yayane ya samu ta isa cikin kwakwalwar shi, watakila ganin shi ya dawo, watakila ya daina jin duniyar na katantanwa da shi. Idanuwan shi ya lumshe yana jin wani shiru a cikin kunnuwan shi, kafin tunanin shi ya dauke gabaki daya. BAYAN KWANA UKU Hannun shi yake ji kamar a daure, yayi kokarin motsa shi amman bayajin karfi ko kadan a jikin shi balle ya iya motsawa, idanuwan shi ma ya dauki wasu dakika yana kokarin motsa su cikin son ya bude su kafin ya samu nasarar yin hakan, wani haske da yaji yayi mishi yawa na saka shi mayar da su ya rufe gam saboda kan shi da ya fara sarawa, sake gwada bude idanuwan na shi yayi, yanayin dakin ya fara karewa kallo, yana kokarin fahimtar inda yake, kafin yabi hannun shi da kallo, karin ruwa ne a jiki "Rayyan..." Yaji wata murya da bai taba sanin ta ba ta kira shi, a hankali ya juya kan shi yana kallon mutumin da kayan jikin shi yasa shi gane likita ne, kafin ya tabbatar da a asibiti yake, runtsa idanuwan shi yayi yana sake bude su da tunanin me yake yi a asibiti, sake runtsa idanuwan shi yayi, komai na dawo mishi kamar shirin film kafin ya bude su yana wata irin mikewa, likitan ya dafa shi "Akwai karin ruwa a jikin ka, kabi a hankali" Hannun likitan da yake kafadarshi ya ture, yana jin makoshin shi kamar sahara ce a ciki saboda bushewa, karin ruwan da yake jikin shi ya fisge yana sauko da kafafuwan shi kasa, maganar da ta daina karasawa kunnuwan shi ita likitan yakeyi, da ya saka kafafuwan na shi a kasa ya taka sai yaji kamar sunyi mishi sanyi, kamar yayi kwanaki bai taka su ba, shigowar Haris da ya fita siyo wata allura ya saka shi daga kai ya kalli Haris din da yaga kamar ya rame "Hamma mu tafi gida" Da alamun gajiya a tattare da Haris din yace "Yanzun ka tashi Rayyyan, dan Allah kayi hakuri ka kara warwarewa tukunna, kaji..." Kai Rayyan yake girgizawa tunda Haris ya fara magana, ba zai zauna ba shi kam, yana son ya ga Ayya, yana son ganin Abbu, da dukkan zuciyar shi yake jin son ganin iyayen na shi kafin ya bude zuciyar shi da koma menene yake ji "Dan Allah Hamma, rokon ka nakeyi, ka kaini wajen Ayya" Kai Haris ya jinjina mishi, bashi da karfin yin gardama da Rayyan. A kwanakin nan ukku shi kadai yasan kalar tashin hankalin da ya gani. "Ka zauna in zo to" Wannan karin Rayyan baiyi musu ba ya koma ya zauna kan gadon. Da ido Haris yayi wa likitan nuni da su dan fita. Dakyar ya samu ya yarda su tafi da Rayyan din, dan likitan na tsoron yanda jinin Rayyan din ya hau, idan ya sake faduwa zai samu babbar matsala. Sai da Haris yayi ma likitan alkawarin zasu dawo sannan. Duk yanda Rayyan yaso yin musu da Haris ya kama hannun shi yana dorawa a kafadar shi saiya kasa, bashi da karfi ko kadan.  Suna fita daga dakin Haris ya cire takalman kafar shi yana sa kafar shi daya ya tura su saitin Rayyan din da yaji wani abu ya tsaya mishi a wuya. Saka takalman yayi, shi Haris din na takawa a haka har suka fita daga asibitin zuwa inda motar shi take, sai da ya taimakawa Rayyan ya shiga sannan ya zagaya ya shiga shima. Gida suka nufa, wannan karin ma sai da Haris ya taimaka mishi suka fita daga motar. Sai Rayyan din yake ganin kamar gidan ya canza, saboda akwai mutane a harabar gidan, an kafa rumfuna, ganin su na kara gudun bugun zuciyar shi. Yana jin Haris yayi musu sallama wasu na furta "Ya karin hakuri?" Yana amsa su da "Mungode Allah" Ya ja Rayyan din suka wuce, har dakin Ayya, nan ma akwai mutane, bai damu da su ba, idanuwan shi Ayya suke nema, harya hangota a zaune da hijabi a jikinta, zame jikin shi yayi daga na Haris da yake rike da shi "Rayyan..." Batare da ya kalli Haris ba yace "Zan iya" Tsaye Haris din yayi yana kallon Rayyan ya taka ya karasa inda Ayya take zaune yana tsugunnawa a gabanta "Ayya" Ya kira, sai lokacin ta kalle shi, idanuwanta duk sun kankance "Rayyan..." Ta furta, yanda muryarta ta karye na tabbatar mishi da abinda yake son ji, dakyar ya dafa kasa yana mikewa, batayi kokarin hana shi ba harya bar dakin. Wuce Haris daya bi bayan shi yayi, bango yake dafawa yana tafiya saboda rashin karfin da yake ji, dakin su ya nufa yana kama kofar ya bude ya shiga, jin Haris a bayan shi ya saka shi juyawa "Dan Allah Hamma, ina son zama ni ka dai ne... Dan Allah" Sai da Haris ya sauke numfashi tukunna ya dan daga kai, su duk sunyi kukan su, ciwon bai fara rage musu ba, amman sun yarda da cewa Allah da ya basu Bilal ya karbi abin shi, Rayyan na bukatar lokaci yaji mutuwar shima, ya yarda da sun rasa Bilal, ya rasa Bilal. Shisa ya juya, anan inda yake tsaye Rayyan ya durkushe yana zama da gwiyoyin shi a kasa, zafin kirjin shi yakeyi, kamar an tura mishi wani abu a ciki haka yake ji, idanuwan shi ya lumshe "Ya rasu Maimuna... Bilal ya rasu" Kalaman Abbu suka dawo mishi, wani irin numfashi yake fisga kamar rayuwar duka na barin shi, sunan Allah yake son kira ko zai samu sauki amman ya kasa motsa labban shi, hade kan shi yayi da jikin shi saboda kirjin shi da yake zafi, kafin yaji an dago shi "Rayyan" Yaji muryar Abbu da ta saka shi dora kan shi a jikin Abbun "Kayi hakuri Rayyan, hakuri zamuyi, bamu da wani zabi daya wuce duk muyi hakuri" Kai Rayyan yake girgizawa Abbu, kalaman Abbu din na saka wasu irin hawaye masu zafin gaske zubo mishi. Da komai na jikin shi yake son yarda da mutuwar Bilal "Kun ga gawar? Kun binne shi Abbu?" Ya bukata wasu hawayen na zubo mishi, yana jin hannuwan Abbu a jikin shi kamar wata fanka da take fifita mishi ciwukan da ke mishi azabar ciwo "Bamu gani ba, baya nufin bai rasu ba, naga motar, munje ni da Yaya Ayuba, babu wanda ya fita a motar Rayyan... Kuma Bilal ita ya shiga... Kayi hakuri dan Allah, kayi hakuri" Wani irin gunjin kuka ya kwace ma Rayyan, kuka yakeyi kamar yaro dan shekara biyu, kukan da idan wani yace zaiyi irin shi koma meye zai faru da shi kuwa zai karyata. Amman yau kara shigewa jikin Abbu yake yana kuka kamar ran shi zai fita, baiga ta inda zai fara yarda ya rasa Bilal bayan ko gawar shi baigani ba, akwai wani abu a kasan zuciyar shi da yake fada mishi bai rasa Bilal ba, koya ne da yaji a jikin shi, da yaji cewa yana gab ko kuma ya rasa Bilal din gabaki daya "Ab.. Abbu zuciyata... Kirjina Abbu" Rayyan yake fadi yana jin kamar shima yabi Bilal din koma ina yake ko zai samu sauki. Kara gyara zaman shi Abbu yayi yana sake riko Rayyan, rabon daya rike shi a jikin shi haka tun yana dan karami, bai taba zaton zai sake samun dama irin haka ba, sai dai yanayin ba mai dadi bane balle yace zaiyi wannan tunanin. Rike yake da Rayyan da sai rashin Bilal yasa shi kasancewa karkashin inuwa daya haka da shi. Da dukkan zuciyar shi yake jinjina kokarin iyayen da suka taba binne yaron su. A gefen zuciyar shi addu'ar samun saukin karbar rashin Bilal yake yiwa Rayyan da har lokacin kuka yake a jikin Abbu kamar ba zai taba dainawa ba. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:09 PM - 111: Jan 4, 2021. 28 Kwance take, dakyar take iya daga idanuwanta. Haris ne ma ya kirata a waya yana tambayar ta ko tana son cin wani abu, tace mishi yoghurt. Da yawa ya siyo ya kai mata daya har daki, sauran yace ya saka mata a fridge. Shima ko rabi bata sha ba ya fita daga ranta, kusan aman shi tayi. Hannun ta dafe yake da cikinta da ta fara ganin alamar ya dan taso, saboda bata da tumbi da can. Lumshe idanuwanta tayi tana jin suna mata wani radadi saboda kukan da takeyi, ko hasken waya bata so a cikin idanuwan nata. Bata taba tunanin zata kwana ta yini ta sake kwana ta yini tana kuka ba sai da labarin rasuwar Bilal ya daki kunnenta. Ita safiyar ranar da akayi rasuwar bacci ta dan samu, saboda ta kwana tana kuka, ta kwana cikin tashin hankalin rabuwa da Rayyan, ta kira shi yafi sau hamsin bai daga ba, ko ya daina son ta tana son ya saurareta, tana son ta fada mishi batasan yanda akayi abinda ya faru din ya faru ba. Tana son ta bashi uzurin da kowa ya kasa yi mata, ta kare kanta kamar yanda Ayya ta kare Bilal, yanda ta kira abinda ya faru da su da sunan kuskure. Saboda idan Rayyan da kan shi ya barta ina zata je? Wa zai karbeta? Waye ba zai dora alhakin komai a kanta ba? Kuskurenta ne daukar kafafuwanta taje gidan su, ta rigada ta san wannan, bata tsaya ba har dakin su. Amman batajin tana da laifi a cikin jirin da ya fara dibarta cikin yan mintina kadan da zamanta. Ta zauna ne ta dan huta, ta maida numfashi, bama zata ce ga dalili kwara daya da yasa ta zauna ba, tunda ko Rayyan yana nan ba ko yaushe take zama ba, baya bari, da ta shigo yake mikewa. Da taji maganar shi kamar yanda ya hana mata zama a dakin, da gidan ma gabaki daya ko da suna nan, balle kuma basa nan, watakila da bata zo in da take ba yanzun. Da tarin burin da take da shi na auren Rayyan bai ruguje ba. Da bata ga tsanarta a cikin idanuwan shi ba. Abbu ya kara hargitsata da furucin shi, saboda idan duniya duka zata hade da ita a waje daya bata hango yanda zata fara zaman aure da Bilal ba. Ko na minti daya zuciyarta bata taba doka mishi ta wannan fannin ba, yanda zata fara kwanciya ta tashi da shi karkashin inuwar aure da sanin ya rabata da komai da take takama da shi, banda Martabar ta harda Rayyan, harda Hamman ta. Ba laifi take kokarin dora mishi ba, amman zata iya farawa idan suka kasance inuwa daya. Tashin hankali ne shimfide take hangoma rayuwarta da ta birkice cikin kankanin lokaci. Da tunani kala-kala a ranta har gari ya waye, da tayi alwalar asuba ma sai da ta koma ta dan kwanta saboda sanyin da ta dinga ji da yake akwai zazzabi a jikinta. Ta samu bacci ne ba jimawa, dan ji tayi kamar tana bude idanuwanta ta mayar da su ta rufe ne taji kamar an fasa kuka, yanayin da ya sakata bude idanuwa babu shiri, ba kuma karya kunnuwanta sukayi mata ba, kuka ne, dakyar ta iya saukowa daga kan gadon, da yake window din dakinta ta wajen harabar motocin gidan ne, zagayawa tayi ta leka ta hango kusan kowa na gidan a wajen. Kafin kunnuwanta su tsinto mata "Bilal ya rasu" Cikin muryar da bata san ko waye bama, bangon wajen ta dafa tana runtsa idanuwanta, duniyar na wulwula mata kafin wani abu ya tsirga mata a ciki yana saka bayanta amsawa. Babu shiri ta durkusa saboda azabar da ta dirar mata ga kidimar mutuwar Bilal da take mata kamar almara, sunan Allah duk wanda yazo bakinta shi take kira, tana dafe cikinta da kamar ana tsinka wani abu a ciki, kafin wasu irin hawaye kamar an kwance wani abu a cikinta su fara zubo mata. Sai a cikin kwanakin mutuwar washegari ta fara jero neman gafarar Allah saboda sabon da tasan ta dinga yi na yanda za'ayi Bilal ya rasu. Kafin wani matsanancin tsoro ya tsirga mata na yanda zai fara amsa tambayoyin shi a kabari, tunanin ko abinda ya gifta a tsakanin su zai rushe tarin ayyukan shi. Ranar bata iya runtsawa ba, gani take kamar da ta rufe idanuwanta itama mutuwa zatayi gaba da ita. Kuma tana jin daudar da take da ita tafi ta Bilal, duk laifukan shi ba zasu wuce abinda ya gifta a tsakanin su ba. Amman ita kam duk wani karami da babban laifi haka ya dinga gifta mata a rai yana kara hautsina mata lissafi. A cikin sujjadar duk sallolin ta na farilla a kwanakin nan yafiya take rokawa Bilal, ko da basu da bayanin da zasuyi akan abinda ya faru, zunubin dayane dana wanda suke da bayanin yi. Amman Allah Mai Rahma ne, tana kuma da yakini mai girma akan hakan. Yau kwana biyar, amman ko motsi taji sai ta dauka shine zai shigo, sai taji kamar wani ne a cikin gidan ya zo ya karyata labarin mutuwar. Zuciyarta tayi wani irin nauyi na ban mamaki, ga zazzabin da take kwana tana yini da shi. Yau ne ma ta balli Panadol ta sha. Ita kadai take kukanta, Mami bata mata magana balle tasa ran zata lallasheta, ko ta gaisheta sama-sama take amsata. Haka zata sha kukanta ta kuma bama kanta hakuri, ta daina kokarin kiran Rayyan tunda baya dagawa, ta dai fada mishi duk wani abu da yazo kanta ta text. Tun tana duba wayarta ko zai amsa harta daina ma. Wani irin kadaici take fama da shi na ban mamaki, sai dai inta rage volume din wayarta sai ta saka karatun Qur'ani, takan ji nauyin da kirjinta yayi mata yayi sauki lokutta da dama, ko yau da ta tashi ta gwada shiga wajen hotunan wayarta ta ga na Bilal, amman yanda zuciyarta take dokawa sai ta kasa. Sai dai rashin ganin hoton bai rage mata zafin rashin Bilal ba, bai kuma hana mata ganin shi a cikin idanuwanta ba, ko suna rufe ko suna bude. Yanzun ma hannunta ta dora saman cikinta tana shafawa a hankali. Tudun shi na tabbatar mata da yana nan, da dane yake girma a cikinta, abinda har yanzun ya kasa samun wajen zama a kwakwalwarta. Gyara kwanciyar ta tayi, tana jin hawayen da ta saba dasu yanzun suna silalowa ta gefen idanuwanta zuwa kan filon da take kwance a kai. Akwai tarin abubuwa da har yanzun basu gama zauna mata ba, taji ciwon su harta san yanda zata fara jinyar ciwukan balle kuma ta fara hango ranar warkewar su. Tunanin Rayyan ne ya kara dirar mata, yana saka hawayenta cigaba da gudu. Rayyan da ya samu dakyar ya raba jikin shi da gado ya fito yana nufar bangaren Ayya dan ya dauko ruwa, babu wanda yayiwa magana ya wuce Kitchen ya dauki ruwan ya sake ficewa. Ayya ma da take zaune kan kujera bin shi tayi da kallo. Rukayya take ce mata ruwan saura leda biyu ajiye a kasa, na cikin fridge din kuma wasu duk sunyi kankara, batama iya amsa Rukayya ba, wayarta da take gefe ta janyo da nufin ta kira Bilal tace mishi ya kira yan gidan ruwan kai tsaye yaji idan zasu shigo yau suna so. Da yake nan makotan su ta gefe matar na siyar da ruwa, zobo da kunan Aya. Harta dauki wayar ta cire daga key zuciyarta tayi wata irin dokawa, komai na dawo mata. Tana tunanin yanda zata fara rayuwa babu Bilal a ciki, babu yaronta. Saboda bata hango ranar da komai zai dawo mata dai-dai ba. A rayuwar ta gabaki daya ko a mugun mafarki batayi hasashen daya daga cikin yaranta zasu barta ba, duk yanda takan hango rayuwa mai karewa ce, ita take ganin zata mutu tabar su, kamar yanda nata iyayen suka mutu suka barta. Sai dai mutuwa ba zabe takeyi ba, lokaci me kawai abinda take dubawa, babu ruwanta da yanda makusantan wanda ta dauka zasu kasance cikin jimami da radadin rashi. Da mutuwa na duba wannan da tabar mata yaron ta. Yanzun ta dandani zafin rashi na daban, ta san yanda kakeji idan ka rasa danka. Sai dai bakowa bane zai fahimci yanda kakeji idan kayiwa dan da aka fada maka ka rasa batare da kaga gawar shi ba kuka. Saboda bata jin har abada wani bangare na zuciyarta zai aminta da ta rasa Bilal, zataci gaba da kallon kofa, da tsammanin shigowar kowa a matsayin danta, saboda bata ga gawar shi ba, bata kalle shi a shimfide a gabanta ba. Shisa mutuwar shi take mata wahalar dauka. Jiya ma Abbu sai da ya fara mata wani wa'azi da bata fahimta, tace mishi "Ahmadi ba ganewa zanyi ba wallahi, ka kyaleni inyi kuka ko zuciyata zatayi mun sauki..." Kyaleta din yayi kuwa. Yanzun ma hannu ta saka tana goge hawayen da suka tarar mata a gefen idanuwanta. Hakuri ya zame musu dole ta sani, amman yanzun zatayi kuka, zataji ciwo, hakurin zai biyo bayan su. Wayar da ta ajiye ce ta dauki ruri, ta dan kalleta, ganin Hajiya Dije rubuce a jiki ya sakata daukar wayar, cikin sanyin murya tayi mata sallamar da ko amsawa batayi ba "Ya karin hakuri Maimuna?" Numfashi Ayya ta sauke, kiran na tuna mata da sau daya Hajiya Dije din tazo mata gaisuwa. Abin na kara bata mamaki duk kusancin su. "Alhamdulillah" Ayya ta sake amsawa har lokacin muryarta a sanyaye "Ina ta so in shigo dan mu samu mu zauna. Ranar naga ga mutane ga shi kuma rasuwa na tabaki" Shiru Ayya tayi tana jin Hajiya Dije ta cigaba da fadin "Wallahi sai kin tashi tsaye sosai. Kinga me nake fada miki ko? Haka ake so a kada miki kan yaran duk su cimma ajalin su. Kudi zaki turo inje miki wajen Sharu dana samo kwanaki" Dan dafe kai Ayya tayi, tana mamakin hali irin na Hajiya Dije da yanda akayi bata ga kuskuren da yake tare da duka shawarwarin da take bata a baya ba. Danta ya mutu ba zata ko barta taji da abinda yake damunta ba, tana son nuna mata cewa mutuwar Bilal din ma ba daga Allah bane ba. Bata ce babu sihiri ba, amman duk abinta tasan abubuwa da yawa daga Allah ne. Da Malaman na da amfani da sun hana ma Mami aure mata miji, sun taimaka mata ta fitar da ita daga gidan. Amman da yake abin duk bigene ga Mami nan zaune daram a cikin. Ita da suna wani aiki duk bugun kasar da sukayi mata da sun hango mata kaddarar Layla da Bilal. "Ba wannan bane a gabana Hajiya Dije. Banda duk wannan lokacin yanzun" Ayya ta furta wani abu na tokare mata makoshi "Bangane baki da wannan lokacin ba? Kar dai an saka miki shashatau ni Dije..." Dan karamin tsaki Ayya taja a cikin ranta "Wai ke babu wani abu da zai faru da ba asiri bane ba? Idan ma shine na bar mutum da Allah. Dan Allah ki kyaleni inji da abu daya" Bata ma jira Hajiya Dije ta amsata ba ta katse kiran. Tana jan tsaki a fili, kawai sai taji ranta na baci da abinda Hajiya Dijen tayi mata. A lokaci daya hawaye masu zafi na zubo mata. Bilal da zai mata hirar shi sai ya ga tayi dariya ma baya nan. Mikewa tayi ta shige daki, ta dan fito ne ko zata sami saukin abinda take ji daman. * Ruwan ya ajiye a gefe, tun jiya da dare ya kare mishi. Haka ya dinga juyi a gado, ya tashi yaje ya dauko abin na mishi wani iri. Guda daya ya fasa ledar ya dauka, anan tsayen ya shanye, yana jin muryar Bilal kamar yana dakin "Ba kyau shan ruwa a tsaye, ka samu waje ka zauna, ka juye a kofi" Da dafe kan shi yayi, kirjin shi na daukar zafi. Karasawa yayi kan gadon ya koma ya kwanta. Gobe ne ya saka ranar da zai koma Kaduna. Saboda sati daya suka bashi, har gida Bappa yazo musu gaisuwa shi da Baba da yayi ma Rayyan din nasiha mai shiga jiki ganin yanda ya rame yayi duhu. Nasihar da bata kai mishi daren ranar ba ya nemeta ya rasa. Kusan kullum ma kuka yake yanzun, daren jiya wando zai dauka ya ga rigar Bilal, kawai yaji idanuwan shi sun cika da hawaye. Yanzun ya yarda da maganar Bilal da suna kallon wani film yana mamakin yanda hawayen jaruman mazan suke a kusa "Kuka fa shi yake yin kan shi Hamma, karka yi mamakin ganin kana hawaye kamar karamin yaro" Kai kawai ya girgiza, saboda yasan suna da bambanci mai nisa da turawan da suke kallo, yanayin rayuwar su, da komai daban ne. Sosai ranar ya dinga tunanin a duniya abinda zai saka hawayen shi zuba. Sai gasu yanzun, kila duk wanda suka taru ne shekara da shekaru suke fitowa gabaki dayan su yanzun. Wayar shi ya mika hannu yana dauka. Da yake ya kashe karar gabaki daya, baima bi ta kan tarin kiran da aka dinga yi mishi ba. Ya san ba zai wuce Layla ba. Bai ganta ba tun rasuwar, baya so ya ganta saboda yayi waje a kasan zuciyar shi ya dannata. Mutuwar Bilal ce a gaban shi, bayason tunanin komai. Haka kawai ya tsinci kan shi da bude bangaren sakon shi, yana cin karo dana Layla sun fi guda arba'in. Can kasa yayi yana cigaba da dubawa, na MTN ya dinga goge su, saina banki ma duk yabi ya goge. Zuciyar shi nayin tsalle zuwa makoshin shi, jikin shi har bari yake lokacin da yaga sakon Bilal. Da sauri ya bude yana soma karanta na farkon: "Ban san me zance ba Hamma, na ce ba zan roki ka yafe mun ba saboda ina jin ban cancanci hakan ba. Amman na kasa, rokon yafiyar ka na daga cikin abu na farko da nake son yi. Ka yafe mun, dan Allah ka samu waje a cikin zuciyarka ka yafe mun" Numfashi yake fitarwa a hankali lokacin da ya sake bude wani sakon "Kana cikin rudani kamar yanda nake ciki daga randa abin ya faru zuwa yau. Baka tambayeni ba, nayi kokarin maka bayani iya yanda zan iya kaqi saurarena, dan Allah ka karanta abinda zan fadi, bance ka fahimce ni ba, ni kaina ban fahimci komai ba. Amman ka karanta" Jikin shi Rayyan yake ji ya dauki dumi kamar ana hura mishi wuta, dakyar ya iya samun karfin motsa yatsan shi ya latsa wayar yana samu ya shiga wani sako da alamu ya nuna mishi dogo ne "Na kaika ta sha ranar na koma gida, laifina ne da ban kunna fitilar dakin ba, amman mun saba Hamma, sai muyi shiga nawa da duhun dakin, ban san tana ciki ba, wallahi ban kawo ma raina Layla na ciki ba, watakila daga baya ta shigo, shima ban san shigowar ta ba. Ruwa kawai na dauka akan tebir na sha, sai kaina ya fara nauyi na kwanta. Ban san me ya faru ba, ban san ya akayi abinda ya faru ya faru ba, ba ina kokarin wanke laifina bane. Ina so ka sani ne kawai, kaji nawa bangaren Hamma, wallahi ban san ya akayi ba. Ka yafe mun, ka yafe mata itama, karka bari kuskurena ya shiga tsakanin tarin kaunar da takeyi maka" Rayyan bai ma duba dayan sakon Bilal din ba, saboda zuwa lokacin ya tashi zaune, da sauri yake shiga sakonnin Layla yana son tabbatar da abinda tunanin shi yake kawo mishi "Dan Allah Hamma, wallahi ban nufin in kwanta bakwa nan ba, ruwa kawai na sha sai in dan huta in tafi, jikina yai mun nauyi, naji bani da lafiya lokaci daya. Shine na dan kwanta in nutsu..." Bai karasa karantawa ba saboda yanda komai yake hautsina mishi. Numfashi yake kokarin fitarwa cike da tashin hankali, baisan lokacin daya danna lambar Layla ba ya kara a kunnen shi, baima ji tayi ringing ba sai dai muryarta da yaji cikin kunnen shi "Hamma... Hamma na" Ta furta tana saka wani abu ya tsirga mishi, dakyar ya iya lalubo yawu ya jika harshen shi da yake ji a bude kafin ya bude bakin shi "Ruwan da kika sha... Layla ruwan da kika sha a roba ne?" Harya bude bakin shi zai sake tambayar ta ta amsa "Eh..." Wani nannauyan numfashi yaja kirjin shi kamar an kulle "Zaki tuna a ina kika dauka? A cikin dakin mu a ina?" Wani shirun ta sakeyi da yake ji har bayan zuciyar shi "Na zauna a gefen gado, anan nagan shi, an sha ne an ajiye kamar, me ya faru?" Wayar ya sauke daga kunnen shi, baima kashe ba ya mike yana dora hannuwan shi saman gwiwoyin shi ya dan rankwafa kamar mai shirin yin raku'u kafin ya sake mikewa yana furzar da iska ta cikin bakin shi. Ruwan da ya ajiyene suka dauka, daga ita har Bilal ruwan da ya durama kwayoyi ne suka dauka suka sha. Laifin da yake fadama Bilal ba zai yafe mishi ba, laifin da ya ke son taba zuciyar Layla kamar yanda ta taba tashi a kai ne yayi yawo ya zagayo ya shaqe mishi wuya yana girgiza gabaki daya rayuwar shi. Dakin yake gani kamar yana kara zurfi, ko kuma shine yake shigewa cikin wani irin rami da baisan akwai a dakin ba ya rasa. Sai da tafukan kafar shi suka taka kasa ya gane sun dauke shi zuwa wajen dakin, sun kuma ja shi zuwa bangaren Ayya. Kamar su suke da iko da shi, yanajin dai zuciyar shi take iko da gabaki dayan su, saboda ita ce take son kallon idanuwan Ayya ta fada mata yanda shine sanadin rayuwar Bilal, dan da tafi shakuwa da shi sama da su. Da bai zuba kwayoyin a ruwa ba, da ya zuba din daya shanye abin shi, ko ya fitar da shi. Da ba su dauka ba, Bilal da Layla da basu gani ba sun sha har sunzo in da suke yanzun. Da suna zaman su lafiya, suna rayuwar su cikin walwala. Duka laifin na shi ne, ko da bai ganta a falo ba dakin baccin ta ya karasa yana kwankwasawa, sai da yaji ta bashi izinin shiga sannan ya tura kofar ya shiga yana mayarwa ya rufe "Ayya laifina ne, ni na kashe Bilal..." Murmushi Ayya tayi mai ciwo, idan aka tsaya zaqule-zaqule tana da tabbacin laifin zai rarrabu, kuma daga Mami har Abbu ba zasu fita ba. Mami ta dauko musu Layla kamar yanda Rukayya ta fadi, Mami kuma tabarta zuwa Zaria da yardar Abbu. Duk da wani abu a kasan zuciyarta yana fada mata kaddarar da tabi Layla da Bilal Zaria zata iya samun su a cikin gida. Amman kuma ba zata ji kamar laifin na su Mami bane ba, idan har kaddarar ta biyo su Bilal har gida, ba zataji duk wannan abin da take ji ba. "Ka bar fadin haka Rayyan, mutuwar sabuwa ce shisa. Kowa ma idan ya zurfafa tunani zai iya ganin kamar laifin shine" Saboda itama tanajin akwai nata laifin, da ta duba Bilal din da dare, bayan yabar dakin Abbu da taje tayi magana da shi. Da ta canza mishi tunani da cewar tafiyar ba mafita bace ba, tafiyar kuma ba zata kawo sauki a zukatan su ba. Amman batayi ba, laifin nan zai zauna da ita na lokaci mai tsayi. Kai Rayyan ya girgiza mata, sosai take kallon shi, zuciyarta na matsewa a cikin kirjinta, duhun da yayi a kwanakin sai kamanin shi da Bilal suka kara fitowa, sai dai Bilal kullum baka raba fuskar shi da fara'a "Laifina ne Ayya... Ni na zuba abu a ruwa ya sha, duka laifin nawa ne" Cike da rashin fahimta Ayya take kallon Rayyan din, Haris yace sai ta dinga mishi addu'a saboda yanda mutuwar Bilal ta dake shi, karya samu matsala. Bata dauki abin da muhimmanci ba saboda itama mutuwar ta dake ta. Sai yanzun da yake mata wasu zantuka da bata ganewa. Numfashi yaja yana kokarin bude kafofin shigi da ficen iskar shi da suka toshe, ba zai manta wayar Bappa da Baba ba, kuma Bappa yace mishi "Sihiri gaskiya ne Rayyan, mutane ba su da kirki wani lokacin, Baba bai gayamun kai tsaye ba, amman ciwon ka na da alaka da hakan" Bai amsa Bappa ba, saboda bashi da abinda zaice, baiga dalilin da wani zai yi mishi sihiri ba, idan anayi din kenan. Kuma ace tunda karancin shekarun da yasan bai isa daukar hakkin kowa ba balle aji haushin shi, ko a yanzun da girman shi bashida wani abu da zai tsarewa wani komai. Kuma sihirin ace an hana kusancin shi da iyayen shi? Abin da wahalar dauka, sai dai a halin da yake ciki yanzun zantukan dawo mishi sukeyi, ko zai samu wanda zasu raba laifin da yake ji tare, dan nauyin laifin yana gab da danne shi idan har bai raba da wani ba. Yau daya zaice da ba'ayi mishi sihiri ba da bai fada depression din da yaja mishi shan kwayoyin da ya zuba a ruwa harsu Bilal suka dauka ba, yana son ya kalli idon ko waye yayi sanadin zuwan su inda suke yanzun ko zai samu sauki "Sihiri akayi mun, ba laifina bane ba nima" Ya tsinci kan shi da furtawa "Baba ne ya fada, kuma yayi mun addu'a na samu sauki yanzun, koma menene Bappa yace naci ne ko na sha a cikina shisa bana son zama waje daya da ku, da Abbu, bana son duk abinda Abbu yake so, Ayya wani marar imani zai raba da iyayen shi? Ribar meye zai samu?" Da farko ta dauka matsala Rayyan ya samu, sai da kalaman shi suka daskarar da ita a inda take zaune suna saka wani irin sanyi ziyartar ta kamar tana cikin fridge. Shi kan shi baisan me yake fadi ba, kawai so yake yau duk abinda zai iya amayarwa ya amayar ko zai daina jin nauyin abinda yayi "Baku sani ba, Bilal bai sani ba amman ina shan kwayoyi, sune na zuba a ruwa har ya samu ya sha, har suka sha da Layla... Laifina ne Ayya... Ina jin laifina ne. Amman idan da gaske sihiri akayi mun, ni wa zan daurawa laifi? Wa zance ya kawo mu inda muke yanzun ko zan samu sauki. Ayya ina zan kai laifin nan?" Rayyan ya tambaya yana kallon cikin idanuwanta "Ya zan fara rayuwa a duk rana da sanin nayi sanadin mutuwar Bilal?" Ya karasa maganar wasu hawaye na cika misji idanuwa. Numfashi me nauyi ya sauke yana sake kallon Ayya da ta sadda kanta kasa, bata son ganin shi, ya kashe mata yaro dole taqi son ganin shi, shima baya son ganin kan shi yanzun nan. Juyawa yayi yana ficewa daga dakin, sai dai baisan inda ya kamata ya nufa ba, bakin kofar dakin su ya tsaya yana tsintar kan shi da kasa shiga. Abu daya zai gani na Bilal abinda yake ji yana gab da ballewa a tare da shi zai balle, tsaye yake yana maida numfashi yana kuma son ganin hawayen da suke cikin idanuwan shi basu zuba ba. Kirjin shi ya dan dafe yana murza inda yake ciwo kamar zai rabe biyu. "Hamma..." Yaji muryar Layla da ta saka shi juyawa, kamar tsayuwar wahala take mata shisa ta dafa bango. Ta dade bakin kofa ko zata ga giccin Mami kafin ta samu ta fito, tana jin numfashin da Rayyan din yake fitarwa ta cikin wayar cikin yanayin daya daga mata hankali, gashi tanata magana shiru kafin kiran ya yanke. Zuciyarta ta kasa hakuri, wata irin soyayyar shi ce take dawainiya da ita, tunanin halin da yake ciki, tsantsar ciwon zuciyar da taji a cikin muryar shi ya hade yana sakata kasa hakuri sai ta gan shi, ko na dakika biyune ta leqa taga yana nan dai zata samu sauki. Sai da ta fara takowa taji kamar tana yawo saman iska. Shikuma kallonta yakeyi, idanuwanta na saka shi jin wani iri, amman ya kasa daina kallon su, saboda a cikin su yake ganin tarin rudani a shimfide, kafin ya samu ya kalli duka fuskarta da har zanen kashin kuncinta ya fito kamar wadda ta dade tana jinya, tayi zuru zuru ta fita hayyacinta. Tana cikin firgicin da yake jin duka shine silar shi "Layla" Ya kira da wani yanayi mai wahala Idanuwanta cike taf da hawaye tana jan numfashin da ta fitar da shi tare da hawayen ta da suka zuba, dayan hannunta ta saka ta share su, tana kallon yanda fuskar shi take cike da gashi, kayan jikin shi sunyi daudar da bata taba ganin shi da ita ba, shi kan shi ya mata wani irin cuku-cuku. Ko takalma babu a kafafuwan shi, Rayyan da ko a daki baya yawo babu takalmi ko safa, Rayyan da ta san zai iya wanka hudu a rana, shine yau a firgice haka. Hannunta ta kai tana dafe cikinta da taji kamar ya kulle, yanayin da ya saka Rayyan bin cikin nata da kallo. Akwai yaron Bilal a cikin nata, a jikinta yana rayuwa, kwai daya da Bilal yake da rabon samu a duniya. Kwan da zaizo ta hanyar da kowa yake gudu saboda shi "Ki yafe mun Layla" Yayi maganar yana sadda kan shi kasa, wasu hawayen ne masu zafi suka zubo mata, bata san me yasa yake rokon ta yafe mishi ba. Bayan ita din ya kamata ta roki ya yafe mata. Jin tayi shiru ya saka shi sauke idanuwan shi cikin nata, yana jin yanda bata kyauta mishi ba "Ban hana ki zama a gidan mu idan bana nan ba? Me yasa kika zauna?" Kafadu ta dan daga mishi, bata da bakin magana bata da wani bayanin da zatayi mishi "Baki kyauta mun ba, kin sani ko?" Da ta taimaka mishi bata zauna ba, da ya gujema abubuwa da yawa. Duk da kukanta na kara mishi zafin da zuciyar shi takeyi. Amman yana bukatar raba laifin da wani. Numfashi ya sauke ya juya da nufin shiga daki "Hamma..." Ta kira shi, juyowa Rayyan yayi, kuka yake so yayi har sai inda hawayen shi suka tsaya. Amman bayason yi a gabanta. Baya son kowa ya lallashe shi. Idan ya gama duk zai roke su da su yafe mishi, sai ya kara yawaita addu'o'in shi akan Bilal ko zasu isa wanke girman abinda yayi mishi idan suka tsaya a gaban Allah. "Idan na kira ka daga, dan Allah kayi mun kowanne hukunci karka rabani da kai, abubuwan da suka rage mun basu da yawa" Kai kawai ya iya daga mata yana shigewa daki. Wani irin numfashi ta sauke mai nauyin gaske tana samu ta koma bangaren su tana wucewa daki. Wannan karin waje ta samu ta zauna, kafafuwanta taja ta hade su da kirjinta, sai taji bata iya fitar da numfashi sosai, kamar ta matse cikin nata da yawa, babu shiri ta sauke kafafuwan nata, kafin wani irin tashin hankali ya dirar mata, cikine a jikinta da gaske, da duk ranar da zata wuce da yanda cikin zai cigaba da fitowa. A hankali take jin yanda ba rabuwa da Rayyan bane matsalarta ta farko, yanda zata fara rayuwa da cikin da in ya tako duniya bata da amsar bashi, cikin da Bilal baya nan ballantana ya tayata yi mishi bayani "Na shiga uku" Ta furta a hankali tana fashewa da kuka, komai nata ya canza, rayuwarta, makaranta, watakila tabarta kenan har abada, idan haihuwa tayi ta ina zata fara yawo da yaro cikin mutane, me zata ce musu idan sun tambayeta? Ya Mami zata fara shiga dangi, wacce tambaya kowa zai jefe ta da ita? Watakila kowa ya fara tunanin Mami bata riketa da kyau ba, su Abbu basu riketa da kyau ba saboda ita din ba yarsu bace ba. Duk yanzun ne ta samu damar yin wannan tunanin da yake kara daga hankalinta, kasa ta kwanta kan tayal din dakin da sanyin shi ke kara mata zazzabin da ya sake saukar mata, kuka takeyi marar sauti, kukan da bata hango ranar da zata daina shi ba. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:09 PM - 111: Jan 7, 2020 29 Tayi kuka fiye da wanda tayi na rasuwar Bilal, kukan da bata tabayin kalar shi a tsayin zaman duniyarta ba. Saboda akwai banbanci a kuka na rashi, akwai kuma banbanci a kukan sanin cewa kaine da laifi a wannan rashin, kuka ne tayi na dana sani kan abubuwa da dama. Yanda duk zata so raba nata laifin da Dije da kuma Gwaggo da suka dorata akan bin Malamai ta kasa, sosai take so ta boye bayan ko da kuruciya ce dan samun sauki. Amman da hankalin ta lokacin, ko da kuwa da shekaru za ayi amfani wajen auna hakan, balle kuma zaman gidan miji da kuma yawan yara. Ba abokai nagari da zatayi shawara da su bane ta rasa a lokacin, da ta dora kacokan laifin akan su Hajiya Dije. Tana zagaye da yan uwanta da suke matukar kaunarta. Yan uwan da ta gujewa saboda suna gaya mata gaskiyar da bataji. Sai ta dinga ganin kamar babu kaunar nan da tayi tunanin akwaita a tsakanin su. Da sun fada mata abinda take son ji kamar yanda su Gwaggo suka dingayi. Yanzun ne da hankalinta ya dawo jikinta take tunani kala-kala. Ko da asiri Mami tayi ta aure Abbu ba zai zama dalilin da itama zata ce ta fara shiga Malamai ba, wannan ba uzuri bane ba sam. Balle da idanuwanta bata shaida hakan ba, Gwaggo ta fara kawo mata wannan tunanin. Kuma ta hau ta zauna saboda yayi dai-dai da abinda take son ji. Akwai tarin son zuciya a abinda tayi. Yanzun tunanin cutar da Haris ko da yaya ne sai da ya sa kanta sarawa saboda tarin kaunar da takeyi mishi. A baya idanuwanta ya rufe da soyayyar da taga Abbu yana nuna mishi, tana manta lokacin tata kuruciyar da girma, da kuma yanda kaf kowa yake maganar kusancin da take da shi da nata baban. Bata kuma duba kalar kusancin da take da shi da Bilal ba, da yanda duka yaranta sukan ce tafi son Bilal akan su. Tunani ne kala-kala yake mata yawo yanzun. Son zuciya ya kaita ya barota, abinda taso da dan wani sai Allah ya juya shi kan nata yaron, ko ma tace nata yaran. Tana ta takamar tana kula da abinda yake faruwa da su, sai ta kasa fahimtar a baudadden halayya irin na Rayyan akwai tarin abubuwan da yake fuskanta. Balle kuma ta kalli Bilal da kullum take dorawa nauyin kula da Rayyan din. Sai ta maida hankalinta wajen raba abinda kaddara ta rigada ta gama rubutawa, a karo na babu adadi tayi kokarin cutar da Layla. Da yake kaddara na biye da su sai gata da cikin Bilal ta hanyar da Ayya zatayi komai da zata iya dan kaucema faruwar hakan. Yanzun da take wannan tunanin sai abin ya kara tsoratata, saboda tana jin yanda cikin jikin Layla ne kwai daya da Bilal yake da rabon samu a duniya. Kwan da bata damu da hanyar da ya samun ba in dai zai taka duniya ta rike shi a cikin hannuwanta. Har cikin zuciyarta take jin son abinda yake cikin Layla din. A gefe daya kuma tana tunanin da idanuwan da zata kalli Rayyan yanzun. Zata so ta fada mishi da ita ya kamata ya raba laifin da yake jin ya mishi nauyi. Amman hakan ma ba mafita bane a hargitsin da yake ciki. Idan ta gaya mishi zata kara rikita shi, amman tana bukatar yafiyar shi, duk da take mahaifiyar shi wannan hakkine mai girman gaske. Balle kuma yanzun ta kula da Rayyan din ya samu lafiya. Saboda kalar kusancin da yake tsakanin su a yan kwanakin nan, ba zata kara jefa shi cikin hargitsi ba. Zata fara da dai-dai ta tsakanin ta da Ubangijin ta da farko, sauran zasu fi zuwar mata da sauki, zata roki Allah da ya saka sauran lamurran zuwa mata cikin sauki. Tana nan zaune a daki taji an kwankwasa, sai da ta share hawayenta sannan ta amsa, ta dauka ma Rukayya ce, sai taga Rayyan ne, yanda ya fara sauko rabin fuskar shi yana sakata runtsa idanuwan ta kafin ta sake bude su akan shi, dan yayi mata kamar Bilal, manya kayane a jikin shi farare kal sai hula ruwan omo mai cizawa. "Ayya yanzun zan wuce, Bappa ya karaso" Numfashi ta sauke tana kallon shi "Har kana da natsuwar komawa?" Tayi tambayar a sanyaye, kafadu Rayyan ya dan daga mata. Idan ma bashi da natsuwar komawa ba zai zauna ya jirata ba. Tunda bashi da tabbacin ranar zuwanta ko zata zo din. Komawar shi yafi mishi, ko bakomai zai samu abin yi banda zama cikin dakin su yana duba hanya kamar zai ga shigowar Bilal kowanne lokaci. "Zai ragemun tunani, idan na koma din" Kai ta jinjina mishi, wani irin yanayi take ji a zuciyarta da ba zai misaltu ba "Kayi wa Abbun ka sallama?" A hankali ya girgiza mata kai, ya shiga dakin Abbun ya samu harya fita. Yana yawan shiga yanzun, saboda yana rage mishi zafin da yake ji a zuciyar shi, ba wai suna hira bane ba. Yanzun ya san rashin son surutu halin shine, kawai yanajin dadin yanda yake iya zama waje daya da Abbu din batare da yaji iskar dakin tayi mishi kadan ba. Idan labarai Abbu yake kallo zasu kalla tare, har sai ya gaji da zaman sannan yake tashi yayiwa Abbu sallama ya koma nasu dakin. Jiyama a dakin Abbu suka ci abincin dare tare, abinda bai tabayi ba a iya yanda zai iya tunawa. Yaji dadin abin saboda shine abu na farko da ya saka a cikin shi duk tsayin jiya. Yana daki yana kukan da ya kasa tsayawarwa sai da ya tsaya da kan shi. Ya fadama Abbu cewa yau zai tafi, amman basuyi sallama ba yau din "Ya tafi sanda na shiga. Zan kira shi a waya..." Ya furta a hankali yana juyawa "Allah ya tsare ya bada sa'a. Ka kula da kanka" Hannun kofar da yake rike da ita ya murza sosai, addu'ar Ayya na nutsar da wani abu cikin kan shi, sai da ya hadiye yawi sannan ya amsa da "Amin thumma amin" Harya bude kofar yana shirin fita ta kira sunan shi, dan juyawa yayi "Idan na kiraka ka daga Rayyan" Kai ya jinjina mata yana ficewa, duk da wani abu a tare da shi na fada mishi ya bata hakuri, da duk lokuttan da ta kira shi yana kallo bai daga ba, ba laifin shi bane ba, a lokacin yanajin magana da ita takura ne, shisa yakan zabi yaki dagawa. Amman abinda yake saka shi kuka yanzun ya kula bashi da wahala. Shisa ya zabi yin shiru, hakurin da zai bata zaiyi shi ta hanyar kiran wayarta kafin ita ta kira shi. Da wannan tunanin ya fice daga dakin, yana nufar dakin Mami da ya dade a tsaye bakin kofa yana tunanin shiga. Wani numfashi yaja mai nauyi yana fitarwa kafin ya shiga dakin da sallama yana cire takalman shi daga bakin kofa ganin Mami zaune a falon, amsawa tayi tana dorawa da "Rayyan..." Bata hadu da shi ba tun ranar rasuwar Bilal, bata ma fita ba saboda dalilai kala-kala, daya daga cikin babban kunya da nauyin Rayyan din kan yanda ta yanke mishi hukunci batare da ta tsaya taji bakin shi ba. Ga shi duniyar duka bata mata dadi a kwanakin, bata da lafiya amman ba zatace ga guri daya da yake mata ciwo ba. A cikin zaman makokin Bilal bata da natsuwar kirki, mutuwar bata daketa ba sai bayan an watse sadakar ukku, saboda zuciyarta bata da natsuwa kar Layla ta gifta cikin danginsu wani ya kula da cikin da take dauke da shi. Nasihar duk da Abbu yayi mata ta kasa natsuwa. Batajin akwai wanda zai taba gane halin da take ciki. Ita kadai tasan abinda take ji. Shisa Layla din ma ta kasa samu ta zauna suyi wata magana. Tana hango yanda ba rayuwar yarinyar bace kawai ta canza harda tata. Da ace tana da mahaifa ko daya da suka rage da taji sauki, zataje wajen su ko kuka tayi su fada mata magana mai sanyi, su karfafa mata gwiwar daukar kaddarar da ta sameta. Amman babu, maraicinta bai taba tsaya mata irin na yanzun ba, saboda Ahmadi na bata dukkan kulawa. Bata da bakin da zata amsa tambayoyin mutane, kunnuwanta da zuciyarta basu da karfin jure ma maganganun su. "Mami" Rayyan ya kira cikin sigar gaisuwa yana karasawa cikin dakin sosai. Kallon mamaki take bin shi da shi, sai take ganin kamar akwai abinda ya canza a tare da shi da bashida alaka da mutuwar Bilal. Kujera ya samu ya zauna yana sauke numfashi a hankali, jin shirun yayi yawa yasa Mami fadin "Abinda ya faru... Kayi hakuri, na yanke maka hukunci da sauri" Murmushi mai ciwo Rayyan yayi "Baya nufin bani da laifi, ina da laifi mai yawa Mami... Kiyi hakuri" Idanuwanta taji sun cika da hawaye, shi baizo dan wani abu ba sai dan Layla. Ba Ayya bace kawai tayi tunani akan cikin da yake jikin Layla, har shi dinma, Bilal bai bar mishi wani abu da zai dinga tunawa da shi ba, ko da hotone yana bukata, suna da hotuna da yawa tare da Bilal, dan shi din baya gajiya da daga camera din wayar shi. Wani lokacin ma yana harar shi haka zai dauke su yana dariya, da zai samu duka wannan hotunan da yaji dadi, ko su zai dinga dubawa, yana bukatar wani abu banda kayan sakawa na Bilal. Cikin da yake jikin Layla ne abu mai girma na Bilal da zai dinga dubawa. A daren jiya bayan rokarwa Bilal gafara da kuma Rahmar Allah harda cikin jikin Layla ya hada. Sosai yake jin son kan da yayi a cikin hakan, saboda yaga Layla, yaga yanda ta koma. Ba karamin kalubale yake hangoma rayuwarta a tare da cikin ba. Amman babu yanda zaiyi, bai isa ya hana zuciyar shi son ganin abinda zata haifo ba. Jinin Bilal ne, yaro ko yarinyar Bilal ce, yana son gani, shine kwai kwara daya na Bilal. Duk da zuciyar shi ta kasa hasko mishi Bilal din da Layla, cikin ya manne a wani waje cikin zuciyar shi, shisa yazo ya bama Mami hakuri, baice ita dole sai taso cikin ba, amman karta tsangwama wa Layla, tana cikin wani hali da alama. "Dan Allah kiyi hakuri Mami, bansan ya kike ji ba. Amman naga Layla... Duka abin ya fara tabata kafin mu ya taba mu, kiyi mata fada, ki zageta idan hakan zaisa ki samu sauki, amman dan Allah kiyi hakuri, ki yafe mata. Ki yafe ma Bilal, nima ki yafe mun... Duka mu din masu laifi ne" Hawayen da take rikewa ne suka zubo mata, tunda take bata taba jin Rayyan yayi magana mai tsayin wadda yayi ba yanzun. Ba kalaman shi bane suka sakata kuka, yanayin yanda yayi maganar ne, sai da ta goge hawayen sannan ta iya amsa shi da "Allah ya yafe mana gabaki daya" Mikewa Rayyan yayi, ganin yanda take ta share hawaye shisa bai iya sake cewa komai ba ya fice daga dakin. Ya so ya ga Layla, amman bai da karfin zuciyar cewa Mami tayi mata magana. Zai kirata a waye idan ya tashi. Yana fita daga dakin mikewa Mami tayi tana share wasu sababbin hawayen da suke zubo mata. Sannan ta iya nufar dakin Layla da ta tura, a zaune ta sameta a kasa, ta dora kanta saman gado, karasawa Mami tayi tana zama gefen gadon, sai da ta zauna, Layla taji gadon ya motsa sannan ta san ta shigo. Nata hawayen da suke zuba ta goge da sauri, muryarta a dishe tace "Mami..." Wani irin kukane ya kwacewa Mami da yasa Layla matsawa tana dora kanta a jikin Mami din, itama kukan takeyi "Dan Allah Mami ki yafe mun, ba zan sake ba. Dan Allah Mami, ban san ina zan saka raina ba, ina jin tsoro Mami...sosai ina jin tsoro" Layla take fadi tana wani irin kuka "Shikenan ko Mami? Babu wanda zai sake ganina da mutunci, kowa zai ce mun yar iska... Wallahi Mami ni ba yar iska bace, ki yarda dani, ban san me ya faru ba, kuskurena daya na dauka, nice naje gidan su Hamma, da banje ba, kuskure daya nayi Mami, amman kowa ba zai jini ba, kowa ba zai mun uzuri ba ko? Kema bakya sona yanzun, na san kin daina sona, Abbu ma haka, na muku laifi, Mami za'a zageku saboda ni..." Hannu Mami ta dora saman kan Layla tana son ta bude baki tace mata tayi shiru, amman ta kasa magana. Tunda abin ya faru ta tattara hankalinta kan yanda mutane zasuyi mata surutu, sam bata duba Layla ba, kaddara ce ta fadama yarinyar, irin kaddarar da take zama darasi akan mutane da yawa. Batayi tunanin halin da Layla take ciki ba, kalar tunanin da takeyi, abinda take ji ita. Duk batayi tunani ba, da gaskiya sosai a zantukan Layla, kuskure daya tayi, amman babu wanda zai mata uzuri, su duka babu wanda zai musu uzuri. Tasan mutane da yawa zasuyi mata kallon uwar da tayi sakaci akan tarbiyar yarinyar ta. Batace ana iyayi a tarbiya ba, amman ana kuskure, ba kuma kullum kuskuren yakan zama sakaci ba. Tsanani na zama mafita a cikin tarbiya, wasu lokuttan kuma tsananin kan zama silar gurbacewar tarbiya, haka sanyi akan tarbiyar ma. Abu daya zata iya cewa ta fahimta a cikin tarin kalubalen da yake zagaye da kula da kuma tarbiyar yara, shine babu abinda yake isa, kullum ka kara idan zaka iya, kayi kokarin karawa koya ne, ka fahimci yaranka, saboda duka kalar tarbiyar su bata zama daya. Akwai banbanci a cikin tarbiyar yaran da suke gabanka ko da suke nakane gabaki daya. Halayen su shine abinda zai banbanta wannan tarbiyar, lokacin da wani yake bukatar tattashi, nasiha da tsantsar kulawa, wani a cikin su, fada harma da duka yake bukata. Kuskure daya a cikin yanayoyin biyu zai iya kwance maka tufka ta bangaren igiyar ka, tsayin igiyar zai sa ka kasa ganin warwarewar tufkar da wuri sai lokaci ya kure maka. Hakan ya faru da ita akan Layla, yanda ta dora tarbiyar sauran yaran itama da shi tayi mata riko, soyayyarta ta rufe mata idanuwa, ta kasa gane cewa tana bukatar riko daban da na sauran. A wasu lokuttan kuma sai ta sakarma Abbu yanke hukuncin, saboda tana tunanin nashi tunanin yafi nata. Amman kaddarar nan ta nuna mata akwai fanni na tarbiya da iyaye maza suke bukatar taimako a kai, ba wai jayayya akan hukuncin su ba, amman yin kokarin fahimtar dasu kuskuren da yake cikin hukuncin ko da rai zai baci abune da yake da matukar muhimmanci. Sai addu'a, ita ce abu daya da take da karfin sauya kaddara, ta fahimci abubuwa da dama, duk da ta fahimce su a kurarren lokaci, hakan baya nufin ba zasuyi mata amfani ba. "Mami dan Allah ki taimaka mun" Layla ta furta cike da bukatar neman dauki, tana sake matsawa jikin Mami, kamar zata koma cikin ta, ta boyewa duk wani tashin hankali da yake cikin kaddarar ta. Sai da Mami ta tabbatar idan tayi magana muryarta ba zatayi rawa ba sannan tace "Ban tsaneki ba Layla, babu wani abu da zakiyi dan tsane ki, duk da na kasa hana zuciyata tsanar abinda kikayi....nima inajin akwai laifina a cikin hakan. Ba zan miki karya ba, a watannin nan da zasu zo, gabaki daya rayuwar mu babu wani abu da zaizo da sauki..." Sai da ta numfasa sannan ta cigaba "Ciki ko karkashin inuwar aure ne ba abu bane mai sauki balle akasin hakan. Rayuwar ki da tamu duka ce tayi sauyi na har abada, Allah Ya san dalilin hakan, shi ya dora mana, zamu karbi kaddarar da hannu biyu mu gode mishi a dukkan yanayi, sai ya taimake mu ya kawo mana saukin da bamuyi zato ba" Sosai Mami taci gaba da tausasa Layla din, tun tana kuka har tayi luf alamar bacci ya dauketa. Kallonta Mami tayi, akwai darasin da ta kasa koya mata, akwai tarbiyar da kaddara ta gyara mata akan Layla, ta hanyar da ta zame musu darasi gabaki daya. Hawayenta ta sake sharewa a karo na babu adadi "Allah Ka san yanda zakayi da mu, Allah Ka kawo mana sauki a cikin lamurran mu. Allah mungode maka a cikin kowanne yanayi" Shine abinda Mami take fadi a zuciyar ta tana maimaita hadi da bin bayan addu'ar da "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Domin samun saukin da yake cikin fadar kalmomin a yayin tashin hankali. * Sai da ya bude gaban motar Bappa ya shiga bayan ya jefa jakar shi bayan motar sannan ya maida hankalin shi kan wayar shi yana kiran lambar Abbu daya dauka a bugun farko yana kiran sunan Rayyan din daya amsa ta hanyar yin sallama yana dorawa da "Abbu ina kwana" Amsawa Abbu yayi, kafin Rayyan yace "Na shiga dakin ka naga ka fita. Daman zan kara maka sallama ne, gamu zamu kama hanya ni da Bappa" Ta dayan bangaren Abbu ya amsa "Ma shaa Allah. Allah ya tsare muku hanya ya taimaka. Ayita hakuri kaji Rayyan, addu'ar ka wa Bilal tafi tunanin shi yawa" Muryar Rayyan can kasan makoshi ta fito "In shaa Allah. Nagode Abbu" Ya furta kafin sukayi sallama. Bappa da yake tukin shi a hankali ya juya ya kalla "Kasan wani da yake aiki a First Bank?" Rayyan ya tambaya, cike da mamaki Bappa ya dan kalli Rayyan kafin ya mayar da hankalin shi kan titi "Akwai kanwata Habiba, acan take aiki" Dan numfashi Rayyan ya sauke, tunanin yau kwana biyu yake mishi yawo akai, amman tsoron furtawa yakeyi. Sosai zuciyar shi take bugawa "Zata iya duba mun bank statement din account haka, sai ta tura maka ka bani?" Sai da Bappa ya sha round sannan ya amsa Rayyan din "Ban san ya tsarin su yake ba, mu tsaya bank din mana ka duba... Kana da account da First Bank ne? Na dauka UBA kake amfani da shi" Girgizawa Bappa kai Rayyan yayi, yana rasa ta inda zai fara fada mishi, saboda a cikin kan shi ma maganar batayi kama da ta mai hankali ba. Amman dole ya tabbatar, zaifi samun nutsuwa idan ya tabbatar, ya san menene depression, idan bai tabbatar ba tunani zai iya zautar da shi, yana bukatar ya tabbatar kafin komai ya zauna mishi harya samu ya koma dai-dai. "Kar kai mun wa'azi Bappa, kar kai mun wa'azi ina so in tabbatar da wani abune, ina bukatar in tabbatar da wani abu" Murmushi Bappa yayi "Banyi alkawarin ba zan maka wa'azi ba" Dafe fuskar shi Rayyan yayi da hannuwan shi biyu, kafin ya furzar da numfashi yana bude su "Account din Bilal ne" Yayi maganar cikin karamar murya "Rayyan..." Bappa ya fara, amman kai Rayyan ya girgiza mishi "Dan Allah Bappa, kar kace mun komai tukunna, idan akwai yiwuwar ta duba mun, ka taimaka mun, ina so in tabbatar, tunanin banga gawar shi ba yana mun wahala, mutuwar Bilal ta kasa zauna mun inda ya kamata ta zauna, kafin ka fara na kalli abin ta fuskar likitanci, ina so in tabbatar" Numfashi Bappa ya sauke yana dan rage gudun motar kafin ya kalli Rayyan yana sake mayar da hankalin shi kan titi "Zan kirata, yanzun zan kirata, amman zan fada maka gaskiya ko baka son ji. Ba lallai sai kaga gawar Bilal bane zai zamana ya rasu, akwai dubban mutanen da labarin mutuwar su baizo ma ahalin su ba, amman sun musu zaman makoki... Ka saka kanka a matsayin su, kuma sun hakura, hakurin nan ba zabi bane ba Rayyan, dole ne, na san me kake ji, naga gawar Mama da ta kowa, amman kullum na shiga dakinta sai naga kamar zan ganta..." Gyaran muryar Bappa yayi kafin yaci gaba da fadin "Zan maka karya idan nace har yanzun babu wani bangare na zuciyata da bayason tashi da safe yaga komai ya kasance mafarki. Ka yarda dani zaka hakura a hankali, ciwon ba zai taba bari ba, amman zaiyi sauki, zaka koyi zama da shi yau da gobe... Idan duba bank statement din Bilal zai baka yardar da kake nema shikenan" Tunda ya fara maganar shiru Rayyan yayi yana jin shi, kuma zantukan na zauna mishi, dan sun tokare mishi makoshi har wani daci-daci yake ji a cikin shi, yana ganin Bappa ya sauka daga gefen hanya a hankali yayi parking, sannan ya dauki wayar shi da take ajiye akan cinyar shi yana danne-danne. Sai da ta fara ringing sannan Rayyan yasan kira ne Bappa yayi, kuma ya saka ta a speaker. Har ta kusan yankewa sannan aka daga da sallamar da Bappa ya amsa "Ya Bappa, ina dan aikine haka..." Kai Bappa ya jinjina "Habiba ko zaki dan taimakawa abokina ki duba mishi bank statement din shi, ya yarda wayar shine haka, to sim din da yake ganin alert yana ciki, kafin yaje yayi swapping idan babu matsala, da zamu shigo bankin tare da shi, amman bamu samu dama ba, muna hanyar Kaduna" Ta dayan bangaren Habiba ta amsa da "Na dauka sai da yamma zaka wuce ai... Ya fadi account number din na shi da email sai in tura mishi" Kai Rayyan yake girgizawa Bappa, bayason yin magana kar taci, amman so yake yace a tura ana Bappa "Wayar ce bai siya ba tukunna, idan babu damuwa ki tura a nawa, barin miki text din account number din da email din" Wani irin numfashi mai nauyi Rayyan ya sauke jin tace babu matsala. Wayar Bappa ya mika mishi bayan sun gama. Da kan shi ya rubuta account number din Bilal da kuma sunan shi cikakke. Sannan ya mikama Bappa wayar ya saka email din shi yana turama Habiba, ya sake mikawa Rayyan din wayar, ya tayar da motar suna hawa titi sosai. Bappa najin da shi kadai ne zai saka karatu ko waka yanaji, amman shi din mutum ne da yasan hakkin mutane, zai iya tambayar Rayyan din ko zai iya kunnawa, amman yaga baya cikin hankalin shi, saiya hakura. Shisa yake mamakin mutanen da zasu kasance daki daya da wani, ko a makaranta sai su kunna kida ko karatun Qur'ani ganin duk dakin musulmine batare da tunanin ko wani a ciki baya jin yanayin sauraren wani abu ba. Shisa idan bashi kadai bane yakan zabi yayi amfani da earpiece, to yanzun wayar da zai saka a jiki tana wajen Rayyan da ya tattara hankalin shi kacokan ya mayar kan wayar, lokaci zuwa lokaci yakan dangwala yaga ko sako ya shigo shine bai gani ba. Har suka fita daga cikin garin Kano bai daina dubawa ba, ko da suka shiga inda babu network ma haka, har ya dawo sannan yaga sako ya shigo. Jikin shi har kyarma yakeyi, da yake yasan lambobin sirrin bude wayar Bappa din, da hanzari ya danna yana budewa, kai tsaye email din ya bude yana dudduba kwanan watan da kudi suka fita, zuciyar shi na wani irin bugawa kamar zata fito ta hau titin da suke tafiya a kai ganin ko jiya an cire dubu daya a account din Bilal din, sai da ya hada kan shi da gaban motar yana wani irin maida numfashi, dariya ce ta kwace mishi a lokaci daya kuma wasu hawaye masu zafi na digowa suka sauka jikin motar, dan ya gansu, kokarin mayar da su yakeyi, jikin shi babu inda baya kyarma. Yanda zuciyar shi take bugawa ne yasa shi kasa cigaba da duba wayar sai da yaji ta dan nutsu tukunna, a kwanakin bakwai an cire kudi sau hudu, dago kan shi yayi yana kallon Bappa "An cire kudi, Bilal ya cire kudi Bappa.... Bilal ya cire kudi" Rayyan yake fadi zuciyar shi na cigaba da dokawa. Bappa bai ce mishi komai ba, baiyi magana ba, haka har suka isa garin Kaduna Rayyan na duba wayar kamar yana tsammamin Bilal zai iya fitowa daga cikinta, lokaci zuwa lokaci yakan juya yace ma Bappa "Bilal ya cire kudi" Ko kuma "Kasan shine yake cire kudi haka kadan-kadan har fada muke saboda ina ganin wahalar da yakeyi, sai yace mun idan ya ciro da yawa zai dinga siyan abubuwan rashin dalili" Haka yaita surutai, Bappa bai dai tanka mishi ba har sai da suka shiga cikin gidan su suka zauna sannan yace "Rayyan" Kallon shi Rayyan yayi, yanayin da yake ji babu wani abu da zai misalta shi, a jikin shi ya dinga jin yanda Bilal bai bar shi ba, daman yasan Bilal ba zai barshi haka ba. "Zai iya yiwuwa an tsinci ATM dinne, ka bude zuciyar ka da yiwuwar hakan" Kai kawai Rayyan ya jinjina ma Bappa yana mika mishi wayar shi ya mike. Ban daki ya shiga da nufin watsa ruwa. Yaga kudin da ya rage account din Bilal din dubu takwas ne, shikam akwai kudi da yawa a account din shi, ga na bautar kasa da aka basu, ga wanda Abbu bai daina tura mishi ba, sannan inda suke bautar kasar ma suna biyan su albashi me kyau. Da murmushi a fuskar shi yayi amfani da wayar shi da ya shiga bandaki da ita yana turama Bilal din kudi ta bankin shi. "Na san ba zaka barni ba Bilal" Ya furta yana shafa screen din yar karamar wayar ta shi, yana jin kamar Bilal din yana tare da shi, ba zai sake zancen nan da Bappa ba, ba zaiyi zancen da kowa ba kuma. Saboda ba zasu yarda ba, zai bar abin a ran shi, shi kadai har sai Bilal din ya dawo sun gan shi. Lumshe idanuwan shi Rayyan yayi "Kar tafiyar taka tayi tsayi, ka waiwaye mu da ka samu nutsuwar da kake bukata" Ya furta a zuciyar shi, kafin ya bude idanuwan shi, da tunani kala-kala a cikin kan shi, hannun shi yakai kirjin shi yanajin kamar an fifita mishi ciwukan da suke ciki, saboda komai yayi wani irin shiru, ciwon da yake ji kamar anyi ruwan shi an dauke. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:09 PM - 111: Jan 12, 2020. 30 Dan ware idanuwa Bappa yayi, yana sake kallon farantin da yake gaban Rayyan a ajiye "Meye wannan Rayyan?" Ya bukata, Rayyan din na dan juya idanuwan shi, yasan sarai Bappa ya gane plantain ce, tunda suka kwaso ta da dankalin turawa, sau biyu yaga Bappa ya soya. Abin a ido kamar ba zai wahala ba, sai da yazo tun daga yankawar ya gane aikin ba karami bane ba, da yake man yayi zafi sosai sanda ya zuba kafin ya juya wata, wata ta kusan konewa, gabaki daya sunyi baki, har cikin makoshin shi yana jin daci-dacin da sukayi. Sai dai yunwa yake ji da yake ranar ta zo musu a karshen mako, Bappa din kuma ya fita, yana jin kwiyar zuwa ya siyo wani abu. "Da me yayi maka kama?" Rayyan ya amsa tambayar Bappa din da wata tambayar, yana sake saka cokali mai yatsu ya caki guda biyu ya saka a bakin shi yana taunawa kamar babu dacin da Bappa yasan zatayi, dariya Bappa yayi "Ka tashi mu fita, nima ba abinda naci" Kafada Rayyan ya makale, bayajin zuwa ko ina "Me yasa bakayo mana take away ba? Dole sai ka dawo ka fitar da ni" Tunanin ne bai zo ma Bappa ba sam, saboda yasan halin Rayyan din, bakomai na waje yake ci ba, idan suka fita tare saiya zaba da kan shi, ba'a cika yi mishi gwaninta ba. "Ka tashi dan Allah, ba kana maganar waya ba? Sai mu biya ka duba" Dan jim Rayyan din yayi, da gaske yana son siyan babbar waya. Saboda yanzun sukanyi kwanaki har biyu ko fiye da hakan ma tunda ya dawo basuyi waya da Layla ba. Sukan yi musayar text dai, ta cikin su yakan fahimci kamar yanzun tana rasa abinda zatace mishi, idan suka gaisa sai ya jima yana kallon wayar yana jiran yaga amsarta, sai yake tsintar kan shi da tunanin ko tana lafiya ko akasin hakan. Idan ya kira ma wasu lokuttan bata dagawa, ba ko yaushe take biyo kiran ba sai dai idan ya sake gajiya ya kara kiranta. Yasan zai iya zuwa gida idan yana so, Bappa da wahala yayi kwana biyar bai shiga Kano ba, yawon shi har mamaki yake bama Rayyan din, gidane bayason zuwa, tunanin ya shiga dakinsu babu Bilal yana mishi wani iri. Duk da akwai damuwar da ta daga a kirjin shi baya nufin baya kewar Bilal din, ba kuma ya nufin tafiyar da Bilal yayi bata mishi ciwo, yana dannewa ne "Zaiyi sauki, In shaa Allah komai zaiyi sauki" Bappa kan yawaita fada mishi haka kawai idan yaga yayi shiru yana kallon bango. Baya amsawa, baya tunanin Bappa nayin maganar ne dan yana jiran ya amsa mishi. Kawai yanayine saboda yasa shi yaji kamar wani ya damu, kamar yana kula da yanayin shi. Kuma yanaji din, har cikin zuciyar shi yanajin kulawar Bappa da baiyi tunanin wani bayan Bilal da Layla zasu gwada mishi ita ba. Su Ayya iyayene, bayajin akwai zabi a tasu kulawar, kamar da haihuwar shi da yanda kula da shi ya zame musu tilas ko da basa son hakan, ko da ta takaitaccen lokaci ce. Watakila Bilal na kula da shi saboda su din yan uwane, Layla kuma dan tana son shi. Kusan suma zaice basu da zabi, amman Bappa na da zabi, sai ya zabi kula da shi, ya zabi yi mishi karamci duk da shi din bashida wani abu da zai iya mayarwa Bappa da shi "Zama da kai ba abu bane mai sauki Hamma" Bilal ya taba fada mishi da sukayi wani rikici, kuma yasan gaskiya ya fada. Amman Bappa na zaune da shi kamar hakan abune mai sauki. Bappa ya bashi abinda bai taba tunanin zai samu ba a rayuwar shi, ya bashi abota. Satin su biyu da dawowa Kaduna aka koma makaranta, da yake akwai kanin Bappa a ABU din shisa ma Rayyan yasan an koma. Rana daya ya tambaya a wajen da suke serving aka kuma bashi, da yacewa Bappa zaije Zaria da mamaki ya kalle shi "Me yasa yau? Ka bari sai weekend mana mu shiga tare" Kai Rayyan ya girgiza mishi "Akwai abinda zanyi yau din shisa" Yana jin dadin da bakomai Bappa yake tsaurara tambaya a kai ba. Fatan alkhairi kawai yayi mishi dana Allah ya tsare hanya. Dan da yace ya kai shi tasha yace zai hau mashin. Abinda duk yake bukata yana cikin yar jakar shi daya goya a baya yana ficewa daga gidan zuwa ta sha. Saura mutum biyu motar ta cika sanda ya shiga, aikam yana zama ana kara samun wani, sosai yaga saurin saukar su, ko dan tunanin da yakeyi ne. Kan shi tsaye makaranta ya wuce, abinda bai taba tunanin zaiyi ba shi yayi, har Office din wasu cikin Malaman shi dan ya tambayi abinda yake bukata din. Sun kuma karbeshi a mutunce haka amsar duk tarin tambayoyin da yayi. Kananun kayane a jikin shi, rigar mai dogon hannu, shigar da baka raba Bilal da ita. Bai taba tsintar kan shi a yanayin da yake ji ba yau, musamman da ya kasa tuna wanne kalar passport ne Bilal ya manna a jikin takardun su, ko kamannin su sun fito ko basu fito ba. Sauran semester daya Bilal ya kammala karatun shi, yana ji a jikin shi zai dawo, yana kuma fata da addu'ar dawowar ta zamana a kusa, ya iya kalar signature din Bilal, dan ya ko shi Bilal yakan yi mamaki "Dan dai kana zane ne, shisa bai maka wahala ba" Cewar Bilal wani lokaci can baya, bai sha wahalar tsayar ma da Bilal karatun ba, yayi amfani da uzurin rashin lafiya ne. Kusan rabin rana yana abu daya, dan akwai kudin da ake biya kafin a iya. Wajen uku saura ya samu ya kammala komai, saiya tsinci kan shi da samun wata natsuwa da baisan daga inda ta fito ba. Baisan kafafuwan shi na daukar shi zuwa gidan su ba sai da ya gan shi a kofar gida, akwai mukullin daki a jakar shi, dan haka bai sha wata wahala ba daya shiga, ya daiyi mamakin yanda jikin shi ya dinga bari wajen budewa. Yaji dadi sosai da bai samu kowa daya sani ba harya shiga. Dakin zaka rantse anyi watanni ba'a shiga ba saboda kurar da yayi. Sai yaji zuciyar shi ta matse a kirjin shi, tsaye yayi a tsakar dakin yana ganin rayuwar da sukayi a cikin shi kamar an kunna film, yana ganin Bilal a ko ina na cikin daki, yana jin shi a ko ina na zuciyar shi da take wani irin ciwo da baiyi tsammani ba. Ba zaice ga lokacin daya dauka a tsaye a wajen ba, wayar shi da ta fara ihu a aljihun shi ce ta katse mishi tunanin da yayi zurfi a ciki, ko dubawa baiyi ba bayan ya dauka ya daga kiran, karawa yayi a kunnen shi "Hello..." Ya fadi muryar shi na fitowa daga can kasan makoshi "Rayyan" Yaji muryar Haris cikin kunnen shi da ta saka shi yin gyaran murya saboda yanayin da yake ji "Hamma" Ya iya fada, muryar shi na fitowa a shake "Kana ina? Me ya faru?" Haris ya tambaya cike da kulawa, yanzun da ya dawo kamar kowa yake jin yanda bai cancanci tarin kaunar da yan uwan shi sukeyi mishi ba, saboda sam bai tuna wani lokaci daya nuna musu ko da kadan a cikin kalar kaunar da sukeyi mishi ba. Amman yana tuna yanda duk ture sun da yayi bai hana su kokarin kusantar shi ba. Kaunar su daban take, kaunar su na da alaka da jinin shi da yake yawo a nasu. "Rayyan kayi mun magana dan Allah" Numfashi ya sauke "Zaria, ina Zaria Hamma" Haris ya dan jima kafin yace "Zan kwashe kayan, munyi maganar da Ayya, ka bar shi karshen makon nan da yardar Allah zan shigo Zaria din" Numfashin Rayyan ya sake saukewa "Kar ka bayar da komai, duka komai da komai" Duk da baya gani yasan kai Haris din yake daga mishi "Babu abinda zan bayar, duka zaka zo gida ka samu kayan. Ka dai fito daga gidan idan kana can, kana jina, ka fito ka tafi...zaka iya ai ko?" Dan murmushi ya kwacewa Rayyan "Ba yaro bane ni Hamma..." Yanajin dariyar Haris din, bai jira yace wani abu ba ya sauke wayar daga kunnen shi yana katse kiran kafin ya mayar da ita aljihun shi. Da gaske kirjin shi zafi yakeyi, kasancewa a cikin dakin ya dawo mishi da abubuwan daya dauka ya rabu da su. Kasancewar shi a dakin ta saka mishi wasi-wasin da bayason zurfafa tunanin shi a kai sam. Shisa ya dauki shawarar Haris din ya fice daga dakin ya mayar da shi ya kulle yana fita daga gidan. Ko daya karasa ya shiga motar da ta mayar da shi Kaduna bai daina jin kirjin shi na zafi ba. "Magana fa nake tayi maka" Muryar Bappa ta daki kunnen shi tana dawo da shi daga tunanin daya zurfafa ciki. Mikewa yayi yana fadin "Dole dai saika fitar da ni..." Bappa bai kula shi ba ya juya, shima bayan Bappa yabi har suka fita daga gidan zuwa inda motar Bappan take suna shiga. * Ba zatace duka duniyar ta daina yi mata dadi ba, saboda yanzun duniyarta ta tattaru ta dawo cikin dakinta. Anan take gudanar da rayuwarta ta yau da kullum, ko da safe ba kullum take samun karfin zuwa su gaisa da Mami din ba. Sai dai ita ta shigo ta dubata, saboda cikinta daya fara fitowa sosai, bata son Mami na ganinta, kowa ma na gidan bataso yana ganin ta. Sai taga kamar basa ganin komai a tare da ita, kamar hatta da sunanta ya bace, banda cikinta babu wani abu da kowa yake gani a tattare da ita yanzun. Jafar ne kadai yakan fito da ita falo wasu lokuttan. "Malama fito kiga wani abu" Yakan ce, duk iya kokarin shi na ganin bai nuna cikin jikinta ya dame shi ba, a muryar shi takan ji canjin da ya faru da rayuwar su gabaki daya. Ta kan biye Jafar din suyi kallo tare har su danyi hirar film din, amman gabaki daya babu wani abu da take jin dadin shi. Ba dai ta iya cin wani abu sai mai manja, in dai ba girkinta ita kadai Mami takeyi mata ba to duka dakin su an koma cin abinci ne da manja. Shima kawai wasu lokuttan takan ji idan bataci ba kamar zata mutu, sai kuma yoghurt da baya yanke musu a cikin fridge. Lokutta kamar irin yau da take zaune dafe da cikinta, hawaye ne masu ciwo suke zubar mata, tun tana daukar zasu kare har ta daina yanzun. Takan yi kukan halin da take ciki, takan kuma yi kukan rashin Bilal ba kadan ba, a hankali a hankali mutuwar ta dinga tabata kamar ciwonta ba zaiyi mata sauki ba. Anisa kuwa yanzun ba sosai suke magana ba, tunda Layla ta fada mata anwa Abbu transfer ne zuwa kudu, shine suka koma gabaki dayan su, sukan gaisa lokaci zuwa lokaci ne. Zuwa yanzun makaranta ce karshen abinda yake ranta, ta rigada ta cire karatun daga zuciyarta. Rayyan na kokarin kiranta, shima batasan me zatace mishi ba a yanzun. Ko wanka ta shiga bata tsayawa kallon kanta, saboda bata son ganin yanda gabaki daya jikinta ya canza. Jiya ma sai taga kamar har fuskarta ta canza, bata san ko dan ta jima bata kallo mudubi bane ba. Yau ma sam batayi marmarin kallo ba, da ta sau wata doguwar riga ta zira a jikinta sai ta koma kan gadonta. Idan har bata son ganin kanta, tana da yakinin Rayyan ma ba zaiso ganinta ba, ita da kanta ba zataso yaga canjin da yake tare da ita ba. Zatayi karya idan tace zuciyarta bata mata zafi, amman a cikin abubuwan da ta nisanta zuciyarta da su, samun Rayyan na daya daga cikin su. Ba abu bane mai sauki, amman da duk ranar da zata wayi gari da yanda take kokarin yin wani tunani na daban, tana hasaso dirowar abin da yake cikinta. Tana kuma tunanin yanda rayuwa zata kasance mata bayan hakan, duk ta yanda ta hasaso abin ba mai sauki bane, tsoro da zullumi sun bata taimako wajen danne Rayyan can kasan zuciyarta. Alamun shigowar sako take ta ji, hawayenta ta share tana sauke ajiyar zuciya, kafin ta dauki wayar tana budewa ta duba. Sai da taji zuciyarta tayo wani tsalle kamar zata baro kirjinta, mamaki na dirar mata ganin Rayyan ne yayi mata magana a manhajar whatsapp "Layla" Sakon shi na farko kenan "Na siya waya" Ta sake karantawa "Bakya magana dani kwana biyu ko?" Murmushi tayi me ciwo, ta fara rubutu yafi a kirga tana gogewa cikin rashin sanin abinda ya kamata tace, kafin ta yanke hukuncin fadin gaskiya, abubuwan da suka rage mata basu da yawa, ba zata bari gaskiyarta ta kwace mata ba, musamman ma a wajen shi "Komai ne baya mun dadi Hamma, duniyar duka ta tsaya mun waje daya" Kallon shi tayi yanata rubutu "Zai wuce wata rana, ki daure" Kai ta jinjina kawai, har zata ajiye wayar saboda bata san me zatace mishi ba ya sake fadin "Ki turomun duka hotunan mu" Bata san me yasa taji cewa harda na Bilal yake nufi ba, duk da bai ambaci suna ba. Jikinta har bari yakeyi lokacin da ta shiga gallery din, tana binciko hotunan da ta kasa dubawa duk yanda taso yin hakan. Idanuwanta cike taf da hawayen da batayi kokarin hanasu zubowa ba ta fara tura mishi duk wani hoto na Bilal da taci karo da shi, kafin ta tura mishi nashi da take da shi, sai na shi shida Bilal wanda idan Bilal ya saka takan ce ya tura mata. Kuka takeyi sosai lokacin da ta gama tura mishi dan harda hotunan Aisha da Bilal din da yawan gaske a wayarta. Hotunan da suka sakata tunanin Aisha da halin da take ciki a yanzun. Bataji shigowar Mami da ta juya a hankali ba, dan Abbu yace ta dinga barin Layla tanayin kukan, dan akwai sauki a cikin shi. Yana nufin tana fito da abinda yake damunta bata barshi a cikinta ba. Amman da wahala, batasan ba cikin Layla bane kawai jarabawa harda damuwar da take gani shimfide a fuskarta a duk rana. Shi kadai yakan jijjiga zuciyarta. Amman ta bar komai a hannun Allah, shi daya kadarta musu ya san yanda zaiyi dasu. Sharar da take kitchen ta dauka dan ta fita da ita can harabar gidan ta zuba a babban wajen da suke zubawa sai a fita da ita duk sati. Ta dawo ne taci karo da Ayya, zasu iya haduwa irin wannan fiye da goma basu cewa juna komai ba, shisa abin yayi mata wani iri yau da taji tace "Maryama" Mamakine bayyane a fuskar Mami sanda ta juya, saboda yanayin da taji a muryar Ayya bana tashin hankali bane ba "Ya Layla?" Ayya ta tambaya tana kallon Mami din, ba abinda taso fadi bane ba, a kwanakin nan da suka wuce mata da wani irin yanayi, baccin kirki bata samu. Saboda tana tunanin makomarta, tana kuma tunanin abinda zata cewa Allah idan mutuwa ta risketa da hakkin mutane da yawa a kanta. Idan ana maganar lahira bata tunanin wani girman kai na da amfani, ta sha fitowa da nufin samun Mami har cikin daki ta roki gafararta amman sai ta tsinci kanta da kasawa. Yau dinma na zatace ga abinda ya fito da ita ba, kuma sai ta hadu da Mami din, ta dauki hakan a matsayin wata ishara ta samun sauki, ba saita taka kafarata zuwa dakinta ba. "Tana lafiya. Alhamdulillah" Mami ta fadi tana shirin raba Ayya ta wuce "Maryama..." Ayya ta sake kira tana saka Mami tsayawa a karo na biyu "Ban san ta ina zan fara ba" Cewar Ayya da muryarta take rawa "Cutar da nayi miki wanda kika sani da wanda baki sani ba..." Kafin ta karasa Mami ta katseta da fadin "Dan Allah Maimuna... Idan kin taba cutar dani ko kokarin hakan Allah ya zama shaida yau na yafe miki. A zaman mu ba zance ko a tunani ban soki da abinki ba, ki yafe mun nima" Numfashi mai nauyin gaske Ayya ta sauke tana jin kamar an dauke mata dutse a kirjinta "Nagode... Ba zan miki karya ba, hakan baya nufin ba zan neme ki da rigima ko ba zanyi tashin hankali ba" Murmushi Mami tayi, murmushin da ta kwana biyu batayi kalar shi ba. Batace komai ba ta raba Ayya ta wuce, in dai wannan ne ta saba da shi, mai hali baya barin halin shi akace. Kishi da rigima halayen Ayya ne, batajin kuma wani abu zai taba canza hakan, bata tsammaci maganar da sukayi yanzun ta saka su zauna kamar aminan juna ba, ko su fara hira da mutuncin da basayi a da. Idan akwai abinda ya fara sakawa take ganin girman Ayya shine matar bata iya munafunci ba, abinda yake ranta ne zata nuna maka, idan kaji haushi ma bai dame ka ba. Ko da wasa bata taba nuna tana sonta ba tun shigowarta, tana kula da yanda taso ta ture har yaranta, sai Haris yayi nasara a kanta, duk da batajin tana son sauran kamar Haris. Da zama da munafiki da zai nuna yana sonka a gabanka a bayanka ba haka ba, gara ka zauna da wanda zai kalli fuskarka ya fada maka baya yinka, hakan ba zaisa ka daga burinka a zaman ku ba. Rigimar Ayya ta jima da sabawa da ita, kamar yanzun yanda take jin wata rana zata zo da zasu saba da wannan yanayin da suke ciki, ranar da komai zaiyi musu sauki. Ayya ma dakinta ta wuce tana jin wani sauki ya saukar mata, tana jin yanda ta rage kadan daga cikin hakkin mutanen da take ji ya shake mata wuya. * Sosai yaji dadin yanda duk watannin daya dauka ko Ayya bata ce mishi yaushe zaije gida ba. Suna waya kullum, yana kiranta sau hudu har fiye da haka a rana, ba hira sukeyi ba, dan yakan ce "Zan sake duba kine daman" Kamar yanda yakan ji Bilal yace mata wasu lokuttan, so yake ya rage mata kewar Bilal da yasan tanayi a lokaci daya kuma bayason ya fama mata ciwon da baisan koya fara warke mata ba. Tun biyan farko da akayi musu Bappa yace mishi anayin wani adashi, yayi bayanin amman badan Rayyan ya gane ba, shi din bamai yawan siye-siye bane ba, badan abinda yake turawa account din Bilal ba, kusan fiye da rabin kudin haka suke zama account din shi. Ko lokacin da suke makaranta sai kudin Bilal ya kare na shi akwai dan saura "Duk yanda kake ciro dubu dai-dai ga kudin nan ya kare" Ya kan fada idan yaji Bilal na maganar kudin shi sun kare shi "Koyon ajiye kudi yana da amfani, ko badan ka siya wani abu ba, tsaron lalura ne. Idan baka saba ware wasu ka ajiye ba tun kana kai kadai, zai maka wahala idan ka fara tara iyali" Bappa ya fada mishi, ya sha dauka yana abubuwan shi a tsare sai yanzun daya hadu da Bappa, sosai yana koyon abubuwa a wajen shi, watakila mu'amala da mutane bashi da aibun da yake tunani. Tunda yanayin Bappa din yanzun yana koyar da shi abubuwa da dama "Ace shekaru kusan talatin amman kaga mutum baya tunanin abinda zaiyi da rayuwar shi, kudin duk da zasu shigo mishi ko bashi da abin siya saiya kirkira" Lokutta da dama zantukan Bappa kan saka shi yayi murmushi, idan kaga yanda yake magana ko tsare-tsare sai kayi tunanin yanada yara fiye da goma da suke karkashin kulawar shi. Amman Bappa ya saka shi tunanin da gaske yana bukatar adana kudade, musamman da haka kawai Bappa din yace mishi "Idan na koma karatu inajin idan ba nawa auren ba nakane zai dawo dani kasar nan" Yana tuna mishi da cewa zai koma, duk da yanajin kamar babu nisan da zai yanke zumuncin da yake tsakanin su. A lokaci daya yana saka shi tunani akan abubuwa da yawa, tunani akan shi da Layla, baisan me take so ba a yanzun, amman shi ya kwana biyu da sanin abinda yake so. Da tunanin yake kwana yana tashi a satin, shisa ya yanke hukunci bin Bappa yau su tafi Kano tare, duk da baice komai ba yaga jin dadin hakan, tunda ya dade yana fama da shi da ko na rana daya ya bishi suje sai su dawo yana ki. Ko bakomai ma yana son ganin Layla, kewarta yake ji har a kasusuwan jikin shi. Yaji dadin yanda Bappa ya sai da ya shiga ya gaishe da Ayya sannan ya wuce da nufin zai dawo da dare su fita da Rayyan din. Ayya ma taji dadin ganin shi, sai da yaje dakin su ya rage kayan jikin shi ya share dakin tas sannan ya shiga yayi wanka ya sake wasu kayan yana dawowa dakin Ayya. Anan ya zauna yaci abincin da ta zubo mishi, sai da ya gama ya dauke kwanonin ya kai kitchen sannan ya dawo ya zauna. Har yanzun bai saba magana da ita har haka ba. Tauna abinda zai fada yakeyi, dagowa yayi yana kallon fuskarta "Ayya ina so muyi magana ne daman" Bata san me yake so ya fada ba, ta dai bashi dukkan hakalinta tun kafin yayi maganar "Ina sauraren ka Rayyan" Gyara zaman shi yayi "Zan auri Layla, idan ta haihu zan aureta. Ina tara kudi Ayya, ban san ko zasu isa ba saboda gasu kama gida da su kayan lefe" Bata san ya taji maganar ba, tunani dayane yake mata yawo kawai "Babu wanda ya isa ya canza kaddara" Ta kuma gani yanzun, duka kudadenta da ya kamata ace tayi wani abu muhimmi da shi ta kwashe ta baiwa Hajiya Dije da sunan a raba Layla da Rayyan, a raba harda Bilal da take gani a kusa da ita. Ga shi yanzun kaddarar da take zagaye da su ta hada su ukkun duka a gaban idanuwanta kuma da yake bata da iko a kai ba abinda zatayi "Ayya..." Rayyan ya kira saboda baisan me shirunta yake nufi ba, ya fara fada mata ne saboda yasan bata son Layla a kusa da shi, bata kuma son Mami, gara taji daga wajen shi. Rayuwar shi duka yayi ta ne cikin rashin daukar duk wani abu da zatace da muhimmanci, shisa yanzun zai fara, ya rigada ya yanke hukunci auren Layla, amman baya nufin zaiyi shi bada yardarta ba. "Kiyi mun magana Ayya, ni din ban saba jin maganar ki ba, ina so in aureta, idan hakan na nufin in jira sai kin amince zan jira in dai bata da matsala da hakan itama, amman kice wani abu dan Allah" Haka kawai taji zantukan shi sun karya mata zuciya. Kai ta jinjina kawai, muryarta na rawa tace "Allah ya tabbatar mana da alkhairi ya kaimu lokacin" Numfashin da baisan yana rike da shi ba ya saki. Ya dan kara jimawa batare da sun cewa juna komai ba sannan ya mike ya fice, sai da yayo sallar azahar ya dawo sannan ya shiga bangaren Mami, itama suna gaisawa kan shi a kasa yace "Layla fa? Ina so inyi magana da ita Mami" Dan jim Mami tayi kafin ta mike, dakin Layla ta nufa tana Kwankwasawa kafin ta tura, tana zaune a kasa da alamar sallah tayi itama, dan ko hijabi bata cire ba "Ga Rayyan a falo yana so yayi magana dake" Mami ta fadi tana juyawa batare da ta jira amsar Layla din ba, dakinta ta koma. Zuciyar Layla har cikin tafukan hannayenta take jin su. Ta ga kiran shi amman bata daga ba, saboda yace mata zaizo bata bashi amsa ba, tunda safe da taga sakon shi take kuka. Yanzun ma idanuwan ta taji cike taf da hawaye, watakila idan yaga bata fita ba ya hakura ya kyaleta, batajin zata iya bari ya ganta a yanda take din nan. Cikinta ya fito sosai tunda ya shiga cikin wata na biyar, har awo na farko tayi, yanzun takan ji motsin abinda yake ciki, har bacci yakan tasheta idan yayi wannan kwakkwaran motsin. Text taji a wayarta, ta mika hannu tana daukowa ta duba, Rayyan ne "Ba zakici gaba da shareni ba, ba zan barki kici gaba da shareni ba. Idan baki fito ba zan shigo" Hawayen da suka zubo mata ta share tana dafa gadon ta mike da dakyar. Cikin yasa tana kallon Mami da wata daraja ta daban yanzun. Ko juyi zatayi a bacci saita tashi zaune idanuwanta tar sannan take juya, ga wani irin ciwon jiki da take fama da shi naban mamaki. A kasan zuciyarta haka kawai take jin kamar kafarta daya a duniya take daya kuma a wani waje da bata da sunan da zata bashi har yanzun. Tana tallafe da cikinta ta fito daga dakinta, bata ga fuskar Rayyan ba, bayan kan shi kawai tagani, amman ya isa ya karyata mata duk wani tunani da tayi na binne mafarkin samun shi. Saboda wata irin soyayyar shi ce ta taso mata tana saka har abinda yake cikinta yayi wani irin motsi daya sakata kiran sunan Allah cikin yanayin da ya saka Rayyan juyawa ya sauke idanuwan shi cikin na Layla da ta bude. Sai taji ta daburce, juyawa take shirin yi ta ruga, wani waje take son kasancewa da baya nan "Layla... Dan Allah... Karki boye mun" Rayyan din ya fadi cike da wani irin tsoro a muryar shi da yayi mata tasiri. Ganin ta tsaya tana juyowa yasa shi mikewa ya zagaya zuwa inda take yana fuskantarta. Jikin shi bari yakeyi daga ciki, hatta da zuciyar shi rawa takeyi mishi. Baice yanayinta bai taba shi ba, bai kuma yi kokarin boye hakan dan karta gani ba. A duk rana tun bayan daya sani da cikin jikinta yake kwana yana tashi. Amman hakan baisa yaji saukin ganinta dauke da shi ba, ganin shi ya fito sosai haka. "Hamma" Layla ta kira da wani yanayi a muryarta, tana saka har dayan hannunta ta kare cikinta kamar tana son boye shi saboda irin kallon da Rayyan din yake mata "Kaima ka daina ganina ko? Ka daina ganina sai cikin da yake jikina" Ta karasa maganar tana jin wani daci a zuciyarta da hawayen da suka zubo mata. Kai Rayyan yake girgiza mata, amman ya kasa hada idanuwa da ita har lokacin, cikin kuka tace "Na sani, kowa baya gani sai cikin nan, kamar ba a jikina yake ba haka nakeji, ina jin kamar tare da cikin ni na bace, shisa kowa baya gani na" Sai lokacin ya iya kallon idanuwanta da suke cike taf da hawaye yana furzar da numfashi ta bakin shi, bayajin akwai wasu kalamai na lallashi da zai fada mata "Ina ganin ki, ina ganin ku duka ba zan miki karya ba. Amman ina ganin ki" Cewar Rayyan yana dorawa da "Na san na fadi abubuwa da yawa. Zan sake fadin wani yanzun. Zan aure ki, ba dan abinda ya faru ba, dan ina son ki, zan aure ki in har yanzun kina jin zaki iya rayuwa da ni" Sai da ta dafa kujerar da take gefenta sannan ta iya tsugunnawa saboda yanda kalaman shi suka daketa. Numfashi take fitarwa wani irin kuka na kwace mata. Tsugunnawa yayi shima, idan zai fada mata sau dari ba zai gaji ba, saboda bayason wannan kadaicin da yake gani a cikin idanuwanta, bayason yanda take jin kamar ita kadai ta rage a duniyarta, kamar babu wanda zai taba fahimtar halin da take ciki, wannan yanayin shi yake kaika fadawa depression, abinda zaiyi komai da yake karkashin ikon shi na ganin bai bari Layla ta dandana wannan duhun ba. "Na fadama Ayya, ta mana fatan alkhairi. Bake kadai bace ba, ba zan fahimta ba nasani. Amman ina tare dake, koma menene ni da ke muna tare" Kamar maganganun shi na kara tunzurata, kuka takeyi sosai, bai hanata ba, bai dai daina gaya mata yana tare da ita ba cikin wata murya da take kara karya mata gabban jikinta. Ba zatace ga iya lokacin da suka dauka a haka ba, ta dai tuna yanda ta samu dakyar tana mikewa. "Ina tare da ke" Da Rayyan ya fadi ce ta rakata dakinta, ya kai mintina biyar kafin shima ya iya mikewa. Idan ma bata yarda ba zaici gaba da fada mata daga nan har lokacin da zata yarda da shi. Saboda wannan zaman da sukayi kawai ya kara tabbatar mishi da ana halittar wani dan wani, dan yanajin zuciyar shi an halitta mishi itane kawai dan ta dokawa Layla ita kadai, ita din tashi ce kamar yanda yake fadi a ko da yaushe. "Aure zanyi Bilal, har yanzun ba zaka dawo ba ko? Da gaske wannan karin ba zan yafe maka ba" Shine abinda ya fadi bayan ya shiga daki da dukkan zuciyar shi yana fatan Bilal din zaiji shi ko ta wanne haline. Saboda kwanakin sun fara mishi tsayi. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:09 PM - 111: Jan 16, 2021. 31 "Abbu ka yafe mun, dan Allah Abbu ka yafe mun, duk ku yafe mun..." Shine kalaman da sukewa Abbu amsa kuwwa a cikin kunnuwan shi harma da kai. Muryar Layla na zauna mishi da wani yanayi, yanda tayi maganar kamar tana saka ran fitar duk abinda yake cikinta zaizo ne da ajalinta. Da kan shi shekaranjiya bayan sun sake kwasowa zuwa asibiti cikin dare ya samu likitan yace "Wai ba zakuyi mata aiki ku ciro abinda yake cikin nata bane? Tun da satin nan ya kama yarinyar nan take cikin wahala, dan Allah ku duba lamarin" Murmushin karfafa gwiwa likitan yayi mishi yana kuma bashi tabbacin babu wata matsala dan wasu matan nayin haka. Ba zai manta ba, ko Mami takan yi doguwar nakuda, ta Layla din ce dai take tsaya mishi a rai fiye da duk wadanda yagani a baya. Nakudar ce saita taho mata gabaki daya sunzo asibiti sai kuma ta lafa ace ba haihuwar bace su sake kwasa su koma, yau ne karo na hudu a sati daya. Ita take ciwon amman zai iya rantsewa rashin natsuwa ya saka sunyi zuru-zuru gabaki dayan su. Yau kam ko da sunce ba haihuwar bace shikam zaice a barta a asibitin ne kawai. Bai san akwai tsoron da zai danne na ganin jikan da zai diro ahalin su da gurbataccen asalin da bashi da masaniya a kai ba sai yau. Ko da yake zaice akan cikin Layla ya fahimci ba mata kadai ke da gulma ba, ba kuma su kadai tsegumi ya tattara ya zaunawa ba. Tun bai gane kallon da akeyi mishi a masallaci ba, da yanda har wani dan jinjina kai wasu a cikin mutanen unguwar sukeyi kamar alamun tausaya mishi duk idan sun hada idanuwa, ciki harda mutanen da gaisuwar musulunci ce kawai take giftawa a tsakanin su. A cikin irin mutanen ne wani ya iya samun karfin gwiwar tarar shi sun fito daga masallaci yana fadin "Alhaji ashe kuma haka wannan lamari ya faru da yar wajen ka? Allah ya kiyaye na gaba, kasan yarane yanzun ka haife su baka haifi halin su ba, kana iya kokarin ka akan tarbiyar su suna dauko maka magana. Allah dai yasa an dauki hukunci mai karfi akan yaron da yayi ta'asar" Tunda ya fara magana kallon shi kawai Abbu yakeyi, shi da kan shi sai da ya tsargu ya fara kame-kame yana barin wajen. Amman tabbas zantukan shi sun rigada sun isar da sakon da yake son su isar a zuciyar Abbu, mutane sunyi gaskiya, zancen duniya baya boyuwa, ba kuma komai bane idan ka binne yake kwanciya lafiya, wasu hawaye yaji masu zafin gaske sun taru a cikin idanuwan shi. Da girman shi da komai, ashe kallon tausayin da kowa yake mishi kenan a cikin unguwar, kallon yanda martabar gidan shi da ahalin shi ta tabu. A ranar sai da ya kasa hakuri yake labartawa Mami abinda ya faru, sai dai murmushi tayi mai cike da karayar zuciya. Don dai batason kara daga mishi hankali shisa bata fada mishi ya taushi zuciyar shi ba, ba zatace ga lokacin da maganar cikin Layla ta bullu a cikin dangin su ba, ko ta hanyar da hakan ya faru. Duk da tana son dora alhakin akan Anty Uwani, dan itace ta zo gidan tayi sa'ar ganin giccin Layla, duk da a lokacin akwai hijabi a jikin Layla, kuma cikin duka bai shige watanni ukku ba. Da farko bata kawo komai a ranta ba akan yawan ziyarar da yan uwa na jiki da na nesa suke kawo mata ba, sai da suka fara tambayar inda Layla take da yanda suka kwana biyu basu ganta ba, suna yin tambayar idanuwan su na yawo a cikin gidan kamar zasu iya hangota ta cikin daya daga bangwayen da suke zagaye da dakin. "Tana lafiya. Alhamdulillah" Shine amsar da suke samu, sai ko murmushi mai ciwon gaske daga wajen Mami din, tana so tace musu Layla tana makaranta ko dan gujema tarin tambayoyin su, shisa a irin lokuttan take zabar ta mike ta kawo musu abin sha ko ta kawo wani zancen da zai sa su kyaleta, amman sai sun san yanda sukayi suka dawo da zancen akan Layla. Tun tana kuka bayan tafiyar kowanne a cikin su har zuciyarta ta bushe. Duk zuwan bai musu ba sai da suka dinga turo yaran su 'yan matan suna kusan yini a gidan. Haka makota ma da suka fara mata zarya, har mutanen da bata taba sanin da zaman su a cikin unguwar ba. A lokacin ma cikin Layla ya shiga wata na bakwai, sun fita kenan zasuje awo, ita da Layla da Jabir da zai kaisu, basu karasa fita kwalta ba Layla ta zage gilashin bangarenta tana zura kanta saboda amai daya taso mata. Hakan yasa dole Jabir din yayi parking a gefe ta fito, wahala ma tasha dan batayi aman ba. Sai ruwa da Jabir ya dauko mata na roba ta kuskure bakinta tana kuma wanke fuskarta. Mami ma hankalinta yana kan Layla da ta jigata, tun da rabonta da wasu amai tun cikin na karami, taji Jabir yace "Da kin karaso ai saiki fi ganin mu da kyau" Hakan ya sata daga kai ta sauke shi kan matar da bata ga fuskarta ba sai bayanta saboda ta wuce da sauri har tana tuntube, kai kawai Mami ta jinjina suka shiga mota suna tafiya. Har suka kai Jabir na kwashewa matar albarka "Aikin banza, shisa rayuwar turawa tayi wallahi, babu wanda ya damu da kai ballantana" Ita dai batace mishi komai ba saboda jikinta da yake a sanyaye. Haka mutane suka dinga shigiwa gidan, wasu da uzurin an kwana biyu ba'a gaisa ba, ko zasu wuce shine suka biyo. Murmushi Mami takanyi, tasan gulmace da tsegumi kawai ya shigo da su, idan basu ga Layla ba ta boye tana daki, lokaci zaizo da zasu shigo gidan kukan duk abinda zata haifa in dai ya taka duniya zai tabbatar da zargin su idan tantama sukeyi. Ta jima da daina gujema kaddarar da ta same su, idan tana boyewa babu abinda zai karawa Layla sai tarin damuwa fiye da wadda take ciki. Ga duk zuwa awon da zasuyi sai likita ya kara musu kashedi kan kwantar mata da hankali saboda jininta da ya hau, abinda ba'a so a tare da mai ciki. Yan uwanta ma gulmar sukeyi, dan wasu yan unguwa sunyi bata ga laifin su ba, masu dalilin da zasuyi mata uzuri ma basuyi ba, kowa dan yatsa ya daga ma kaddarar da ta same su kamar su din sunfi karfin hakan, kamar su din suna da dabarun kaucewa abinda ya sameta. Dan akwai matar da tana shigowa gidan sun gaisa ta zauna sai ga Jabir shima ya shigo ya gaishe da matar yana wucewa kitchen. Kallon sani Mami takeyi mata, amman ta rasa inda tasan ta "Nasan baki gane ni ba ko? Matar Balarabe ce da muka zauna nan baya" Kai Mami ta jinjina, shekaru wajen tara ba wasa bane ba, kuma ko da can din da suka zauna anan unguwar tasu in ba jaje ko barka ba, babu abinda yake hadasu "Allah Sarki, shekarun ne da yawa shisa, duk ina yaran, ya wajen Salamatu" Wata yar dariya matar tayi "Kowa lafiya, na shigo unguwar ne nake jin rasuwar Bilal, nace aikam zan shigo in muku gaisuwa. Allah yayi mishi Rahma" Bayan Mami ta amsa tana shirin mikewa kenan dan ta kawo mata ruwa tace "Allah dai ya kara karemu, ashe haka abubuwa duk suka faru, ga yar wajen ki din nan da akace kina riko ya take da suna ita kuma ta dauko magana, abin ya bani mamaki kwarai..." Kallonta Mami takeyi, kafin ta iya yin wani tunani Jabir ya fito yana fadin "Menene abin mamaki?" Ko ina na jikin shi bari yake da bacin rai, sosai yanzun mutane suke bashi mamaki, yana kuma sake jinjina ma Rayyan da tun da wuri ya gane halayen mutane ya nisanta kan shi da su. Shima abinda yakeyi kenan yanzun, saboda su din basa gajiya da yin abubuwan da zakayi komai dan ka gujewa zama jinsun su "Jabir" Mami ta kira, kai ya girgiza mata yana fadin "Layla! Layla!!" Yana kallon matar da take ta kifkif da idanuwa cike da tarin rashin gaskiya "Layla!" Jabir ya sake kira lokacin da yayi dai-dai da fitowar Layla da take rike da bayanta, idanuwanta na fara sauka akan Jabir da yake takawa ya karasa inda take yana kamo hannunta, bin shi take cikin rashin fahimta harya zo da ita tsakiyar falon yana tsayar da ita a gaban matar "Ki daina mamaki yanzun, ki gani da idanuwan ki, saiki fita ki sake tabbatar musu idan akwai mai sauran mamaki ya bari, idan suma zasu shigone su ganta su shigo" Kanta Mami ta sadda kasa tana kai yatsanta a hankali ta share kwallan daya taru a cikin idanuwanta, zuciyarta na wata irin kuna, mikewa matar tayi babu ko sallama ta raba Layla ta wuce. Har lokacin jikin Jabir bari yakeyi. Sakin hannun Layla yayi yana wucewa dakinta da kan shi ya dauko hijabi ya mika mata "Hamma..." Ta fadi muryarta na rawa, idanuwanta cike da hawaye, kai Jabir ya girgiza. Zuciyar shi sam ba zata iya dauka ba. Baice abinda Layla tayi bashi da muni ba, amman tsakaninta ne da Ubangiji, a cikin duk tarin mutanen da suke mata surutu, suke nunata da yatsa babu wanda za'a binne su a tare, sanda za'a kaita a rufo a barta da ayyukanta ba lallai su sani ba, addu'ar neman Rahma ma ba lallai bane su bita da ita. Baisan inda tarin mutanen suka shiga ba a lokacin da ta samu makaranta, lokacin da tayi saukar Al'Qur'ani mai girma, duka bai gansu sun shigo tayata murna ko jinjina ma su Mami kan kokarin su ba. Sai yanzun da kowa yake tunanin sunyi kuskure a rikon Layla, sai yanzun da ita kanta Layla din wani abu mai muni ya sameta, tarin mutanen da basu da masaniya akan kominta sune a gaba wajen yanke mata hukuncin da basuda hurumin yin haka. Yana gab da fara sakawa mutane hannu idan yana gidan suka shigo, baisan me yasa Mami bata binsu da tabarya ba, shi bashida wannan hakurin sam "Ba zaki kare duka rayuwarki a cikin bango hudu na dakin ki ba Layla, idan baki fita da cikin nan ba zaki fita da yaro ko yarinya. Mutane suna magana yanzun, ba zasu daina magana ba, karki barsu, karki bari su takura ki fiye da yanda kike a takure" Jabir ya karasa maganar da wani irin yanayi a muryar shi da yasa hawayen da ke cikin idanuwan ta zuba "Jabir ka kyaleta, me yasa baka da hankaline kai?" Mami tayi maganar tana kokarin tarbe kukan da yake barazanar kwace mata, hijabin Layla ta karba tana sakawa a jikinta. Zuciyarta na wata irin dokawa kamar zata baro kirjinta. Mami bata hana su ba, tana kallo Jabir ya koma ya daukowa Layla takalmanta, fitar sukayi, daga farkon layin har titi, Layla tana jinta kamar babu kaya a jikinta saboda kallon da mutane suke binta da shi, kamar yanda Jabir ya fadane, ba zata cigaba da boyewa ba har abada, zancen ya rigada ya bazu, gara ta fara koyan yanda zatayi rayuwa da tabon da yake jikinta. Sanda suka koma numfashi ma dakyar take fitar da shi, har bakin kofar dakinta Jabir ya rakata sannan ya tsaya yana fadin "Babu hakkin mutane a kanki. Ba zan miki karya ba kin sani, duka rayuwar ki ta duniya ce ta samu tangarda, ba zancen zancen ki ba zai wuce a baku nan mutane ba, amman duk sanda zaki gifta zaki tuna musu abinda yake adane a zukatan sune, bansan al'adun mu na hausawa basawa mata adalci ba sai yanzun Layla, sai da rashin adalcin ya biyo ta cikin gidan mu...." Wani irin numfashi Jabir yaja, bayason hawayen shi su zuba a gabanta, zai kara karya mata zuciya "Ba zaki iya gyara tsakanin ki da mutane ba, ki gyara abinda kike da tabbas akan shi, ki gyara tsakanin ki da Allah, sai Ya tausaya miki ya gyara duniyar ki, karki bar su, karki bari su takura ki fiye da yanda kike a takure, kina jina" Kai ta daga mishi tana goge hawayenta. Sai da yaga ta shiga daki sannan ya juya yana komawa wajen Mami ma da tun da suka fita tana zaune tana wani irin kuka mai cin rai "Dan Allah ki rage sanyin halin nan Mami, ki daina barin mutane suna bi takan ki akan abinda baya karkashin ikon ki, idan ba zaki iya korar su ba Mami ki daina sauraren me zasu ce suna bata miki rai, dan Allah. Wallahi zuciyata zafi takeyi mun, sosai da sosai" Cewar Jabir yana ficewa daga dakin saboda bayason ganin kukan da Mami takeyi. Har Abbu ya samu da daren ranar, dan Abbu ba zai manta yanda Jabir ya shiga dakin babu ko sallama ba "Yaushe abin nan zai wuce mana Abbu? Me yasa mutane ba zasu kyale mu ba? Ina ruwan su da rayuwar mu?" Hannu Abbu ya dan bubbuga a gefen shi yanawa Jabir din alamu daya je ya zauna, bai musa ba kuwa ya karasa yana zama inda Abbu ya nuna mishi, idanuwan shi sun kada sunyi ja, watakila da yayi kuka zai samu sauki "Nagaji da ganin Mami na kuka kullum, ina jina so helpless..." Dan murmushi Abbu yayi "Ka kalleni Jabir, ban san inda nake samun karfin bude idanuwa ba a duk safiya, saboda wannan ne karo na farko da ko kalaman lallashi bani da su, damuwar ku gabaki daya ta tarar mun, ni ya kake tunanin ina ji? Um Jabir? Dan Allah ka dan kara daurewa, komai zaiyi sauki In shaa Allah" Jabir ya dade zaune a dakin ya hade kan shi da gwiwa yana neman sauki koyaya ne. Kamar yanda shima Abbu yake tsaye a wajen yana neman sauki a yanzun, daga shi, Ayya sai kuma Mami a asibitin, da yake dare ya farayi sanda suka fito din, wajen sha daya. Addu'ar duk da tazo bakin Abbu ita yakeyi, kafin wayar shi da take aljihun shi ta fara ringing, yana fito da ita yaga Rayyan ne, yana dagawa ya saka a kunnen shi muryar Rayyan din ta daki kunnen shi "Ina ta kiran Ayya bata daga ba, Mami ma haka, Layla fa? Nakudar ce ta sake dawowa ko Abbu? Ina magana da ita naji shiru, sai kira nakeyi itama bata dagawa" Dan siririn numfashi Abbu ya sauke "Gamu nan a asibiti m..." Rayyan bai bari Abbu ya karasa ba yace "Me suka ce? Ga shi dare yayi ni ba zan iya tahowa ba yanzun" Duk da halin da Abbu yake ciki sai da yayi dan murmushi "Ka kwantar da hankalin ka. Babu abinda zai faru sai alkhairi da yardar Allah, zan dinga kiran ka ina fada maka yanda ake ciki, kayi mata addu'a kai dai kaji" Sai da ya amsa sannan sukayi sallama, su Mami ya kalla "Rayyan ne" Kai Mami ta jinjina, ko lokacin da ake maganar soyayya a dangin su, zancen baya wuce "Anya akwai matar da tayi sa'a irin Maimunan Ahmadi?" Ko da ta aure shi ta sabajin yanda ake fadin "Maimunan Ahmadi" Shisa sam bata jin kishin haka, zata so a yanzun na minti daya idanuwa da hankulan kowa su dauke daga cikin Layla su koma kan ita da Rayyan, tana da tabbacin tsantsar kaunar da take tsakanin su zai saka su fara sabon mamaki, ba kowanne namiji bane zaiyi abinda Rayyan din yayi. Ko ita maganar ta daketa da tajita daga farko, sai ta dinga ganin kamar mafarkine, duk da tasan da yawa zasu ce tayi azarbabi, kamar ta jira taga yanda zaman Rayyan da Layla zai kasance a karkashin inuwar aure kafin ta yanke hukunci akan tarin kaunar da suke yiwa juna. Sai dai ta kasa, tana da yakini mai girma akan kaunar Layla da take gani tattare da Rayyan din. Watakila kuma idanuwanta ne suka rufe saboda nauyin da Rayyan din ya dauke mata na tunanin wanda zai zamo miji a wajen Layla, wanda zai kauda kai daga tabon da yake tare da ita harya ganta din, da tarin kalubalen da zata iya fuskanta daga wajen dangin shi idan har ta samu din ma. Duka rayuwar 'ya mace zagaye take da martabar da tabuwarta yake dai-dai da nakasun da zai taba gabaki daya ahalinta. Kuskure daya tak zai iya canza komai ta fannin da gyaruwar shi zatayi wahala. Dukan su a tsaye suke duk kuwa da kujerun da suke a wajen, babu mai natsuwar zama, kowa da abinda yake sakawa yana kwancewa a cikin zuciyar shi. * Motar farko ya samu daga Kaduna zuwa Kano, asuba ma a tasha yayita. Da yake Bappa ya kai shi, amman gani yakeyi kamar motar bata sauri, yau ne ya sake jin takaicin rashin iya tuqi, da yana da mota a hannun shi iya gudun da yake so zaiyi. Abbu ma da safen nan kira biyu yayi mishi bai daga ba, ga shi yanzun sun fara shiga wajajen da babu network me karfi, ko shi tun yana gwada kira harya hakura ma, ko baccin kirki bai samu ba, lokaci zuwa lokaci yake kira yaji ko ta haihu. "Har yanzun dai, da ta sauka din zan kiraka In shaa Allah" Shine amsar da yake samu wajen Abbu. Ba dan baisan yawan yan gidan su gabaki daya ba, amman a daren sai da ya tsinci kan shi da kirgasu, saboda yana son yaga sau nawa Abbu ya jure tashin hankali irin wanda yake jin shi a ciki. Yama fi jinjinawa matan, dan yana da yakinin idan shine a matsayin su babu abinda zai hada shi da ciki. Yara ne ya ga na yan uwa sun ishe shi, amman da yake Allah yayi wa mata wata irin jarumar zuciya, sai ka sha wahalar nan kuma gobe ma ka sake maya wata. Babu kalar tunanin da baiyi ba, ciki harda na yanda da yasan cewar kaso kusan casa'in cikin matsalar shi bata da alaka da asibiti, da saiya tafi fannin mata wato Gynecology ko dan rana irin wannan. Sanda ya sauka garin Kano, daga tasha kan shi tsaye asibitin da Layla take wanda na kudine ya tari mashin yana nufa. Tun bai karasa sauka ba yake kiran Abbu da ayi mishi kwatancen inda suke din, shisa sanda ya karasa Abbu din ma ya fito bakin kofar asibitin yana jiran shi "Da ka zauna ai Rayyan" Abbu yace bayan sun gaisa, kai Rayyan din ya girgiza mishi "Hankalina ba zai kwanta ba Abbu. Gara ina nan din dai" Da gaske yakeyi, dan duk abinda suke fada mishi jinsu kawai yake, yafi so yana gani da idanuwan shi. Sauran duk da tayi ba'a dadewa haka ake ce mishi ta samu bacci ba haihuwar bace da ta tashi zasu tafi gida, ko kuma gasu a hanya zasu koma. Amman yau har yanzun da suke takawa suna shiga cikin asibitin babu wani labari. "Ayya..." Cewar Rayyan cikin sigar gaisuwa, ita da Mami suka juya a tare, kafin su amsa shi daya daga cikin Nurses din ta fito da murmushi a fuskarta "Ta sauka lafiya" Ta fadi tana saka su tattara hankulan su zuwa kanta gabaki daya. Lumshe idanuwan shi Rayyan yayi yana sauke wani numfashi da baisan yana rike da shi ba. Duk wani abu da suke fadi baya karasawa kunnuwan shi sam. Ba zaice ga asalin abinda yake ji ba, kafafuwan shi ne sukayi wani irin sanyi, baisan lokacin daya tsugunna ba, banda numfashi kamar wanda ya sha gudu babu abinda yakeyi, baisan lokacin daya dauka a wajen ba sai da yaji Abbu ya dafa kafadar shi "Ka zo ka fara karbar ta" Kalmar "ta" na fada mishi 'ya mace ce Layla ta haifa, zuciyar shi yake ji cikin tafukan kafafuwan shi a lokacin daya mike yana bin bayan Abbu zuwa dakin da aka dawo da Layla din da akanwa lakabi dana hutu. Amman baya ganin komai, idanuwan shi kafe suke kan yarinyar da take hannun wata Nurse da taketa murmushi ta karaso tana mikowa Rayyan yarinyar, hannuwan shi duka rawa suke lokacin da ta saka mishi yarinyar, yana mamakin rashin nauyinta, dan ji yake kamar zata subuce mishi idan yayi wasa. Yawu yake nema a cikin bakin shi da yayi wata irin bushewa lokacin da ya kafa yarinyar da take ta mutsilniya a cikin farin towel din da take nade ciki har wuyanta. Kafafuwan shi yake ji suna son karayin sanyi, dakyar ya iya dan rankwafawa da kan shi saitin kunnenta yana mata kiran sallah a ciki kafin yayi mata hudu da "Maimunatu" Kamar yanda yasan burin Bilal kenan, maganar shi kenan, zancen shi akan yara baya wuce farawa da samun 'ya mace da zai sakawa sunan Ayya, yana dagowa ya sake kallon yarinyar yana jin yanda a duniyar shi bai taba sauke idanuwa akan halitta mai kyawunta ba, bai taba ganin wankakke abu da babu dauda a jikin shi ba sai ita, kafin yaji wani abu ya tsirga mishi yana saka shi tallafeta a kirjinta kamar yana son kareta daga tunanin shi, yana son kareta daga furucin mutane akan laifin da bata da alaka da shi "Idan baka dawo danni ba, dan Ayya, ka dawo dan ita Bilal, dan Allah ka dawo haka" Ya furta a cikin kan shi yana jin wani irin radadi na ratsa duk wata gaba ta jikin shi, ko da su Ayya suka shigo dakyar suka iya raba Rayyan da yarinyar daya fara kira "Nur" Saboda da gaske ita ce hasken daya gani a cikin yan watannin da rayuwar su gabaki daya tayi wani irin sauyi. Ko da taje hannun Ayya, bata san lokacin da hawaye suka fara zubar mata ba, Mami ta mikawa ita tana ficewa daga dakin gabaki daya, waje ta samu ta zauna a bakin kofa, kuka takeyi da ta kwana biyu batayi irin shi ba. Kuka takeyi na abubuwa kala-kala, kuka take musamman akan rashin danta, kuka takeyi na hakkin Rayyan da har yanzun ta kasa samun karfin gwiwar kallon idanuwan shi ta fada mishi balle ya yafe mata. Anan bakin kofa ta samu kujera tayi zamanta, Mami ma tayi kuka ba kadan ba, jikar tace ta farko ta rike, jikar da tazo mata ta wani fanni mai wahalar gaske. "Ina nemar kariyar Allah a kanki daga dukkan wani abu mai muni, daga saukin shafar da kaddarar iyayenki zatayi miki" Shine addu'ar farko da tayi bayan ta karbi yarinyar. Abbu ma tunda ya karbeta yayi mata addu'a ya basu ita, saboda shine yake da karfin zuwa yaji ko akwai sauran kudaden da zasu biya. Da yake Layla din ba wata matsala ta samu ba, sai jigata da tayi, wajen azahar aka sallame su gabaki daya suka dunguma zuwa gida. Rayyan bai samu sunyi wata magana da Layla ba, ko idanuwa ta kasa hadawa da shi har suka sauka gida, yana gani Mami ta jata suna shigewa bangaren su, har daki ta kaita, sannan ta koma dan ta hada ruwan wanka, zaune Layla take inda Mami ta barta, sai Nur a gefe da take bacci kamar bata da wata damuwa a fadin duniya. Sai lokacin hawayen da suke cike da idanuwan Layla suka zubo. Nur take kallo, wasu hawayen suna kara zubo mata, bata dauka zata haifota batare da ta rasa tata rayuwar ba, ta sallama da lamarin duniya gabaki daya, saboda duk wani ciwo da ta taba tunanin taji nafila ne akan zafin nakuda, jikinta babu wata gaba da bata amsa da ciwon ba, ta sha wahalar da bata taba hangowa ba, wahalar da take fatan ta zame mata kaffara saboda tana kokarin ganin ta cika duka sharuddan tuba, tana kuma da yakinin Allah mai Rahma ne "Ga kaddarar mu Hamma, kaddarar da mu duka bamu hango ba. Allah ya yafe maka, Allah ya yafe mana" Ta furta a hankali, tana kai hannu ta share siririyar kwallar da ta zubo mata. Babu wani abu da yake da sauki a cikin rayuwa banda bautar Allah, ita ce zakayi ka samu natsuwa, ita ce kuma zakayi a kyauta. Amman yanzun take ganin kacokan wahala ce a cikin zaman duniya, a da tunanin yanda zata bada labarin kaddarar da ta gifta tsakanin ta da Bilal ne, kafin fuskantar su Mami, sannan kuma rayuwa da cikin da kowa yake nunawa 'yatsa. Tunanij ta gabaki daya ya sauya lokacin da kukan Nur ya dira a kunnenta a karo na farko, ta sake gane komai ba komai bane in dai ba zai taba yarinyarta ba lokacin da aka saka mata ita a cikin hannunta. Yanzun gabaki daya babu wani tunani a cikin kanta banda na kare Nur daga duk wani abu da zata iya, a lokaci daya darajar su Abbu na kara daguwa a idanuwanta, ashe haka iyaye suke ji, ashe haka 'da yake, cikin awanni kalilan ta dandani fargabar da take cikin kula da amana mai girma har haka. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:09 PM - 111: Jan 22, 2021. 32 Yafi mintuna sha biyar tsaye yana juya hular da ya kamata ace tana sanye a kan shi. Yau na daya daga cikin ranakun da suke da muhimmanci a rayuwar shi, ranar daya kamata yayi ta da mutanen da suke da muhimmanci a wajen shi, bai ma su Abbu gardama ba da sukace ya bari Layla tayi arba'in, yarinyarta ta danyi kwari sannan. Duk da ba wannan dalilin bane ya saka shi jiran, har a kasan zuciyar shi Bilal yake jira, a cikin kwanakin babu ranar da zata wuce idan ya kira gida baiyi tsammanin zasuce mishi Bilal din ya dawo ba. Watakila harda kewar Bilal da yake ji a duk wata gaba ta jikin shi, kamar zuciyar shi na son gaya mishi baiji mutuwar Bilal yanda ya kamata ba saboda yana tunanin kamar bai rasa shi ba. Tun lokacin daya fara tunanin aure yasan baya bukatar wata hayaniya, a daura mishi aure kowa yayi fatan alkhairi ya tafi. Idan akwai abinda ya hango bai wuce shi da Bilal zaune a daki suna cin abinci suna hira bayan an daura aure, amman bayajin zai samu hakan yau. Baiyi kokarin danne Layla ba, ya tambaye ta "Wanne irin biki kike so Layla? Dan Allah ki fada mun, bikin ki ba zai dawo sau biyu ba..." Ita ma din tana daya daga cikin mutanen da basa son wata hayaniya ta biki, tuni suna fada ita da Jabir, bikin su daga su sai mutanen da suke da kusanci da zuciyoyin su suke bukata a lokacin bikin su "Bikin da zan zama matar ka Hamma, daurin aure, shi kawai nake bukata" Duk yanda idanuwanta ke kara gudun zuciyar shi sai da ya jima yana kallon cikin su yana neman gaskiyar maganarta. Bayason taji cewa kamar ita din bata cancanci kalar bikin da take mafarki ba "Wai me kakeyi ne har yanzun?" Bappa da a gidan ya kwana duk kuwa yanda Rayyan din yace mishi ba wani abu za'ayi ba, ya koma gida da safe ya dawo "Ina ruwan ka dani ne Rayyan? Gidan nan naga na Abbu ne, kuma baice in tafi ba..." Har a zuciyar shi yaji dadin zaman Bappa din, tunda kusan kwana yayi yana kallon ceiling cike da tunani kala-kala har wayewar garin "Ku fa ake jira" Haris ya fadi yana leko kan shi, turarukan daya hango na saka shi shiga cikin dakin sosai. Dauka yayi ya sake feshe jikin shi, Rayyan na bin hular da take kan shi da kallo, zuciyar shi na matsewa a cikin kirjin shi "Hular Bilal ce ko?" Ya bukata muryar shi can kasan makoshi. Kai kawai Haris ya daga mishi yana ficewa daga dakin. Kamar yanda ya fadawa Rayyan cewa zaije Zaria ya kwashe kayan su haka akayi. Rana daya ya ware, da wani irin karfin zuciya ya shiga garin Zaria har zuwa unguwar su Bilal. Harya shiga cikin gidan ma haka, ya san duk yawancin yan gidan, da Abdul ya fara cin karo daya karaso da sauri suna gaisawa yana dorawa da "Ina Bilal? Lambobin shi gabaki daya a rufe, mun kasa samun lambar Rayyan, kaima taka tayi wahala saboda babu yan set dinku da sukayi saura, wallahi tunda aka dawo muke tunanin ko lafiya....sai yanzun muke tunanin kalar zaman da mukeyi da yanda ya kamata ace kowa yana da adireshin gidan kowa ko da halin ziyara bai samu ba" Wani murmushi mai ciwo Haris yayi, zuciyar shi daya dauka ta dake yaji tana rawa, muryar shi ma a raunane yaji ta lokacin daya kalli Abdul da fadin "Ya rasu, hatsari yayi. Ya rasu..." Ya karasa maganar wani abu na tokare mishi makoshi "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Din da Abdul ya furta cike da tashin hankali na saka shi raba Abdul ya wuce cikin gidan. Da yake ya karbi mukulli a wajen Ayya, shiya dauko ya saka yana bude dakin, bai shiga tashin hankali ba sai daya kunna kwan dakin yana ganin yanda yayi wata irin kura kamar mutane basuyi rayuwa a ciki ba. Dakin yake karewa kallo, yana hango wajeje da lokuttan da suke zaune a ciki shi da Bilal, sai yaji har kirjin shi ma zafi yake. Ba zaice ga mintinan daya dauka a cikin dakin ba kafin yaji shigowar yan gidan su Bilal din da babu wanda yace mishi komai, dakin suka fara taya shi sharewa. Kusan babu wani abu da yayi, su suka dinga hada komai, duk yanda ya so ya kwashe komai saiya kasa, daga takardun da yake tunanin suna da muhimmanci sai suttura ya dauka, sauran hatta da katifa nan yabar ma su Abdul da yake ganin yanda mutuwar Bilal din ta dake su sosai. Lambar shi suka karba da fadin zasu shiga Kano suyi wa Ayya gaisuwa. Kai kawai ya jinjina musu yana ficewa ya shiga motar shi da aka loda kayayyakin a ciki. Sai daya zauna sannan yaji jikin shi na rawa ba kadan ba. Rayuwa aikin banza, babu wani abu da yake da tabbaci a cikinta, ba mutuwar Bilal kadai yake ji ba, harda tashi mutuwar yake hangowa, duk tarin burukan da suka ci shi da Sa'adatun shi mutuwa zata iya yanke musu shi, ga Bilal nan da Aisha, ya tabbata yarinyar bata taba hango auren wani ba Bilal ba, soyayya tun firamari ake yinta, ta ina zata fara yanzun? Wa zata budewa zuciyar ta, wanne waje ma zai samu bayan ko ina cike yake da kaunar Bilal? Hawayen da yaji ya share a kasan zuciyar shi yana fadin "Allah ya jikan ka Bilal, kai din mutumin kirki ne. Allah ya sa mutuwa hutun ka ce" Sai dai daya ajiye kayan Bilal a dakin su akwai wanda ya dauka, duk yanda yaso ya barwa Rayyan komai saiya kasa, ciki harda wannan hular da ya saka a kan shi, tare sukaje suka siya da Bilal ba zai manta ba, shi da kan shi ya dauketa ya dora ma Bilal din a kai "Hamma ni fa bana son wannan zanen, ina da shigen shi" Maganar Bilal din ta dawo mishi a lokacin "Ni ina son shi, tunda ni zan biya" Dariya Bilal yayi "Jiba ikon Allah, dan zaka sai mun shine ba zan zabi abinda nake so ba? Yaushe aka taba yin haka?" Shima dariyar yayi "Yau za'a fara idan ba'a taba ba" Sai kuma ya dinga yawan ganin Bilal din da hular, duk kuwa yanda manyan kaya ba damun shi sukayi ba "Na dauka baka son zanen?" Ya tambaya yana saka Bilal din yin dariya "Dana dan shiga haske da ita rannan sai naga ya danyi kyau" Hannu Haris ya kai da nufin cire hular daga kan Bilal daya kauce yana dariya "Ba'a kyauta a kwace Hamma" Shi din da Bilal zai iya cewa kamar abokai ne ba Yaya da Kani ba, ba zaiyi son kai ba, tunda ya kula kusan kowa zaice da kadan shakuwar da take tsakanin Rayyan da Bilal tafi wadda take tsakanin su. Amman yau Rayyan ya saka shi jin wani iri, yanda ya tambayi hular Bilal ce a kan shi kamar babu wanda yake da damar saka wani abu na Bilal banda shi, kuma har ga Allah bai san ya akayi ya sakata ba, har sababbin huluna yana da su daya keta siya na tanadin bikin shi da aka hada lokacin shi dana Rukayya. Kawai ya dauki wadda hannun shi ya fara kaiwa ne, sai kuma akayi dai-daito ya dauki wannan din. Shisa ya daga mishi kai kawai yana ficewa, ba zasu fara gwada waya fi kusanci da Bilal ba. Musamman yau din, wani irin numfashi Rayyan yaja yana fitarwa cikin yanayin da ya saka Bappa kallon shi "Idan ya mutun kuma fa? Bappa idan ya mutun da gaske ya zanyi?" Rayyan ya karasa muryar shi a tsorace, saboda da gaske baisan yanda zaiyi din ba idan ya rasa Bilal na har abada "Hakuri... Shi zakayi Bilal, hakurin da kowa yakeyi a yayin rashin, hakurin da su Ayya sukayi..." Kai Rayyan yake girgizawa Bappa, saboda yanajin kamar bai shirya ba, kamar ba zai iya ba. Ba duka labarin Bappa ya sani ba, kadan daga ciki da Rayyan ya fada mishi sai kuma sauran guntayen da yake tattarawa a kullum, sai ka dauka labarin ka cike yake da hargitsi, sai kaji na wani saiya saka ka gode Allah da kalar taka kaddarar "Hakuri zakayi Rayyan, ayyukan ka zaka cigaba da gyarawa idan kana son sake rayuwa da shi" Cike da rashin fahimta Rayyan ya kalli Bappa, kalaman Baba ne shima zai ara yau, duk da sun jima basuyi mishi aiki ba, amman sun gyara abubuwa da yawa a tare da shi, sun samar mishi natsuwar da yake fatan su samarwa Rayyan a yanzun "Rayuwa ba ita bace karshen mu, duk da itace farkon mu, amman karshenta mu musulmai shine farkon wata rayuwar, kasan Bilal da ya tafi ba sauri yayi ba, mu da muke nan lokaci muke jira. Ka gyara ayyukan ka, duk da basu bane zasu tsirar damu, amman ka gyara a duk rana dan ka samu damar tambayar Bilal idan ka natsu waje daya a aljanna, idan ya rigaka wuce karya jira na tsayin lokaci. Ba nan bane karshen zaman da zakuyi Rayyan, ka sani, ina tuna maka ne kawai" Numfashi Bappa ya sauke "Soyayyar da zaka yiwa Bilal a yanzun tana cikin yawan addu'ar ka ba kuncin ka ba... Ka karasa ka fito mu tafi" Cewar Bappa yana ficewa daga dakin, numfashi Rayyan yake ja yana fitarwa. Wani irin ciwo zuciyar shi takeyi da yanda yake son tursasa mata amincewa da sun rasa Bilal amman wani bangare nata yana mishi taurin kai. Ruwa ya karasa ya dauka ya sha, abinda yakeji yana nan tokare da kirjin shi, hular shi ya dora saman kan shi yana zira takalma a kafar shi ya fita shima. A bakin kofa ya tsaya yaja numfashi yana danne abinda yake ji kafin ya samu ya dora murmushi saman fuskar shi. * Zaune take a gefen Rayyan a cikin dakin Abbu, ta hade yatsunta da take wasa dasu waje daya. Gani takeyi komai da yake faruwa kamar mafarki tun da safe da ta tashi, da taimakon su Rukayya ta shirya, da yake Sa'adatu yar gidan Yaya Ayuba tana kunshi ita tazo har gida tayi wa Layla din. Kafin wani lokaci ta fito tsaf a amaryarta, tayi wani irin kyau cikin leshin da ta saka kafin a dawo daurin aure. Akwai banbanci kadan a yanda ta hango aurenta da kuma yanda ya kasance a yau din, ba mutanen bane sukayi kadan, wasu a cikin sune babu, musamman Bilal da kewar shi take tabata a cikin kwanakin. Amman akwai kowa da take fatan ace ya kasance a cikin duk wani hoto da aka dauka na bikin, ba wani taro akayi ba tunda duk yan uwane kawai. Sau daya taga Nur tunda ba rigima yarinyar gareta ba, itama ba zatace ga wanda ya kawo mata ita ta bata tasha ba aka sake daukarta, daman ba yini takeyi a wajenta ba, idan Rukayya bata shigo ta dauki yarinyar ba ko Huda zata shigo ko wani a gidan, idan an dawo mata da ita kuka tayi, sai kuma dare yayi, wani lokacin har goma na dare, zatace haihuwar Nur tayi, amman a kwanakin da tayi a duniya bata san wani abu rainon yarinyar ba. Sai take ganin kamar labarin ta yasha bamban dana sauran mutanen da suka samu yarinya ta hanyar da ta samu tata, saboda akwai yarda da kaddara a cikin nata lamarin, bata fuskanci kyamata daga yan gidan su ba, amman hakan baya nufin laifinta ya wanke, baya nufin zai mantu, da duk ranar da Nur zata gifta ita kadai ta isa ta tunasar da kowa. Shine abinda yake cin ran Layla, abinda yake damunta yana kuma saka mata tunanin Bilal fiye da yanda ya kamata. Laifukan sune take gani zai taba Nur babu kuma yanda zata iyayi. Yanda kowa yake son saukaka mata ranar yau har mamaki ta dingayi. Ta kuma yi kokarin ganin bata sa kokarin su ya tashi a banza ba, murmushin duk da ta dora akan fuskarta a hotunan daga zuciyarta ya fito, tana da tarin dalilai na yin farin ciki koya yake, tana zagaye da mutanen da suka tabbatar mata babu wani yanayi na rayuwa da zata shiga da zasu kasa karbarta, da zai canza kaunar da suke mata. Kowa ya fadi abinda zai fada in dai suna tare da ita zai zo mata da sauki. Murmushin da Rayyan yayi mata bayan sun hada ido da safen ya samu wajen zama a zuciyar ta. Bata san ko wani ya lura ba, ko ita kadai ta fassara murmushin shi da "Tawa, tawa har abada" Yana kara sata jin kamar a mafarki, yanzun ma har Abbu ya fara da fadin "Yau kam kalamai sun mun karanci, nasiha ya kamata inyi muku, sai dai na rasa abinda zan fada muku a cikin yan mintina da ban fada muku shi a duk tsayin shekarun da na samu a tare da ku ba...." Saboda sosai yake mamakin me yasa sai an aurar da yarinya ko yaro sai a dauko shi a kai wajen iyaye wai suyi mishi nasiha. Musamman yara mata, ko da bikin Zubaida haka aka kawo mishi ita, yarinyar ma tana ta kuka bayajin zata fahimci duk wani abu da zai fada mata, shisa ya kalli kanwar shi da take rike da ita yace "Nasan yarinyata, na san tarbiyar da na bata, ba ita zanwa nasiha ba, ku turo mun yaron" Hakan kuwa akayi, shi yayiwa fada, shi ya baiwa amanar yar shi, kamar yanzun yanda ya kalli Rayyan da fadin "Ga amanar 'yata nan Rayyan, kayi hakuri da ita a lokacin da zata kuskure maka, ka kauda kai a lokacin da nata idanuwan suka rufe ko da kuwa kaine da gaskiya. Zamana da Ayyar ka bai kawo mu yau ba sai da hakan, hakurin da ake jaddadawa mata mu ya kamata a jaddadawa shi, kayi hakuri, kayi hakuri da duka halayenta, karka cutar da ita, kanwar ka ce ita kafin yanzun ta zama matar ka, ka kula da ita kamar yanda kake so a kula da su Rukayya, ka kare martabar ta kamar yanda zaka so a kare ta yaranka wata rana, karka daga mata murya kamar yanda ba zaka so in dagawa Ayyar ka ba" Idanuwan shi Rayyan ya saka cikin na Abbu kafin ya dan daga kan shi, yana jin nauyin maganganun Abbu din da girman amanar daya dora mishi. "Zanyi magana da yarinyata Rayyan" Abbu ya fadi yana saka Rayyan din mikewa ya fice daga dakin, zuwa lokacin idanuwan Layla cike suke taf da hawayen da suka fara zubo mata "Abbu..." Ta kira muryarta na karyewa, wannan karin ba da kukan da takeyi ba, da tarin kaunar da takeyi mishi, da godiyar da bata da kalaman da zata fara yi mishi ita, batama san ta inda zata fara ba, saboda akwai tarin abubuwa da suka fi karfin godiyar.  Kallon ta Abbu yayi yana jin yanda zuciyar shi ta karye, su duka yaran yake kula da yanda girman daya fi shekarun su ya saukar musu, yanda tarbiyar da rayuwa take bawa dan adam ta saka sukayi wani irin laushi da kalaman shi zasu dauki wani lokaci basuyi musu wannan tasirin ba. "Kar zamana da Mamin ki ya zama tsanin da zaki gina taki rayuwar auren, ba lallai tazo iri daya da tamu ba, sai kinyi hakuri Layla, kinji? Zaki iya kiran mu ko da yaushe, kin san haka ko?" Kai ta daga ma Abbu wasu sababbin hawayen na kara zubar mata. Da kan shi ya mike yana kamata ta mike, kuka takeyi sosai dan zaka iya fahimta da yanda jikinta yake bari. Abbu ya rakata har wajen mota inda ta toge tana girgiza mishi kai, dan wajen shi aka fara kawota "Mami... Abbu...Mami na" Layla take fadi tana jin wani irin tsoro na ratsata. Zama matar Rayyan ne mafarkin ta, amman bata dauka haka zai kasance ba sai yanzun da zata bar gida, yanzun da bata san me rayuwa ta tanadar mata a cikin gidan shi ba, musamman yanda zataje mishi din, tana da yakinin shima ba haka ya hasaso auren shi ba, bai hango bayan mata harda yarinya za'a tafar mishi da ita ba, shine abinda ya kara gigita lissafinta. Kafin Abbu yayi wani motsi Layla ta kubce daga rikon shi tana bude lullubin da yake kanta saboda bata ganin hanya sam, da sauri gudu-gudu take nufar bangaren Mami, tun daga bakin kofa take kwala mata kira harta shiga can cikin dakin inda Mami take zaune a gefen gado tana sharar kwalla. Tana daga cikin mutanen da suke ganin ranar da ka aurar da 'ya ya kamata ya zamana rana mai girman gaske a wajenka, bata ga dalilin da zai saka ta fara kuka da za a kai mata yarinya gidan aure ba, tunda abin farin cikine, sai da ta wayi gari safiyar yau ko giccin Layla ta gani sai taji idanuwanta sun cika da hawaye. Saima da Jafar ya shigo bayan an dawo daurin aure yana kamata ya jata dole akayi hotuna da ita. Ta ga da gaske dai auren Layla aka daura, da gasken tafiya zatayi, balle kuma da aka shigo aka fita da ita, tana zaune ne tana jiran su tasan za'a kawo Layla ace tayi mata nasiha. Bata tsammaci ganin Laylar ta shigo a firgice haka ba "Mami..." Layla ta sake kira a karo na babu adadi ta karasa cikin dakin tana fadawa jikin Mami tare da sakin wani irin kuka mai tsuma zuciya "Ni bana son sakarci, ke baki san yanzun girma ya kamaki ba? Ki dagani karki karyamun kafada" Mami take fadi cikin karfin hali, amman ta kasa raba Layla da jikinta, idan ma akwai abinda take sonyi bai wuce sake riko Layla din ba. Addu'a ce yi mata takeyi ba tun yau ba "Allah ya saka miki albarka a gidan auren ki Layla. Allah kar ya saka hawayen ki su zuba a sanadin kaddara ta gidan aure" Shi Mami take furtawa a ranta, har sai da matar Yaya Ayuba ta shigo dakin tana kama Layla dakyar ta fita da ita. Da kanta ta saka Layla a mota suna jiran Rayyan ya fito tunda su kadai zasu tafi abinsu, ba wani rakata za'ayi ba. Sai Bappa da zai kaisu, yana zaune a gaba cikin mota suna jiran Rayyan din. Shi kuma bangaren Ayya ya tafi yace mata sun wuce ya kuma karbo Nur da yasan tana can. "Ayya zamu wuce ne... Ina Nur?" Rayyan ya fadi bayan ya shiga dakin Ayya din, kallon shi takeyi cikin fararen kayan shi, ya sake wasu duk da na safen ma farare ne, amman da babbar riga. Wannan kuma babu babbar riga, yayi kyau. Sai taga yau fuskar shi tayi mata fayau, ana cewa yana kama da ita, amman akwai wani abu a fuskar shi da yake mata kamar Abbu yau din nan "Rayyan" Ta kira da wani irin yanayi, nauyin hakkin shi take ji a duk rana, ta kasa samun karfin zuciyar fada mishi balle ta roke shi ya yafe mata, ta samu damarmaki da yawa tana kasawa, batasan me yasa yau din bakinta ya subuce da fadin "Laifina ne, komai daya faru laifina ne, ni nayi kuskuren da ku da Bilal kuka biya, Bilal ya biya fiye da kowa, alhakin Haris da naso cutarwa ne ya kamani Rayyan, alhakin shi ya sa ka dauki shayin daya kamata ya sha ka sha... Shine mafarin komai" Kallon ta Rayyan yakeyi tunda ta fara magana saboda yanda kalamanta suke dukan kunnen shi da wata irin iska "Me yasa?" Ya bukata muryar shi na fitowa can kasa kafin ya dora da "Ayya me yasa sai yau?" Duk ranakun da zata iya fada mishi maganar da zata fada sai ta zabi yau da yake neman duk wata natsuwa da zai iya. Hannu Ayya ta kai tana share hawayen da suka zubar mata, itama ba zatace ga dalili ba, amman abin ne yake cinta, musamman shekaranjiya zuwa yau. A shekaranjiya da ta zabi ta biya gidan Hajiya Dije da kanta bayan ta dawo daga kasuwa ta gayyace ta bikin Rayyan din duk da tun cikin rasuwar Bilal rabon da suyi magana, ta gwada kiran wayarta taji ta a rufe shisa ta biya. Sai ta sha mamakin jin Hajiya Dije tana gidan iyayenta. Gidan kuwa ta biya, ta sha mamakin ganin yanda rayuwa tayi da Hajiya Dije, wani irin hawan jini ne ya kamata, ta fadi, tashin da tayi a asibiti babu idanuwa, shine bayanin da Mamuda, dan uwan Hajiya Dijen da yake zaune a gidan su da shiya gada aka kuma bata daki daya ya fadama Ayya, amman data shiga wajen Hajiya Dije sai labarin ya banbanta dan kuka Hajiya Dije takeyi kamar zata tsiyayar da abinda ya rage cikin idanuwanta "Kinga inda rayuwa ta kawoni ko Maimuna? Hawan jini sukace a asibiti, ni nasan ba hawan jini bane ba, hakkin Balaraba ne, sharadin magani na karya ya dawo kaina, dan Allah Maimuna ki taimaka mun, bansan wa zan fadawa ba ya fahimta sai ke, ki taimaka mun Alhaji saki dayan daya rage tsakanin mu yai mun, yanda nake tsugunnen nan suma wallahi sai sun tsugunna" Ko sallama Ayya batayi mata ba ta tashi ta fice daga dakin, saboda tsoro Hajiya Dije ta bata, zame mata tayi kamar wata dodanniya. Makantar da take tare da ita bata zame mata ishara ba ita, neman hanyar da zata cutar da wasu take karayi maimakon neman yafiyar su, da gaske akwai mutanen da basu da rabo, tun daga ayyukan su a doron duniya zaka gane hakan, ba zatayi shisshigi ba shisa ba zata yankewa Hajiya Dije hukunci ba. Baccin kirki ma a ranar bata samu ba, ta gaji, sosai ta gaji da barin abin a cikinta shisa ta fadawa Rayyan din. Kallon shi tayi da nufin magana sai ga Huda ta shigo rike da Nur da take kuka, hannu Rayyan ya mika ya karbi yarinyar "Na bata ruwa taki ta sha, banga Adda Layla ba..." Kai Rayyan ya jinjina ma Huda yana cewa "Ina jakar goyon ta? Ki dauko mun da feeding bottle din, kiyi sauri" Ficewa kuwa tayi da sauri, baisan inda zai saka kalaman Ayya ba ko abinda yake ji, shisa ya kwantar da Nur a jikin shi yana kokarin ganin tayi shiru, dan jijjigata yakeyi a hankali. "Rayyan..." Ayya ta kira, amman bai kalleta ba, kirjin shi zafi yakeyi na gaske. Huda da ta dawo ta taimaka mishi yayi strapping Nur daya goya a ta gaba yana karba feeder din ya fice daga dakin batare daya cewa Ayya komai ba. Inda motar Bappa da aka saka Layla a ciki take ya karasa ya bude ta dayan bangaren ya shiga, yana jin addu'ar da mutane suke binsu da ita. Amman sam hankalin shi ba'a kan su yake ba lokacin daya ja murfin motar yana fadin "Muje Bappa" Ya sake tallabe Nur da ya dan kalla yaga tayi shiru, sumbatar gefen fuskar yarinyar yayi yana gyara zaman shi hadi da sauke numfashi. Addu'ar duk da tazo mishi ita yake karantawa ko zai samu natsuwa har suka karasa Hotoro inda gidan daya kama yake. * Da yake ba mai gadi gare su ba, sai da ya tsaya Bappa ya fita da motar, da suka hada ido da shi yace mishi "Koma menene karka sauke a kanta" Saboda ya kula da yanayin Rayyan din, bai amsa shi ba, da addu'a ya kulle gate din yana saka sarka da kwadon da yake jiki ya datse, sai bayan ya rufene ya laluba aljihun shi ya tabbatar da mukullin yana nan, kafin su fara neman taimako a hauro a yanke kwado. Sai da ya dauki ledojin shi da ya ajiye a kasa sannan ya kama hannun Layla da take kuka har lokacin ya jata suna nufar bakin kofa, ganin yayi tsaye ya sata dan kallon shi, addu'a ta ga yanayi cikin yanayin da ya tunasar da ita itama tayi. Suka shiga da sallama bayan kiran sunan Allah, bai saki hannunta ba sai da suka shiga dakin baccin su sannan. Ya ajiye ledojin ya zagaya gefen gadon. Nur ya kwance a hankali yana zarota, duk motsin da tayi sai gabanshi ya fadi karta tashi, ya samu ya kwantar da ita. Bai cewa Layla komai ba har lokacin. Kofar falon yaje ya rufe ya dawo. Zuciyar shi wani iri yake jinta harya shiga bandaki, alwala ya daura ya fito yana kallon Layla da ta goge fuskarta itama tana mikewa tunda ta samu tsarki tun satin daya fita. Alwala ta dauro sukayi sallah ita da shi, tana zaune ya sake tashi ya shiga bandaki, ruwa ya watsa ko zai dan samu sararin abinda yake ji ya mishi tsaye a kirji. Daya fito kaya ya sake, shaddar ta ishe shi, nan kasa inda Layla take zaune ta sadda kanta ya zauna a gefenta, sai lokacin ta kalle shi, farar riga ce ya saka T-shirt, da alama bai goge jikin shi ba dan fuskar shi da alamun ruwa a jiki har lokacin, kamar damuwa take karanta a shimfide a fuskar shi, yanda yaji idanuwanta na mishi yawo ne yasa ka shi kallon cikin nata idanuwa yana girgiza mata kai "Wani abune daban Layla, ba ke bace ba" Saboda zai rantse yana jin sautin tunanin ta cikin kunnuwan shi, idanuwanta da yake ganin hawaye a ciki na saka shi gyara zaman shi ya saka hannuwa yana riko fuskarta "Na san banda wani abu da zan baka Hamma, ba haka na hango yau ta kasance mana ba..." Layla ta ke fadi wasu hawaye masu zafi na zubo mata. Kai Rayyan yake girgiza mata, sam bayason inda tunaninta yake so ya dauketa "Bana so, bana son wannan shirmen tunanin naki. Kin zo mun dake, kin zo mun da Nur, kin bani duk abinda nake so harda abinda banyi zato ba, dan Allah ki bari, karki kara mun damuwa da tunanin nan naki... Raina a bace yake, amman bake bace" Ya karasa maganar yana matsawa sosai ya sumbaci goshin ta, yana sake sumbatar kuncinta kafin ya riko ta jikin shi yana sauke wani irin numfashi, ya manta yanda kusanci da ita haka yake samar mishi natsuwa, ya manta yanda jinta a jikin shi kawai yake kwantar da duk wata murya da take neman daga mishi hankali, sosai ya kara riketa a jikin shi yana sumbatar duk wani waje da labban shi zasu iya sauka kafin ya sake riketa kamar zai koma jikinta "Nagode Hamma..." Layla tace tana dorawa da "Nagode da ka zamar dani matar ka" Dariya yayi mai sauti yana sake riketa "Nagode da kika zama matata, nagode Layla. Ba zan miki alkawarin baki farin ciki ko da yaushe ba, amman In shaa Allah zanyi kokarin ganin kinyi farin ciki koyaya ne a duk ranar da zan samu aronta tare dake, Nagode... Nagode" Yana jin amsarta ta yanda ta kara shigewa a jikin shi, Ayya tace itace mafarin komai, tace laifin duka nata ne, baisan ko Layla da take jikin shi bane ta sauya tunanin shi, bai san ko dan Ayya din daga jikinta ya fita ba, amman ya kasa dora duka laifin a kanta, ya ga fuskarta, ya ga idanuwanta, ba tun yanzun yasan duka rayuwarta ta ta'allaqa ne wajen ganin ta kare su daga duk wani abu da zata iya ba. Idan da ta hango abinda tayi zai iya tabasu ba zatayi ba, yana ganinta ita da Haris, tana kaunar shi kamar daga jikinta ya fito. Kuskure ne tayi, kowa baifi karfin yayi kuskuren ba, ko da akwai son kai a cikin shi, baice ran shi bai sosu ba, baice ba za'a dauki lokaci ba kafin ya daina jin ciwon abin. Amman zasu kai wajen, kamar yanda shi da Layla suka kawo yau. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:09 PM - 111: Jan 30, 2021 33 Fitowa tayi daga wanka, idanuwan ta kan Nur suka fara sauka kafin ta saki salati "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un..." Idanuwan shi Rayyan ya daga ya kalleta a kasalance, kamar bai san dalilin yin salatin nata ba, yana kallo ta karaso ta kama Nur tana karewa gashinta da yake tsaye birci-birci duk ya cakude waje daya kallo wani malolon bakin ciki ya taso ya tokare mata wuya. Ita kadai tasan wahalar da tasha daren jiya tayi mata kitson, da kuka da komai, har dukanta sai da tayi, saboda Rayyan din ya kwana asibiti wajen aiki, Aminu Kano bangaren masu matsalar kwakwalwa. Ta san indai ya dawo ba za'ayi ba tunda Nur ba son kitso takeyi ba, ko kibiya ta gani a hannun Layla sai ta saka kuka. "Kwance mata kayi?" Ta tambaya, gira Rayyan ya daga "Me yasa zakiyi mata kitso? Kin matse mata kai dakyar take motsa wuyanta, har gefen kan ya fara yin alamar kurji" Sakin Nur tayi kawai, idan tayi magana tsaf hawayen takaici zasu biyo baya. A shekaru uku da aurenta da Rayyan ba zata ce bata cikin kwanciyar hankali ba. Amman tunanin da tayi na cewar auren Rayyan shine zai gyara mata komai, idan tana tare da shi babu wani abu da zai dameta ne ya sha bamban. Mutane ne suka nuna mata damuwar ta babu inda zata je, kamar yanda suka koya mata rayuwa da damuwar a kasan zuciyar ta. Ko biki akeyi ko suna idanuwan mutane akan Nur suke fara sauka, Nur suke fara gani, kamar yanzun rayuwar ta gabaki daya ta tattara ne akan yarinyar "Ita ce wannan ko? Allah sarki" Sune kalaman da suka fi tsaya mata a kirji suna sakata jin wani irin ciwo na ban mamaki. Ba manta yanda aka sami Nur tayi ba, amman na rana daya tana so ta rufe idanuwan ta, ta bude su ta kalli yarta a matsayin ya, ta kalleta batare da taga tabon da tayi mata ba, tabon da shi kowa yake fara dubawa. Ba son kai zatayi ba, amman Nur tana da kyau, sosai tana da kyau saboda tana kama da Bilal, kamannin da yasa in ba sanin su kayi ba sam ba zaka gane ba daga jikin Rayyan ta fito ba, gashi tana da hasken fata kamar na Rayyan din. Sai dai kyawunta ya kasa dishe munin tabon da yake tare da ita. Shekarar su daya da aure, Rayyan ya saka ta sake yin jamb ta nemi gurbin karatu a BUK. "Kina da buri kafin faruwar komai, abubuwa da yawa sun canza miki, bana son ya zamana harda wannan...ki koma makaranta Layla, kiyi karatu, ki fita da sakamakon da kike burin fita, ki nemi aikin da kike fatan samu" Shine kalaman shi, kalaman da suka bude mata zuciyarta suna dawo mata da burin ta sabo. Ko ba komai makarantar ta rage mata damuwa, yanzun tana shekara ta biyu, ta sha wahala a farkon zango na biyun a shekarar saboda laulayin cikin da yake jikinta, ga kula da Nur, tunda Rayyan yaki yarda a sakata makaranta sai a sabon zangon da za'a shiga, dan ma bakomai take yiwa yarinyar ba saboda Rayyan in dai yana gida fiye da rabi da kwata na lokacin shi yana kan Nur dinne, in ba bacci tayi ba ita Layla bata samun kan shi sam. Duk da haka ta sha wahala, tunda in dai aikin safe yakeyi sai ta dafa mishi abinda zai tafi da shi. Wata ukku na farkon cikin ta wahala sosai, yanzun ne ma ta dan samu saukin laulayin. Yau da ya kama asabar zasu je gida ne gabaki dayan su. Basu ma tashi da wuri ba, indomie da kwai ta dafa ma Rayyan din da Nur, ita tana da sauran doyar da sukaci da daddare, ita tayi warming taci. Yanzun ma mai ta shafa ta dauki kayanta tana ficewa daga dakin ta kyale su. Sanda ta dawo ta gama shiryawa tsaf "Ki gyara mata kan, ina takalman ta?" Ya bukata, inda suke Layla bata kalla ba "Magana fa nake yi" Rayyan ya sake fadi da alamar dariya a muryar shi, sarai yasan ta kule, ranta a bace yake. Babu yanda zatayi da shine kawai tunda ya fita rikici, ya kuma fita iya fada. Baisan sau nawa zai gaya mata ta daina ma Nur kitso ba, duka yarinyar yaushe kanta yayi kwarin da za'a kama shi ana mai kitso, ko gashin kirki ma babu, keyar ba komai har yanzun. Kawai salon a saka mata ciwon kai. Ya ce ta dinga shafa mai sai tayi mata kalba ta saka mata hula, kan da za'a rufe in ba rigima ba meye nayi mishi kitso. Sanin Layla ba kula su zatayi ba yasa ya mike yana daukar Nur din, da kan shi ya karasa in da kayanta suke ya samo wata farar hula mai duwatsu a jiki ya saka mata, takalman ma shi ya dauko mata. A shekarun natsuwar da bai taba sanin akwaita ba ita ya samu da auren Layla, rayuwar su bata cike da farin ciki ko da yaushe, suna da nasu matsalolin, amman babu rana daya da zaice baiyi dariya daga dukkan zuciyar shi ba, iya wannan yakan isa ya kori koma menene yayi ma farin cikin shi kutse a ranar, balle kuma Nur da yake jin ita din duka rayuwar shi ce. Akan ta yake jin damuwar da a fuskar Abbu kawai yakan ganta, damuwa ce da iyaye suke ji a lokuttan da yaran su basu da lafiya, a lokuttan da zasu ji kukan yaran nasu batare da sanin me yake damun su ba. Ko faduwa tayi yaga jini duk wani abu da yake kwance a tare da shi saiya ta shi. Yana son Layla, daga baya yasan soyayyar su Ayya, amman son da yake yiwa Nur daban ne, bai san ko dan ita yake gani tana rage mishi kewar Bilal ba, ko rike ta yayi yakan ji wani kusanci da Bilal na ban mamaki. Bai san lokacin da ya daina duba hanyar dawowar Bilal ba, rana daya ya tashi yaji zuciyar shi tayi wani sanyi da yake tare da hakuri, sanyin da yazo mishi da daukar kaddara. Yayi kuka dai ranar, sosai yayi kuka a jikin Layla, kukan da bai bari zuciyar shi tayi mishi ba saboda yana saka ran dawowar Bilal din. Abinda ya zame mishi jiki shine tura kudi a account din Bilal, duk da yana da wani bankin da yake ajiya, duk yanda yaso ya daina saiya kasa, daga safiyar da aka biya albashi zuwa yamma sai ya kasa samun natsuwa idan bai tura ba, a lokutta irin ranar yakan ji daman ace yaga gawar Bilal, da ya dibi kasa ya zuba a kabarin shi, da tuni ya aminta da rashin shi. Amman har abada akwai bangaren shi da ba zai taba daina jin kamar Bilal din yana da rai ba. "Layla ki kira mun Bilya a wayata, ki saka mun a speaker..." Rayyan ya fadi yana gyarawa Nur madaurin takalmin ta "Mota na mun wata kara tun jiya, mutuwa tayi jiya fa a hanya, dakyar ma ta tashi, in munje gida sai yazo ya dauka" Wayar tashi Layla ta dauko can karshen gado "Yaushe screen dinka ya kara fashewa?" Ta bukata "Nur ta fado da ita shekaranjiya" Kai kawai Layla ta girgiza, idan tace ya daina bata wayar shi ba zaiji ba. Tunda yana da kudin sake screen. Tana jin dadin yanda bako da yaushe soyayyar yarinyar take rufe mishi ido ba. Kusan tama fi tsoron shi duk da baya dukanta, yana mata ihun da ba ita ba har Layla sai ta tsorata. "Na ga karamar wayar ka, bayan gado ta fada...mantawa nayi tun jiya... Na saka ta caji tana falo..." Layla ta fadi tana duba contacts din shi, amsa ta yayi hakan yasa ta daga kai ta kalle shi, da yake suna ne ta fara rubutawa ta saka "Bil..." bata karasa ba sai ta kira lambar farko data fito, ta amsa Rayyan ta mayar da hankalin ta kan screen din, zuciyarta na wata irin dokawa. Jikinta har rawa yake lokacin da ta kashe kiran ganin lambar Bilal, wajen kiran ta shiga ta goge kar Rayyan ma ya gani. Kafin ta kira mishi Bilya din, sai da ta fara ringing sannan ta karasa ta mikawa Rayyan din. Mayafin ta, jaka da sauran tarkacen da zasu bukata ta dauka suka fice daga gidan. Sosai suka bata lokaci akan hanya saboda Rayyan yayi kwana ya tsaya siyawa Nur mangoron da tunda ta hango shi ta cikin motar take zillo tana dukan gilashin kamar zata fita ta dauka "Daada...ina so, ina so" Take fadi tana sake maimaitawa "Dan ubanki sai kin fasa mun kunne ne?" Cewar Layla tana juyawa ta harari Nur din da take sake ziro kai tana kiran "Daada" Kamar yanda take cewa Rayyan, duk yanda Layla taso ta gyara mata ya koma "Daddy" taki. Harta hakura ta kyaleta. "Da ni nace ka tsaya a siya mangoro babu surutun da ba zakayi mun ba" Layla ta fadi cikin sigar mitar da Rayyan bai ko kulata ba. Bayan motar ya ajiyewa Nur ledar yana fadin "Karki taba sai munje gidan Ayya sai a wanke a yanka" Kai ta daga mishi tana murmushin jin dadi. Da suka karasa ma, Rayyan bai shigar da motar ba tunda Bilya zai zo ya dauka. Anan kofar gida ya ajiye ta, shi ya fara fita ya bude bayan ya taimakawa Nur yana sauko da ita, ledar mangoron ya dauka, kiciniyar da zata fara yi da shi yasa ya sakar mata yana kallon ta, ganin zata fadi yasa shi karba ya zare guda daya a ciki ya bata ta rungume shi kamar ta rike jariri. Dariya yayi kawai yana rufe motar. Tare suka shiga gidan, Nur na rugawa da gudu ta nufi bangaren Ayya, shi baima karasa ba yaga Bilya na kiran shi, dagawa yayi yana sakawa a kunnen shi "Gani a kofar gida yallabai" Batare da Rayyan ya amsa ba ya sauke wayar daga kunnen shi yana juyawa. A can gefe ya hango Bilya da yana ganin shi ya fara takowa, sake gaisawa sukayi Rayyan ya mika mishi mukullin motar, yana fada mishi abinda yaji tana yi "Dan Allah ka duba min kafin anjima in dai ba wata matsala bace babba" Rayyan ya fadi, saboda gabaki daya satin da zai kama aikin dare gare shi, yafi jin dadi ace da motar shi, gashi yasan halin Bilya, ya iya gyara ga ba ha'inci, amman akwai shiririta. "In shaa Allah zan kiraka dana duba" Sallama suka yi, ya tsaya duba text din MTN da suka cire mishi har naira dari na wani caller tune da bai san lokacin da ya shiga tsarin ba. Karamin tsaki yaja kawai, yana tura musu sakon da zai bashi damar fita daga tsarin, matsalar shi da su kenan. Sai su fara cire maka kudin da babu dalili. Sakon Bappa ya amsa ta manhajar WhatsApp, shima Allah ya kama shi, addu'ar Baba taci, sosai yaso ya sake gudu yabar kasar, yanzun gashi nan da matar shi harda yaro daya. Sai dai yaki garin Kano sam, a Kaduna yayi zaman shi, in dai ya shigo sai dai ziyara, zumunci mai karfi ne a tsakanin su, duk da Rayyan ba zai kira matar Bappan da Layla kawaye ba. Sukan gaisa dai idan sun shigo gari da Bappa din, da ta haihu kuma Layla taje ranar suna ta dawo washegari. Iya wannan din ya ishi su biyun, dan suna zumunci babu inda ya zamana dole matan su ma suyi. Juyawa Rayyan yayi bayan ya saka wayar a aljihun shi, ya kama kofar gidan zai tura kenan yaji kamar iska ta dibo mishi muryar da take cikin kan shi ta fito da ita waje tana dukan kunnuwan shi da muryar "Hamma..." Sai da ya runtsa idanuwan shi kafin ya bude su yana tura kofar "Hamma..." Aka sake kiran shi cikin muryar da wannan karin ba kunnuwan shi kawai ta daka ba, har da zuciyar shi. Idanuwan shi ya sake runtsawa a hankali ya furta "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Saboda ya bawa shekara wajen biyu baya rabon daya shiga cikin wannan yanayin, ba zai koma ba, ba zai koma lokuttan da yake jin kamar takun tafiyar Bilal da baisan yana da sauti ba sai bayan ya rasa shi, ba zai koma lokacin da yake neman fuskar Bilal a cikin duk wani taro da zai gani, a masallacin juma'a, har a wajen jana'iza idan ya samu halarta. Lokuttan da muryoyin mutane da yawa a cikin gidan su take mishi kama da ta Bilal, lokuttan da zai iya rantsewa ba'a cikin kan shi kawai yakan ji muryar Bilal ba. Yana da yarinya yanzun, yana da Nur, zaiyi duk wani kokarin ganin bai rabu da nutsuwar da yake tare da ita ba koya ne. Saboda tana bukatar shi da duka wata natsuwa da yake da ita. Ba yanzun ba kawai, har lokuttan da zasu zo a gaba, lokuttan da ko tunanin su yayi sai kirjin shi ya dauki zafi, tana bukatar tsayayyen uba da zata rugo wajen shi da dukkan tambayoyin da mutane zasu saka tayi mishi, ba zai bari rashin Bilal ya raunana shi ba. Kafar shi ya daga ya saka guda daya a cikin gidan yaji an dafa mishi kafada "Hamma" Wannan karin da rauni muryar ta fito tana tsinka abubuwan da Rayyan bai san suna hade a jikin shi ba, kafin zuciyar shi ta fara dokawa cikin sautin da yake ji har cikin kunnuwan shi, a hankali ya juyo yana fara sauke idanuwan shi kan fuskar Bilal, yawu yake tattarawa yana so ya hadiye ko zai jika makoshin shi da yake ji a bushe, ya bude bakin shi yafi sau biyar yana mayar da shi ya rufe "Hamma ni ne" Bilal ya sake fadi, Rayyan bai yarda ba, ko yaushe zai iya farkawa, wani zai iya zuwa ya tashe shi abinda yake faruwa ya zamana mafarki. Hannun shi ya daga yana kaiwa fuskar Bilal ya taba, ba zai tuna ko ya yanayin Bilal yake a duk mafarkan shi ba, sake taba fuskar yayi, wannan karin samu yayi ya gyara tsayuwar shi ya saka duka hannuwan shi biyu yana taba fuskar Bilal din yana son tabbatar da cewa shine a tsaye a gaban shi ba mafarki yake yi ba "Ni ne, ni ne Hamma" Bilal ya sake fadi muryar shi na karyewa sosai, wani irin numfashi Rayyan yaja yana sauke shi hadi dayin dariya mai sauti, dariyar da ta saka yaji idanuwan shi sun cika taf da hawaye, dariya ce da babu wani nishadi a tare da ita, wani abu yake so ya fadi amman ya kasa "Kace wani abu Hamma... Dan Allah kayi magana" Dariyar Rayyan ya sake yi, yana kai hannuwa ya share kwallar da yake ji a cikin idanuwan shi, juyawa kawai yayi ya tura kofar wannan karin yana shigewa cikin gidan, yana jin Bilal na bin bayan shi, juyawa yayi ya daga mishi hannu cikin alamar da take nuna ya daina bin shi, kafin ya sake juyawa yaci gaba da tafiya, ko hanya baya gani sosai saboda idanuwan shi da suke cike taf da hawaye. Sake juyowa yayi wannan karin duka hannayen shi biyu ya saka ya hankade Bilal din "Hamma" Bilal ya kira yana dafe kirjin shi inda Rayyan din ya hankade yana dorawa da "Kayi hakuri..." Na shi idanuwan cike da hawaye shima, sai da Rayyan ya dan duqa saboda yanda yake jin numfashin shi kamar baya kaiwa kirjin shi, kafin ya mike tsaye sosai yana kallon Bilal "Ba kwanaki ba, ba satika ba, Bilal ba wata daya ba. Shekaru, shekaru fa... Shekaru zaka dora akan kalmar hakuri?" Bayan hannun shi Bilal ya saka yana murza idanuwan shi kafin ya dan daga kafadun shi cikin alamar helplessness, bai san me zai fada ba, baisan ya zaice ba. Abu daya ya sani, har cikin motar Lagos ya shiga, har zama yayi ya kasa, bai zaice ga dalili guda daya ba, amman nisan awannin da suke tsakanin Kano da Lagos ne sukayi mishi yawa, nisa yake so yayi da gida, nisa yake so yayi da kowa saboda laifn shi da yake ji yafi karfin yafuwa. Nisa yaso yayi musu ko zai rage musu zafin laifin da yayi, amman ba nisa mai yawan wannan ba. Yana bukatar ya bude idanuwan shi a duk lokacin da bacci ya dauke shi da sanin cewa suna kusa da shi duk da yayi musu nisa, ko kudin shi bai tsaya an mayar mishi ba, tunda zasu iya siyarwa da wani kujerar, lokacin ana ta saka kaya, jakar shi kawai ya dauka, daman dayar tana goye a bayan shi. Hotel ya kama, wayar shi kasheta yayi, satin shi biyu a hotel din batare daya fito ko ina ba, jinya yayi ba karama ba ta rashin su, ta nisa da gida, ta tunanin halin da kowa zai shiga. Ranar daya fita kuwa sabon sim ya siya ya saka a wayar shi ya adana wancen. Yasan kudi zasu kare mishi, dole yana bukatar neman wata hanya ta samun kudi, sana'ar karfi ce karshen abinda zaiyi, ba zai karya ba in ba dole ta kama mishi ba ba zai iya ba. Bai saba wahala ba, baima san wani abu wahala ba tun tashin shi. Su Abbu sun tabbatar da hakan, unguwannin da ko da wasa bai tabajin su Ayya na kaiwa ziyara ba nan ya fara nufa yana shiga duk wata private school da yaci karo da ita, bai boye musu cewa shi din bashi da takardu ba, amman yayi karatu har zuwa shekarar shi ta karshe, ya dai ce musu matsala ce ta saka shi ajiyewa dole, fiye da makarantu biyar sun so rike shi, musamman bayan sunyi mishi gwaji, amman sai suka so yin amfani da wannan damar ta cewa ba shi da takardu wajen biyan shi kudin da basu taka kara sun karya ba, haka yaci gaba da yawo wajen sati daya, kafin ya samu wata makaranta a cikin rijiyar lemo can wajen layin masallacin espa. Da yake shugaban makarantar musulmi ne, mutum mai matuqar kirki da sanin ya kamata. Har kara ma Bilal din kudi yayi daga baya ganin yana da sani ta bangaren addini, makarantar kuma boko ce hade da islamiyya, sai yake koyarwa a duka bangarorin biyu. Anan cikin rijiyar lemon ya samu karamin gida daki biyu ya kama. Watan daya duba account balance din shi yaje cire kudi yaga sun karu sosai, daga farko ya dauka ko wani yayi kuskuren tura mishi kudi, tunda layin da yake ganin alert yana kasa, amman yakan duba ta email din shi. Hakan yayi, yaga Rayyan ne "Hamma, nauyin zai mun yawa....dan Allah Hamma" Shine kalaman da ya dinga furtawa yana maimaitawa, yayi nisa da sune dan su sami sauki, ba dan ya kara dora musu wata wahala ba. Sai dai ba zaiyi karya ba, kudin suna taimaka mishi sosai da sosai. Ba zaice ya nemi wani abu ya rasa ba, iya cikin shi da abinda ba za'a rasa ba, kudin ya ishe shi har ma yayi mishi yawa. Watanni shidda ya dauka cir kafin mafarkan kowa na gidan ya fara damun shi, rana daya ya wayi gari yaji kewar su ta danne mishi kirji, numfashin kirki ma baya iyawa, shisa ya dauki sim din shi ya saka a wayar, hankalin shi rabi da rabine ko da yaje wajen aiki, ba zai manta uzurin rashin lafiya daya bayar ba ya kama hanyar gida, a hanya ya tsaya ya siyi kati ya saka a layin "Watakila ko dan babu kudi shisa sako ko daya bai shigo ba" Ya fadi a zuciyar shi, har wajen sha biyun dare yana kallon wayar "Kirana kawai zakuyi, zan dawo gida" Tunanin da yakeyi kenan a cikin kan shi har wayewar gari inda ya zare layin daga wayar shi, daga lokacin ne kuma ya sami karamar waya ya siya inda ya saka layin a ciki. Daga ranar kuma ya fara kunna wayar daga safiya zuwa karfe biyu na rana, wani lokacin ma yana kwana bai kashe ba, banda yan MTN babu wanda yake kiran shi, ko sako yaji ya shigo sai zuciyar shi ta doka, sai dai idan ya duba yaga ko bankin shi ko MTN din ne dai. Fushi sukeyi, ya san fushi sukeyi da shi shisa basu kira ba, laifin shi ya so wankewa da karin wani laifin na tafiya, amman bai taba cire rai ba, yasan zasu kira shi, komin dadewa zasu kira. Ba zaice ga yanda yayi shekarun nan batare da su a kusa da shi ba, bai san me ya rike nutsuwar shi har haka ba. Yau din ma kamar kowacce ranar karshen mako, zaune yake bayan ya karya yana marking assignment din yara, sai wasu azuzuwan da test ne yayi musu kasancewar an kusan fara jarabawa yaji karamar wayar shi na ruri, karamin tsaki yaja kawai yana cigaba da abinda yake yi saboda yasan MTN ne, su kadai zasu fara kiran shi kamar suna bin shi bashi. Wutar da aka kawo yasa shi daukar babbar wayar shi da ba wani amfanin kirki yakeyi da ita ba, tunda ya koyi rayuwa babu kafar sada zumunta, abinda bai taba tunanin zai iya yakicewa ba. Sai dai ya iya karfin halin barin su Rayyan ma, ballantana wani whatsapp, hannu ya mika ya dauki karamar wayar ya duba yaga ko akwai sauran caji tunda ya kwana wajen hudu bai sakata a caji ba, latsawa yayi kawai dan sabo yana shiga yaga missed call din da yasaka shi mikewa babu shiri ganin lambar Rayyan da ko a bacci ya ganta zai ganeta. Mukulli kawai ya dauka yana saka takalma a kafafuwan shi, zai iya tuna ya kulle gidan, amman ko mai mashin daya sauke shi a kofar gidan su, hannu kawai ya saka a aljihun shi yana lalubawa ya kuwa samu dari biyu ya mika mishi, zuciyar shi yake ji a tafukan kafafuwan shi a duk takun da yakeyi, shisa yake jin kafafuwan sun mishi wani irin nauyi na ban mamaki. Basu kara nauyin ba sai da ya hango Rayyan, wannan karin tsallen da zuciyar shi tayi a ko ina na jikin shi yake jin dokawar ta, shi da kan shi bai gane muryar shi ba lokacin daya kira Rayyan din, yanzun ma da suke tsaye ji yake kamar mafarki, kamar bashi bane tsaye a gaban Rayyan da yaga kamar bai canza ba a shekarun nan, yana nan yanda ya san shi, sai dai akwai wata natsuwa da yake gani a fuskae Rayyan da bai taba sanin yana da ita ba haka. "Me zance Hamma?" Wannan karin rashin madafar a muryar Bilal ya fito "Baku kirani ba. Hamma kirana kawai zakuyi kamar yau..." Da rashin fahimta Rayyan yake kallon shi, saboda baya gane abinda yake fadi, baya ma gane abinda yake ji balle kuma zantukan Bilal din, wayar shi Bilal ya daga duk da baya tunanin Rayyan yana ganin screen din saboda kankantar wayar "Baku kira ni ba, kai ma baka kira ni ba, ni din mai laifi ne, ban san ya zan nuna fuskata ba baku neme ni ba Hamma" Dariya Rayyan yayi mai sauti yana kallon Bilal din sosai, duk shekarun nan jira yake yi su kira shi kafin ya dawo, sau nawa yana daga wayar shi ya danna lambar Bilal din yayi ta kallon ta, saboda yasan koya kira a rufe zaiji ta, kiran ba zai mishi amfanin komai ba sai karin daga mishi burin cewa bai rasa Bilal din ba, daga baya ma daina dannawa yayi saboda yasan an siyarwa da wani daban lambar, balle harya gwada kira wani ya dauka ya tabbatar mishi da yanda ba Bilal kawai ya rasa ba har lambar wayar shi ma ta tafi. "Ta ya zamu fara kiran ka idan duka muna tunanin ka rasu?" Kallon shi Bilal yayi, saboda maganganun shi sun daki kunnuwan shi da wani yanayi mai wahalar misaltawa "Motar da ka shiga, babu wanda ya fita a motar, da alama kai ka dai ka fita" Kai Bilal yake girgizawa Rayyan "Ta ina zamu kira ka Bilal? Ta ya zaka jira kiran da bamu san kana jira ba? Kiran da banda karfin zuciyar yin shi in sake jin wayarka a kashe..." Kan dai Bilal yake girgiza mishi "Na shiga motar da kuke tunani, amman ban zauna ba, na kasa yin nisa mai tsayin wannan... Ban zauna ba Hamma" Bilal yake fadi cikin tashin hankali, yana jin zuciyar shi kamar zata tsaga kirjin shi ta fito da halin da yake hasaso sun shiga, sanin tafiya yayi daban, amman tunanin ya rasu? Tunanin sun rasa shi gabaki daya, baisan ta inda zai fara hasaso tashin hankalin su ba "Ayya fa?" Ya tambaya, kallon "Sai yanzun tunanin ta yazo maka? Sai yanzun kake tunanin halin da ta shiga? Me yasa kafin ka tafi bakayi tunanin ta ba?" Rayyan yake yi wa Bilal din. Kafin ya dora wasu tambayoyin akan harshen shi yana jifan Bilal da su "Me yasa zaka tafi? Nace ba zan yafe maka ba na sani, amman me yasa zaka tafi? Idan baka duba ni ba, me yasa zaka bar Ayya? Me yasa ka tafi Bilal?" Ba tambayoyin Rayyan bane suka saka hawayen shi zuba, yanayin yanda yayi mishi sune, muryar shi, yanayin da yake kan fuskar shi da cikin idanuwan shi "Hamma..." Kai kawai Rayyan ya girgiza mishi yana juyawa, komai ne yake dawo mishi sabo, duk wani ciwo da yake tunanin lokaci ya dishe mishi zafin shine yake budewa yana dawowa sabo fil, kiran duk da Bilal yake mishi baisa ya juya ba. Amman takun tafiyar Bilal din da yake bin shi a baya jinta yake har cikin zuciyar shi. Kan shi tsaye bangaren Ayya ya wuce, bata ma falon sai Huda da tana ganin shi tace "Hamma, yanzun naga Nur, nace tare kuka zo tayi banza ta kyaleni, ko kallona fa batayi ba ta wuce tana neman Ayya....har..." Maganar da ta dauke mata ya tabbatar wa da Rayyan din cewa ta ga Bilal ne da yake bayan shi, da sauri ta karasa inda Rayyan yake ta kama hannun shi tana girgiza shi, idanuwanta yana kan Bilal, so take ya juya yaga abinda take gani, ya tabbatar mata da yana ganin Bilal din ba ita kadai bace take ganin fatalwa a cikin dakin su, tasan tsoro, amman bata san firgici ba sai yau, muryarta a wahalace ta fito "Hamma... Hamma" Ta ke fadi tana sake girgiza Rayyan daya kama hannuwan ta duka biyun ganin tana shirin shidewa "Na gan shi, ki kalle ni Huda, na gan shi... It's okay...bake ka dai kike ganin shi ba" Rayyan yace yana so ta dauke idanuwan ta daga kan Bilal ta kalle shi, amman kai take girgiza mishi hawayen da yake cikin idanuwan ta yana zubowa "Ayya! Ayya!!" Take kira cikin firgici tana kokarin kwacewa daga rikon da Rayyan yayi mata, amman yaki sakin ta saboda yanda jikinta yake bari zata iya samun matsala idan ya sake ta "Ayya!!!" Huda ta sake kira tana neman taimako daga wajen Ayya "Huda!" Rayyan ya kira, wani irin kuka take tana fitar da numfashi dakyar, lokacin da Ayya ta fito a gigice itama saboda bata taba jin Huda ta kirata cikin yanayin da ta kirata yanzun ba, sam bata kai hankalinta kan Bilal da ganin ta ya saka shi dafa bangon da yake kusa da shi saboda yanda yaji gabaki daya gwiwoyin shi sunyi mishi sanyi "Ayya" Ya kira, amman labban shine kawai suka iya motsawa, sam sauti ko daya bai fito ba, Ayya kuwa Huda ta kama daga hannun Rayyan "Me ya faru? Lafiya? Me ya faru?" Take tambayar Huda din, tana karasa tambayar hadi da kallon Rayyan daya sauke idanuwan shi daga cikin nata "Ayya..." Huda ta kira cikin sabon tashin hankali tana juyawa, yanayin da yasa Ayya kallon inda ta kalla, tana ganin Bilal, runtsa idanuwan tayi tana sake bude su hadi da jin kamar wani ya watsa mata ruwan kankara saboda tsikar jikinta da ta mike gabaki daya, wani irin yanayi ne da babu kalaman da zasu misalta shi, dole Huda zata firgice, ta sha hasaso ganin Bilal, ba'a mafarki ba a ido biyu, amman da gaske ne, girman kusanci ba zai taba hanaka tsorata ba idan har zakaci karo da mutumin da kasan mutuwa ta rabaku, saboda wani irin tsoro ne kamar bargo ya nannade daga kafafuwanta har zuwa kanta kafin ya sami wajen zama a cikin zuciyar ta. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya) 1/30/21, 8:09 PM - 111: Jan 30, 2021. 34 "Ayya..." Bilal ya kira yana sa ta raba idanuwanta da inda yake tsaye tana kallon Rayyan daya daga mata kai yana tabbatar mata da yaji kiran, ba kunnuwanta bane kawai suka ji cewa Bilal ba tsaye kawai yake a cikin dakin ba, har magana yakeyi. Hankalinta ta sake mayarwa kan shi tana ganin yanda yake takawa yana karasawa inda take kamar wanda yake koyon tafiya, da duk takun da zaiyi da yanda zuciyarta take kara dokawa a cikin kirjinta da wani irin tsoro, sai dai kamar jira kawai yake ya karasa inda take kafafuwan shi su kasa daukar shi dan anan gabanta ya durkushe. Yayi kuka mai yawa bayan da ya tafi, amman baiji kalar kukan da yake tattarowa daga duk wani lungu na zuciyar shi daya taba yin ciwo ba irin yanzun. Dan wani irin gunji ya saki mai tsuma zuciya yana rike kafafuwan Ayya da itama taji sunyi mata wani sanyi, Huda ta ture gefe, ba tsugunna tayi ba, zama tayi akan kafafuwan ta kamar mai zaman sallah tana kallon Bilal, ya sha bamban da fatalwin da take gani a fina-finai, jikin su baiyi kalar na shi ba, batajin kuma ana iya jiyo hucin numfashin su, a hankali ta daga hannunta da kafin ta kai shi fuskar Bilal ya kama shi da duka nashi biyun. Ko da fatalwa ne shi na danta ne, Bilal ne. Hannun shi na shine, hannu ne daya saba kama nata tun kafin yakai girman haka. Duk da yanzun girman bai canza yanayin shi ba, zata gane hannun Bilal a cikin dubban hannaye, saboda zai rike nata hannun kamar yanda ya rike shi yanzun, cike da yarda da kaunar shi da batajin wani da bai san zafin da ba zai iya fahimta. "Bilal" Ayya ta kira yana daga mata kai kawai saboda kukan da yake yi, abu na farko da duk wata mahaifiya takeyi a lokacin da take ganin hawayen da na ita bace sanadin zubar su shi Ayya tayi, zame hannun daga cikin na Bilal ta kama shi zuwa jikinta duk kuwa da girman shi, kan shi ya dora a jikinta yana sake sakin wani sabon kukan, kukane na kewar ta, na kewar su gabaki daya, kukane na ban hakuri, kukane na abubuwa da yawa. Ba zaice ga lokacin daya dauka a haka ba, amman bai dago ba sai da yaji zuciyar shi ta daina nauyin da take mishi tukunna ya dago yana kallonta, ita yau ta nemi inda hawaye suke ta rasa, da kansu sun san cewa yanayin da take ciki sun girme su. "Bana cikin motar Ayya, ban shiga ba, bana ciki" Sune kalaman da suka zo ma Bilal, kallon shi Ayya takeyi, kallon shi take saboda bata taba saka ran sake ganin shi ba, kallon shi takeyi kaunar shi da babu inda taje mata tana tasowa tana kuma shafe duk wani bangarori na zuciyar ta daya hakura da shi, bangarorin da sukayi jinyar rashin shi, hannuwan shi ta kama tana saka fuskarta a ciki hadi da sauke wata irin ajiyar zuciya da ta budewa hawayenta waje, wannan karin ita ta kwantar da kanta a jikin Bilal, kukan ta yana sake fito mishi da sababbin hawaye "Kaga me kayi ko Bilal? Kaga me tafiyar ka tayi mana?" Rayyan yake fadi yana kifta idanuwa saboda baya son ya fara kuka, yanajin su duka ba kuka sukeyi ba, idan ya fara ba zaiji lallashi ba "Daada" Nur da ta fito ta kira Rayyan din, da gudu take tahowa tana saka zuciyar shi mantawa da komai da yake faruwa saboda yanda take dokawa da tsoron karta fadi, bai sami natsuwa ba sai da yaga ta zagayo ta kama kafafuwan shi kamar ta dade bata gan shi ba, ko daki ya shiga tana wani dakin, idan ya fito haka take barin duk abinda takeyi ta tashi ta rugo ta rike shi kamar yayi wata tafiya mai nisa, sai yaji ta nutsar da shi, ta saka zuciyar shi wani irin sanyi. Ganin ta dago daga jikin shi tana kallon Bilal yasa shi kallon Bilal din shima. Sosai Nur take kallon Bilal kamar ta san shi. Abinda kafin psychology yayi mishi bayanin shi yake ganin tsakanin Ayya da Bilal, tsakaninta da sauran yan gidan shi yake gani tsakanin Nur da Bilal da har lokacin baima kula da ita ba. Hankalin shi gabaki daya yana kan Ayya da ta dago tana saka hannunta ta goge fuskarta da shi. Shima Bilal tashi fuskar yake gogewa, hakuri yake so ya bata, amman kalaman sunki fitowa. Ko da Nur bata kai haka ba, sam yarinyar batayi qwiya ba, kowa ya dauketa zuwa takeyi, gashi bata tsoron mutane, kawai magana ce batayi sosai "Yarinyar nan ko dai kurma ce Hamma?" Layla ta tambaye shi, yayi dariya sosai ranar, har yanzun ko shi kadai ya tuna sai yayi dariya "Allah da gaske nakeyi fa, ko irin wakar nan ta yara Nur batayi sam, in ba kuka take ba bakajin sautin komai" Kai kawai ya girgiza saboda dariya da ta hana shi magana, shi yanajin wakar da take magana, ba ko yaushe ba, haka ta dade bata fara magana ba, da ta fara din ma ba sosai ba, duk rashin surutun shi yana iya ba Nur labari har ya gama yanayin fuskarta ne kawai zai nuna tana jin shi, ko in abin amsawa ne ta daga mishi kai. Ko kayan wasa tafi son wanda suke kamar bulalluka tayi ta hadawa, sai kuma puzzle da zata zazzage ta yini tana shiryawa, shisa yanzun ma baya tarkato mata komai sai kalaluwan su. Yar tsana da teddy duk inda ka ajiye nan zaka dawo ka dauka, bata so, in ya tare mata hanya zata dauka tayi cilli da shi gefe. Yanzun ma Rayyan ta kalla, kamar tana son ya bata izini ne bai fahimta ba, ya dai daga mata kai, sannan ta juya, hannunta daya rike da rigar Rayyan, dayan kuma mika shi tayi tana bubbuga bayan Bilal da yana juyowa ta kara matsawa tana shigewa jikin Rayyan, kallonta Bilal yakeyi, itama kallon shi takeyi. Zuciyar shi ta gama shan duk wani mamaki na duniya, watakila shisa yaji ta natsu waje daya yanzun. Rayyan ya kalla yana neman tabbaci,kai Rayyan ya daga mishi "Maimunatu... Nur" Rayyan ya furta a hankali, yaso ya dora da "Bamu ka dai ka bari ba har da ita, ka rasa abubuwa da yawa Bilal" Amman sai ya kasa, yanayin da yake fuskar Bilal din ya saka shi ya kasa cewa komai. Nur ya rankwafa ya dauka yana sabata a kafadar shi ya raba su ya wuce, cikin dakin ya shiga sosai ya samu kujera ya zauna tare da Nur a jikin shi. Banda Huda data bar falon, daga Ayya har Bilal nan inda suke suka zauna, da alama babu wanda ya iya motsa. Rayyan bai musu magana ba, asalima Nur ya tashi yabi da taja hannun shi, mangwaronta ta dauko ya kamata zuwa kitchen ya wanke ya dauki wuka da filet, yayyanka mata yayi ya bata ta fita falo taje ta zauna. Shikam jin ana kiran sallah yasa shi shiga dakin Ayya ya dauro alwala ya fito "Idan zakayi sallah ka tashi kayi alwala mu tafi masallaci..." Juya kai Bilal yayi yana kallon Rayyan din "Zan taho yanzun..." Sosai Rayyan ya kalle shi "Baka da hankali ne halan? Baka da 'yancin fita kai kadai, idan na tafi sai dai kayi sallah a gida" Murmushi Bilal yayi cikin yanayin daya manta rabon da yayi shi "Babu inda zanje Hamma" Kai Rayyan ya girgiza "Na manta yanda yarda da kai take, zai dauki lokaci kafin ta dawo, ka tashi" Bai musu ba ya samu ya mike, yanajin jikin shi a wani irin mace, alwalar yaje ya dauro shima yana fitowa "Daada..." Nur ta kira cike da alamun tambaya "Masallaci zanje Nur, yanzun zan dawo kinji?" Sai da ta daga mishi kai sannan ya kalli Bilal da idanuwan shi suke kan Nur din, kallonta yake yana rasa abinda yake ji akan ta, saboda kaunarta ko akwaita baisan inda ta labe ba, ciwon da samunta ya haifar mishi kawai yake ji, ciwon da bata da laifin shi, tabon da sukayi wa rayuwar ta yake gani a tare da yarinyar "Ki yafe mun, ki yafe mun kafin mu tsaya dake a gaban Allah, wallahi bani da hujja" Ya furta can kasan zuciyar shi, kafafuwan shi na daukar shi dakyar lokacin da suka fita masallaci, ga wani tsoro da yake ji har ran shi. Gidan bai sake rudewa ba sai bayan da suka dawo sallah, saboda lokacin duk yan gidan sun zo, da yake asabar ne, yawanci har masu auren idan basu zo da matan su ba suna zuwa su kadai, haka matan gidan ma, su Zubaida suna zuwa, kusan duk asabar din duniya da wahala kaga basu hadu a gidan ba, dan Rukayya sun dade akanta kafin ta dawo hayyacin ta, tana ganin Bilal din ta mike, sulalewa tayi gabaki daya, ga ciki da yake jikinta. Gabaki daya Bilal a rude yake jin shi "Kuyi hakuri, dan Allah kuyi hakuri" Shine abinda yake furtawa yana sake maimaitawa yana wani irin kuka da daga baya su suka koma suna lallashin shi. Layla itama sai da Rayyan ya riketa, duk kuwa kunyar da daga ita har shi basu san suna da ita ba sai bayan auren su, dan kujera ma in suka zauna a cikin gidan ko babu kowa sai sun dan bada tazara a tsakanin su. Ranar kuwa da ya rike hannunta ta yana daura mata agogo sun zo gidan zasu tafi saboda tana rike da Nur, sai ta rike agogon a hannu, sai ga Abbu ya fito sakin agogon yayi har ya fashe, saboda kunyar da yaji, ita kanta Layla kasa hada idanuwa tayi da Abbun. Murmushi yayi kawai ya rabasu ya wuce. Amman yau gaban kowa ya riketa har kitchen ya jata ya dibi ruwa ya bata "Ki rufa mun asiri Layla, babyna a jikin ki, dan Allah ki natsu" Yake fadi, amman bata san yanda zata fara natsuwa ba, sai da ya kamata yana riketa a jikin shi, tafi mintina goma kafin numfashin ta ya dai-daita, sannan ta iya raba jikinta dana Rayyan, suka samu suka baro kitchen din zuwa falo, kan kujera suka samu suka zauna. Banda ajiyar zuciya babu abinda take saukewa, ganin Bilal din ya nutsar da wani shimfidadden kalubale da take hangowa a gaba, ko ba komai tambayoyin da Nur zatayi mata wata rana ba ita kadai zata yiwa ba, yanzun addu'a takeyi Allah ya bama Bilal aron tsayin kwanaki tare da su, saboda ganin shi ya tuna mata akwai tambayoyin da koya Rayyan zai rike hannunta ba zai isa ba. Sam Bilal da Rayyan basu samu wani lokaci su kadai ba sai da dare, sai bayan isha'i, sannan, kallon shi Bilal yake yi, amman maganganun Abbu suke dawo mishi "Da yana nisa da iyayen shi haka Bilal?" A idanuwan su yake ganin yanda bai kyauta ba, yayi tunanin su kafin ya tafi, amman tunanin kan shi yafi yawa, ba zai iya fuskantar su ba shisa ya zabi ya gudu. Amman gudun nashi bai canza komai ba, bai rage musu ciwo ba kamar yanda yayi tunani, asalima ya kara musu wani ciwon ne na daban "Hamma kace wani abu" Bilal ya bukata, saboda shirun yayi mishi yawa "Me zance? Bani da wasu kalamai" Numfasawa Bilal yayi "Kace ka yafe mun" Dan juyawa Rayyan yayi yana kallon shi, ba yafe mishi bane baiyi ba, ko da bai yafe mishi ba, dawowar da yayi ta wanke komai, amman ba zai fada mishi yaji ba dan yanzun, ya jira kamar yanda ya saka shi jiran shi duk tsayin shekarun nan. "Da kana son ji da baka dade har haka ba" Kai Bilal ya jinjina, yana son ji, zai jira duk lokacin da hakan zai dauka, zai jira, zai kuma nunama Rayyan din da gaske yakeyi ya dawo. Babu inda zaije, yana kallo Rayyan ya mike, Nur da tayi bacci akan kujera ya dauka yana sabata a kafadar shi kafin ya kalli Bilal "Karka bar gidan nan, da gaske nakeyi Bilal, ko ina zakaje ka jira sai gobe idan Allah ya kaimu, ka jirani sai gobe mu tafi tare" Kai Bilal din ya jinjina mishi kawai, yana hada idanuwa da shi, dan baisan kome Rayyan din yake nema a cikin idanuwan shi ba "Ka rantse mun babu inda zakaje" Saboda a tsorace yake, ji yake kamar kar su koma su kwana a gidan yasa ido akan Bilal din karya sake tafiya "Ba inda zanje Hamma, babu inda zanje. Ka yarda dani, babu inda zani" Numfashi Rayyan ya sauke yana wucewa ba dan zuciyar shi ta so ba. Bangaren Mami yaje yana yiwa Layla magana ta fito su tafi gida. Da yake Bilya ya dawo mishi da motar shi, ko kudin shima bai tura mishi ba saboda bashi da wadatacciyar natsuwa, sai dai inya isa gida tukunna sai ya samu yayi mishi transfer, kafin su karasa kira biyu yayi wa Bilal duk idan ya daga amsa daya yake bashi "Ba inda zanje Hamma, ina nan" Har sai da Layla ta dafa shi sannan ya sauke numfashi "Ka yarda da shi ko yayane, babu inda zaije. Wannan karin ko da zaka rasa shi, rashin zaizo maka da tabbaci, ba zaka kwanta da rashin natsuwa ba saboda in shaa Allah" Kai kawai ya iya dagawa Layla, saboda a zantukan akwai tunatarwa, dawowar Bilal baya nufin mutuwa idan ta tashi zata tsallake shi, a yanzun din ma zai iya sake rasa shi, amman duk firgicin da kalaman ta suka sake jefa shi sun zo mishi da wata natsuwa da ba zata misaltu ba, addu'a yakeyi ko da zai sake rasa Bilal din ya samu damar da ko bashi zai suturta gawar shi ba ya halarci jana'iza, ya ga ya binne shi, yayi mishi bankwana, sai ya dawo yayi jira hakurin da yake saukarwa kowanne bawa a yayin rashi, ya kuma shiryawa tashi mutuwar, tunda babu wanda zai tsallake, babu wanda zata bari, kowa cikar lokaci yake jira. *** Hutun da baisan yana bukata ba shi yayi, satika biyun da basu dai-dai ta mishi komai ba, amman sun nutsar da rayuwar shi, sun dawo mishi da abinda ya rasa, sun dawo mishi da yan uwan shi. Duk da har yanzun Ayya bata daina kallon shi kamar zai sake tafiya ba. Ko sun gaisa da asuba idan takwas tayi bai sake fitowa ba sai ta kira wayar shi taji ko lafiya. Da yake satin farko yaci gaba da zuwa aiki dan karamcin da mai makarantar ya nuna mishi, sai ya tsaya har sati daya ya bashi damar neman replacement kafin ya dawo, sai lokacin sukaje da Rayyan ya tattara duka yan kayan shi da suke gidan da yake haya. Daman saura wata daya kudin shekarar ya kare, mukulli kawai ya kaiwa mai gidan. Yau kam tsaye yake kofar gidan su Aisha yana neman kwarin gwiwar shiga cikin gidan. Dakyar ya iya kwankwasa maigadi ya bude mishi, kallon Bilal yakeyi yana mamakin inda ya shiga a duk tsayin shekarun, gaishe da shi Bilal yayi yana wucewa harabar gidan, zufa har cikin tafukan hannayen shi yake jinta. Ba tunaninta bane baiyi, sosai take fado mishi. Ko bayan ya dawo dinma tana ran shi, yana tunanin inda rayuwa ta kaita, kasa hakuri yayi yace ma Rayyan "Aisha tayi aure na sani... Tayi aure yanzun" Tafiyar shi ta saka ya rasa abubuwa da dama, bayajin wata zata so shi yanda Aisha taso shi. Ya rasa shekaru uku a tare da su, baiga auren da yawa daga cikin yan uwan shi ba, baya cikin hotunan su da rayuwar da sukayi a shekarun, ya kuma rasa Aisha, kai Rayyan ya girgiza mishi "Bana so in maka magana baka shirya ba. In ba a watan nan tayi aure ba tana nan, naganta a gidan mai last month" Dan ba zai manta bayan sun gaisa ba, shi duk daburcewa yayi da yaji ta tace, yana zaune cikin mota, ya juyo ya ganta "Hamma" Saukowa yayi, da suka gaisa saiya rasa abinda zaice mata, kamanninta suna nan, amman ba yarinyar da yasani bace, ba budurwar Bilal din shi da take yi musu girki bace a makaranta, wannan ta girma, ta zama cikakkiyar budurwa, idan sa'anni daya suke da Layla ba zata shige shekaru ashirin da biyar zuwa da shida ba yanzun. Ba kamar sanda ya santa tana sha wani abu ba. Haka kawai ya tsinci kan shi da son tambayar ko tayi aure, sai ya kasa, bakin shi yayi mishi nauyi, dan yana jiran Bilal ba shida tabbas din zai dawo, baiga dalilin da zaisa yayi mata tambayar ba, amman ga mamakin shi dariya tayi a nutse "Banyi aure ba Hamma, ban dade da gama bautar kasa ba..." Kai ya jinjina mata, labarin yayi mishi dadin ji, sallama sukayi da sakon ta na ya gaishe da Layla "Ka dauki kafafuwan ka kaje kafin ka rasata gabaki daya" Shine abinda Rayyan ya fada mishi "Kana tunanin zata so ni har yanzun? Ni din bani da komai da zan bata, ga Nur kuma..." Kallon shi Rayyan yayi "Kana da zuciyar ka, ni bansan me zance maka ba, ban iya kalamai kamar Abbu ba, idan kana tunanin makaranta ne na fada maka ina sake tsayar maka duk shekara, zaka iya cigaba sanda ka shirya. Zaka iya fara zuwa kasuwa kasani in ka fadama Abbu, zaka samu sana'ar da zaka iya rike mata..." Sauraren Rayyan yakeyi "Nur ba zata hana komai ba in dai tana son ka har yanzun, zata fahimce ka, kuskuren ka a wajen Allah ma mai yafuwa ne balle kuma mutum, rashin ta ne idan bata fahimta ba, sai ka hakura, sai ku hakura da juna. Amman kaje, ko ba komai ta cancanci kayi mata bayani" Numfashi ya sauke yana sake kallon Rayyan daya dakuna mishi fuska "Na gaji da magana Bilal, bansan me zan kara ce maka ba" Dariya yayi, kamar yanda yayi murmushi yanzun duk kuwa da yanda yake jin zuciyar shi na mishi rawa. Wayar shi ya zaro daga aljihun shi yana kiran lambarta, sai da ta kusa yankewa sannan aka daga "Aisha" Ya fadi yana jin yanda take fitar da numfashi daga dayan bangaren "Nawan?" Ta kira cike da shakku da tsoron da yake karanta a yanda muryarta take rawa. "Ni ne Aisha, ina cikin gidan ku..." Jin yanda take fitar da numfashi yasa shi dorawa da "Ban rasu ba, bana cikin motar da ake tunani, bana ciki Aisha" Daina jin ko motsinta ta dayan bangaren da yayine ya saka shi sauke wayar daga kunnen shi, mintina ya bata ta tattara nutsuwar kafin ya sake kira har sau biyu, amman ba'a daga ba "Ki daga dan Allah, Aisha ki daga" Yake fadi yana sake kiranta, da yake kan shi na duke yana kallon wayar baisan ta karaso ba "Nawan" Ta fadi tana saka shi dagowa yana kallon ta, tunda yake da ita yaune karo na biyu da take tsaye a gaban shi babu hijabi, na farkon kuma a asibiti ne. Ko takalma babu a kafafunta, shisa baiji takun tafiyarta ba "Nawan..." Ta kira wannan karin muryarta na karyewa, kai yake iya daga mata, kafin yayi wani motsin kirki ta hade space din da yake tsakanin su, a jikin shi ya jita, ba haramcin hakan bane tashin hankalin shi, asalima so yake ya zagaya hannuwan shi ya riketa a karo na farko a jikin shi ko dan kewarta da yake ji a ko ina na jikin shi. Amman a cikin gidan su yake, baida idon da zai kalli wani na gidan su idan ya fito ya gansu a haka. Shisa ya kamata yana dago ta daga jikin shi "Ki rufamun asiri Aisha, laifina mai yawane har a idanuwan yan gidan ku, kar ki mu kara musu dalilin da zasu hana mun ke" Hannu tasa tana goge hawayen da ta rasa ta inda zata fara tsayar da su. Duk yanda Bilal yaso ta koma gida ta dauko takalma da hijabi kiya tayi, haka ya hakura ya kyaleta, anan suka tsaya yana rasa ta inda zai fara yi mata bayani. Sai ya zabi yaji yanda take a maimakon bayani "Ban sani ba Nawan, ban san ya nake ba, amman na san komai zai dai-daita tunda ka dawo kafin a hadani aure da wanda bana jin soyayyar shi ko kadan a cikin zuciyata" Hira sukayi, hirar duk da tazo musu ita sukeyi, dakyar ya iya barinta da tarin alkawurran da yake fatan cikawa. Bai mata bayanin komai ba sai da yaje gida, har aka kira asuba suna manne da juna a waya. A washegarin ranar ya samu Abbu da maganar aje gidan su Aisha, bai musa mishi ba kuwa, da yake itama Aisha ta samu Baban nata da cewar za'a zo a gan shi. Ana isha'i su Abbu sukaje gidan. Bilal da yake gida ya kasa zaune ya kasa tsaye yana jiran dawowar su, sai kiran Aisha yakeyi sai tace mishi "Ba su tafi ba har yanzun, ban san me suke cewa ba, bana jiyo su daga inda nake. Nawan ba zan iya sake rasaka ba, bana jin zan dawo dai-dai wannan karin" Bashi da kalaman bata tabbaci idan ba dawowar su Abbu ya gani ba, shisa yake fada mata na shi tsoron. Saboda da gaske ne, babu macen da zata so shi kamar ita. Su Abbu kam da albishir din an bashi Aisha din suka dawo mishi "Kaddarar su mai girma ce, ni ba zan hana Bilal ita ba, ba zan hana shi Aisha ba. Allah ya san dalilin da ya sake hada su" Sune kalaman Baban Aisha, shisa Abbu bai boye mishi komai ba har da kaddarar rabon Nur, da yake mutane ne masu dattako da wadataccen ilimin addini daya fadada fahimtar su, hakan bai zame musu matsala ba. Baban Aisha ya jima yana juyayin kaddara irin ta yaran. Bilal kasa hakuri yayi, motar Ayya ya ara yana zuwa gidan Rayyan dan bayason ya fada mishi a waya, ya fi so ya gan shi ido da ido "Hamma an bani Aisha, an bani ita" Shine kalaman shi na farko bayan ya shiga gidan Rayyan din "Shine ba zaka yi sallama ba" Dariya kawai yayi yana yin sallamar ya karasa cikin falon ya zauna. "Zan fara zuwa kasuwa, ina son samun abinda zan rike Aisha da shi, makaranta ta jirani na tsayin lokacin nan, zata kara jira shekara daya idan Allah ya aramun lokacin" Kai Rayyan ya jinjina mishi yana murmushi, dadi yake ji ganin farin cikin da yake shimfide akan fuskar Bilal din, muryar shi can kasan makoshi lokacin daya kalli Bilal yace "Ba zan baka Nur ba, ba zan baka ita ba Bilal... Yarinyata ce" Da bayanannen mamaki Bilal yake kallon Rayyan din, ko na rana daya tunanin yarinyar a matsayin tashi duk da daga jikin shi ta fita bai taba je mishi ba. Ya dauke ta sau daya, ya riketa a jikin shi, yanda yaji kaunarta sai da ya tsorata, bai kuma sake daukarta ba. Duka gani nawa ma yayi mata tun dawowar shi, baisan me yasa Rayyan zaiyi wannan tunanij ba, baya nan shekaru uku da suka wuce, ko yana nan ma bashi da zuciyar kiranta tashi. "Hamma..." Ya iya kira kawai, yana ganin Rayyan yaja wani numfashi yana fitarwa a hankali, ya fadane saboda ya tabbatar, saboda a tsorace yake, tsoron shi ya karu da yaji Bilal din yana maganar yanda rayuwar zata karasa nutsar mishi, kamar Nur tasan maganarta sukeyi ta fito, tana ganin Bilal ta tsaya tana kallon shi "Kawu" Ta fadi, murmushi Bilal yayi mata, Rayyan ya mika mata hannun shi ta karaso ta kama, daukar ta yayi ya dora akan kujera a gefen shi, sai da ya sumbaci hannunta sannan ya sake shi, yana lumshe idanuwan shi da taja kafafuwanta ta dora akan kujera tana kwanciya a jikin shi, kafin ya bude su akan Bilal da yake kallon su da murmushi a fuskar shi. "Kawu..." Rayyan ya maimaita sunayin dariya gabaki dayan su. Duka sauran Uncle take kiran su da shi, da gangan Rayyan din yake nuna mata hotunan Jabir yana kiran shi da Kawu. "Kasan Jabir kawai take kira da Kawu" Ware idanuwa Bilal yayi, Rayyan ya jinjina mishi kai yana dariya. Ranar farko da ta kalli Jabir tace "Kawu" Sai da ya matsa ya fara kalle-kalle yana neman wanda ta kira da Kawu "Da kai take" Haris yace mishi, cikin tashin hankali Jabir din yake kallon su "Nur ya sunana?" Ya tambaya "Kawu" Ta maimaita tana saka Jabir fadin "La hawla wala quwwata ila billah, wai me yasa? Wa taji ya fada? Me yasa take cemun Kawu saboda Allah?" Dariya suka dinga mishi, har Abbu saida yayi, dan wani lokaci yakan tsokane shi yace "Kawu Jabir" Sai dai yace "Haba Abbu...idan kuna fada ba zata daina ba wallahi" Hira suke a nutse suna dariya, wanda duk zai gan su zaiyi tunanin basu da wata damuwa a fadin duniya gabaki daya, zai tunanin basu taba sanin matsala ba, kuma ba haka bane ba, matsala kan tsaida komai, amman zabin kane kayi farin ciki koya yake da yakinin cewa babu wata damuwa da take dawamammiya, da kuma sanin cewa ikon komai ba a hannun ka yake ba, addu'a ce kawai kake da ita, addu'a fa take da karfin sauya kaddarar da take a rubuce tun kafin samuwar ka, shisa suke dariya duk da sanin ko da sun kwanta yau ba lallai su tashi gobe ba, idan sun tashi babu wani tabbaci na ranar zata zo musu da daidaito, amman suna da junan su, komai zai zo da sauki. * ALHAMDULILLAH!!! Ina godiya ga tarin mutanen da basa gajiya da nuna mun kaunar su ta hanyar siyan littafina, bina da fatan alkhairi da addu'o'i. Allah ya saka da alkhairi ya biya muku dukkan bukatun. Allah kuma ya yafe kuskuren mu yayi mana Rahma. Amin thumma amin Ma'assalam. * Littafina na siyarwa ne akan naira #300 Account details 3029530320 Lubabatu Sufyan Polaris Bank Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)