HADA DOCUMNTS BY ESHAAT SMILER HOM OF HAUSA AND ENGLISH NOVELS @ WASAPP 08066360176 BAKIN CIKI 1***1 Sarautar Uban dawaki babbar sarauta ce a garin fandagori can cikin jihar naija. Babban gari ne wanda al'ummar cikinsa suka bunkasa wajen noma da kiwo. Gidan uban dwk Alh Awaisu Malami katafaren gida ne cike da zuri'a masu yawa na kannensa guda 2 kuma shine babbansu kat! Sassan sa yafi na kowa girma da tsari ginin zamani. Matarsa daya Haj Halima da yaya maza uku a jere. Abdulkadeer, Abdulkareem da Abdulrahman sai kandensu "ya mace tilo a cikinsu Sakina, sunan mahaifiyar uban dwk gareta shiyasa suke kiranta "Mama". Santaleliyar yarinya wacce Allah yayiwa sura tamkar ita tayi kanta kusan zuri'ar gidan haka suke da kyau na fulani. Amma ita mama ta fita daban wajen cikar sura daka gganta dole gabanka ya fadi sbd tsabar kyau. Shiyasa tun shekarunta basu kai ko'ina ba samari suka yanyameta kowa na so, musamman cikin gidansu watau yan'uwanta abin har yana so ya zama rigima a tsakaninsu. Saida Uban dwk da kansa ya tara su ya soke maganr soyayya da Mama ya kuma kar wanda ya kara kiranta da sunan tadi. Yayi haka ne don a sami masalaha da zaman lfy. Allah kuwa ya taimaka kowa ya gama bacin ransa ya hakura. Baya ga haka yana ganin Sakeena bata kai shekarun da zata tsoma kanta kogin soyayya ba alhali tana tsaka da karatunta mafarin kenan da zata tafi babbar sakandire yayi kokari ya samar mata makarantar kwana ta yanmata dake bakori (FGGC Bakori) Sannan hankalinsa ya kwanta amma wann hukunci nasa yayiwa wasu daga cikin iyaye mata ciwo har suna ganin sbd kyaun da Mama take dashi ne yasa ake wulakanta yayansu suka rinka ganin kamar suna sn su dauki dogon buri ne su dora mata. Tabbas uban dwk nada buri akan yarsa tilo mace saidai yasha bamban da irin burin da matan gidan ke nufin ciki zukatansu wanda bazai wuce ya aurar da ita ga hamshakin me kudi ba ko basarake. Shi burinsa yarsa tayi zurfin karatu kamar sauran yayyinta maza wadanda a halin yanzu Abdulkadeer major nr na soja, Abdulkareem accountant ne a CBN, sai Abdulrahman dake NYSC a Jalingo. Ya kuwa lashi takobin ko bashi da rai yan'uwanta su cika masa wann buri nasa. Kwanci tashi Mama ta shiga SS2 kuma yau sukayi hutun 2nd term tun safe Uban dwk ya tura drivernsa ya daukota, basu iso fandagori ba sai bayan la'sar kowa na ta murna musamman yara da suka yanyameta suka kwashe mata kaya zuwa sassansu. Ta shigo da sallama Ummanta ta tarbeta ta rungumeta, ta shiga sauran sassan ta gaishesu, Salisu da Danlami kadai ta samu acikin samarin sassan. Ta zauna suka taba yar hirar skul sannn ta tashi koma sassansu tana shiga ummanta tace Abbanki na nan ya dawo ta wuce da sauri ta sameshi a falonsa, bakinta har kunne ta dan rankwafa tace Allah ya taimaki mai martaba! Fara'arsa ta karu: Allah yabar min Mamana na shigo akace kin shiga sassa. Ta zube gabansa tace eh naje gaishesu ne, ina yini Abba? Lfy lau ya karatu? To mungode Allah, yace ina report sheet a kawo na gani. Ta mike taje ta kwaso duk takardun yayi ta dubawa yana fadin da kyau! Bayan ta kammala ya dubeta kinyi kokari sosai Mamana na baya miki amma har yanzu kina da yar matsala a biology sai kin kara bada himma kinsan dalili? Ta kada kai yace kara matsowa kiji ta matso kusa dashi sosai kafin yace: buri na ki zama likita Mamana, sbd a rayuwa ta ina sha'awar in ga ya mace likita, abin yana burgeni kwarai, shiyasa tun ranar da Allah ya bani ke nake ta addu'ar Allah ya raya minke in samu in cika burina, ko kuwa ke bakya sha'awa? Tace sosai ma nakeson zama likita Abbana. Kuma I.S.A zan kara himma don ganin na gama da biology. Ya dafa kanta cike da farin ciki yace yauwa Mamana, Allah yai miki albarka tace ameen Abbana. Daga nan suka ci gaba da hirarsu saida akayi sallama dashi ya tashi ya shiga babban zaure inda Majalisarsa ke taruwa. Mamana ta koma gurin Ummanta a kicin suna aikin abinci tana bata labarin abnd Abbanta yace, Umma tace yallabai kenan Allah dai ya cika masa wann buri nasa tace I.S.A Umma saina zama likita. Tace Allah ya yarda wai waya gane min Mama da farafen kayan nan? Mama tana dariya tace na dan ratayo wann abun da suke sawa a kunne ina takawa ana ga Dr Sakeena nan zuwa. Suka fashe da dariya. Washegari misalin 10:am Mama ta fesa ado da koriyar atamfa sannn ta dora after dress ta yafa mayafinta ta sami Umma a daki, sai ina? Zani gaida Inna saude ne. A'a kice dai zaki gun Baraka. Tayi dan murmushi Umma ai duk dayane Idan na gaida Inna ta sai muyi hira da Baraka kawata... Uhummmn... To kodai lauya zaki zama a fasa likitan nan? Tayi dariya wai kinaso ki hada ni da Abba kenan.. Lallai kam to kice ina gaida Sauden idan ta gama dinkunan ta baki kizo min dasu, shikenan amma ina fata akwai nawa aciki. Umma tace babu naki aciki duk nawa ne, Mama ta dan kirne fuska kai umma ai kuwa zan zabi daya aciki, tace duk zannuwa ne ciki da alakum rigunan kuma masu hannu ne, zan canja style ni inaso a haka, to ban yarda ba ki anso min kayana kawai idan ta gama. Ta jinjina kai shikenan umma nina tafi, adawo lfy karki dade... Ta saba jakarta tana fadin to Umma.. Salis ne zaune a kofar gida tana fitowa ya kare mata kallo sama da kasa kafin yace sai ina kuma? "Gidan Inna Saude zanje" 'Okay na kuwa ga Baraka jiya itama ta dawo". Ya mike muje in rakaki ko bakiso? "Muje mana ta wuce ya biyota suka jera. Wai Mama meyasa Abba yake takuraki dayawa? "Kamar yaya?" Baya son kina kula samari kin kuwa san har yanzu yaya Ali yana sonki? Ta dube shi farin sani kuwa tunda yana gaya min a sace amma fitinar duk waya fara daukota? Yace a'a ba don muna uwa daya uba daya dashi ba, abnd yaya Sa'ed yayi bai kyauta ba, tunda yasan shi yana sonki menene na shi na shigo nemanki? Ya fa san halin Yaya Ali ba hakuri ne dashi ba yanzun nan sai ya nuna maka hauka. Ta dan tabe baki tace hmmmnn... Kai nifa karatu ma zanyi dama sun sa ransu a inuwa, babu wanda zan aura acikinsu koda Abba bai dakatar dasu ba.. Ya zura mata ido kina wulakanci Mama kice dama kema ba sonsu kike ba? Baka gane ba.. Me kikeso ki fada? Karatu zai hanaki aure ne? Ta kada kai nutsuwa nafi bukata sbd karatuna mai son nutsuwa ne.. Me zaki karanta? "Akikin likita" ya ware ido Uhmmnn.. Dokta Sakeena kenan! Tayi murmushi har kasa naji gingiringin! Yayi dariya daidai lokacin da suke tsayawa gefen babban titi.. To Dr Sakeena ni anan zan juya.. "Ngd ai kaga har nayi sauri da yake ana hira" yace dadin abokin rayuwa kenan, don ma ba Ya Ali bane tayi dan tsaki get lost donAllah ka rabani da wann zancen, yana dariya ta tsallaka titi ta barshi hanya shi kuma ya juya ya koma gida. Mota yake kakkabewa ya cire shimfidar foot mat lokacin da Mama tazo wucewa, yayi tsaye yana kallon wata surar da bai taba gamo da irin ta ba.. Kai ya kasa daurewa saida yayi mata sallama.. Ta dago ido ta dube shi tare da amsawa, sautin muryarta ya kara rikita shi ya bita da sauri donAllah ko zaki 5mins kadai in tambayeki? Ta tsaya caka tana dubansa, dogo ne sosai "Allah yasa na sani" yace donAllah anan garin kike? Tambayar tasata a mamaki tace eh mana, amma ban taba ganinki ba sai yau. Tace kasan daurowa take , gsky ne, ah suna nan Al- Ameen ina minna amma nan gidan kaka ta ne, na kawo Mamana ne ma yanzu sau dayawa ina zuwa nan shiyasa kikaji na tambayeki. Haka ne yau ne Allah ya nufa zamu hadu. Ya sauke numfashi gsky ne, allah ya hadamu kuma take nan kin kwanta min a rai ko zan san sunanki? Ta dan kauda kai yanayin mata saida gabansa ya fadi tsoro ya kamashi kada ya sha kayi. Ya marairaice dan daure ki gaya min ba don hali na ba, hali? Nasan halinka ne? Yace na mita da bakin naci! Tayi dan murmushi Sunana Sakeena' kai! Sunan nan ya dace da kykkyawar fuskar nan! Anan unguwar kike? Ta dan kada kai can gidan zani wajen kanwar Ummana, ok to gidanku fa? Ta yatsuna fuska alamun ta kosa ta wuce, harta fara takawa ya biyota na dameki ko? Yi hakuri so ne ya kamani ki taimake ni, ta tsaya ta dube shi da idanuwanta farare kal dasu tace kasan Uban dawaki? Can tsallaken titi kenan? Ni yarsa ce idan kasan gidan, nan ne gidan mu saidai akwai matsala. Ya hadiye murmushin sa Matsala? Na shiga uku a ina matsalar take? Tace Abbana baya bari azo zance wajena yace sai na gama karatu hasali ma bording skul nakeyi daga hutu sai hutu ake ganina, ya danyi shiru jim kafin yace to ya za'ayi yanzu Sakeena? Gsky ba da wasa nakeyi ba ya kike ganin za'ayi? Tace ban sani ba amma ina ganin hakuri zai fi kyau, mu saurari lokacin kammala karatun, ba kai kadai bane akwai wasu wadanda suka rigaka magana kuma sun hakura. Yace su zasu iya ne nikam bazan iya ba Sakeena! Ina sonki sosai babu abnd nake rayawa a cikin rain aface na aureki. Ta dan kara dubansa sai taji ya fara zama cikin ranta. Matsalar kawai batasan yanda zatayi dashi ba har tace yaje gidansu. Don haka tace kayi hakuri Al-Ameen.. Ta wuce da sauri ta barshi yana kira Sakeena! DonAllah tsaya mana kiji.. Gidaje biyu ta wuce na ukun shien nasu Inna Saude. Ta sa kai ciki tare da sallama baraka dake tsaye tsakar gida tana gyara zaman mayafinta ta juya da sauri baki sake suka rungume juna.. Gidanku zan tafi yanzu a haba? Wllh yanzun nan kewa Inna sallama har ta bani dinkunan Umma tace dama nima ta aikoni akansu, ina Innar? Tana ciki suka shige tare Inna tace au Mama ce? Har kin rigata kenan tana dariya ta zauna sannu Inna ina kwana? Ta amsa lfy lau an dawo lfy? Tace wllh lfy lau inna, kinga dinkinta dama za'aje kai mata Mama ta fiddo su a leda ta daddaga kai amma atamfofin masu kyau. Suka dan taba hira suka wuce dakin Baraka kowacce ta cire after dress. Mama ta fada katifa tace tun dazu ya kamata in shigo gidan nan bakon unguwarku ya tare ni. Bako? A ina?tace oho! Wai nan gidan Alh lado suke cewa ko? Eh nan ne gidan kakarsa Al- Ameen yace min sunansa, bakinta har kunne ta jawo hannunta suka tafa ban mu kashe yar'uwa bakar fata kice kinyi gamao da katar. Likita bokan turai yau shiya kawo Maman tasa kenan. Ta ware ido kina nufin Dr ne? Kwarai kuwa ko bai kammala ba kiris ya rage, don tuntuni naji ana fadin sabis yake, ta kama baki har kin kara min son shi ina ma ace wann abu ya tabbata kusa bikin likitoci, au kema likitance? Tace zauna nan in gaya miki jiy-jiya Abba ya gaya mina bnd zan karanta kenan, kuma gsky Al- ameen yayi min matsalar kawai Abba. A'a ina cewa ya soke maganar su Ya Ali? Eh mana to ai baki sani ba soke maganar ita ta janyo min tsiyar. Kina zaton su kawu baza suji haushi ba? Ance karatu zanyi kuma wani yazo an bashi? Ai sai Umma tayi bakin jini acikin gidan. Bansan yanda zanyi ba shi kanshi yaban tausayi tahowata kawai nayi na barshi kinsanni da karfin hali Baraka ta bata rai kai yakamata a nemi mafita Al-Ameen yayi kawata zan soki dashi don na hango kun dace kwarai. Ta sata ta zabga tagumi ta zuba mata ido, ina tsoron Abba Baraka bazan iya dumfararsa da wann maganr ba bayan jiyan nan yaja min kunne ya gaya min burinsa akaina ina zansa raina nima inason Al-Ameen! Ta dafe goshi ga koshi ga kwanan yunwa, Baraka tayi iya tunaninta ta rasa mafita, sbd tsoron hanyar da za'abi a dumfari Uban dwk don haka ta numfasa tace to ai shikenan sai ku dauki hakuri idan kuma yana iya dakatawa ya jiraki ko kuwa? Tace kyaleni haushi ya isheni dauko wani topic din kona manta da wann. Tayi yar dariya to ya skul? Mu koma wancan fannin dame-dame suka faru? Ta gyara zama suka tsinke da hirar makaranta daga abinci sai sallah har zuwa bayan la'asar lokacin da Mama ke niyyar tafiya da zarar ta idar da sallah.Tana sallamewa yaro ya shigo wai ana kiran Mama ta leko tace jeka kace ta tafi Inna ta leko tace uwaki baki zuwa ko wanene? Kai kace gata nan zuwa. Yaro ya fice inna taci gaba da fada ba kyau wulakanci ko baki son sa ki saurare shi ki bashi hakuri a zauan lfy, ta shige daki Inna kenan bazaki gane ba. Ta maida after dress dinta tasa mayafi tace Baraka zoki rakani, donAllah ki tafi ke kadai kinsan sirrin da zakuyi? Ta ja tsaki ta fito yana tsaye a kofar gidan haba gimbiya, kuma saiki tafi kibarni da tension? Ina kikeso nasa raina yau wllh ko abinci na kasa ci sbd tunanin matsalar da kika ambato. Tayi masa zuru tausayinsa ne zalla ke bin jinin jinkinta tace kasan Allah nima tunani na ya kara na rasa me zancewa Abba ganin yan'uwana ma na jini ya dakatar dasu balle wani kuma watakila kana bukatar auren ne da wuri kaga Abba bazai amince ba. Ya goge zufar goshinsa da hankici, don dai in jure ki karee sakandire zan iya jira mana. Idan ma kinaso cigaba ne bayan munyi aure ni zan dauki nauyin ki karanta duk fannin da kikeso donAllah ki taimakeni kiyiwa Abba wann bayanin. Ta dafe goshi! Wane zan masa ya gane? Ya fada a ransa yace na dameki ko? Yes nima nasan na fiye naci ga duk abnd nake so. Yace mata tunda baki da abinyi ni ina dashi abnd nake bukata daga gareki kawai ki tabbatar min tsakaninki da Allah har cikin mind dinki kina sona? Ki fada kanki tsaya kawai! Mamana tana gab da fitowa zamu tafi.Tace Al- Ameen na amince kar kaji wani shakku a ranka amma...... Ya dan daga mata hannu don't sai it pls! Kin faranta min rai Sakeena na tabbata zan samu inci abinci ya wuce min. Sauran magana ki kyale min, nace yanzu me zaki bani na rike na alkawari? Al-Ameen fa na bata mmk na yadda gaba daya ya sallama kansa gareta ko shiyasa itama ya mamaye mata ko ina? Tayi dan murmushi me zan baka kuwa? Ya nuna yatsanta wann ring din yayi min kyau shi zaki bani, ai bazai yi maka ba, inji wa? Miko shinan ki gani. Ba musu ta zaro ta mika masa ya turawa karamin yatsarsa zobe yayi zamansa daram kamar daman can na sane. BAKIN CIKI 1***2 Ya dubeta yana murmushi U see? Mu biyu akayiwa zoben nan kika kama ke kadai kika rike, tayi yar dariya "haka naji" "nima kuwa hakan naji" amma matsalar ni bani da jar azurfa dana baki wann kuma saidai kiyi warwaro dashi ba dai zobe ba. Ta zubawa zoben ido yana ta daukar ido ko in baki zoben haka? "Kawo" ai yayi miki yawa gimbiya ayi min hakuri a biyoni bashi in Shaa Allahu zan biya. To Allah ya baka iko, ya kara zubo mata ido yace to ameen gimbiyata. Ya cigaba da kallonta sannan ya sauke numfashi wai yanzu zamu tafi gashi ban gaji da ganinki ba. Yadda kikasan in saki a aljihu in tafi dake. Tace ka saceni kenan? Yayi yar dariya me karawa fuskarsa kyau da kwarjini kamar yanda kika sace ni ba. Ji sukayi ana tambaya ina Al-Ameen din ya nufa ne? Yace gani Mama anan. Ta fada zaure da saurinta ta fara dariya zoki ganta Mama donAlla! Ta kama baki Oh ni Hafsatu Goggo fito kiga ikon Allah! Itama yar tsohuwa ta fito ina kishiyar tawa duk ta susuta min miji! Mama ta manne da bango ta rufe fuska ruf da mayafi. Ta sulale kasa tun kafin su karaso, Goggo zoki sha kallon yar bebi ba irinki ba bude fuskar su ganki. Maman da kanta ta bude fuskar yayin da take gaishesu. Ta amsa cike da fara'a ah! Mashaa Allahu Al- Ameen ka iya zabe, Allah yasa albarka Goggo tace ameen dai. Ai ka kwantar da hankalinka nan gida ne babu abnd zai gagara In Shaa Allahu! Yace Allah yasa Goggo suka baro zauren Hajiar na fadin kai fa nake jira karka shanya ni.. Gani nan Mama, Mama tace Allah ya kiyaye ta amsa da ameen. Ya gyara tsayuwa yace kingani? Bani kadai nake sonki ba Sakeena sbd haka ki saurare ni, tace ina nan ina sararonka Allah ya tabbatar mana da alahiri, ameen gimbiyata to bari mu lallaba tace Allah ya tsare amma zaka yi min alkawari? Me zai hana? Fade shi indai ba zakice in daina zuwa gunki bane , tayi yar dariya bashi bane kayi min alkawarin zaka ci abinci idan son samu nema mama ta dan jiraka kaci ko yaya ne, kai Dr ne kasan matsalar rashin cin abinci ya ware sosai yace waya gaya miki ni Dr ne? Tayi nuni cikin gida yar'uwata dake nan gidan. Yayi jim! Murmushi kawai yake fiddawa kafin yace its true 4mnths back aka damka min letter of appointment a ABUTH Zaria hope kinason Dr? ta dube shi da gefen ido sai ya tsira mata ido domin kallon yayi masa sosai ko shi kadai ya isa amsar tambayarsa, in ba don son jin baki ba bata ga ma dalilin wann tambayar ba don haka ta juya zata shiga gida. Sakeena! Ya kirata a sanyaye ta juyo dauke da murmushi tace a sauka lfy Allah ya tsare ta karasa cikin gida don ta lura idan ba hakan tayi ba bazai tafi ba kuma ana jirransa. Gaba daya kasala ta sauko masa ya sauke numfashi ya jima tsaye bakin zauren sannan ya fito wajen mota inda Mamansa ke jiransa. A hakikanin gaskiya Al-ameen ya kamu da wata sabuwar cuta wacce shi kansa a matsaynsa na likita bai taba cin karo da maganinta ba. Duk iya karatnsa da yayi kuwa. Sosai yake ji a ckn ransa idan bai auri mama ba babu makawa zai fusknci matsala. Shi yasa tunda ya damki hnya baya iya magana da kowa illa addu'ar Allah yasa sakeena matarsa ce! Hakazalika al'amarn yake wajn mama, tas! Al'ameen ke neman rusa shirinta na son zurfn karatu, kamar ynda tayi wa Abbanta alkawari. A halin ynzu kam shirun da tayi bisa shimfida tun shigowarta gidan, tunanin auren al'ameen take yi, kuma da son samu ne kar aja lokaci mai tsawo. Anya abbanta zai yarda kuwa? Baraka ma taso ta kauda mata wannan tunanin, amma ta kasa. Ta yunkura ta tashi zaune tace, "bari in wuce baraka". Kallnta kawai take yi, ta mika hannu ta jawo jakarta ta rataya, tayi waje. Yaynda baraka ta dauko mayafi ta biyo ta. A dakin inna ta sameta suna sallama, hannunta daya rike da ledar kayan dinkin umman ta, "ki gaida min ita da kyau, sai na zo" tace, "to zata ji insha Allahu". Ta juya suka fito tare da baraka. Sawun tayoyn motarsa ta tsaya tana kallo tsawn lokaci, kafn ta dubi baraka, "al'ameen ya wuce, ban jin zan sake ganinsa......." "wannan mugun zato ne, me yasa kike wa kanki mugun fata?" ta kada kai, "ba mugun fata bane, sauya ra'ayin abba shine fargaba na, tabbas babu abnda zai hana shi dakatar da al'ameen, tunda ya iya dakatar da 'ya'yan 'yan uwansa na jini daya". Tace, "ni kuwa a tawa wautar gani nake al'ameen zai iya jiranki, tnda yana sonki". "lallai kam wauta, baki ganin al'ameen ya girma sosai, na tabbata a halin yanzu iyaynsa basu da wani buri da ya wuce su ga yayi aure. Yaushe zasu lamunci jirana shekaru barkatai masu zuwa? Banzan tunani kike yi baraka, kawai ki yarda zan iya rasa al'amee".! Ta fizgo hannunta suka wuce tana fadin, "ni banji a jikina ba, kuma ai Allah na nan, ba sai mu kai kukanmu gunsa ba" "haka ne, dole in gayawa Allah, don gaskiya ban taba jin wani sauyi a zuciyata ba, sai a kansa. Zaki tayani kawata?" tayi dan murmushi tare da kamo habar ta, "mama kenan, sai ma kin tambaya? Matsalarki ai tawa ce. Ki sha kuruminki, insha Allahu by nxt year zamu sha bikin likitoci, ranar duk wani mai ciwo a fandagori zai warke" Ta fara dariya, "au dariya na baki ko? Kinag dai PANADOL shine tekaway dinmu, ANTI BIOTIC kuwa su kowa zai sha a wajen dinner, to ina cuta zata zauna?" Ta buge kafadarta tana kara darawa, "surutunki yayi yawa baraka, ubangiji ya cika mana burnmu" ta amsa da amin. A bakin titi suka yi sallama akan zata ji duk yadda al'amarin ya kaya nan gaba. Ta tsallako hanya tana tafe zuciyarta kunshe da sake-sake kala- kala. Wani lokacin ta kanji kamar kwalla zasu zubo mata sbd tsabar damuwa. Ta shigo gida yaran gidan sunyi nisa da karatun allo, kamar kullum. Malamin su ke zuwa ya basu darasi. Taja birki ta gaishe shi, ta wuce da sauri ta shige gida, ta mika wa ummanta dinkunan ta. Bata tsaya bata lokaci ba ta sungumo Kur'aninta da sauran littattafai ta koma wajen malam ta kwashi karatu. Sai da ta tabbatar karatun ya kama bakinta, sannan ta koma dakinta ta ci gaba da nazari. Hakan ya dan kauda mata damuwar da ta tsinci kanta ciki yau. Shi yas ma taki sassauta wa karatun, don bata son ummanta ta fahmci wani sauyi a game da ita. Sun Sallaci Isha'I sun ci abinci tana like gefen Abbanta Umma ke fadin wann karon kuma ina zaki hutu? Kanta tasye ta bata amsa wajen Ya abdulkareem zani. Baki sake take kallonta wai! Wai! Yau kuma aljanun can suka buga? Tayi yar dariya umma kenan ai dama ba wai bana son zuwa minna bane kawai Anti rabi ce matsalata kayita aiki kamar boyinta. Ta dan harareta uhumn ke kuma malalaciya uwar son jiki ba a haka ake koyo ba? Ta kada kai a'a wllh naje hutu kuma inyi ta aiki ina amfanin hutun ko Abba? Yace kyalle Umman nan kema kike zuwa gunsu kiyi zamanki wajen Abbanki inga me samin ke aiki. Umma tace oho! Shi zaki goya miki baya? Ta ai gidan wani zata aiki kam dole tayi shi ko anan dinma. Yace ok hakane? Kinga kiyi tafiyarki Abj wajen soja. Ta kada kai bari dai in tafi minnar Abba, kasan shima yaya yana ta korafi wai ban zuwa gun sa. Yace amma nasha mamaki..... Name Abba? Son zuwa minar nan koda yake duk yarinta ce take saki zuwa hutun nan da zarar kin fara jami'a ajewa zakiyi, Umma tace likita ba! Dokta Sakeena! Ta langwabe jikin Abbanta tana dariyar dole amma cikin ranta tausayawa junan su takeyi musamman Al-Ameen da kansa yake rawa yana ganin matsalar me sauki ce abin ya kara kashe mata jiki data dubi Abbanta taga yadda muraran fuskarsa ta nuna alfahari da kalaman Umma. Kwance bisa gadonta amma barci yaki yuwuwa dabarar ta taje hutu minna ko Allah yasa su kara ganawa da Al-Ameen koda Uban Dwk ya soke bukatarsa. Shin yaya zatayi ne? Mafita kam babu sai abnd Allah yayi. Ta kuwa kwana gayawa Allah don ya zaba mata abnd yafi alhairi. Ko karatu ko auren Al-Ameen wanda zamu iya kiransa mai sa'a gwarzon da yayi nasarar ciwo zuciyar Mama da yaki har take tunanin dama ace burin Abban ta aure ne bason zama likita ba. Shawara ta zauna kan jibi da yardar Allah zata wuce minna. Sha biyun rana daidai tana shimfide bisa gadonta tare da muguwar kasala, shigowar Uban Dwk gida dawowarsa kenan daga kewayen gonakinsa. Ya daga labulen dakinta tare da fadin yaya dai yar gidan Abba? Ta tashi zaune tana murmushi, babu komai Abbana har ka dawo? Yace na dawo Mamana lfy dai? Naga kamar jikinki a mace yake. Ta amsa Allah ya taimaki mai martaba lfy kalau Mamanka take bacci ne bai isheni ba. Ya karasa shigowa dakin ya tsaya akanta yace ni kuwa banason ki saba da yawan bacci Mamana kin fa san karatun da zakiyi mai wahala ne bayason lalaci ko kin manta ne? Ta dan rausaya kai tana murmushi ban manta ba Abba ko yanzun ma rashin abin yine yasa. Rashin abin yi? To taso muje in dai abin yine ni zan baki shi yanzun nan. Ta fara dariya meye shi Abbana? Yace ki zagaye tsakar gidan nan sau 12, ta kame baki wuuu! Abbba a tsakar ranar nan? Ai sai in zube sumammiya, duk suka dauki dariya yayin da wani matashin yaro yayi sallama sassan yace ana sallama da Alhaji. Umma dake waje ta karaso da sakon. Shi mutum ne me girmama bakinsa don haka bai bata lokaci ba ya fice don ansa sallama, wata zungureriyar marsandi ya fara cin karo da ita a kofar gidan sannan idanuwansa suka kai ga bakinsa maza su 2 a tsaye wanda kallo daya zakai musu ka tabbatar manyan mutane ne. Kai! Guda a cikinsu ma Uban Dwk ya sanshi farin sani kuwa domin fitaccen mutum ne a gwamnatin data shude ambassador ne 10yrs back, watau Alh Saifullahi Sodangi Lafai kuma marafan lafai. Take nan mamaki ya saukarwa Uban Dwk ganin cewa babu abnd ya taba hadasu na mu'amala. Cike da mamaki ya bisu da sallama cikn fara'a suka yi musabaha, sannan ya kira yaronsa Kalla yace maza ya bude masa falon baki. Can suka rankaya da bakin nasa, ya nuna masu kujeru yana fadin "bismilla! Kai sannunku da zuwa!" Sun fara gaisawa kenan kalla yayi sallama ya shigo da gorunan ruwan (Swan) bisa tire da kofuna, ya aje gabansu. Ya sake dibar gaisuwa ya fice ya bar falon. Uban dawaki ya shayar da bakinsa suwan sanyi. Bayan sun natsa Ambasada ya soma da cewa, "watakila ka shaida ni, watakila kuma baka taba sanina ba". Uban dawaki ya cafe, "farin sani kuwa, mai girma marafan lafai". Suka yi 'yar dariya, "babu shakka, to wannan kuma kanina ne uwa daya uba daya, alh. Nuhu lafai". Uban dawaki ya jinjina kai, "tabbas kuwa, ga kama nan, sannunku da zuwa" Suka kara amsawa, sannan alh. Nuhu ya zarce da bayani, "Allah mai yadda yaso, kuma shi yake shirya al'amuransa yadda yaga dama. Watau jiya yaron wajenmu yazo garin nan, domin mahaifiyarsa, ya kuma ga 'yar wajenka wacce ta tabbatar masa cewa ita 'yarka ce. A hakikanin gaskiya dai yaro ya gani yana kuma so da aure, shi yasa yana zuwa ya sanar mana, mu kuma muka ce ai babu bata lokaci dole mu kawo gaisuwa, tare da neman izini. Domin a haln ynzu bamu da wani buri da ya wuce Allah ya nuna mana aurensa, tnda ya kammala karatu har aiki ya samu. Don a gaskiya mun yaba da bayanin da yayi mana, yarinyar ta fito daga babban gida. Ina fatan za'a karbi kokon barar mu? Go to Home BAKIN CIKI 1***3 Uban dawaki yayi jim, shiru yana tunanin me zaice da manyan bakinsa da suka wanko kafa takanas takano suka zo da babban alkhairi gidansa? Girma da kwarjinin Marafa sun cika masu ido, har ya rika ji ckn zuciyarsa bazai iya kabar da kokon bararsu ba. Amma abin tambayar shine, ina burinsa na tuntuni da ya kwallafa akan mama? Tun tana ckn zanin goynta? Muryar ambasada yaji yana fadin, "nasa daliln shirunka alh., Al'ameen yayi min bayanin komai game da burinka na sakeena tayi zurfin karatu. Wannan kuduri ne mai kyau, kuma ni kaina ina sha'awar hakan. To amma ina son in tunasar da kai cewar aure baya hana ilimi. Ina roknka da ka tausayawa halin da al'ameen ya shiga na fadawa tarkon son sakeena. Shi kadai gareni alh, kuma daidai gwargwado soyayyar da na nuna masa bata gurbata tarbiyyarsa ba. Yaro ne mai ladabi da biyayya ga kowa, tare da tsananin bin dukkan abnda muka umarce shi. Dalilin da yasa kenan nima nake tsananin son abnda yake so. Bana sanya wajen taimaka masa da addu'a, a duk lokacn da ya tsinci kansa cikn wata matsala kamar ynda na lura ya shiga wani hali daga jiya zuwa yau da muka baro shi. Babu sukuni a zuciyarsa, alh. Ka taimaka ka amince wa al'ameen auren sakeena da zarar ta kammala sakandare, karatu kuwa ko wane iri ne, ko a ina ne sakeena zata yi shi da yardar Allah" Wannan dogon bayani na marafa ya kwabe wa uban dawaki guiwa, zcyrsa tayi rauni, ba zai iya ja da nufin Allah ba. Ya gyara zama sosai yace, "ba shakka naji duk abnda kuka fadi, kuma nayi farin ciki kwarai da gaske, sbd haka na amsa kiranku, duk da cewar ya kamata in shawarci sauran 'yan uwana, amma babu komai zan yi musu bayana idan muka zauna. Al'ameen ya ci gaba da neman sakeena, Allah ya tabbatar mana da alkhairi" Kawai gani yayi marafa ya daga hannu sama yana fadin, "Alhamdu lillah!" ya maimaita har sau uku, sannan ya dubi uban dawaki, "bansan kalmar da zan fada ba alh......." yayi murmushi, "ai ka fadi alh., tnda kayi godiya ga Allah". Ya jinjina kai, "haka ne, to mun kara godiya gareka Allah, ka nuna mana lokacin" duk suka amsa da amin. Alh. Nuhu ya zarce da fadin, "yanzu dame-dame ake bukata na gaisuwa da baiko?" yace, "kar ku damu da wannan, da zarar mun zauna da 'yan uwana zaku ji bayani insha Allahu". "to babu laifi, muna saurare. Ina sakeenar take? A kira min ita mu gaisa, don in cika alkawarin da na dauko......" "alkawari?" "kwarai kuwa, har mota ya biyoni yana fadin, don Allah daddy in kunje ku isar da gaisuwata ga sakeena, koda mahaifnta bai amince min auranta ba. To kaji, dole in cika wannan alkawari. A kira min ita inga farin cikn al'ameen" Farin ciki ya lullube uban dawaki, bakinsa har kunne ya mike, "Allah sarki, to tana zuwa". Yayi ckn gida da hanzari ya sami Hajiya Halima, "ina mama? Ashe bakin nata ne" tare da mamaki ta tambaya, "bakinta? Kamar yaya?" "zan miki bayani, je kice ta shiryo tsaf ta sameni falon baki". Ya juya ya koma. Ita kuma dakin mama ta wuce, gaban madubi ta sameta zaune tana shafe-shafe, fitowarta kenan daga wanka. Ta matsa gareta tace, "dama kinsan da zuwan wasu baki gunki?" "baki?" ta kada kai, "daga ina umma?" "ni zaki tambaya? To kiyi maza suna falon baki inji abbanki". Ta juya ckn juyayi ta fice. Mama kuwa kasake tayi tana tunani, "baki?" Al'ameen ya fado mata a rai, nan da nan farin ciki ya rufeta, ta mike da gudu ta nufi dirowar kaynta, ta zuba ado ta rufa mayafi, ta fito ta doshi falon baki gabanta na harbawa, amma zuciyarta fara sol! Duk da cewar bata tabbatar da hukuncin da abbanta ya yanke ba. Sai dai tana da yakinin akwai alamun nasara, tnda aka ce taje da gaishe su . Tayi sallama ckn kunya ta shiga, ta sami wuri gefe ta tankwashe kafa, "sannunku da zuwa". Kai bakin marafa da kaninsa kamar gonar auduga, su kansu mama ta girgiza su, sun tabbatar da al'ameen ya darzo, fatan da suke yi Ubangiji yasa kyanta har ckn zuciyarta yake. Cikin ladabi da tsananin kunya ta gaishesu, su kuma suka amsa ckn farin ciki da nuna kauna a zahiri. Marafa ya taso yazo gabanta, ya tsuguna yace, "al'ameen ya zabe ki, nima haka. Sbd haka sai ku rike juna amana. Har Allah ya nuna mana lokacin da muke dakon zuwansa, kin ji?". Ta kara yin kasa da kai, sannan ta amsa da kai. Yace, "madalla, to mun gode". Yasa hannu a aljihu ya zaro sababbin bandir 'yan wazobia ya aje a gabnta, "wannan kyauta ce don nuna farin cikina gare ki, sbd zabar dana ya zama mijinki". Kunya kamar ta nutse, da kyar ta iya fadin, "na gode. Allah ya saka da alkhairi". Yace, "to me zan ce wa al'ameen idan mun koma?". Ta yunkura a guje ta bar falon, suna mata dariya. Shi kansa Uban dawaki yana mamakin kansa, irin farn ckn da ya tsinci kansa. Alh. Saifullahi ya mike, "to bari muyi harama, mun gode kwarai, Allah ya tabbatar mana da alkhairi". Suka yi musabaha, uban dawaki na fadin, "amin". Yayi musu rakiya, sai da yaga tashnsu sannan ya shigo gida. "Saboda Allah mama haka kuka yi da abbanki?" ummanta ke tambaya, ta kada kai, "wlh umma ba laifina bane. Babu abnda ban gaya masa ba, yaki yarda. Kinga wannan turowar ma ni bansan da ita ba, kawai ce min yayi shi yasan ynda zai bullowa al'amarin, don haka in sa masa ido". Tace, "ke din ma kina sonsa ne, ai nasan halinki sarai mama, ba don haka ba ko kallo bai isheki ba. Kin bani mamaki wlh, watau shi yasa jiya kika ce minna zaki hutu, ashe da manufarki....." Abbanta ya cafe, "tabbas haka ne....." ya karaso ciki ya zauna, yana dubanta yaynda gabanta ke ci gaba da harbawa da sauri. "ya aka yi haka mama na? Ki turo min babban mutum irin marafa, bayan kisan zai yi wuya ince a'a ko?". Hankalnta ya kara tashi, ido tam da hawaye tace, "wlh abba ba haka bane, hasali ma ni bansan shine mahaifnsa ba, domin ni bai gaya min ba, ka yarda dani abba, don bani da nufin saba maka. Duk hukuncn da ka yanke akan wannan al'amarin bazan bijire ba". Tasa hannu ta goge kwallan da suka zubo bisa kuncnta. Yace, "matso nan mamana". Da rarrafe ta isa gunsa, ya kamo kafadarta yace, "dubeni nan". Ta dago manyan idanuwnta da suka fara jirkita ta kalle shi, "na yarda da ke dari-bisa-dari mamana, sai dai abnda nake hangowa watakila ke ba zaki hango shi ba. Bayn aure mata sukan fuskanci 'yan matsaloli musamman idan Allah ya kawo rabo ckn gaggawa, wanda idan ba ayi sa'a ba sai ya jawo koma baya ga komai nata, ba ma karatu ba kadai. Amma bazan matsa ba mamana, ya kasance nayi jayayya da shirn Allah, don haka ina muku fatan alkhairi". Ta rufe fuska da tafin hannunta, fuskarta na bayyanar da murmushi. Jiknsa ta langwabe, dadi kamar ya kasheta. Yace, "ho 'yar nema! Watau kice kina son al'ameen ko?". Ta tashi a guje ta bar musu dakin. Uban Dwk ya numfasa sannan ya dubi Umma to ya kika ce? Kinga dai yanda al'amarin ya kasance. Fuska sake tace yaya kuwa za'ayi Alh? Tunda ka amince ai shikenan Allah yasa hakan shine mafi alkhairi, yace Ameen. Baki ma sani ba wai shima likita ne mun fito ina musu rakiya shi baban nasa ke gaya min. Nace itama abnd take son ta karanta din kenan. A hakikanin gsky ya tabbatar min babu damuwa I.S.A zataci gaba da karatunta, kinji inda muka tsaya dasu. Sauran maganar gaisuwa da baiko nace su bari mu zauna da yan'uwana. Ta numfasa gsky ne hakan kuma yayi kyau saidai kana ganin bazasy dora wani abu a zukatansu ba? Kasan fa su Ali sun so ta ka hana kace karatu zatayi. Yayi dan shiru jim, kafin yace kinyi magana amma ba komai nina san bayanin da zanyi musu. Tace shikenan sun dan jima suna maida zancen. Mama kuwa tana dakinta rayuwa ta zame mata sabuwa. Duk. Inda tajefa ido Al-Ameen din take gani kwarjininsa murmushinsa salon maganarsa da taushin murya mai dadi. Bayan sallar la'asar lokaci ne da kannen Uban dwk ke dawowa daga gonakinsu. Yaran nata daukar darasin Muhammadiyya kamar kullum. Uban Dwk ya tara kannensa a falonsa ya zayyane musu komai game da abnd ya faru, nan taje ransu ya sosu ba kadan ba kallon juna suke cikin al'ajabi suna tambayar zukatansu. Ina karatun da akace Mama zatayi? Ya kara gyara zama yace nasan zakuyi wa zukatanku wann tambayoyu a game da magana ta, sbd Aliyu da Sa'aeed dama sauran samarin da suka yo caa akan Mama, suna neman aurenta amma na hana, sbd dalilin zurfin karatunta. Wannan magana wllh haka take cikin zuciyata kuma shine buri na saidai marafan lafai ya cika min ido kwarai da gaske, banjin kuma zaku goyi bayan na bada masa kasa a ido ba, alhalin da kansa yayi tattaki neman alfarmar da bata fi karfina ba. Abnd nakeso in rokeku shine donAllah don son Manzon Allah SAW kuyi min uziri akan wann hukunci dana yanke karku zargi komai sai alkhairi, ina fatan zaku bani hadin kai dari bisa dari. Alh Basiru mahaifin su Aliyu kuma yafi kowa yaya a gidan ya gyara zama yace Alh ai wann al'amari na Allah ne kuma abin alfaharinmu ne ace Mama ta sami cigaba domin cigaba ne samun irin wann hamshakin zuriya ta marafan lafai. Mama yar mu ce kuma muna farin ciki tare da fatan Allah ya tabbatar da wann abu kome kace Adamu? Alh Adamu karamin cikinsu ubansu Sa'eed yace wann magana haka take Alh mu munsan cewa Mama bazata auri kowa ba sai wanda Allah yace shine mijinta sbd haka muna murnar samun wann babban rabo daga Allah. Cikin jin dadi Uban Dwk ke magana "godiya ta tabbata ga Allah da yasa na sami hadin kanku cikin sauki nayi godiya sosai, abu na gaba shine sunyi maganar gaisuwa da baiko nace su dan saurara min muyi shawara da yan'uwana. Me zaku ce akai? Alh Basiru yace hakan shi ma yayi kyau sai ta gama sakandiran ne ko kuwa yanzu suke so? Yace a'a sai ta gama tukunna. Idan haka ne zaifi kyau a bari ta gama din sai ayi baiko a sa rana ko kuwa? Alh Adamu yace haka yayi daidai. Allah ya nuna mana lokacin lfy. Kowa ya amsa da ameen. Uban dwk ya shaida musu kyautar kudin da Marafan yayiwa Mama na tsabar kudi naira dubu hamsin. Aha! Gsky ta bayyana abnd Uban Dwk yake so kenan ruwan kudi. Haka zuciyoyinsu suka saka musu, ya fiddo kudi ya nuna musu kafin yace saidai maganata gsky wann kudi ko sisi bazan taba a cikinsu ba zanci gaba da ajiyarsu cikin banki da dukkan wata kyauta dazata zo daga baya har sai wann abu ya tabbara iidan kuma an sami akasi ba fata muke ba sai a mayar musu kayansu. Ko yaya kuka gani? Sasan alh. Basiru suka tasu da matansu suka kwnce musu abnda ya wakana a falon uban dawaki. H. Hajo matar alh. Basiru ita ta fara tsoma baki, "amma kuwa idan baka mutu ba zaka ga abin mamaki kala-kala. Ynzu da gske alh. Babba ne ya iya tararku da wannan maganar? Ko ya mance abnda yayi a kan su ali ne?" Alh. Adamu yace, "ya manta? Babu abnda ya manta. Hasali ma sai da ya kara maimaita zancn su". "tafdi!" inji h. Gaje, matar alh. Adamu. "kai dai kaga dan-uwa kawai, ai dama tun farko na fada, ba wani karatn da ake so tayi, burnsu mai kudi ko basarake, sbd su ganin mama tafi kowa kyau a duniya. Shi yasa suka dauketa a matsayn wani jari gare su. Ai shikenan, Allah ya bamu lfya. Muma namu 'ya'yan bamu fidda ran Allah zai azurta su ba. Ba Dai kowannensu ya kama aiki ba? To muje zuwa wai mahaukaci ya hau kura. Harda wani za'a tara kudi a banki, don kawai kar ya baku wani abu ne a ciki, shine yake muku 'yan dabaru" "ni dama bance a bani ba, me zanci da su?" inji alh. Basiru. Alh. Adamu yace, "balle kuma ni, ai tuni na haramtawa kaina komai na alh, tnda ya nuna mana kiyayya a fili". Ya tashi yayi waje, alh. Basiru yabi baynsa. Yaynda h. Gaje ke fadin, "sai musa ido mu gani, da wane bakin h. Halima zata gaya mana zancan". H. Hajo tace, "kema dai da son jin baki kike. Tnda mijnta ya furta, ai ba sai ta maimaita ba, tana nan tasa ido muje mata murna 'yarta tayi farin jin". Tayi 'yar shewa, "Allah mai iko, kiri-kiri an raina mana wayau?". H. Hajo ta ja tsaki, "mtsww! Kina mamaki kenan, dama kin daina wlh, domin an jima ana ruwa kasa na shnyewa. Ba girin-girin ba dai, tayi mai. Ba auran gidan kudin ba, kwancyar hnkali!" Tana rufe baki tare da sallamar umma, suka amsa suna wani yatsina suna yarfarwa. Ta zauna tana fadin, "na shiga sasanki yara suka ce kina nan" "uhm! Ina nan" "dama maganar 'yarku ce, ban sani ba ko su alh. Sun gaya muku halin da ake ciki?". H. Hajo tace, "sun gaya mana, yanzu haka ma shirn zuwa sasan naki muke, sai kuma gaki. Ashe kuma mama an fasa karatu aure za'ayi?" Tace, "to yaya zamu yi, mutane sun cikawa alh. ido, sannan da alama ita ma maman tana son yaron. 'ya mace kuwa idan ta nuna tana son aure, to yi mata auran shine mafi alkhairi ga iyaynta". H. Gaje tace, "gaskya kuwa, gidan hutu ai dole a so shi. Ai kinga wadancan da yake ya ku bayi ne bata ce tana so ba". Umma ta dube ta sosai, "me kike nufi gaje?" tace, "me kuwa? Ita gaskya ai daya ce, sannan arziki na Allah ne. Daga ali har sa'eed bamu fidda masu rai ba". Ta tsura mata ido cike da mamaki, kfn tace, "na wuce kiyi min habaici gaje, domin ni ba sa'arki bace. Kasancewar ali da sa'eed 'yan uwa ga mama bai zama dole wani a cknsu ya aureta ba, domin shi aure nufi ne na Allah. Shi ke kullashi, kuma duk fassarar da zaku yi man kun dade ba kuyi ba. Allah yasan zcyrmu akan komai". Ta tashi ta bar sasan. Wata uwar shewa suka kwasa hannu bibiyu suka tafa, "tabarmar kunya....," inji h. Gaje, "da hauka ake nade ta!" h. Hajo ta bata amsa.! AKIN CIKI 1***4 Sasan alh. Basiru suka tasu da matansu suka kwnce musu abnda ya wakana a falon uban dawaki. H. Hajo matar alh. Basiru ita ta fara tsoma baki, "amma kuwa idan baka mutu ba zaka ga abin mamaki kala-kala. Ynzu da gske alh. Babba ne ya iya tararku da wannan maganar? Ko ya mance abnda yayi a kan su ali ne?" Alh. Adamu yace, "ya manta? Babu abnda ya manta. Hasali ma sai da ya kara maimaita zancn su". "tafdi!" inji h. Gaje, matar alh. Adamu. "kai dai kaga dan-uwa kawai, ai dama tun farko na fada, ba wani karatn da ake so tayi, burnsu mai kudi ko basarake, sbd su ganin mama tafi kowa kyau a duniya. Shi yasa suka dauketa a matsayn wani jari gare su. Ai shikenan, Allah ya bamu lfya. Muma namu 'ya'yan bamu fidda ran Allah zai azurta su ba. Ba Dai kowannensu ya kama aiki ba? To muje zuwa wai mahaukaci ya hau kura. Harda wani za'a tara kudi a banki, don kawai kar ya baku wani abu ne a ciki, shine yake muku 'yan dabaru" "ni dama bance a bani ba, me zanci da su?" inji alh. Basiru. Alh. Adamu yace, "balle kuma ni, ai tuni na haramtawa kaina komai na alh, tnda ya nuna mana kiyayya a fili". Ya tashi yayi waje, alh. Basiru yabi baynsa. Yaynda h. Gaje ke fadin, "sai musa ido mu gani, da wane bakin h. Halima zata gaya mana zancan". H. Hajo tace, "kema dai da son jin baki kike. Tnda mijnta ya furta, ai ba sai ta maimaita ba, tana nan tasa ido muje mata murna 'yarta tayi farin jin". Tayi 'yar shewa, "Allah mai iko, kiri-kiri an raina mana wayau?". H. Hajo ta ja tsaki, "mtsww! Kina mamaki kenan, dama kin daina wlh, domin an jima ana ruwa kasa na shnyewa. Ba girin-girin ba dai, tayi mai. Ba auran gidan kudin ba, kwancyar hnkali!" Tana rufe baki tare da sallamar umma, suka amsa suna wani yatsina suna yarfarwa. Ta zauna tana fadin, "na shiga sasanki yara suka ce kina nan" "uhm! Ina nan" "dama maganar 'yarku ce, ban sani ba ko su alh. Sun gaya muku halin da ake ciki?". H. Hajo tace, "sun gaya mana, yanzu haka ma shirn zuwa sasan naki muke, sai kuma gaki. Ashe kuma mama an fasa karatu aure za'ayi?" Tace, "to yaya zamu yi, mutane sun cikawa alh. ido, sannan da alama ita ma maman tana son yaron. 'ya mace kuwa idan ta nuna tana son aure, to yi mata auran shine mafi alkhairi ga iyaynta". H. Gaje tace, "gaskya kuwa, gidan hutu ai dole a so shi. Ai kinga wadancan da yake ya ku bayi ne bata ce tana so ba". Umma ta dube ta sosai, "me kike nufi gaje?" tace, "me kuwa? Ita gaskya ai daya ce, sannan arziki na Allah ne. Daga ali har sa'eed bamu fidda masu rai ba". Ta tsura mata ido cike da mamaki, kfn tace, "na wuce kiyi min habaici gaje, domin ni ba sa'arki bace. Kasancewar ali da sa'eed 'yan uwa ga mama bai zama dole wani a cknsu ya aureta ba, domin shi aure nufi ne na Allah. Shi ke kullashi, kuma duk fassarar da zaku yi man kun dade ba kuyi ba. Allah yasan zcyrmu akan komai". Ta tashi ta bar sasan. Wata uwar shewa suka kwasa hannu bibiyu suka tafa, "tabarmar kunya....," inji h. Gaje, "da hauka ake nade ta!" h. Hajo ta bata amsa.! Umma na shiga sasanta ta iske baraka, shigowarta kenan suna murnar ganin juna ita da mama. "a'a baraka ce?" "nice umma, ina yini?" "lfya kalau. Ya babanki da innar taki?" "duk suna lfy. Tace a gaisheki. Wai dinkunan sunyi miki kuwa?" "wle sunyi kyau" Mama ta cafe, "baki ga ta cabawa abba ado ba yau tun safe?". Ta yo mata dakuwa, "gidanku!". Ta wuce suna mata dariya har da tafawa. Janye ta mama tayi ckn daknta, "kamar kinsan ina nemanki kawata" tace, "nima haka kawai naji ina son ganinki, nacewa inna zanzo nan. Har tana min tsiya, wai anyi hutun kenan, bama gajiya da bin hanya". Suka yi 'yar drya, kafn mama tace, "kinsan wani abu?" ta kada kai. "kawai dazu da rana sai ga mahaifn al'ameen........" ta katseta ido waje, "don Allah? Sai aka yi yaya?" tace, "uhm! In gaya miki Abba ya amince! Kimji ynda nake ji yau a duniya?". Ta cika da mamaki, "tafdi! Allah ya saka masa da alkhairi" "ameen ke dai. Ni ynzu al'ameen din nake son gani, idan yaji wannan albishir din. Kinsan Allah, da ni duk na hakura ina 'yar dabara inje hutu minna, idan Abba ya hana ma rika gaisawa a can" Tace, "amma idonki ya rufe, wa ya gaya miki a minna yake da zama?" "nasan a zariya yake, amma dole yaje minna, musamman idan yasan zai ganni a can". "ke mama......" "meye?" "meye kuwa? Allah dai ya nuna mana lokacn lfya". "to ynzu zaki je hutun ko kin fasa?" "Gobe insha Allahu zan tafi, amma dole in dan saurara in ga ko zaizo goben" Tace, "kema kinsan dole gobe ya dauko hanya, wannan babban albishir ina zai tsoma ransa, idan bai zo ya ganki ba?". Suka tafa suna 'yar driya. Har gab da magariba suna tare, sannan mama tayi mata rakiya ta koma gida. Inna saude kanta tayi farin cikin jin wannan labari.! Duk da cewar maganganun su Haj Gaji sun bala'in batawa Umma rai sam bata gayawa Uban dwk ba gudun tashin hsnkali da sabani, hakan yasa bata kwana da zancen cikin ranta ba taci gaba da sabgoginta kamar ba abnd ya farau. Mama kuwa ta kintsa kayanta a jaka tare da sakonnin Umma wanda zata tafi dasu don yin tsaraba, Abba da kansa yake gaya mata kar tayi gaggawar tafiya watakila Al-Ameen yazo kada suyi sabani, ya wuce gona da kazzin idan har ya dawo daga goba bai zo ba shi zai kaita, ba karamin dadi Mama taji ba sbd a zahiri Abbanta yana nuna jin dadinsa da sauyin da Allah ya kawo musu a lokaci guda. Mama ta caba kwalliyar mamaki irin wacce take gigita samarin gidansu duk sanda sukai tozali da ita duk da cewar basanan Ali yana aiki da karamar hukumar birnin gwari shi kuwa Sa'eed dan- sandan-bada-hannu ne a Kd. Shi Sa'eed Mamansa ce ta dauki abin da zafi tuni ya gane ta wuce ajinsa ya fara neman wata anan Kd. Can sassan ta shiga don gaishesu tare da shaida musu zata tafi hutu kamar yanda ta saba idan zata tafin. Tana shiga danlami ta samu yana wankin kayansa ya zura mata ido harta iso gunsa tana murmushi duk da cewar shi tasa fuskar a daure take "wanki kakeyi?" "Uhmmn..... Kuma a zaune don lalaci yaushe zai fita.. Yace ni banson iyayinki.. Tace iyayi?? Wai naga sai wani cin magani kakeyi baka koshi bane halan? Ya dubeta sosai Yace Eh yunwa nakeji.. Saiki kawo min abinci matar masu kudi! Baki sake take kallonsa "matar masu kudi? Ban gane nuffinka ba? Yace jeki abnd ya kawoki karki hanani aiki na.. Ta gyara tsayuwa tace maganarka tana da manufa danlami me kake nufi da matar masu kudi? Sai taji magana daga bakin Haj Gaje ai ba karya bane yaga kinyi kalar matar masu kudi ne shiyasa ya fadi haka ai kinga masu kudin suna zuwa aure ya tabbata! Gaba daya ta daburce ta rasa ina wann magana ta dosa ba shiyasa tayi tsaye tana kallon Haj Gaje. Tace ki daina kallona idan baki gane ba ki tambayi mai hankali yayi miki bayani. Ta wuce abin ta cikin daki. Take nan ran Mama ya baci. Ta juya cikin sauri ta bar sassan, kicibis sukayi da Salisu ya dubeta da kyau yace ashe dama duk abun yaudara ce koda yake dama kin gaya min su Ya Ali basa gabanki, ta kalleshi tace kwarai haka ne ko akwa me yi min dole? Sannan yin kwadayi ma ai dace ne wani idan zai like yayi kwadayin ma bai samu mtsewww... Taja dogon tsaki tabar gurin yayin da Haj Hajjo ta tsaya gabansa amma kai sakarai ne tsayawa kayi tana gaya maka magana son ranta? Kai tsaranta ne? Sakarai kawai. Itama taja tsakin ta wuce shi. Haushi kamar ya hadiyi zuciya cikin sauri ya fice kofar gida. Gaban Ummanta ta zube idanuwa cike da kwalla tace Umma meke faruwa ne cikin gidan nan ake yada habaici? Tace shine zakiwa kuka? To ina ruwanki da abnd ke faruwa? Tunda ba matsalar mu bace. Umma kinsan ban son abin haushi idan su salisu sukaci gaba da yi min habaici wllh zan basu mmk gara ki gayawa Abba yayiwa tufkar hanci tun kafin gidan nan ya yamutse. Ta zura mata ido kinga babu abnd ya shafeki da surutunsu domin ba shi zai hana abnd Allah ya shirya ba, biye masu zakiyi duk ku haukace gaba daya? Ina so ki dauke kanki daga gare su tamkar yadda nayi. Ta goge kwalla tace kema sunyi miki ne? Tace tun jiya iyayensu suka fara amma bai dameni ba don nasan wann abu bani na shkirya shi ba ba kuma Abban ki bane balle ke. Shiyasa ko shi Alhajin ban gayawa ba sbd bana son hayaniya kin gane? Ta dan yi jim sannan ta amsa da ka tana goge kwalla. Tashi ki je ki wanke fuskarki. Ta mike zata wuce yaro yayi sallama yace wai ance Sakeena tazo Al- Ameen yazo. Gabanta ya yanke ya fadi ta zurawa yaron ido ta rasa me zatace? Umman ce ta bashi amsa to kace tana zuwa. Ya juya ya fita, kin tsaya ki kam kije ki shiryo mana. Ta shige dakinta sanyi na kwarar zuciyarta. Ta tsaya gaban mudubi ta gyara fuskarta ta suro gyalenta ta yafa tayo waje. Umma na tsakar gida ta mika mata makulli tace ki kaishi falo karku tsaya a waje. Fuska sake ta amsa ranta ya kara sol. Tayi kofar gida cikin sauri amma cikin sanda ta leko yana tsaye jingine da motarsa ya zurawa zauren ido shiyasa tayi arba da idanuwansa masu haske da girma. Sbd haka kunya ta lullubeta ta koma zauren ta lafe tana maida numfashi kawai muryarsa taji bisa kanta yana fadin sallama gareki ma'abociyar kyau! Jim tayi shiru kamar ruwa ya cita hannunta daya rufe da fuskarta haka shima ya tsaya ya zura mata ido dauke da murmushi mai isar da sako barkatai. A nutse ta bude fuskarta ta dubeshi "sannu da zuwa" taushin muryarta yasa jinin jikinsa ya tsinke yaji son Mama ya kara malale kowane lungu cikin zuciyarsa tamkar ya hadiyeta yakeji kai bai tabajin azababben so irin wanda ya kama hsi ba, ya numfasa yace gimbiya ta kenan. An fito lfy? Tace kalau ya hanya? Yasu Baba sukaje gida? Ya amsa duka lfy lau, tace mungide Allah. Yanzu ka ban minti daya zan bude maka inda zaka zauna, yace ni kadai? Gsky ban yarda ba! Tayi dan murmushi to inda zamu zauna. Yauwa yanzu naji batu gara da kika gyara. Ta wuce tana 'yar drya. Shi kuma yayi wawan ajiyar zcya, ya dawo jkn motrsa ya harde. Jimawa kadan ta budo babban kofar get da ke can wani bangare na katangar gidan, ta fito tace dashi, "bismillah!". Bai yarda ta tsere masa ba, jerawa suka yi suna tafe yana fadin, "ga Amarya ga Ango!". Ta ballo masa harara, fuskarta kunshe da kyakkawan murmushi, har suka shige falon. Ta nuna masa kujera ya zauna, ita ma ta koma gefen damarsa ta zauna, suka sake gaisawa. Yace, "to Alhamdu lillah, godiya ta tabbata ga Allah wnda ya nufi al'ameen ya zama angon sakeena. Ko kinsan cewa jiya banyi barcin kirki ba?". Ta kada kai, "me yasa?" "ban taba zaton abba zai saurari kukana ba, shi yasa na kasance tamkar maraya, ni kadai cikn daki, bana aikn komai sai na addu'a, idanuwan nan sun fidda hawaye gaban Ubangiji don neman biyan bukata. Beliete me ma jinina ya hau kfn dady ya dawo......." ta katse shi, "amma da ya dawo fa?" yace, "albishir din da ya dawo min dashi ya hana min barci sbd tsabar murna da farin ciki, cnt explain sakeena" tace, "ka mamayi abba, kuma ni kaina nayi mamakin amincewarsa, koda yake abba mai saukn kai ne, kuma bai cika jayayya ckn al'amarn rayuwa ba" "na yarda da ke. allah ya sakawa abba da alkhairi, domin ya ceci rayuwata. Ko har da taki?" Ta dube shi suka hada ido, ta dan kauda kai. Tayi 'yar drya. Yace, "ban damu ba, tnda ni nayi nasara". Tace, "ni kuma bazan yarda da kai ba, sai naga alkawari na". Ya zuro mata ido, "a tunaninki zan manta ne? No sakeena, kece komai nawa, bazan taba mantawa da wani abu wnda ke alaka da ke ba, balle kuma ace alkawari ne......," Ya tura hannu aljihu ya dauko wani dan karamin mazubi ya bude, ya nuno mata wani gangariyan zoben zinari yace, "ina jin wannan shine alkawarin ko?" Baknta yaki rufuwa, ya matso gabnta ya tsugunna ya miko mata, tasa hannu ta dauka ta zurawa yatsanta. Wayyo! Al'ameen zuru kawai yayi yana kalln zara-zaran yatsnta, zoben nan ya zauna kamar da shi aka halicce ta. "tsarki ya tabbata ga Ubangijn da ya halicce ki sakeena". Ya dago ido ya dubeta, "kiyi min alkawari har abada ba zaki daina sona ba". Tace, "insha Allahu zaka sameni mai cika alkawari komai wuya, komai tsanani zan jure akan alkawarinka. Har abada kai kadai ne, ba wani sai kai" Idanuwnsa suka kawo kwalla, murya sanyaye yace, "na gode sakeena" tace, "kar ka damu". Ya mika mata gidan zoben ta karba. Ya koma mazauninsa ya zauna, abba ya gaya wa dadyna kema irin karatu zaki yi, kinga ta kwana gidan sauki, wai matar likita ta haifi panadol" Ta fara drya, "oh, drya na baki ko? To shikenan, ai ba ke matar likitan zaki haifi panadol din ba........" tace, "au son kai ne abin?" "eh mana. Nawa bouncing baby ne, baby boy ko girl? Zabar min". Ta mako masa harara, ya hau drya. "well, daga nan idan na tashi zariya zan wuce, sai kuma nxt week zan dawo in sake ganin gimbiyata" tace, "Allah ya kaimu lfya, nima anjiman zan wuce minna wajn yayana zanyi hutu" Ya bude ido, "owk, kuma shine tnda nazo baki gaya min ba, ai sai in juya in kaiki, daga can in wuce". Ta kada kai, "bana son ka wahala, ka wuce wurin aiki abinka. Babu komai". Yace, "uhm...... To na gode, amma ina fatan akwai phon number a can, kin ga sai mu rika gaisawa ko?" tace, "eh akwai land-line zan baka" Yayi ajiyar zuciya, sannan yace, "yanzu ki bani labari, ku nawa ne a daknku?" tace, "mu hudu, yaya abdul-kadeer soja, shine babba, sai yaya abdul-kareem yana CBN Minna, shine zani hutu gunsa, then yaya Abdul-rahman yana kadna, lst year ya fara aiki da ma'aikatar kimiyya da fasaha ta jiha, shi kadai ne bai yi aure ba......" "sai kuma ke ko?". Tayi 'yar dryar nan da yake so. Yace, "kun burgeni, Abdul 3, ni kuwa tilo ne ckn gdnmu, bani da yaya balle kani. Kadaicn yayi min yawa sakeena". Tace, "kamar ynda gata yayi maka yawa ba" "haka kike gani? No ba zaki gane ba, naso ace akwai wasu, musamman kanne, na rika yi musu 'yan mazurai ina cewa, kai ku bari mana! You knw, smthn like that dai. Amma ka zauna shiru babu mai maka fada, babu wnda zaka yi wa? Babu dadi abin". Ckn tausayi tace, "ai shirin na Allah ne" yace, "yes haka ne, na yarda. Amma very soon zan samu many babies, su zagayeni, dady kalla! Dady bani wannan! Dady sa min riga! Kin gane? Ina son hayaniyar yara sosai" Tana drya tace, "kana da aiki" "come on, muna da aiki dai. Ai mu biyu ne muna tsakhya, sun zagaye mu, na 6 can 6. Wuu! Confusion! Wa zai gane min ke?" Hannunta tallafe da kunci, ta zuba masa ido tana kallnsa yana ta zuba bayani, idanuwanta suna nuna mata yaran zagaye da shi. Shi yasa yana sa aya ta fashe da drya. Yace, "drya ma na baki ko? Yarnya gudu zanyi in kyaleki dasu" Ta dan tabe baki, ta tashi tsam! Zata bar falon, yace "ina za ki? Har kinji tsoro ne?" tace, "tsorn me? Ruwa zan kawo maka, kaji dadin santin". Sosai yayi drya, har ta bar falon. Ya koma a hnkali ya jingina bayansa da kujera, ya rufe ido tamkar mai barci. Wani kasaitaccen taro yake hangowa, wnda cikarsa baya misaltuwa. Jimawa kadan ya keto taron rike da hannun sakeenarsa, da ka dube su kaga amarya da ango. Jama'a na musu tafi, su kuwa baki yaki rufuwa. Bisa wasu kasaitattun kujeru suka zauna, ta tsiyaya lemu a kofi ta mika masa a baki, ya dauka zai fara sha...... "Assalamu alaikum!". Ya bude ido a hnkali, tana tsugunne gabansa rike da kofin ruwa. "barci kayi? Lallai na dade da yawa, ayi min afuwa". Ya saki wani wawan numfashi, ya girgiza kai, "dogon tunani ne ya dauke ni. A duniya bani da wani burin da ya wuce aurenki sakeena.....". Yayi dan shiru jim! Yana kallnta, ya kada kai, sannan ya karbi kofin hannunta, "na gode". Ya shanye ruwan, ta zuba masa lemu, ta koma ta zauna, ilahirin jiknta ya mutu. Wane irn so al'ameen ke mata? Ta tambayi kanta. Tana ganin ita ma irnsa take yi masa, domin itama burinta ta zama mata a gareshi. Ko don ita kunya na maida ita kurma, shi yasa yake ganin shi kadai ke da buri a kanta? Zurun da tayi masa a rashn sani, shi ya jawo hnkalnsa ya daina kurbar lemun. Ya matso gabnta yasa mata kofn a baknta, ta sha kadan ta dube shi, "ba kai kadai ke da buri ba Dr., sanin kanka ne mu duka muna da bukatar kasncewa tare. Idan baka sani, ynzu na gaya maka ka sani, don ka daina damuwa". Ya numfasa yace, "Allah ya tabbatar mana da wannan buri" tace, "amin". A natse suka zauna suka ci gaba da faranta wa junansu rai da dad'ad'an kalamai. A nan yayi sallar azahar, ya ci abnci, sannan yayi shirn wucewa zrya. Ita ta jagorance shi ya shiga ya gaida umma, don ya matsa kwarai yana son kai mata gaisuwa. Ta kuwa ji dadi, ta kuma yaba da tarbiyyar sa, yanaynsa da alkunyar sa.! Suna tsaye jikin motarsa sallama taki karewa Ya Ali ya danno kofar gidan da jakarsa akafada, bakinta har kunne ta tarbeshi Ya Ali! Sannu da zuwa, ya kalleta ya kalli wanda take tsaye dashi kafin ya amsa. Ya mikawa bako hannu tare da sallama (Allah Sarki ubana akwai jarumta!). Ita kuma tana fadin Ya Aliyu kenan cosin dina ne, Allah sarki inji Al-Ameen an dawo lfy? Yace lfy lau! To madalla. Aliyu yace dauke da matsanancin kishi da mamaki a ransa. Al-Ameen kuwa fadi yake kuna satar kama da juna da an ganshi an ga dan'uwanki, tace ko? To ai da Baban shi da Abba duk dakinsu daya. A Birnin gwari yake aiki. That's gud' ina ganin ya kamata in lallaba in barki ku wuce ko? Kar dare yayi. Tace hakane, kai din ma bana son dare yayi maka. To shikenan karfe tara ISA zakiji wayata. Allah ya yarda a sauka lfy. Ameen. Ya shiga mota ta rufe masa tana kara fadin kayi tuki a hankali, yace thank U. Ta juya zata wuce yayai kiranta Skaeena! Ta juyo tare da murmushi yace "I love you!" Ta kara fadada murmushinta ta rausaya kai ta juya zata wuce Sakeena! Ta sake juyowa. I love u! Tayi jim kafin tace I love U too! Ta ruga cikin gida ya rakata da kallo bakinsa kamar gonar auduga kasala ta rufe ya kasa tada motar. Ta sake lekowa tayi masa bye-bye shima ya daga mata hannu sannan ya sami karfin tada motar yayi ribas yai kwana ya fada hanya ya kara dago mata hannu ya wuce cike da begenta tamkar yadda takeji a ranta. Tana shiga cikin gida muryar Ya Ali kawai ke tashi yana bambamin fada "ai dama haka rayuwa take kiri'kiri jininka saiya wulakantaka don baka da kudi! Muma muna kan hanya indai arzikine abuna Allah! (Kana da gsky Baffaba!) Mama tayi tsaye jikin kofar sassansu tana saurare haj Hajjo tace nace dai kayi shiru haka ko? To kaci gaba idan hakan shi zai sa a baka ita. Mama dai ba saurana mata tafi ba ga yanmata nan bila adadin duk wacce ka zaba sonka zatayi idan ita ma ba kwadayi tasa wa ranta ba. Sbd haka kar in sake jin wata magana ta fito daga bakinka akan wata Mama! BARKA DA SALLAH HAUSA Novels BOOK BAKIN CIKI 1****5 H. Gaje ta cafe, "ki kyale shi ya amayar da bacin ransa, kar ya zame masa ciwo! Da wanne zai ji?" yace, "ai inna ba zata gane ba mama gaje, wannan rainin arziki ne a ckn gida. Uwa daya uba daya? Haba! Ya kamata a duba!". H. Hajo tace, "wa zai duba? Lallai ranka zai fita idan har zaka kwallafa wa kanka wannan maganar!" Tana sa aya daidai da sallamar uban dawaki, yayi tsaye yana kalln mama na zubda kwalla, yaynda yaji muryar h. Gaje na fadin, "babu wnda zai duba wannan al'amari, tnda dai shi da kansa alh. Babban ya ya yamutsa al'amarin!". Kalaman da suka fada kunnuwan uban dawaki tare da bugun zcy, ya zurawa mama ido tamkar ynda take kallnsa, "me ke faruwa?". Bai gama rufe baki ba yaga Ali ya fito a fusace, idanuwnsa na tsatso kwalla. Shi kansa gabnsa yayi mugun faduwa, kasala ta kama shi, ya rage sauri, "kai ali lfy?". Ya gnge fuska, ya dan rankwafa yace, "sannu abba!" "nace me ya faru?" "babu komai" "ina wasa da kai ne? Kake gaya min babu komai!". Mama tace, "abba tun jiya gidan nan a yamutse yake, ana ta habaici tare da yada magana akan zancen al'ameen. Umma taki gaya maka ne sbd gudun fitina. Amma kowa gani yake yi sbd kudi ne yasa ka amince inyi aure, bayn ka hana kowa kace karatu zanyi. Me yasa za'ayi mana mugun zato?" Nan da nan ransa ya baci, yayi fushi sosai, ya kwalawa umma kira. Ta fito ta samesu ransa bace. Ckn fushi yace, "kira min matan gidan nan!" "lfya alh?" yace, "ban son jin wata magana". Tace, "alh ka kwntar da hnkalnka kayi hakuri har zuwa lokcn da mazajnsu zasu dawo. Zai fi kyau duk abnda zaka fadi ka fada a gabnsu. Ina rokn wannan alfarmar don girmn Allah!". Alh. yayi jim! Shiru yana kalln umma, kafn ya dubi mama yace, "kin shirya kayanki?" tace, "eh" "to kwaso ki zuba a mota maza mu tafi". Ya wuce da sauri daknsa, kowa ya kama gabnsa, har da ali ba tare da wani ya kara cewa komai ba. Kayn jiknsa kawai uban dawaki ya canza, yayi rawani kamar ynda ya saba, ya fito lokacn mama na tsakar gida da jakar kaynta tare da tsarabar da umma ta bayar a kaiwa yara. "Baki kai kayan motar ba?" inji abba. Tace, "ai basu da yawa, su kenan" "wuce muje". Umma tace, "Allah ya tsare, a sauka lfya". Ya amsa da amin, yayi waje. Mama ta biyo baynsa. Ali na zaune bisa dakali tmkar yayi bindiga sbd tsabar fushi da kishi, domin sosai yake son mama. Kuma yayi wa ransa alkawari zai ci gaba da farautarta, sai yaga abnda ya turewa buzu nad'i. Shi yasa ya aje wa ransa zai iya jiran ta gama karatnta. Shi kuma zai ci gaba da gina kansa da duk wani tanadi wnda zaizo daidai da jin dadin rayuwr aurnsu. Ina zai sa ransa yau yaji dadi? Yana ganin mama ta shige mota idanuwnsa suka yo tam! da hawaye. Musamman wannan zuwan ita yazo gani, sanin cewa sunyi hutu. Kamar ya kwarma ihu. Ya mike ya sake fadawa ckn gida. Alh. Ya bude mota, kalla ya matso, "ranka ya dade tfya za kuyi?" yace, "ai tare zamu tafi da kai, taso ka shiga mota. Minna zan kai mama na" yace, "to shi kenan". Ya mika masa makulli, "ka tuka motar kalla, bana jin dadin jiki na". Ya amsa yana fadin, "assha! Allah ya sauwake" "amin". Ya bude gidan baya inda mama take, shima ya shiga. Jikn mama ya kara sanyi, tasan abbanta ya kanso suyi tfya su 2 kacal! Suna tafe yana bata labarin duniya. Ta tabbata bacin rai ne yasa ya gayyato kalla ya tuka su, gudun afkuwar wani abu. Sun mika tfya shi babu mai magana, shirun sam baya mata dadi, sbd haka tace, "Abbana kayi hakuri don girman Allah, kar hnkalnka ya tashi akan wannan maganar". Ya dubeta sosai yace, "dole raina ya baci, sbd an zarge ni akan abnda ba shine a ckn zcyata ba. 'Yan uwana basu yi min adalci ba, na tabbatar da saninsu mataynsu ke yada habaici da kananan maganganu. Amma zanyi wa tufkar hanci. Tnda babu wnda ya haifa min ke". "kara kayi fada dasu abba....." yace, "ya za'ayi in tsaya ina fada da kannina? Umarni kawai zan bayar, kuma dole kowa yabi idan ana son zaman lfya. A iya sanina na basu hakknsu, na zauna da su na gaya musu uzuri na. Amma duk da haka basu gane cewar komai na Allah bane. Ke dai abnda nake soki dashi, ki rike yarn nan amana, sannan ki kara kula da kanki, don tsare martabar gidan nan" tace, "Allah ya taimaki mai martaba. Mamanka na tare da albarkar umma da abbanta, da yardar Allah ba zata basu kunya ba". Yayi dan murmushi yace, "Allah ya kara yi miki albarka". Tare da kalla suka amsa, "Amin abba Sun iso minna la'asar sakaliya, shi yasa ruwan alwala kawai alh. Ya fara tambaya. Yayi sallah a babban falon gidan, yaynda jerin kayan abincnsa ke jiransa. 'yan jikoknsa kuwa sai safa da marwa suke yi. Ya idar da sallar, suna jiran su tumurmushe shi. Ilai kuwa yana idarwa suka zube a jiknsa, yana drya ya soma tsokanarsu" "ameera tsohuwa mai majina" tace, "Allah ameer ne mai majina" ameer yace, "karya ne abba, kullum wa ake ba tishu in zamu skul?". Abba yace, "kyaleta Uwair, waye bai san halima tsohuwa bace? Mai majina kawai". Ai nan da nan tayi fushi ta tashi fuu.... Zata fice,suna mata drya. Sai ga sallamar anti Rabi. "momy kin gansu ko? Wai nice mai majina". Ita ma dryar tayi ta wuce ta zube gabn abba ta kwashi gaisuwa, sannan ta tambayi mutan gida. Yace, "duk lfyrsu kalau" Kuka ameera ke yi, yaynda mama ta shigo da ita falon, "ynzu don Allah wa ya taba min umma na?" yace, "kyale ta mai majina ce, ni bana auranta!". Ta kara kware baki, mama ta rungume ta, "kiyi shiru ki kyale shi, ke ma baki auran. Me zaki yi da shi tsoho?" ameer sai drya yake mata. Da yaga kukan da gaske take ynsa sai ya jawota jiknsa, "wanene ya taba min madam dita? Manta da ameer, tsoho ne shima. Ina dady bai dawo bane?" ta amsa da kai tana murzar ido. Anti rabi tace, "bai shigo gida ba tukuna, amma yana bisa hnya". Yace, "To Allah ya dawo dashi lfya" suka ce amin..anti rabi da mama suka bashi wuri yaci abinci tare da jikoknsa. Yan minticoci bayan kammalawarsa motar Ya Abdulkareem tayi fakin a harabar gidan, ganin motar Abbansu yasa ya fito da sauri kalla ya tarbe shi ya karbi jakarsa yayi masa sannu da zuwa suka gaisa, tare suka shigo falon ya zube gaban Alh yana fadin oyoyo abbanmu! Yace Abdulkareem dan Abba sadauki! Ya kara fadada dariyarsa domin yana jin dadin kirarin da Abba yake masa tun yana yaro sbd tsananin kokarinsa wajen neman duk abnd yake so musamman ilimi. A yaran gidan kaf! Babu wanda ya fara sauke Qur'ani da karancin shekaru sai shi, yana 14yrs yayi sauka kuma yasan littattafai dayawa. Daka dubeshi kaga Mama illa dara daran idanuwanta ne kadai suka banbantasu. Kazo lfy Abba? Yasu Umma? Yace lfy lau Mamana na kawo maka hutu.....Mama? Yanzu haka tana ciki? Sai gata ta shigo falon ta karaso gunsa da gudu ta zube jikinsa Yayana!. Ya kamo kunnenta ba wani yayankitashi zakiyi ki koma inda kika fito! Tace Allah sarki yayana dan Abba sadauki! Ya dada mata duka suna ta dariya "maras kunya ba Abj kika fiso ba? Ai dama nace duk randa kikazo yan kafafuwan zan karya.. Tace, "tuba nake yayana, daga yau duk hutu anan zan yi shi" yace, "naji amma ban yarda ba, ke da soja ai sai Allah, watakila kema sojan zaki aura". Ta kada kai ckn shagwaba, "a'a!" Abba yace, "ai baka ma sani ba? To karkade kunnenka kasha labari". "ko abba? To bani insha". Abba na bashi labari, ita kuma mama na boye a bayn yayn nata. Tas! Ya zayyane masa abnda ke faruwa. Abdul-kareem ya cika da mamaki, "to menene abn tashn hnkali a nan?" yace, "nima shi na gani, har ga Allah zcya ta bata da wani nufi akan wannan al'amari, amma tnda haka suka dauko zamu tafi a hakan, kuma mama zata auri wnda take so". Ya dan kada kai yace, "kayi hakuri abba, kasan shi mutm a kullm yakan fi son kansa maimakn neman zabn Allah. Abu kankani sai a ruruta shi yayi girman da zai rarraba kan zumunci. Abba ka dauki girma kamar ynda ka saba, ka dauke kai ga tsegunguman mata". Ya zura masa ido yana murmushi, "dan abba sadauki! Duk abnda ka fadi gskiya ne, shi yasa ma bazan gaya wa yaynku ba, don nasan halnsa, daga ali har mutn gidan babu wnda zai kyale idan hauknsa ta tashi". Yace, "haka ne, kuma nasan ali yana son mama, dole yaji zafi a rnsa, amma su a matsaynsu na manya ai bai kamata su rika tnzira shi ba. Abnda ya dace shine su nuna masa komai na Allah ne. Amma muna musu fatan Allah ya ganas da su. Ke kuma mama ki rike amana, domin duk garin nan babu wnda bai san familn marafan lafai ba. Babban gida ne masu mutnci. So u hv 2 b very carefl, ke ma ki nuna wa duniya kin fito daga babban gida mai cike da tarbiyya, OK?" Tace, "insha Allahu yaya zanyi iya kokari na". Yace, "to da kyau likita matar likita. Abba kasan wani abu? Ai mu juma munyi bye-bye da rashn lfya". Suna ta drya, anti rabi ta shigo itama. Sun jima suna hira, sannan uban dawaki ya bar garin minna tare da yarnsa kalla.! Anyi sallar magriba lokacn da suka shigo Fandogari, don haka a guje uban dawaki ya nemi bada farali. Bai wani ci abnci sosai ba, sbd abncn da ya ci da yammacin dazu a minna. Umma ya aika ta tattaro masa kaf kannensa da 'ya'yan gidan tare da ali. Duk suka hallara a falnsa, ya dubesu ya fara magana ckn rashn jin dadi, "abnda yasa nace a kira min ku, a gskya abnda ya biyo baya sakamakn maganar da muka yi da ku jiya, sam banji dadnsa ba. Basiru da amamu kar ku manta gaba daynmu ciki daya muka fito, babu bare. Kar ku bari tsegunguman mata su raba kawunan mu, domin da halima da hajo da gaje tare suka same mu. Bai kamata in gaya muku uzuri na ba, ku kuma ku koma kuna min yankn baya wajn mataynku, har su sami damar yada maganganu marasa dadi akai ba. Ko ban haifi daya daga cknku ba, ina zatn ni uba ne a gareku, kuma daidai gwargwado ban shiga hakkn kowa ba. Ali da sa'eed a wancn lokaci sun yunkuro, kowannensu yana son auren mama, a gabnku yaran nan suka rika rigima a junansu, gaba ta kullu, babu mai kalln dan uwnsa. Sbd Allah idan ban ynke wancan hukunci ba me ya kamata inyi? Shi za'a tsaga mama gida 2 ne, ali ya auri rabi sa'eed ya auri rabi? A gani na idn aka hana kowa zai fi mana alkhairi. Ko da bani da ra'ayn mama tayi zurfn karatu, ballantana ina da shi. Wlh bani da wani buri akan mama da ya wuce tayi zurfn karatu ta zama likita gabana. Amma da Allah ya sauya al'amarinsa, ba zan iya jayayya ba. Sai dai a cknku laf din nan na bar muku zabi, idn akwai mai iya yin wani abu bayn wnda Allah ya zartar bismilla, ina saurarnsa. Ni kam na yarda nayi gmanin al'ameen Allah ne ya turo shi, ban isa in koreshi ba. Kuna iya kirana kuda sbd kwadayi, ba zai sauya komai a jikina ba, don nasan har ga Allah bana bukatar sisin kwabo daga al'ameen ko mahaifnsa. Na kare maganata, idan akwai mai abin cewa yana da damar fadi". Gaba daya ka rasa mai yin koda motsi, sbd dogn jawabn uban dawaki ya tattaro musu kunya ckn idanuwnsu, musamman matan. Jin sunyi shiru, uban dawaki ya kara da cewa, "idan babu mai magana kuna iya tfya, shikenan magana ta kare" Har matan sun mike, alh. Basiru yace, "ku zauna. A gskya munyi kuskure, amma ynzu mun gane bamu kyauta ba ko kadan. Kayi hakuri alh. Da yardar Allah wata magana ba zata sake bullowa akan mama ba. Ku kuma hajo da gaje ku ba alh. hakuri, har ma da h. Halima" Da ganin fuskoknsu kowacce ba akan son ranta take magana ba. Sun dai bada hakurin, kuma abba da umma sun yafe, sun maida komai ba komai ba, a matsaynsu na manyan gida, sun nada gammo sun dauki girman kamar ynda hausawa ke fadin Babba juji ne. Aik. Adamu ma yayi nasa dan guntun jawabin na neman afuwa. Kowa ya tashi aka bar Ali a zaune, ba tare da yace wani abu ba. Abba ya dube shi yace, "akwai magana ne ali?" ya karkada kansa da ke sunkuye, sai hawaye shar-shar! Suka hau zuba. Uban dawaki ya sauke numfashi, gaba daya jiknsa ya mutu. Harga Allah bai taba tunanin soyayyar mama tayi zurfi ckn zcyar ali haka ba, wa ke ganin hawayn ali? Da yarntarsa ma ba karamar azaba ke sanyashi kuka ba, shi yasa yaci sunansa Gadanga! Domin kaf tsaransa babu mai nuna masa yatsa. "zo nan ali!" yayi kirnsa yana nuna masa waje bisa kujera kusa da shi, "zauna kaji". Ya zauna yana goge kwalla. "abnda nake sonka dashi ali kayi wa girman Allah ka dauki imani ckn ranka. Wlh a zatona tuni kun share maganar mama a zuktnku, ganin na jima da soke maganar. Amma kayi hakuri, ka dauki dangana kasa wa ranka, duk abnda Allah ya hukunta daidai ne" Ya dan gnge kwalla ya dube shi, "abba sa'eed ne ya hakura, amma ni burina inyi ta jiran mama har zuwa lokacn da zata gama karatnta. Kullum addu'a nake yi Allah yasa a tsayn shekarun nan zcyr mama ta aminta da ni". Ya numfasa ya kada kai, sannan ya ci gaba, "bansan yanda zanyi ba abba". Abba ya rungumo kafadarsa, "hakuri magani ne ali, ban son ka tashi hnkalnka. Mama 'yar uwarka ce, ka taimaka ka bata goyn baya tare da addu'ar fatan alkhairi, kaji? Ka kwntar da hnkalnka, nayi rantsuwa da mama tana da kanwa da na baka ita. Amma tnda babu, ina son kasa natsuwa ckn ranka, ka ji ni?" Yace, "naji abba, kuma na gode". Umma tace, "nima dai hakurn nan shi zan baka ali, gaba daya hawaynka sun kashe min jiki. Amma babu abnda zamu iya yi, sai dai ince Allah ya musnya maka da alkhairi" yace, "amin umma". Abba yace, "to tashi kaje ka kwnta, ka ci gaba da addu'a, komai zai wuce". Ya mike babu kuzari ya bar falon. Shiru su umma suka yi tsawn lokaci, kafn abba yace, "Allah ya kyauta!". Ta cire tagumi tace, "amin. Da gaske ali yake yi" "mtsw!" yayi dan tsaki ya tashi ya shige daknsa dauke da tausayn ali, ya bar umma zugum! Tana tunanin iska. Gidan yayi tsit! Ko da tasa damuwar. Washe gari da wuri ali ya koma birnin gwari don kara samun natsuwa. Idan bakwa comments sai inga kamar littafin ne baiyi muku dadi ba, na kuma sai inji bana son turowa din. BAKIN CIKI 1***6 Karfe bakwai da rabi na safiya wayar tebur ke ta bugawa a babban faln. Dawowar anti rabi kenan daga rakiyar mai gidan da yara da zai aje makrnta, kfn ya wuce wajn aiki. Can gefn wayar ta nufa ta dauka tare da sallama. Bai mance muryar da ya fara ji jiya tawaya ba, don haka ya zarce da fadn, "ina kwana anti?" tace, "lfya kalau, wa ke magana?" "al'ameen ne'. Take ta fara fara'a, "au Allah sarki, ya aiki?" "Alhamdu lillahi" "madalla, bari in kira ta" "to na gode". Ta aje kan wayar gefe ta wuce da sauri tana kira, "mama! Mama ki aje girkn nan kizo, mutumin naki ya bugo!". Ta fito daga kicn da sauri, suka hade a kofa. "wannan likita naki da naci yake" "kai anti!" ta fadi cike da fara'a. "ke dai jeki da sauri". Ta wuce tana drya, ta dauki wayar, daddadar muryarta a sanyaye tace, "hello!". Ya runtse ido yace, "hello 'yan mata ya aka yi?" tace, "kalau, an kwana lfya?" "sosai ma, har da miyan barci". Tayi 'yar drya, "kaji dadnka" yace, "har na kai ki? Nasan barci kike yi aka taso ki". "haba, kamar wata raguwa?" "ita ce mana. Kowa ya ganki ai yaga kalalatu" "kai kuma kalala ba" Yayi drya yace, "tun asuba nake tsaye ina shirn ofis. Na rataya neck tie, shine nace bari in kira madam ta daura min" Ta dan rufe fuska da hannu daya tana murmushi. Yace, "baki ce komai ba" tace, "to me zance?" "au ba zaki daura min ba?" tace, "na daura!" yace, "ga abu a wuyana yana lilo kice kin daura, don Allah ki daura min" Ya fada a shagwabe. Tace, "yau na bani! To rufe idnka". Ya kuwa runtse yace "na rufe" "me ka gani?". Ya danne kan wayar a gefn wuynsa ckn tunaninsa yake magana ido ruee, hannaynsa na aikin daura neck tie din. Yace, "ga ki nan kin fito daga dakn barci, kin zuba kwalliya da wani farin less, kin yi kyau bebyna. Sai murmushi kike min, kin kama neck tie din kina daura min........ "Wash!" ya bude ido firgigi, jin ya shake wuyansa. "menene?" Ta tambaya ido waje, ji tayi ya shagwabe, "Gaskiya ba haka ake yi ba, ba haka ake yi ba sakeena. Ai dai ba'a shake wuya". Drya sosai ta kubce mata, "ni na shake ka?". Yana sassauta daurn wuyn yana fadin, "da kyar fa nake numfashi, so kike in suma?" tace, "kaga zaka makara wlh, idan suka ma bulala babu ruwana". Yace, "ya zaki ce in tafi? Kin bani brkfst ne? Ga kofn tea nan a gabana, yi sauri ki ban insha in wuce". Tace, "oya, dauki kofi kayi bismilla". Ya dauka ya rufe ido yana kurba, yana ganinta ckn idanuwnsa, itace ke bashi. "ka shnye?" "minti daya, na kusa saura kadan". Ya kwalkwale ya aje kofn, "yauwa, na koshi". Tace, "good boy. To sai ka dawo ko?" "to me zan cewa zobenki?" "ina gaishe shi". Ya zura wa zoben ido, sannan ya sumbace shi yace, "wai yana amsawa". Tayi murmushi, "shikenan, tek care, ok?". Murya sanyaye ya amsa, "i will......." yayi dan jim, tace, "ina jinka!" ya rada mata, "I love u!". Ta dan numfasa tace, "me too!". Tayi saurn kife kan wayar. Da baya da baya ta tafi har ta jingina da kujera, ta wuce a natse ta zauna shiru, hannunta na gugar zoben yatsnta. A lokaci guda shi kuma al'ameen ya rataye kot dinsa, ya suri makullai da jaka ckn kuzari ya fito ya kulle gida, ya fada motarsa. Mai gadin rukunin gidajen ya bude masa get. Bayn sun gaisa ya mika masa dubu daya ya wuce. Mai gadi na ta murna tare da sa albarka. Shi kam kullm ckn sawa Dr. Al'ameen albarka yake, domin shi kadai yake masa alkhairi duk safiya, yace yaci abnci. Da ka dubi fuskar al'ameen zaka tabbatar yana tattare da farn ciki ba karami ba. Tamkar ynda mama ta kasnce babu sukuni sbd tsabar kewar al'ameen dnta. Bayn ta gama ayyuknta tayi wnka ta kimtsa, sai ta kwnta bisa gado ita kadai, bata aikn komai sai tunaninsa. Al'amarn kamar zai zautar da ita, domin da zarar ta tuna shagwabar sa, "GASKIYA BA HAKA AKE YI BA! Ba haka ake yi ba SAKEENA!! AI DAI BA'A SHAKE WUYA!". Ta kan yi kamar zata mutu da drya. Idan ta rufe ido shi take gani yana mata yawo tare da yin abnda yake fadi a aikace. Kai a hakikanin gaskiya al'ameen ya gigita zcyr mama, ita kanta ba zata iya fayyace ynda take ji ba game da so da kaunarsa. Duk ta kosa ya dawo ofis, don tabbatar zai sake bugowa taji muryar sa. Ilai kuwa yana shigowa gida biyar da rabi na yamma a gajiye, kai tsaye wayar ya dosa ya kira. Sai da yaji muryarta tsawn minti talatin, sannan ya daina jin kasala. Har ya sami natsuwar yin wnka, ya dan kwanta ya huta kamar ynda ita gimbiyar ta umurce shi. Haka suka kasnce suna renon jaririyar soyayyar su gwanin ban sha'awa. Ita knta anti rabi abin na birgeta har ta kan yiwa mama addu'ar Allah yasa ynda al'ameen ke ji da ita abin ya dore har ckn rayuwar aurnsu. Sun saba sosa, ba da mama kadai ba, da kowa na ckn gidan babba da yaro yasan al'ameen ta waya, kuma gaba daynsu babu wnda bai kosa sati ya kare ba, don al'ameen yazo su ganshi. Sai dai kash! Yanayn aiki bai shigo minna ba sai karfe takwas da rabi na safiyar asabar. Lallai ba karamin asubnci yayi ba, sbd tsabar kosawa kai tsaye gidnsu ya wuce. Kamar koda yaushe haka aka shrya masa tarba, amma sammaknsa yai matukar ba maminra mamaki, bata dai tmbaya bane don tasan daliln ba zai wuce na sakeena ba, sbd gaba daya wannan satin ita knta ta tabbata danta ya kusan zautuwa, duk wayar da zai bugo labarin sakeena yake bata. Suna gama gaisawa ya nufi kan waya, tayi zuru tana kallnsa tare da saurarn da wa zaiyi waya daga isowrsa? Tsammaninta ya zama gaskiya, iabin ran nasa ya kira ya shaida mata ya iso, kuma karfe goma insha Allahu yana nan karasowa. Dadi kasheta mana! Ta kamo su ameera abokn hirarta ta zayyane musu yaya zai iso anjima kadan, duk suka dauki murna da tsalle. Gagarumin shiri ya kankama, ta tsala ado na fita tsara. Kai mama akwai kyau, yarnya kamar aljana. Yaynta da anti rabi kansu kallnta suke yi, duk da cewar sun saba ganin ta, kuma sunsan mai kyau ce. Motsi kadan ta duba agogo, karfe goma taki yi mata sauri.!! Dan alkawarn kuwa goma daidai yana fakin a harabar gidan, abnka da dan gari adireshn da ta gaya masa tiryn-tiryn ya kawoshi gidn ba wata matsala. Ya fito yayi tsaye jikn motrsa,ba tare da yasan gimbiyr tasa na kallnsa ta tagar daknsu ba. Da alama bai san ynda zaiyi bane asan ya iso. Murya kawai taji a baynta ana fadin, "au leknsa ma kike yi?". Ta juyo a firgice, duk kunya ta rufeta, domin dai yaynta ne mai maganar. Tana murmushi tare da boye fuska a jikn labule tace, "a'a yaya". Yace, "zai fi kyau kije ki shigo dashi, ba leknsa ta taga ba". Tace, to, ta wuce simi- simi, yabi baynta da kallo yan 'yar drya. Ta kama hannayn yaran suka fito tare. Kiris ya rage al'ameen ya zube kasa, amma ilahirn jiknsa babu inda baya rawa. Da sauri ya tokare jiknsa damota ya zubo mata ido. Ita kuma sanyn gurin ne ya bugeta, ya ratsha ckn fatarta har ya tilasta wa tsigar jiknta tashi, sannan ta gane ashe bata dauko mayafi ba sbd daburcewar da tayi lokacn da yaynta ya kamata tana leke. Sbd haka ta duka ta dauki ameera, suka karasa gunsa. Fara'ar dole take yi a zahiri, amma gaba daya ta tsargu, sam bata ji dadn fitowrta haka ba. "oyoyo!" tace dashi. Ya sauke wawan numfashi, murxa a dishe ya amsa, "kema oyoyo!". Ya maida kallnsa kan yaran. Ya ci gaba, "ga abokina ameer, ga kawata ameera. Zo mana". Ya mika mata hannu. Da sauri taje gunsa tana drya. Ya mama ta iya? Haka nan ta dake tana jinsa da yaran, "wu! Kawata kina da nauyi sosai. Shekarnki nawa?" tace, "4" tana nunawa da yatnta. Yace, "kai kai kai! Gskya kin girme ni, amma don gata har daukarki ake yi. Antnki na sonki ko?". Mama ta watso masa harara, nufnsa ya ganota ne? Ko kuwa duk tsabar tsarguwar ce? Ita kuwa ameera drya kawai take yi. Ameer ya tmbaya, "dama kai ne yaya al'ameen din?" yace, "ni ne. Kana sona kaima?" ya makale a jiknsa yace, "ina sonka". Ya rungumo kafadarsa, "to Allah ya barmu tare". Yaynda ameera ita ma take faman fadin, "nima ina sonka yaya". Ya zura mata ido, yanaynta kamar sakeenarsa, nan da nan ya sumbaceta yace, "nima haka ameera ta!" Mama tace, "ya kamata mushiga daga ciki, surutn yarn nan ba zai kare ba". Ya zura mata ido baice komai ba. Tace, "muje mana" yace, "ai ke muke jira". Bata so ta wuce gaba, shi yasa tace, "Bismilla muje". Ya sauke ameera yana fadin, "bari in dauko muku tsarabarku ko?". Ya bude gidan baya ya kwaso ledoji 2 manya, ya mika wa ameera 1 yace, "to muje ckn gida". Yara suka yi gaba suka bar mama na ta nuku- nuknta.! Suna shiga falon kafin ya gama sallamar yaran ta sukake tabar falon, shi dai ya dagi kai ne bai ganta ba yaran suka wuce da ledar tsarabarsu. Ya aje ta hannunsa gefe ya nemi waje ya zauna yana maida numfashi domin har yanzu kirjinsa bugawa yakeyi shiyasa yana zama kasala ta rufeshi. Jim kadan Ya AbdulKadeer ya shigo tare da sallama Al-Ameen yayi wuf ya mike dauke da fara'a ya mika masa hannu suka gaisa suka tambayi juna aiki. Ya AK yace kuma harda dawainiya? Yace ahaba ba wani abu. Madalla an gode, zauna mana nizan dan fita ne saina dawo yace to a dawo lfy. Baiyi sakwan uku da zama ba Sakeena ta shigo jikinta rufe da mayafi hannunta dauke da tire cike da abubuwan sha gabansa ta aje, shi kuwa bai daina kallonta ba ta dago ta dubeshi suka hada ido tayi dan murmushi ta kauda kai, jikinsa ya kara mutuwa, Sakeena! Ya kirata a sanyaye. Ta kalleshi a nutse ido cikin ido suke kallon juna wucewar some seconds kafin yace "nayi rantsuwa zan iya rasa raina duk ranar da kikace ba kya sona" ta sunkuyar da kai shiru batace komai ba. Rayuwa zata yi min wuya muddin ban tare dake. Don naga misali within these 7days. Ba don inajin muyraki ba da bansan yanda zan kasance ba. Idanuwanta suka ciki taf da kwalla ta zura masa su tace sai ina gani kamar baka yarda dani ba dokta, meyasa? Kwallarta dake neman zubowa su yake kallo hankalinsa yayi tashin gwauron zabi ya kada kai. Yace ba haka nake nufi ba don girman Allah kar kiji min ciwo a zucia hawayenki daya na digowa zai zama tamkar tafasasshiyar dalma cikin raina. Nayi rantsuwa Sakeena tsananin sonki ke zautar dani yana sanyani sambatu ba tare dana sani ba. Kiyi min uzuri bayin kaina bane kuma bazan iya jurewa ba kin yarda dani? Take ta hadiye hawayen tace na yarda da kai da duk abnd kakeji nima ina jinsa. Kaga kuwa abnd yace doma ba zai bar awai ba. Ya danyi lum da ido ya bude tace rufe idonki. Ta danyi jim tana kallonsa kafin ta rufe idon. Gashin girarta baki wulik! Hakazalika na idanuwanta. Tasbihi Al- Ameen kewa Allah mafificin halitta wanda ya zana surar Sakeenar sa kafin yace bani labarin abnd kika gani. Tayi wug ta bude idon tace ni ban iya wann imagination din na ka ba. Nan da nan ya shagwabe fuska gsky ba haka akeyi ba! Ba haka akeyi ba sakeenan! Dariya sosai ta kubuce mata ya bita da kallo komai kara mata kyau yake yace gsky sai kin bani lbr kawai. Ta gyara zama tace to shikenan, ta rufe ido ya zura mata nasa idanun menene labarin? Tace wani busasshen likita zaune bisa kujera kaga gemunsa.......? Yayi saurin katseta bani bane sake wani! Ta bude ido tana yar dariya. Pls kabar maganar lbrn nan, kinsan Allah saikin bani lbr come on close Ur eyes! Ta dan numfasa ta dafe kirji, Oh ni ya su! Ta sake rufe ido tayi dan shiru yana kallonta meye lbrn? Tace duk inda ka duba tsaf yake cikin gidan haka dakin amaryar yake. Bansan yanda zan bayyana kyaun ta ba, daga nin wanda ya shigo ango ne adonsa ya bayyanar da kyaun surarsa. Gefenta ya zauna ya dauke mayafin kanta sannan yayi kiran sunan Sakeena! firgigi ta bude ido kamar an kira sunana? Ya kada kai a hnkli cigaba da lbrnki ba wanda ya kira ki. Tace ai nagama. Ya rumtse ido ya dafe goshi Ya Salam! Kin katsewa angon nan jin dadi gsky ba haka akeyi ba. Tayi murmushi ta matso gaban tire ta tsiyaya masa juice din ta bashi Ungo ka sha zahiri. Ya dan ware ido kina nufin nine angon? Sosai ma" yasa hannu ya karba yana fadin amazing watau nine angon? Ya kurbi juice yaci gaba "Hakika ban taba jin lbr mai dadin na yau ba" ko? Gsky ina ganin ma shiyasa Mami tace in kawo miki wadannan kayayyakin. Ya turo mata jakar ledar katuwar gaske tabita da kallo tace kai Mami harda dawainiya haka? Yace dan Mami ya zama ango kinga dole ta kawo kayan siyen baki koba haka ba? Ta dan rufe fuska ta bude tace hakane to nagode Allah ya saka da alhairi. Ya amsa da amin. "Amma kinsan wani abu? Nifa ban yarda labarnki ya kare ba, sbd haka ina binki bashi, duk ranar da na nema dole ki biyani". Tace, "Allah ko?" "ba sai na rantse ba, wannan dole ne". Ckn zolaya tace, "na'am?". Yayi 'yar drya yana kallnta. Shi yasa tana dago ido suka hada, tace, "ka ga yayana?" "naga yaya, har mun gaisa. Kunyi kama sosai, haka ma saurn suke?" tace, "haka suke". Yace, "bambancnku ido, naki kamar na agolan nufawa!" Fuska kumbure take harararsa. Ya kylkayle da drya, haushi ya isheta, bata san lokacn da ta figi filon kujera ta jefa masa ba. Ya ko cafe filon ya rungume a kirjnsa yace, "ni kika jefa?". Ta juya idanuwatana ci gaba da harararsa. Kai! Kamar ya zare yake ji. "ba komai, nima zan rama" ya fadi yana mata duban kauna. Sun kwarari hira kamar ba gobe, kawai basu ankara ba suka ji azahar tayi. Ko wannensu yayi sallah, ta kawo masa abnci da saurn kayan tande tande. Shi yasa ta kira masa su ameera suka ci abncn tare suna ba juna labari. Tabbas mama ta yarda al'ameen na son yara. Nama har na hannun ameera ci yake wnda ta tattauna ta gutsira ta sanya masa a baki, yaran na tare dasu har karfe 3. Anti rabi tayi sallama falon suka gaisa da al'ameen, sannan ta kada yaran don shirin islamiyya. Jimawa kadan suka fito, ameera sanye da hijabi. Tace, "yaya sai mun dawo!" yace, "daga ina? Come on kuzo nan". Suka ruga gunsa. Ya mika musu kunci, "oya kiss me". Kowannensu ya sumbace shi, shima ya sumbace su yace, "to a dawo lfy" suka ce, "nty bye-bye. Tana murmurhi ta daga musu hannu, ita ma tace, "sai kun dawo". Suka ruga suka bar falon. A lokaci guda mama da al'ameen suka kalli juna, suka yi murmushi mai isar da sako iri-iri. Mama tayi zugum! Tunaninta lallai idan al'ameen ya zama uban 'ya'ynta, tabbas za su sami kulawa. Saukar filo taji gum! A jiknta, kai ba karamin firgitata yayi ba. Ta dubeshi yana mata drya, "ai na gaya miki zan rama, me kike tunani?". Ta kara sakan masa harara, sannan ta dauke kai. Yace, "nasan tunani iri daya muke yi, ko ba tunanin 'ya'yanmu kike yi ba?". Ta sha mamaki, ta ynda take kallnsa kawai ya gane ya canki abnda take tunani.! Ya amsa da amin. "Amma kinsan wani abu? Nifa ban yarda labarnki ya kare ba, sbd haka ina binki bashi, duk ranar da na nema dole ki biyani". Tace, "Allah ko?" "ba sai na rantse ba, wannan dole ne". Ckn zolaya tace, "na'am?". Yayi 'yar drya yana kallnta. Shi yasa tana dago ido suka hada, tace, "ka ga yayana?" "naga yaya, har mun gaisa. Kunyi kama sosai, haka ma saurn suke?" tace, "haka suke". Yace, "bambancnku ido, naki kamar na agolan nufawa!" Fuska kumbure take harararsa. Ya kylkayle da drya, haushi ya isheta, bata san lokacn da ta figi filon kujera ta jefa masa ba. Ya ko cafe filon ya rungume a kirjnsa yace, "ni kika jefa?". Ta juya idanuwatana ci gaba da harararsa. Kai! Kamar ya zare yake ji. "ba komai, nima zan rama" ya fadi yana mata duban kauna. Sun kwarari hira kamar ba gobe, kawai basu ankara ba suka ji azahar tayi. Ko wannensu yayi sallah, ta kawo masa abnci da saurn kayan tande tande. Shi yasa ta kira masa su ameera suka ci abncn tare suna ba juna labari. Tabbas mama ta yarda al'ameen na son yara. Nama har na hannun ameera ci yake wnda ta tattauna ta gutsira ta sanya masa a baki, yaran na tare dasu har karfe 3. Anti rabi tayi sallama falon suka gaisa da al'ameen, sannan ta kada yaran don shirin islamiyya. Jimawa kadan suka fito, ameera sanye da hijabi. Tace, "yaya sai mun dawo!" yace, "daga ina? Come on kuzo nan". Suka ruga gunsa. Ya mika musu kunci, "oya kiss me". Kowannensu ya sumbace shi, shima ya sumbace su yace, "to a dawo lfy" suka ce, "nty bye-bye. Tana murmurhi ta daga musu hannu, ita ma tace, "sai kun dawo". Suka ruga suka bar falon. A lokaci guda mama da al'ameen suka kalli juna, suka yi murmushi mai isar da sako iri-iri. Mama tayi zugum! Tunaninta lallai idan al'ameen ya zama uban 'ya'ynta, tabbas za su sami kulawa. Saukar filo taji gum! A jiknta, kai ba karamin firgitata yayi ba. Ta dubeshi yana mata drya, "ai na gaya miki zan rama, me kike tunani?". Ta kara sakan masa harara, sannan ta dauke kai. Yace, "nasan tunani iri daya muke yi, ko ba tunanin 'ya'yanmu kike yi ba?". Ta sha mamaki, ta ynda take kallnsa kawai ya gane ya canki abnda take tunani.! Ya kada kai yana dan murmushi, "haka zaki haifa min su, nima in sanya sunan dady da mamyna ko?". Ta dauke kai don ya bata kunya. Yace, "no ba maganar kunya bace, ai daga ni sai ke ne anan, Allah shine shaida, shine kuma zai bamu muna zaune, tnda yasan muna so, muna kuma bukata. Ubangiji kasa hakan ya tabbata, kice min amin!". Ta kara kasa da kai, amma ckn randa da manyan baki tace AMIN.! Yace, "shikenan, ai nasan kin amsa, mata da irin nasu salon? Wanne ne al'ameen bai sani ba? Kice in rufe ido in baki labari". Tace, "bana son ji". "yarnya da kinsha labari, don sunaynsu kaf! Sai na gaya miki". A karkace ta kalle shi, bata dai ce komai ba. Zai kara magana tasa yatsnta 2 ta toshe kunnuwnta. Ya kece da drya, "baki son ji ko? Ai nima na fasa fadi, sai ranar tazo, da kaina zan yiwa idanuwan nan tiyata in cire kunyar". Ta mike tana 'yar drya, tace, "kaje kayi sallah, lokaci yayi". Yace, "yes madam!". Al'ameen kenan, tare da gimbiyarsa ya wuni zungur! Amma ganinta bai ginshe shi ba. Har abuja yasa ta kira waya suka gaisa da ya A-kadir da matarsa amina. Yarnsu daya mai sunan kakansu Isma'il, shi yasa ma suke kiransa Malami. Hnkaln al'ameen bai kwnta ba sai da ya amsa gaisuwar karamin yaya, watau A-rahman, ya gabatar da kansa, ya tabbatar da kowa na maraba da shi. Sannan ya kara samun natsuwa. Gab da kiran magriba da kyar da jibin goshi yayi ta maza, yayi sallama da kowa ya koma gida. Duk da haka sai da ya sake kirnta a waya da daddare. Tsoro mama ta rika ji, irn wannan sabo da al'ameen yayi da ita! Tabbas zai sha wuya idan ta koma makrnta. Tausaynsa ya zauna a ranta, don ba shi kadai ba har ita kanta zata ji jiki, domin kuwa dai al'ameen ya riga ya zama bargo da jini, kashi da tsoka, jijiya da fatar da suka hade suka zama SAKEENAH! BAKIN CIKI 1***7 Washegari ma kamar jiya karfe goma zuwa bayan sallar azahar. Tayo masa raki tare da su ameera, haka ya zura mata ido ya rasa inda zai tsoma tsumman ransa. Gajiya tayi da tsayuwar ta kada yaran tace, "ku wuce muje". "sakeena!" ya kirata, ta tsaya cak! Sannan ta dawo baya ta tsaya saitinsa. Bata kalle shi ba sai da yace, "pls ki dubeni sakeena" Ta dago su raurau da kwalla ta kalle shi. Yace, "ki taimakeni ko fasfot ne na hotnki ki bani na wuce dashi". Tace, "sai dai in duba maka wajn anti". "hnzarta don Allah ko na iya tfya". Da sauri ta wuce ta barshi da yaran. A daki ta sami anti rabi tace, "ki taimakeni anti, Dr. yaki tfya wai sai na kawo masa hotona". Tayi dan murmushi, "ai wannan likita naki sai a hnkali, je ki dauko album ki duba masa". Ta kwaso manyan album guda 4 ta darzar masa guda 2, daya nata, daya suna tare da su ameera. Ta nemo ambulan ckn takardn yayanta ta saka su ciki, tayi waje. Tana mika masa ya bude ya zaro su ya duba, yayi jim! Kafn ya sumbaci hoton, 'yar kunya ta kamata, ta kauda kai. "Sakeena!". Ta dube shi, yace, "na gode, kinga na sami abokiyar hira ko? Ga kuma abokina da babbar kawata". Tayi shiru, ya sake cewa, "kinyi shiru, are u jelous?" Da mamaknta tace, "na me?" "zan wuce da madam dina, kuma a gabnki na fara nuna mata love". Tayi dan murmushi, "lokaci na wucewa Dr. ban son dare yayi maka" Ya lumshe ido, ya bude yace, "zan tafi sakeena, sai munyi waya ko?" ta amsa da kai. Ya juya kan yaran, "to ameera, sai wani satin ko?" tace, "zaka kira waya?" "sosai ma. Ameer sai na kira ko?" suka yi musabaha ya tafi yana fadin, "to yaya?". Ya shige mota suka rufe masa, "Safe journey! Allah ya tsaye". Ya amsa, "amin SAKEENA TA! I love u". Tace, "me too". Ya yiwa mota key, ta janye yaran gida. Yayi kwana ya bar harabar gidan, suna yi wa juna bye-bye! Al'amura sunci gaba irn haka, kullm son sakeena kara zama yake wani wuri na musamman ckn zcyar al'ameen, tamkar ynda mama ke jin rayuwarta ba zata taba tfya daidai ba, ian bata jin ko da muryar Dr. nata ba. A haka ta kammala hutnta na sati 3, duk sati yake zuwa suga juna. Yau shine satin karshe da mama zata koma gida, daga can sai makrnta. Akwai alkawarn zata je gaida maminsa kfn ta koma, sbd haka tana zaune ckn shiri tare da 'ya'ynta 'yan rakiya. Karfe goma na safiya yana kofar gidan. Babu bata lokaci ya kwashesu ya aje katafaran gidan mahaifnsa. Suna ckn mota basu fito ba yake fadin, "saura ki shiga kina min kauyanci, sai nai miki allura a gaban mamin, inga tsiya" . Ta watso masa harara, kunyar me zanji? Muje ckn ka gani". Yace, "kamar da gaske" "uhm.... Bari ka gani". Ta bude murfn mota ta fito tana fadin, "ameer ku fito mu je". Ya fito yana drya, ya budewa su ameera kofa suka fito, ya kamo hannaynsu ya dubeta, "to muje ko?". Tace, "muje mana". Yana murmushi yana fadin, "ha! Ha!! Yarnya yau zanga ynda zaki yi a gaban surika". Ta yamutsa fuska tace, "kasan Allah zan koma". "to shikenan!" "wlh baki isa ba, idan na rika kururuwa ina ihu, duk sai na tara miki jama'ar unguwar nan". Ta bishi da kallo yana mata drya, ita kuma tana wani irin murmushi mai sace zcya. A zahiri ya ganota kunya take ji, shi yasa take 'yan kame- kame. Kawai fitowar mami suka gani, "oyoyo sakeenar mu!". Nan da nan ta daburce, kasa zata shige ko sama? Da sauri ta durkusa, "sannu mami!" ta mika hannaynta ta dago ta, "taso, taso muje". Ta rungumeta jiknta, "yan yarori sannunku da zuwa". Ta fadi tana kallnsu ameer. "shigo dasu mana". Ta wuce rike da mama, ya bisu da kallo kamar ya zubda kwalla sbd murna da farin cikn da ya lullube shi. Ya sauke numfashi, ya ja hannunsu ameera ya bi bayansu mami. Har dakn barci ta shige da mama, ta nuna mata kujera, "zauna nan!". Ta zauna kai a sunkuye, ya shigo da yaran, yaynda mami ke fadin, "ki saki jiknki sakeena, nan gdnku ne, kuma ni bana surukar, 'yata ce ke. Kinji?". Ta kara rufe fuska da mayafi tana dan murmushi, ta silalo ta kwashi gaisuwa, mami na amsawa baknta kamar gonar auduga. Yaran ma suka gaisheta, ta tambayi sunaynsu, kowannensu ya gaya mata. Kusa da mama al'ameen ya zauna baknsa har kunne, "mami ya kika ganmu? Munyi matchn ko?" tace, "ai kana zama kawai naji na kosa ta shigo gidan nan, yanda kasan in boyeta". Yace, "kinsan ynda za'a yi? Mu kulleta a wani daki, muce bamu ganta ba". Dariyar mama ta karu, ta kara sunke kai tana jan mayafi. Mami tace, "idan ma muka yi hakuri dan lokaci kankani ne, Ubangiji dai ya bamu aron rai da lfya. Kuma Allah yayi muku albarka, na gode kwarai da gaske sakeena. Duk mai son tilon dana gaskiya nima bani da kamar sa. Sbd haka ku rike amanar junanku, kinji sakeena?". Ta amsa da kai. Yace, "ina su Iya? Basu san amaryata ta iso bane?" tace, "suna kicin tun safe suke shirya mata abncin tarba". Ya mike, "bari in kirasu, ai ko ladi bata zo ba ya kamata Iya tazo taga amaryar dan Iya.!" tace, "maza jeka". Ya fice. Mami na masa drya, wannan amarya ana ji da ita. 'Yar dattijuwar na zaune tana yankar ganyen latas, ya fado yana kira, "ina Iya ta ne?" tace, "gani nan dan Iya". Ya tsugunna baynta ya yada kansa a kafadar ta, a shagwabe yake magana, "baki san amaryar dan Iya ta iso bane?". Ta kara fadada fara'arta, ta aje wuka, "ina na sani? Ynzu tana nan ciki?" "tana dakin mami, taso muje. Iya yau mu 2 zaki goya". Tace, "ya zama dole". Ta yunkura ta tashi tana kiran Ladi, "maza kizo amarya ta iso!". Tayi gaba ya biyota suka shigo dakin, yayi azama ya koma kusa da mama. "ya kika ganmu?". Ta rangada guda, daidai ladi na kawo kai, "lallai iya harda guda?". Tace, "abnda yafi guda ma zanyi ladi, wannan amarya zubin larabawa? Gskya dan iya kayi sabe, Allah ya tabbatar da alkhairi". Gaba daya suka amsa, amin. Shi kuwa ji yake tamkar yau yake angwanci, bai san lokacin da ya kai hannu ya rungumo kafadarta ba yace, "Iya kenan, mai raino na". Da sauri ta zame ta sulale kasa ta makure. Mami tace, "hayaniyar ta isa haka, aje a kawo musu abin sha" Kafn kace kwabo tsakar dakin mami ya cika da kayn lashe- lashe da jus kala-kala. Al'ameen ya zuzzuba musu, ya mikawa yaran. Sannan ya juya kan gimbiyar ya miko mata, taki karba. "nifa ban son kauynci, kinsan Allah zan miki dure!". Mami tace, "wai tsaya, bakuwarka ce ko tawa?" yace, "taki ce maminmu". Tace, "to tashi ka bamu wuri. Don me zaka dameta? Duk ka kanainaye min ita, maza tashi ka tafi harkoknka". Ya marairaice, "baki tausayina mami? Daga yau fa bazan sake ganinta ba sai karshn watan da zamu shiga, sannan ba waya ba komai? Pls mami ki barni in zauna". Ta tafa hannu, "ya Rasulu, ni indo! To bari in tashi, watakila ni take jin kunya". Ta yunkura zata tashi, "don Allah kar ki daka ta tashi, ki dauki komai ki ci, ki sha lemu kinji? Sai kinci kin koshi a gidan nan zan tabbatar kina son dan Aminu na". Ta fice, al'ameen din yana drya. Ya kara matsowa, "kinji abnda tace ko? Nima yau zan gani, kina sona ko a'a". Ya jawo tiran soyayyen naman kaji, meat pie, donat, lafiyayyen cincin da samosa, yace, "to Bismillah, iya cinki iya son da kike min". Ta dubeshi tace, "wannan wayau ne, a wane ckn zan zura tulin kayan nan?" yace, "oho! Ni dai na kare magana, kuma kina jin abnda mami tace". Tayi shiru tana kalln tire, kafn ta dubeshi, "don Allah ka tayani ci". Yayi 'yar drya, ya dauki samosa ya kakkara wa yaran. Ya sake daukar daya ya kai baknsa, "mu tayaki, kema fara ci". Duk kunya ta isheta, da kyar tasa hannu ta dauki meat pie, ta juya gefe ta gutsira. Ya zura mata ido jim! Sannan ya dauki kofin lemun ya miko mata, "sha in kara ganin ynda kike so na". Ta karba ta dan kurba. Ya jawo ameera jiknsa ya rungume, "kinga ynda antinki ke so na?". Oho! Ina ruwan ameera, me ma ta sani banda drya, tana amsawa da kai. Sai ga ladi dauke da wani tiren ta aje wani dan matsaikaicn kek da duminsa. Yace, "a gaida ladi". Tace, "likita irin wannan zaman da kake yi kyanshi a buga muku hoto". Yace, "ko ladi?" "gaskiya". Ya fice suna masa drya, jimawa kadan ya dawo da 'yar karamar kyamara a hannunsa. "ai kema zaki iya daukar mu ladi, ba wuya. Duba nan ki gani, saman nan kawai zaki latsa". Yana saitawa ya fara bada misali, sai dai kawai mama taji wal! Haske ya wuce. "ai kin gane ko ladi?" "na gane likita". Ya mika mata. Mama kuwa sai kalln ikn Allah take yi, ya dawo gefnta ya zauna, ya taro su ameera, ladi tayi ta yi musu hotuna. Wasu tare da yaran, wasu su kadai. Ladin ya tura ta kira mami, itama ta zauna suka yi hotunan tare, fadi take, "wannan shagali yayi kyau". Mama kuma bata sake ba sai da al'ameen ya tafi sallah. Sunci sun sha, sun bar gara birjik! Kamar ma basu taba ba. Kafn ya dawo ta gama shirin tafya. Ga ledoji tuli, kayayyakin da mami ta bata. "ban gane ba?" Ya tambaya, har da kama kugu hannu 2. Tace, "gida mana". Ya langabe kai, "gaskya ba haka ake yi ba, ba haka ake yi ba sakeena. Ai dai sai la'asar ya kamata ko?'. Tuni take ta drya zancnsa, kafn tace, 'ka manta yaya na jirana ne?'. Ya runtse ido tamau! "oh my God!". Ya bude ya kara matsota, ya zura mata ido, "kamar ki ta zama a gidn nan sakeena, bana so ki tafi". Ta sauke numfashi, "kayi hakuri". Yace, "yaya zanyi sakeena? Ya zama dole, amma ki bari zuwa karfe 3 sai mu tafi" "Allah yaya zai yi fada, kana so ya bata min rai ne?" ya kada kai, "bana son kowa ya bata miki rai sakeena, kin gama shiryawa?". Ta amsa, "na gama. Ka ga kayan da mami ta ba ni? Sunyi yawa Dr, kace ta rage". Yace, "me yasa ke baki ce ta rage ba?" "kunya nake ji" "oh, nine mara kunya kenan?". Tayi dan murmushi, "ba haka nake nufi ba yallabai". "to ai mami tasan kinfi karfn wadannan tarkacen ne, shi yasa ta baki su. Gaba daya shopping din makarnta ne. Bari in zuba miki a mota ko?". Tace, "na gode!". Sai ga mami ta shigo. "mami barin in maidata gida, yaynta na jiranta zasu wuce". Tace, "yana da kyau! Sakeena na gode, a gaida min mutan gidan. Insha Allahu duk ranar da na shigo fandagorin zanje mu gaisa da umman taki". Tace to. Ya kwashe kaya ledoji hudu, mami ta riko hannayen yaran suka fito, tayi sallama da su iya. Har mota mami ta raka su, tana tsaye suka fice. Suna tafe a mota suna hirar Mami, zcyar mama gwanin dadi, surikarta na sonta, kuma ta nuna mata kauna. Yayanta na waje yana ta faman duban agogo. Al'ameen yayi fakin suka fito. Yaran suka ruga gunsa, take nan suka fara bashi labarin ina da ina suka je, kamar shi ma bai sani ba. Bayan sun gaisa. Yace mama tayi sauri ta fito da kaynta, don shi a shirye yake, ita kadai yake jira. Ta shiga ciki da sauri dauke da kayan da ta samo, sbd tana so ta nuna wa anti Rabi, kuma ta dibarwa su ameer wani abu. Haka kuwa aka yi, anti rabi na ta sa albarka, ita kanta ta samu mayuka masu tsadar gaske, da turare guda 2. Mama da yara suka fhto da kaya suka zuba. Hankalnsa a tashe yake. Ganin suna satar kalln juna, shi yasa yaya yace, "ina zuwa". Ya shiga daga ciki don ya basu guri suyi sallama. Ya zura mata ido yace, "sai nazo visting, Ok?"tace, "shikenan, ina saurarnka". "zanzo miki da pictures din da muka dauka ki gani". "to". Suka yi shiru sai kalln-kalln suke yi. Idanuwnsa tam da kwalla yace, "gskiya gobe ba don da wuri zaku wuce ba, zuwa zanyi. Ban ganki ba, banji muryarki ba. Anya kuwa zan jure?". Haka nan nata idanuwn suka yi ja, ta bishi da kallo, amma ta kasa cewa wani abu. Motsin fitowar yayanta yasa tayi firgigi, ta wuce da sauri ta bude mota ta fada. Muryar anti rabi taji bisa kanta tana fadin, "to matar likita a sauka lfya, ace ina gaida umma da kyau da kyau". Tace, "zata ji". Ameera kuwa kuka take yi zata bi ta. Hnkaln mama ya kara tashi, tace, "yaya mu tafi dasu mana" yace, "islamiyya ce bana son suyi missing, kyale su kawai sai wani lokaci". Ya ja murfin mota ya rufe, yayi mata key. Al'ameen ne ya dauke ta, "yi hakuri kawata, anjima kadan muma zamu bi su". Bata yi shiru ba, amma ta rage sautin kukan. Suna kalln motar ta bar harabar gidan, ameera kuwa ta kara wage baki. Al'ameen ya jefata a kafadarsa ya rungune, kirjnsa shima sai bugawa yake. Shi kansa yana bukatar rarrashin, shi yasa yayi tsaye jiki ba kwari. Tsawn lokaci sannan ya dagota ya share mata hawaye. "Manta da anti, ba ma yi da ita, tnda ta tafi ta barmu. Yi shiru, yi shiru. To jeki wajen momi, sai na dawo ko?". Tace, "yaushe zaka dawo?" "duk lokacn da nazo garin nan zanzo insha Allahu". Ya ajeta gaban mominsu, yace, "anti zan wuce, sai wani lokaci". Tace, "to mun gode kwarai da gaske. A gaida mutan gidan". "zasu ji". Ya wuce yana dagawa yaran hannu. har suka iso fandogari mama bata cikin sukuni ranta bace yake kwarai. Ganin Ummanta yasa ta saki jikinta. Kowane sassa umma ta turata, tace taje ta gaishesu kuma ta gaya mata an sulhunta. Gab da sallar magrib uban dwk ya dawo daga Kd gaba 1 siyayyar skul yai mata bayan isha' suka taru a falo suna cin abnc. Umma ta baje masa kayan data sami a gidansu al-ameen yasa abarka,sann yace ta aje su tukunna. Umma tace a'a Alh naga akwai abubuwan ci wadanda zasu iya lalacewa, yace banason amsar kayayyakin nan amma bakomai ki bata wadanda kike ganin zasu iya lalacewa kibar sauran. Tayi murmushi Alh ho! Abdulkareem yace danAllah kubar mata kayanta tayi amfani dasu. Menene? Aiba fata akeyi ba kuma sani kanka ne Abba babu abnd zai gagara koda an sami akasi karka da mu Abba. Nasan surutai sunyi yawa akan mama cikin gidannan haka bazai hana ta amsar kyauta daga masoyinta ba. Yace Allah ya shige mana gaba suka amsa da amin. Yayan yaci gaba da fadin gsky yaron nan yana son mama kullum waya sau 2 sau 3 wkend kuwa idan yazo tun safe sai yamma. Umma tace ai ta kare kuma tunda ba a waya a makaranta Abba yace baki tausayinsu kenan? Tace ina ruwana? Suka fara dariya mama ta hada rai. Abba yace ni inaji kyaleta kinji yar Abba? Ta kara matsawa gunsa ta lafe. Yaya yai yar dariya yace abin harda shagwaba? Ido kamar an matse kwado ba inji Umma. Duk suka fashe da dariya ita kuwa kukan shagwaba takeyi. Washe gari da sassafe karfe 8am tare da yayanta suka iso gidansu baraka sbd shima yanason ya gaida innarsu. Ta kuwa ji dadin zuwansa ita da megidanta su kuwa kawayen suna can kebe lbr ya tsunke kamar kurna na zuba. Ita dai baraka wangame baki kawai tayi tana mamakin wann kasaitacciyar soyayya data kullu cikin kankanin lokaci. Tabbas ta shaida domin itama na tattalin kayan skul da mama ta kawo mata sun ishe ta tafiya skul. Jaka inna tasa albarka banda alhairin da AK yai mata da megidan. Kafin ya gama sallama dasu inna mama da baraka sun sulale sun tafi gidan goggo wato kakar alameen. Harda manya goro guda 10 suka satowa inna cikin wanda take siyarwa Goggo ta nuna nata murnar taga kishiya suka bata goro ta amsa ta jujjuyashi tace na toshiyar bakine wann? Lallai kinsa in bar miki mijin. To naki wayon kenan? Suna ta dariya suka fito ta rakosu har zaure tana sa musu albarka. Suna fitowa suka hangi yaya tsaye yana jira suka karasa da sauri, yi hakuri yaya. Ina kukaje masu yawon tsiya? Baraka tace mun danje wajen wata kawarmu ce. Yace I see.. Daga zaure inna ke fadin kaji karya ko? Ni nasan gidan goggo Hausi sukaje kakar alameen. Ya kama baki yace Allah ya shiryeku. Inna sai wani lokaci. Ya bude mota ya shiga inna na fadin Allah ya tsare agaida Rabi da yara. Mama da baraka suka rungume juna sannan ta shiga mota tana yiwa inna sallama yaja suka wuce. BAKIN CIKI 1***8 Suna isowa gida, me mama zata gani? Motar al'ameen aje gefe guda. Gabnta ya yanke ya fadi, haka ma yayanta ke mamaki, "wannan ba motar al'ameen bace?" "ita ce yaya". "mama biyoki yayi?". Tayi shiru tana 'yar drya. Yana fakin yabe fadin, "kai wannan mutum yana damun kansa da yawa. Pls ki gaya masa ya rage sonkh, kaq ya zame masa illa". Ta sauke ido kasa tana murmushi, tana kuma murzar zobensa da ke yatsanta". Yace, "je ki mana, tnda ba zaki iya gaya masa ba". Tace, "yaya kenan". Ta fito yaynda yayan ke fadin, "nayi laifi ko?". Ta kada kai, "a'a wlh". Ba shi ckn motar, sbd haka ta tabbatar yana falo. Don haka ta wuce ckn gida. Ido waje tana magana, "umma sai naga motar al'ameen a waje?" tace, "nima haka abbankuya gaya min. Yana can falo tare da alhajin"". Ta nemi waje ta zauna har da tagumi. "au zama kuma zaki yi?" "ummi kince suna tare da abba, sai kuma imje?" tace, "to zauna. Amma kinsan dama ku yake jira ku dawo ya maida ki makrnta ko?". Tayi shiru. "saura kije ki shantake da surutu. Sannan ki gaya masa don Allah ya rage sonki, zai iya zame masa damuwa". Tuni take kallon umma ido waje, har ta wuce ta bata wuri. Ta zabga tagumi hannu biyu zugum! Tunaninta yaya zata yi ta dumfari al'ameen da wannan maganar? Tabbas ita kanta tasan al'ameen ya makance a sonta, da zai rage din da zata so hakan, don bata son duk wani abnda zai raunana mata shi. "Mama!" taji an kwala mata kira, ta dawo daga duniyar tunani firgigi, ta dubesu tsaye bisa kanta. Abba yace, "tunanin me kike yi?" tace, "ba komai abba". "to yana falo, kiyi sauri ki ganshi muce. Wai rokona yake in barshi ya kaiki, tnda duk hanyar daya ce. Nace masa a'a, ya barshi yaje gun aiknsa". Jiknta ya kara mutuwa, ta juya salalau-salalau. Yayanta na fadin, "ni dai nace ta gaya masa ya rage sonta. Dis is 2 much!". Abba yace, "duk wannan ma bai taso ba, amma a ganshi tare da ita a mota, ai zan shiga bakin duniya, kuma daga ckn gdn nan maganar zata fara. Ba ni a ckn wannan tsarin, ba wai kuma don ban yarda dashi bane. Je kayi wanka kayi shirn komawa". Ya wuce, shi kuma ya wuce sashn da ya kwana don yin wanka. Kwalla ta tsaya take sharewa a kofar falon, zallar tausayn al'ameen ne ya tilasta mata zubar su. So ba zai taba zama laifi ba, amma ya kamata al'ameen ya rika bi a hnkali, kar son da yake nuna mata ya zama laifi a wajn iyaynta. Sai da ta natsu sosai ckn ranta, sannan ta tura kofar ta shi shiga tare da sallama. Ya amsa yana kallnta, ta wuce ta zauna rai bace. Da sauri ya matso gunta ya tsuguna, "da inga irhn wannan fuskar taki gara na kwanta gadn asibiti sakeena. Gaya min waye ya taba min rayuwa ta?". Gaba daya tsigar jiknta sun tashi, ta dan numfasa tace, "kai da kanka ka tabani Dr." "ni? Me nayi?" "nasan kana sona Dr, ni kaina zan iya dafa Kur'ani in rantse. Wlh yadda kake ji haka nima nake ji. Bana son kana tsananta damuwa ckn son da kake min, domin ina jin tsorn kar wani abu ya illata min kai. Ganinka da nayi yau ya fadar min da gaba ba kadan ba. Wnda ya tabbatar min cewa zaiyi wuya jiya in kayi barcin kirki, sbd ba muyi waya ba. Me yasa? Kar ka mance makrnta zan koma, inda ba waya, sai fa in kazo visiting. Kana nufin ba zaka yi sukuni ba tsawn wannan lokacin? Rashn sukuni ba shi zai tara maka damuwa ba? Kai fa likita ne. Ka gaya min me yawan sa damuwa a rai yake haifarwa?" Yayi zuru yana kalln ynda idanuwnta suka kawo kwalla. Ta kara fadin, "tmbayarka nake, ka gaya min?". Ckn sanyin murya yace, "abubuwa masu dama da kan iya nakasa lafyar mutum. Amma kar kiga laifina sakeena, sonki nake yi". Kwalla suka malalo bisa kuncnta, lebe na rawa tace, "yayi yawa Dr.! Ka rage don Allah, bana son na rasa lfyrka". Tasa hannaynta da sauri ta rufe fuska, ta ja numfashi mai sarke da kuka mai tsuma rai. Wani kululu ya tokare masa wuya, kansa ya dau zafi, zcyrsa na zugi tare da tashn hnkali. Da kyar ya kalato miya a baknsa, ya iya fadin, "SA... SAKEENA!". Ta dago ido jajur! ta dubeshi. Ya mika mata hankicif, "don girman Allah ki gnge hawayn nan Sakeena. Kin kuwa san ciwon da kika dasa min yazu? Komai zai iya faruwa dani, muddin hawaynki ya ci gaba da zuba". Tasa hannu ta karba ta goge kwallan ta numfasa ta dubeshi a hnkl alkawarin da mukayi wa juna Allah zai tabbtr mana dashi nima ina sonka Dr. Ya koma dirshan ya zauna farin ciki ya mamaye zuciyarsa yace duk jawabin ki na yarda dasu sakeena. Kuma zan kiyaye shawarwarin da kika bani, tare da yin adduar Allah ya sanyaya min zuciyata duk lokacin da ciwon son ganinki ya kamani, rokona gareki shine ki taimakeni ki daina zubda hawayen ki ko alama banason ganinsu. Tace daga yau bazan sake ba, muddin ina ganin ka cikin nutsuwa. Yayi dan murmushi an gama my princess. Tace to yanzu ka tashi in rakaka ka kama hanya ka isa wajen aiki da wuri. Yace a'a kar muyi haka dake kije ki shirya ku fito kina gaba a motar Abba ni kuma ina take miki baya. Kash! Saidai babu jiniya dana makala kowa yaji ya kauce hanya gimbiyata zata koma skul. Ko ba haka ba? Ta dan shagwabe gsky ba haka akeyi ba, ba haka akeyi ba Dr! Aidai zaka sa Abba yayi min fada. Ya zura mata idanu yana dariya to shikenan bari inyi gaba tunda kin amince min..... Ka zama prince ba ta tari numfashinsa. Ya kara rausaya kai ah! Lallai ngd. Ya mike to muje ki rakani. Ta tashi suka jero na shiga na gaida goggo. Ah haba yaushe? Dazu da mukaje gidan Inna ta da yaya. Amma kin kyauta naji dadi nima idan nabar nan zan shiga in kai mata cfane karfa kiyi kishi. Tayi yar dariya aini bana kishi da goggo, sbd me? Ya tambayeta yana kallonta ido cikin ido ta bashi amsa sbd aronka na bata! Ya fashe da dariya zan kuwa gaya mata idan ta zauneki ba ruwana. Sukaci gaba da dariya har gaban mota ya bude ya shiga ta rufe nasa "take care" Allah ya tsare. Ameen kikace arona kika ba goggo ko? Ta tura masa hula gaban goshi ta ruga cikin gida yabita da kallo duk kasala ta rufeshi. Ya sauke wawan numfashi ya gyara zaman hular yana kada kai fuskarsa dauke da murmushin kauna. Yayiwa motar key yayi ribas zai wuce kamar walkiya ta bullo ta daga masa hannu da sauri ya dago nasa fara'arsa ta karu. Hanklinsa ya kwanta yaga abar sonsa. Bayan ya gama da goggo da kanta ta kaishi ya gaida inna daga nan ya tambayi baraka don ya sha jin lbrnta a bakin mama. Ta fito suka gaisa babu wanda baiyiwa hasafi ba musamman baraka da yake ganin zuwa wajenta shine silar haduwarsa da mama yarinyar da yakeji tamkar itace ransa. yana fitowa ya shige mota ya doshi babban titi yana kawo kai motar Uban dwk na hayewa kwalta. Abba bai sahida shi ba Amma ita mama tuni suka hada ido sukaiwa juna murmushin mmki nan da nan ya takewa motarsu baya wann sa'a da yawa take (dan anace saida ya bitan kuwa). Cikin kuzari yake tukinsa suna tafe yana biye dasu a hnkl har zariya daidai shataletalen kofar doka take cewa Abba ko kasan Al-ameen na binmu a baya? Ya dan dubeta kadan ya juya bansani ba ina yake? Tace gashi can bayanmu ai tun daga fandogari tare muke. Yace oho! Nidai ina ganin mota tana bina a baya- baya ban ganeshi ba. Kofar get din asibitin (A.B.U.T.H ZARIA) daura da kamfanin maizar nan sukayi fakin kowa ya fito. Ashe kai ke bina a baya? Ya dan sunkuyar da kai yace ai ina fitowa gidan kakata na ganku. Yace yayi kyau to bari mu wuce aikai ka iso gida ya amsa eh yana satar kalllon mama. To shikenan mama mu wuce . Ya koma cikin mota itama ta shige yayi azama ya rufe yana fadin a sauka lfy Abba. Ya amsa amin. Idanusa na kan mama sukaja suka tafi. Alameen ya kama aiki kamr yanda mma ta maida kai ga karatunta amma zukatan suna cike da tunanin junansu. 43 days cif da komawarsu kasancewar sun koma a tsakiyar mnth shiyasa ba ai musu visiting ba sai nxt mnth ending. Kai sun sha wuya musamman dr da yake ganin kamr 43yrs sukayi ya kosa sosai yazo domin lahadin ce yake rawar jikin zuwa yaganta. Isowarsa kenan da safe ogansu na sashin Doctors ya kirashi ya mika masa takarda tare da cewa zai representing dinsa a taron fida na arewa wanda za*ayi a bauchi. Nan take hnklinsa ya fita daga jikinsa a kasalance ya dawo office dinsa ya cilla paper din on table ya dora hannu aka kamar ya kurma ihu sai innalillahi kawai yake furtawa! Wayyo Allah na shiga 3! Tamkar ya mutu. Jiyayi anyi knocking table dinsa ya dago ido jajur! Ya dubi mutumin dake tsaye yaya dai? Yayi guntun tsaki yace dr lawan yaushe ka shigo? Yace jst nw menene? Yace noting kawai banson zuwa bauchin nan ne gsky ina da abinyi wkend dinnan kuma idan ta raya min zanki zuwa saidai mu kwashi yan kallo da prof! Tofah. Ya ware ido sosai yace kai lallai kana neman barin kujerarka! To don me? Yace ba damuwata bace..... Ya katseshi look Alameen ban taba jin haka a bakinka bana tabbata uzurinka me karfine amma karka bata 10 1 bata gyaru ba. Kayi hakuri kawai! Kai tsaye yace bazan iya ba! I want to see her! Raina namin ciwo sosai konaje seminar nan oga bazai sami bayanin da yake bukata ba. Ya bude baki yace mutumina kace U re in luff kawai! To menene prob din? Nxt wk basai kaje ba. Yace bazai yiwu ba boarding skul take sunday za'ai musu visiting day idan ya wuce sai nxt mnth, mundade bamuga juna ba. Cool dwn dr naga ka harzuko dayawa amma shawarata kawai kayi hakuri. Itama bazata so taji ka sami prob da aikinka sbd ita ba, I believe she wl understand ur excuse duk ranar daka gaya mata.n Yaysi shiru yana nazarinmaganganun hakika yace wani abu daya tuna irin nasihar da sakeena take masa akan ya daina matsantawa akansa akan soyayyarsu somin sun amince da juna. Ya numfasa yace na hakura dr lawal, sky da hnklina yayi mugun tashi ina bukatar ganita dr. Aikai kana da mata kasan sirrin abun. Yayi yar dariya ya buga kafadarsa mutumina ka tashi daga dr ka koma mr lover-lover tunda dai ka amince bari na koma office. Yaushe zaka tafi? Idan mun tashi I.S.A. To a dawo lfy ya amsa ameen. Ya wuce yana me lover-lover! Yayi dan tsaki yace kp quite my frnd! Yayi dariya ya fice. Ranar lahadi cikin skul kowacce kagani tana cike da farin ciki sbd yau zasu ga mutanen gida wuri ya rincabe da baki kala kala sun zauna ana hira da ciye ciye kusan mama ce kadai ke kaiwa da komowa tana bilayin neman ta inda dr zai bullo. Wanda dalilin zuwansa ne yasa ba wanda yazo mata daga gida. Amma har la'asar ta bada baya ba lbrnsa. Tun tana fitowa har tay zamanta cikin hostel. Tunaninta meya hana shi zuwa? Babu amsar data fara zuwa ma ranta sai wata gagarumar matsala ce ta rashin lfy. Anya kuwa rashin lfy zata iya hanashi zuwa yau? Kai babu makawa yana kwance ranga ranga baisan hakin da yake ciki ba nan take hawaye suka tsnike mata harda na zuci kanta yayi dum! Har cikin idonta takejin ciwon har dare tana kudundune a gado duk iya rarrashin da frnds dinta sukayi a banza. Bata iya cin komi ba sai jiri ke dibarta idan ta tashi sallah ba bacci jikin yaci gaba da dumamewa kafin safiya ta kwana a skul clinic. Wasa wasa fa mama jiki yaki dadi. Kwananta 2 a asibitn makarnta, amma abu kullm kara gaba yake. Zazzabi, ga rashn cin abnci. Ko an matsa mata amayar dashi take yi, duk ta galabaita ta fita hayyacnta. Ganin haka yasa shugabar makrnta ta tura babban asibtin koyarwa dake zariya don ta sami kulawa sosai. Nan take aka bata gado, metiro din hostel ke jinyarta. A wannan ranar biyar na yamma Dr. Al'ameen da Dr. Lawal suka hadu a ma'ajiyar motoci, kowanne yayi fakin ya fito, "Ah! Mr. Lover!". Fuska ba walwala yace, "Don Allah ka daina, kar ka ynka min sabn suna". Ya matso yana masa drya. Suka tafa, "to ya aka yi? U look very weak, me ke faruwa ne?" "menene ma bai faru ba? In gaya maka tnda na dawo Bauci bani da lfya, kawai bankadar magunguna nake yi kar in kwnta warwas!". Ya nuna shi yana masa drya, "bebinka ko? Come on kar ka damu, zaka ganta da zarar wata ya kare. Zaka rnd ne?" "no, kawai na fito ne sbd bana son kwnciya a gida, tunani ke damuna" "ok, to zo ka raki ni female ward in duba wata yarnya da na kwntar dazu da safe. Na barta uncncios, ban sani ba ko ynzu ta fara gane mutane". Yace, "ba matsala, muje". Suka wuce yana fadin, "ai naji oga yana ta fada, wai report din nan kamar ba kai ka rubuta shi ba". Yace, "kyale dan rainin wayau, nima ina jinsa tn jiya ya fara conplain. "Dr. Lafai ka kuwa zauna wajn seminar nan? Naji kana kame-kame ne?". A raina nace, "ai sai kayi, wa yace kaki zuwa da kanka? Ai kadan ma ka gani ckn aikn magudi". Dr. Lawal ya kama drya, "bansn ka da haka ba mutumina, gskya wannan baby ana ji da ita" "sosai ma". Suka fada dakin ckn natsuwa. Kai tsaye wajn gadn sabuwai mai jinyarsa ya dosa, al'ameen na biye dashi. Tana kwnce rabin jiknta na rufe, gaba daya ta rame, fuskarta ta tsuke kwarai. Alameen bai gasgata idonsa ba shiyasa ya runtse ya sake budewa yayin da dr lawal ke tambayar mai jinyarta yaya dai mama? Ta kuwa tashi? Tace har yanzu dr amma da aka yi mata allurar dazu ta motsa. Dokta lawal bai kara fadin komi ba sbd mamakin yadda Alameen ke zare ido yana takawa a hnkl bakinsa na ambatar Sakeena! Jnkl tashe ya kalli dr lawal yaushe aka kawota? Yace dazu da safe kasanta ne? Sakeena ce. Yace yes sunanta kenan. To ai itace nake baka lbr. Baki sake yace kai danAllah? Ya dubi mama kamar yayi kuka meya faru da ita mama? Tace kawayenta dai sunce tun ranar lahadi wai ko babu wanda yazo wajenta visiting shine take ta kuka taki cin abnci har abin ya zame mata ciwo. Ina ganin ma principal ta aika aka gayawa iyayenta don suzo suga halin da take ciki. Tuni ya nemi kujera ya zauna yana fadin Innalillahi......! Kaga irnta ko dr lawal? Yace be a man karka manta acikin ward muke ido jajur yake dubansa dame-dame ka shirya mata? Yace karka damu duk abnd ya dace na riga na bata duba folder din kagani. Ya karba hannunsa na rawa ya karanta abnd ke rubuce dole tasa ya gamsu da abubuwan da dr lawal ya shirya mata don yasan abnd yake. Amma da son samu ne a bata maganin da zata warke yanzu yanzun nan shi yake so. Ya mika masa folder yace is this ur only plan? Yace zomuje daga waje... Hodijan! To nima zanyi daga wajen office sai kuma naje gida In Shaa Allah! Al'ameen yace, "no! I cnt go any where. Dr. Lawal je ka gama aiknka ka koma gida". Maman mkrnta bata gane ba, don haka ta tambaya, "haka dai kasn sakeena ne?" Dr. Lawal ya bata amsa, "shine wnda zata aura, kuma likitnmu ne a nan asibitn". Da mamaknta tace, "ba shakka! Lallai baiga ta tfya ba, sai yaga mata ta mike. To Allah ya taimake mu, ya kawo sauki da gaggawa". Suka amsa da amin. Ya kai hannunsa ya dafa saman goshnta, ya zuqa mata ido, ckn zcyrsa kuwa tambaya yake, "why? Why Sakeena?". Ya kada kai yayi dan tsaki ya sauke numfashi mai dauke da hucin zafi. Anan Dr. Lawal ya bar shi, haka maman makrnta ta bashi wuri, ta fito ta baza tabarma tayi kwnciyarta tana hutawa. Ya maida kallnsa bisa ledar ruwan da ake kara mata, kamar yasa hannu ya kara gudnsa ko zaisa sakeenarsa ta mike. Ya rike kai hannu 2-2, zufa yaci gaba da kwarara ckn jiknsa. Ya dago kai a hnkali ya ci gaba da kallnta, yana hadiye hawayn idanuwnsa. Ji yayi an dafa shi, muryar Dr. Lawal ke magana, "an kira sallah Dr." ya dube shi gwanin tausayi yace, "har ynzu fa bata farfado ba". Dr. Lawal yace, "come on al'ameen, ka barwa Allah komai mana. Taso muje muyi sallah mu dawo" ya mike yana ajiyar zcya, suka fice yana waignta. Cikn sujada ya dade yana addu'ar neman agaji wajn Allah. Tare da Dr. Lwl suka sake dawowa. Tun daga shigowarsu suka hngo maman mkrnta dafe da hannun da ake kara mata ruwa, kamar baknta motsi yake? Al'ameen ya kwaso sauri iya dire gabnta. Dr. Lwl na biye da shi, fadi yake, "matsa! Matsa mama." maman makrnta ta kauce da sauri. Ya zauna ya kamo hannun sakeena, yana kira. Ita kuwa sai zare ido take tana dube- dube. Bata gane inda take ba. "yaya dai?" Dr. Lwl ya tambaya. "she is back!" ya bashi amsa, jiknsa na rawa. Gaba daya suka dauke hnkaln masu jinyar dakin zuwa gare su. Kowa sai kallo yake yana Wa kansa tambayoyi. Alameen kuwa kira yake sakeena! Sakeena! Ta zura masa ido sannu a hnkli brain dinta ta ta dawo aiki idanuwanta suka fara washewa face din da takeson gani ta bayyana a idonta shiyasa ta rage kallon da take masa yace nine sakena! Kiyi magana naji hawaye suka tsinke mata shar! Shar! Ya zaro hankici ya shige share mata. No pls karkiyi kuka my Queen! Dr lawal ya yafito maman skul da hannu ya juya suka fice ita kuwa sakena kallonsa takeyi har yanzu bata gasganta abnd take gani ba. Nace ki daina kuka nine Alameen dinki. Kwallar basu daina sauka ba tace a ina nake? Ya hadiye hawayen da suka cika masa ido yace asibiti ne sakena me yasa zaki kwanta ciwo? Tace dama lfyrka kalau ka kasa cika min alkawari? Ba haka bane sakena ogana ne ya turani seminar bauchi ba yadda zanyi ne kinsan yanayin aikin kuma dole nayiwa shugabana biyayya. Ta runtse ido ta matse hawaye sannan ta bude tana kalllon sama tace Allah nagode maka daka sa tunani na ba gsky bane. Ta maido kallonta gareshi taci gaba, gaba 1 tunanina ya tsayane ga rashin lfy ce kadai zata iya hanaka zuwa guna na yarda na amince da hakan kuma zuciata tana kara tabbatr min kwance kake magashiyan. Bansan ciwon nan ya kamani ba dr amma nasan yawan tunanina da tsananin da zuciata ta shiga.jikinsa ya kara mutuwa tausayinta ya kara lullubeshi ki yafe min sakena ISA bazan sake ba ni kaina naji ajikina na tsananin rashinki, tace ba laifinka bane Allah na yarda daka kai farin ciki nakeyi da Allah ya nuna min kai cikin koshin lfy. Yadan numfasa yace ngd sakenata zaki sami sauki a hnkl dr lawal ya shirya miki magaunguna masu kyau da zasu taimaka ki samu sauki kuma ga Alameen dinki a kusa dake. Go to Home BAKIN CIKI 1***9 Ta dauke kai tana murmushi. Ya bita da kallo yana jin kamar ya tsaga zcyrsa ya saka ta. "sakeena!" yayi kirnta, ta juyo ta dube shi, "ya zaki juya baki ce min komai ba?" ta lumshe ido. "ko ganina ba zaisa ki warke ba?". Bata bude idon ba ta amsa, "sai dai in jikaka likita in sha". Yayi 'yar drya, "ko? To in shiga bokitin can kenan?" "Um" "zan shiga fa! Da gske nake yi. Kin wani rufe ido, ko labari zaki bani" "uhm...." ta sake fadi. Ya gyara zama yace, "to ina jinki, bani in sha". Tayi shiru, "ko barci kike ji?" ta bude ido ta kalleshi, idanuwn ta sun dan kada. Ya kura mata ido, "yaya dai?" ba komai" "a'a sakeena. Me ke miki ciwo?" "kar ka damu" Ya kara matsowa, "ba zaki gaya min ba? To wa kike so ki gaya wa wnda ya fi ni? Ki gaya min shi in kira miki shi" tace, "cikina ne kawai ba wani sosai bane. Dr. Nasan zai daina". Rai bace yace, "ya aka yi kika sani?" tace, "sbd ina ganinka Dr. Allah kar ka damu, ba sosai bane". Ya dafe goshi tare da sauke numfashi, "da akwai maganin da yafi wannan da na baki sakeena!". Ta yunkura tana kokarn tashi, "ina zaki?" "zan tashi zaune ne, don in nuna maka na ma warke" "no, ki kwnta na yarda kin warke". Ya sa hannu ya maida ta, ya kara ja mata mayafi, "kinsan abnda nake so da ke?" ta kada kai. "duk snda aka sami mishkila baki ganni ba, don Allah ki daina mummunan tunani a kaina. Kin ji?". Tace, "insha Allahu bazan sake ba". "kinga haka ake yi, idan ban ganki ba inyi hakuri, haka kema in baki ganni ba kiyi hakuri. Shikenan baza muyi ciwo ba ko?" "gskya ne. To bani labarin Bauchi. Ya garin yake?" "bansan komai ba game da garin, domin nima a yamutse na shige shi. Bansan ko'ina ba, daga dakin taso sai dakin barci na......." "gaskya ba haka ake yi ba, ba haka ake yi ba Dr.". Ya dan murmusa, "ya ake yi sakeena?" "ni dai ka bani labari" "ok labari? To saurara kiji". Ya lumshe eyes ya zazzage mata halin da ya shiga, kaf a bauchi. Ya bude idon a hnkali, suka kura wa juna eyes, "kinji labarin?" "naji, amma wane bayani ka rubuta a wannan shiriritar?" "me kuwa banda shiriritar. Kinga shi bai sami abnda yake so ba, nima ban samu ba" "magudi ko?" "ba shi bane. Allah haushi ya bani" "nima haka" "Allah ko?" "ah! To bambance min zukatan" yayi drya ya lakuce mata hanci, "kin kureni". Ta kauda kai tana murmushi. Hira fa ta tsinke, sun ma mance inda suke. Dr. Lwl ne ke tsaye hannaye ckn aljihu, sannan al'ameen ya dago ya dube shi. Yayi murmushi, "mr. Lover lover, kace ba haka ba, ynzu sbd Allah bayn likita, kai wanene?" yace, "al'ameen ofcourse! Ko my princess?" "ahaf! Ita tana ma da bakn magana ne? Ta dare min gadn patient, ashe duk karya ne lfyrta lau". Suna drya yace, "banda sharri" "tsakani da Allah haka mai ciwo yake? Well ku dai kuka sani. Ni zan wuce gida" "da wuri haka?" "da wuri? Lallai ne. To duba agognka ka gani". Ya dubi agogo cike da mamaki, "12 saura kwata?" "kana tmbaya ne? Baka yarda ba kenan". Yayi shiru yana kalln mama. Dr. Lwl ya kara matsawa yana duba ta yana fadin, "ina fatan dai kayi issha'i?" "ina fa! Shi yasa nake mamakn gudun lokacin". Yayi rubuce2 ckn file din, ya rufe "ina zaka san lokaci na gudu, kana kalln mai kyau. Nan zaka kwana?" "yes, amma bari muje nayi sallah. Sakeena inje inyi sallah ko?" tace, "maza hnzrta". Suka yi sallama da Dr. Lwl yana ta yi mata tsiya, sai da taja mayafi ta rufe fuska sbd kunyar maganganunsa. Sun fito dr lawal ke tambyrsa donAllah ina ka samo wann sarauniyar kyau haka? Yana murmushi yace itama yar niger state ce iyayenta yan fandogari, yace gsky yarinyar tayi ko kasan na kusayin barmbabama? Kamr yaya? Yace aini nan na dage ne iya karfina in samu ta warke saina gabatr da kaima. Yaja ya tsaya ya watso masa harara me kake nufi? Ya kamoshi yana dariya a'a dr maida wukar pls! Aini an wuce nan wajen tunda dara taci gida. Trust me wllh tuni na janye kudurina kasan ni banda rufi ya fizgoshi come on mu tafi mana ai ya wuce. Yace bakikkirin nake ganinka bazan iya jerawa dakai ba in banda iskanci ma last year kayi aure hange-hangen me kakeyi? Ya kyalkyale da dariya karkayi zato ba daina son matata nayi ba nikaina bansan abnd ya rikitani ba amma ina baka shawara ka gayawa sakena ta rika sa nikab kyaunta is too mcuh gsky! Ya murtuke duk kishi ya cikashi ya dunkule hannu ya nunashi "kayi sa'a kaine wllh dana farfasa maka baki!" Yace fasa mana nima nasan I deserve it but is nt my fault. Alameen yace u noe wat? Ka kyalemin ita ni zan dinga duba kayata. Kaga kuma inda baka isa ba kenan, ya zura masa ido yace I noe wat to do! Ya wuceshi da sauri yana kwafa. Dr lawal ya bishi da gudu yana fadin do ur best my frnd ina maka fatar Allah yasa sakeena matarka ce. Suka jeru suna kaoon juna ya amsa ameen ameen kuma ya isheka haka! Ya fashe da dariya suka tafa mr lover lover! Suna tafe yana tsokanarsa. A taikace Alameen nan ya kwana duk da mama ta roke shi akan ya koma gida abinsa amma ya kafe don yasan ko ya koma gidan hankalinsa bazai taba kwanciya ba balle ya samu yin bacci. Kafin a sallameta sai da iyaynta suka samu labari, suka isa asibitin. Bayan taji garas aka sallameta, principal da kanta tazo da mota aka wuce da ita makrnta, suna ta kewar juna da Dr. ****** Karshn wannan watan Allah ya yarda ya sami zuwa mkrnta ganin sakeenarsa. Wuri na musamman ta tanadar musu, shoppn kuwa har maman da tayi jiyyarta sai da ta samu. Sun tsunduma ckn hirar dnya ckn jin dadi da farntawa juna rai. Har gaba da azahar yaya Abdl-kareem da yarnsa suka iso. Kawai ji tayi nana kirnta wai tayi baki. Tana isowa ta hngo su ameer, ta kwaso gudu ta rungume su, suna ta murna. Ta koma gun yaynta tayi masa sannu da zuwa tare da tmbayar anti Rabi. Yace, ita ma taso zuwa, amma bata jin dadi ne, tana kwnce. Tana drya tace, "Uhmmm.... Nasan maganar" "ban gane kin san maganar ba?""ai da kaji anti na ciwo to ta kamu ne". Yayi murmushi, "gidanku! Ashe baki da kunya?" "wayyo yayana, ba haka bane. Allah ya bata lfya". Du koma gun su ameer, "kuzo muje, yaya al'ameen na nan yazo". Suka rankaya gaba daya wajnsa. Yaran na hango al'ameen, ameera ta kwala masa kira, "yaya!" ya juyo cike da mamak ya tarbe su. Sama yayi da ameera, bakinsu yaxi rufuwa. Bayn sun natsa, al'ameen ya gaida yayan, sannan ya koma kan yarn yana ta biyewa shirmensu. Mama ta fiddo kayayyakn da suka kawo mata, harda lafiyayyn abinci da soyayyar miyar kaji, ga drnks masu sanyi. Ta zuba wa kowa suka ci, ga ice cream din da al'ameen ya kawo manyn robobi, su kai ta sha. Suna yn azahar suka juya, yarn basu so hakn ba, dadynsu ne ya takura musu, domin suna son hira da yaya al'ameen. Shi kuwa dan gogan bai baro bakori ba sai shida na yamma ckn kewa da tunanin juna mai yawa. Haka al'amura suka kasnce, duk kashn wata ya samun kai mata ziyar. Idan suka samu hutu bata zama a fandogari, tana minni ko abj sbd al'ameen yafi samun saukn zuwa ganinta duk sati. Rantsatssiyar soyayyarsu mai ban sha'awace, domin tana da tsafta, basu da burin da ya wuce na aurn juna. Sannu a hnkali mama ta fada zangn karatu na karshe, jarabawa kawai suka fusknta. Kowa ya zage damtse yana neman ya tsallake kalubalen da ke gabnsa, ranar kawai suke jira. Yaynda iyaye da 'yan uwa da abokn arziki suka dukufa taya su addu'a, Al'ameen na gaba-gaba. Kwatsam! Sakamakn takardn da suka tuwa wata jami'ar binciken cututtukan kwakwalwa da ke Rasha ya fito, bayan shekara 1 wa wata 2 da aika takardun. Su 3 ne suka yi nasara, 1 daga ibadan, 1 daga Legas sai al'ameen daga nan arewa. Wayyo Allah! Wannan tfya tayi masa bazata, ynda ya kosa mama ta gama makrnta a sa musu rana! Ga kuma tfya ta fado masa na watanni har 9. Yaya kenan? Hakika al'ameen na farn cikn wannan nasara, tare da godewa Allah. Amma wani bangare na zcyarsa cike yake da damuwar nisan da zai yi, wnda zai kara tsawn lokacn aurnsu. A tunaninsa da zarar ta gama mkrnta za'a saka ranar aurnsu, wnda ba zai wuce wata 2 ba don kammala shirye2. Ynzu mecece mafita? Sati 3 cur! Yana kai kawo don kammala takardun da suka kamata tun daga 9ja har Rashan. Duk da haka damuwr da yake kaynta na ckn zcyrsa tana wahalar dashi kwarai da gaske. Yau komai ya kammalu a hannunsa, kuma ana sa ran saura kwana 8 jirgnsu ya daga zuwa kasar Rasha. Yau din ne ya iso gida, amma don ya kawo kuknsa wajn mahaifnsa tare da neman mafita. Yana zaune cknsu, da ka dubi ynda yake maida jawabn zaka gane yana ckn damuwa. "ba wai bana farn ckn wannan ci gabn bane, matsalata sakeena. Dole za'a ce sai ta dawo za'a sa biknmu". Mami ta fara magana, "wannan wajibi ne, kaima ka sani......" "bana son haka mami, ya kamata kuyi wani abu. Ko da ranar a sanya kafn in bar kasar nan". Dady yace, "saurn me kake yi na neman asa ranar kafn ka tafi? Yarnyar nan bakina da na babnta yace min an baka ita, bana jin akwai wani abnda zaisa ya sauya baki. Uban dawaki dattijo ne na kwarai, kuma sakeena na sonka, tamkar ynda kake son ta. Insha Allahu zaka dawo ka sameta a matsaynda ka barta, watau matar da zaka aura". Kwalla suka cika masa idanu,yace, "na fahmci duk abnda kuke nufi dady, sai dai zanfi samun natsuwa idan da zaka taimaka min ka koma wajn abba ka kai masa kuka na. Pls dady ka taimaka min". Gaba daya jiknsu yayi sanyi, barin mami. Ta dubi marafa ckn taushn murya, "ka taimaka masa alh. Ko ya sami natsuwar karatun. Allah ne ya jarabe shi da tsananin son yarnyar nan. Babu ynda muka iya da al'amarn Ubangiji, illa taya shi da addu'ar fatan alkhairi". Ya sauke numfashi, "kema knsan dole in je, don bani da wani farin ckn da ya wuce na al'ameen. Kawai nauyn uban dawaki nake ji, sbd tun farko ba haka muka yi dashi ba". Taceh "ai muna da kwakkwaran dalili, nasan shima zai fahimci uzurnmu"."haka ne, karka damu Al'ameen, ina tashi daga nan Fandogarn zan wuce. Allah ya shige mana gaba". Sai a lokacn ya saki fuska, murmushnsa ya bayyana sirrin zcyrsa. Ya rarrafo ya aje kansa jikn marafa, "na godo sosai Abbana". Ya dafa kansa yana sa masa albarka. Kamar yanda marafa yayi alkawari bai bata tym ba fandogari ya nufa shi kadai yayi sa'ar samun uban dwk a gida. Bayn sun nutsa ya kwashe abnd ke tafe dashi kaf ya gaya masa nan take Abba yace ni kaina nayi wann tunanin tun randa na sami lbrn taiyarsa. Amma ban furta ba tunda baku bukata ba sbd haka Alamen yayi tunani, yaushe ne zai tafin? Cikin fara'a ya amsa saura kwana 8, yace to kuna iya kawo komai konan da jibine sai asa ranar. Bakinsa har kunne yace mashaa Allah kai mungode Alh Allah yasaka da alhairi. Yace kai haba ai duk meson naka ya gama maka komi. Ya kara godiya sukai sallama cikin nishadi. Ba karamin farin ciki Alameen yayi ba kowa nata murna. Ranar litinin tawagar mata da manyan maza 2 daga lafai dauke da kayan sa rana suka sauka gidan goggo hausi tasawa kaya albrk sann suka wuce gidan uban dwk harda innar baraka, sbd kara sassan Alh Basiru aka saukesu bayan an gaisa matan suka gabatar da kayayyaki komi 12, sann ga wani akwatin kaya suttura zalla da takalma kamar wani lefe. Mazan kuwa suna tare da iyaye maza a falo ba bata tym suka yanke 10mnths, bayan sun dan taba kayan abincin da aka kawo musu suka tafi suna godia suma sunayi. Alameen na kwance yaji shigowarsu ya makale a falo yana jin yadda suke yabon yan gidansu mama da sauri ya shige dakin iya yace. Ki goyani ansa min rana tace har sun dawo ne? Sun dawo iya wata 10 aka sa, ta rangada guda tace Allah ya nuna mana lfy yace zaki goyani a ranar ko iya? Dadi ya lullubeshi ya kankame iya yana murna. Can ma sun tarar da mata'yan tarba cikin su harda Innasaude watau Innar Baraka. Sabodakara, asasan Alh. Basiru aka sauke su,bayan an gaisa,matan suka gabatae da kayayyakikomai doxin.Sannan ga wani akwatin kayasutturu ne zallah datakalma kai kace kafe aka hado.Yayin da mata da kesa albarka, su kuma maza sun tareda 'yan uwansu maza a falo. Babubata lokaci su yanke watanni gomamasu xuwa, in Allah ya kaimu.Daga nan aka wadatabaki da abinci kala-kala da ababensha. Kai! Kowannebangare sun ga karamci, don hakabaki sun wucesuna xuba godiya suma 'yan gidansuna yi. Al-ameenna kwance a gida yana jirandawowar 'yan kai kaya, yanamakale gefe cikin falon, yana jiyadda sukemaida bayani, har da kyakkyawartarbar da akayimusu. Da sauri ya tashi ya sulaleya fada dakun Iyabakinsa kamar gonar aduga, yatsugunna a bayanta,ya kwantar da kansa, Iya ki goyani, an samin rana.Tace, har sun dawo ne? Sun dawoiya, wata god,a aka sa, ina dawowaxaku sha biki. Ta ramgada gudakafin tace, Allah ya nuna manalokacun lfya. Yaceameen, amma dai zaki goyaniranar ko iya! Dadinxancenta yasa ya kara kankame tayace, haka nanne iya, yanxu me ya rage? Tacebabu, sai fatan Allahya tabbatr da alkhairi. Yace AminIya ta. Yace laluba aljihunsa ya ciro goronfari kalda shi ya mika mata, tasa hannu taansa, ta bishi dakallo yace, xan xo ki gutsiri goronnan, ki taunasaboda mahimmancinsa. Kai tsayeta ba shi amsagaskiyya baxan gutsira ba, ka fadilabarinka kawaiinaji, ya wuce shikenan. Yayi kyarda ido yana kallonta sannan yace,jiya iyaye na sun kia wasuabba kaya an sa mana rana. Kaibata yarda da abindataji ba, shi ya sa ta xura masa ido,ba ake yi ba Dr. Aidai be kamata ka xolayeni ba.Alhalin kasan halin danake ciki. Yayi mumrmushin jindadi yace, ba xolayabane my Princess. Magana hakatake kuma ni na nace sai aka sakamana ranar, dan in samu sukuninda nutsuwa idan na tafi. Ta saukegwauron numfashiyana kallo ta gutsiri goron, shiyasa tana dagowasuka hada ido. Dariya ya kubcemata, ta rufe fuskatanayi. Sanyi ya kwarara cikinransa, ya dafe kirji yasauke numfsahi alhmdlh! Nagodema Allah daka nufi xan yi tafiyarnan cikin farinciki. Bakin Mamayakirufuwa, duk iya yinta, don ta katseshi, abin yagagara, hakan ya hana wata kalmafitowa dagabakinta, shi kuwa so yake yajitabakinta, bazaki cedani komai bane? Tace me xan ce?Ya kamata kitayani murna. Tace, to ina tayakamurna. Allah ya nuna mana lokacinlfya. Yace ameen my Princess.Toki kwantar da hankalini, sabodaxams dinki kinsabamu da wani buri a halain yanxunda ya wuceabubuwa guda biyu, kicijarabawarki, sannan Allah yanuna mana ranar auranmu. Kingawadannan abubuwaguda biyu, su nake so ki aje acikin ranki a waje na musamman.Bayan haka ki sance mai yawanaddu'atare da neman biyan bukatunkiwajen Allah. Kifahimce ni? Tace, sosai na fahimceka dr. Kuma ISAxan nutsu, bisa hanyar dakadorani, ina fatan baza'ayo min kishiya a Rasha ba.Kyar yake kallontayace, me ake nufi da kishiya? Tana'yar dariya tace, baka ma santa ba?Yace gaskiya ban taba jin wannankalmar ba, ko za kimin bayani? Kinga sai in karu.Tace abar maganar tunda baka saniba, ni kuma induk jikina hankaline , baxan tabayarda ba. Ya maidahularsa kansa, dariya sosai yakeyi,ni kinga nayi kalarmatan turawa? Ni wlh mace ta cikafari ma bata birgeni. Amma kigakalar ki? Ke ba fara ke ba wankantarwada ba, kina gigita ni ba kadanba. Gabadaya kinhada abubuwan da nakeso, banjinakwai 'ya macen daxata tsokane min ido, ballewadannan kaxaman masuwarin najasa...... Ta katse shi, yaisa haka dadinbakin.... Baki yarda ba kenan?Tace, ai ba anan take ba, mkrntarba ko ina daga kasashen duniyaakexuwa ba? kasani ko wata mai iriinkalar da kake sozata bayyana? Loacin da xakagigice. Sakeena na Yayi xugum! Yana kallon ta takare, ya dankada kai yace, Ina fatan dukkalamn nan wasa nekike min, idan kuwa da gaske nasai ince kaico na niAl'ameen da xan iya cin amanarsakeena. Xanso kifayyace min gaskiyar dakexuciyarki, don ki fiddanidaga kokwanto. Jikinta yayi sanyi,ganin tsabar gaskiyya cikin kwayaridonsa. Murya sanyaye tace,Allah wasa nake yi dr. Har cikinraina, na hakikanceka amsa sunan ka. Ya xura mataido, haka itamatake kallonsa. Kamar bai gamsu dabayaninta ba.Tayi dan murmushi da sake fadin,wlh, kaji rantsuwarmusulmi? Dari bisa dari na yardadakai, na amince cewar babuabinda xai faru da xoben alkwarina. Yamaida kallonsa bisa xoben, yayidan murmushi yace,sai na mutu xa'a raba ni dashi. Yadubeta, kinsanwani abu! Ban taba yi wata fargabaa game dake ba,me yasa ke kika samu shakkuakaina? Tacetambayar ka na ta nuna min bakauarda wasa nakeyi ba, yacenayarda, amma ina mamaki ne,baka yardanbakenan, to kar ka ga laifina kishine, yayi 'ya dariya,naga alama, sai dai naji dadi,domin sai ana sonmutum ake kishinsa ko? Ka ganekenan. Yace, Iya!To ni ya aka yi na boye nawakishin? Tace oho.Watakila kuma naka sikelin yayikasa nan, me kike nufi? Tayi shirubata son ta bayyana. Yace kinsnAllah karya kikeyi. Ta dubeshi,tana dariya tacekarya? To fiddo xuciyarka a gwada.Yace. Na yarda,kema fiddo taki. Tun yaushe ni nafiddo? Kaine kamakara, shi yasa nace sikelin ya yikasa. Dole kayarda. Ban yarda ba! Dole kayarda, ban yarda ba! Dole kayarda! Ta Marairaice, gaskiyya bahaka akeyi ba! Ba haka ake yi ba sakeena,zaki yi min wayau?Tuni take masa dariya, ganin yaddayayi turus! Doleya sha kaye, kallonta kawai yakeyi,dadi ya karakamshi. Sun nannagihira har xuwagabatowar la'asar.Dole yayi harama, a zahiri ma harya makara, yaushe ya kai minna,ya gama shrinsa, ya wuce abuja? Koaahalin yanxun din ma xaune yakeshiru, gabadayansu ido ya raina fata. Shirunyayi yawa. Mamace tayi ta maza ta mike tace, mujena rakaka. Yakunkuwa ya tashi da kuar, ya wuceya bi bayanta,babu mai magana har jikinmotarsa. Ya jingina rungume dahannayen sa ya xubi mata ido, dongirman Allah kuna bari mkrntar,karki bata lokaci afandogori ki koma Minna ko abuja.Zan cigaba da kirahar xuwa ranar da zanyi dacensamunku. Idanuwan tasuka fara tara kwalla tace, kar kadamu, ko kwanabaxanyi ba, xan wuce, ISA.Shikenan, in tafi? Tace, xansohakan, don kar kai dare. Ya budemota yashiga ta rufe masa. A sauka lfya,ina gaida Mami daIya. Yace zasu ji, don Allah ki kulamin da kanki,kinji? Tace ISA zaka sameni yaddaka barni.Promise? Promise Dr. Yayi danmurmushin damuwayace, I love u! Tace me too! Yakara fadin so much? Ta juya dagudu tayi cikin makaranta..... bita da kallon kirjin sa na bugawa,ji yake kamar ganin karshe yayimata a duniya. Nan taje idanuwasasuka kawo kwalla, cikin tashinhakalin yayiwa mota key, ya maida hular sakeya, sannan yaja mota. Can tamadubi yahango ta tsaye rungume dahannayenta, babu alamun laka ajikinta. Tausayintaya kama shi, nan da na hawayen samasu dumi suka soma kwarara.Yayi sauriya jawo hankacif, yana sharewa harya fice daga gate din sch din. Hakamama ta ke ta xubda hawaye,daren nan bata iya cin abincin kirkiba. A gurguje, ya tsayazariya yayi sallama da jama'arsa,musamman mutuminsa Dr. Lwal.Daga nanyayi wa minna tsinke, kai tsayeyana shiga Minna gidan Yaabdulkareem ya nufayayi musu sallama. Sai alokacin yalura aunty Rabi na kayan tsohonciki. Yashare minti goma tare da suAmeera, sannan ya rarrashe shu yatafi. Yaya natayimasa fatan alkhairi. Ya karaso gidayayi sallolin dake kansa, ya dawofalo inda su dady ke jiransa. Ladita baibaaye shi da abinshi daabubuwan sha, amma baicina kirki ba, wai don ma Mami tasabaki ne, shi yasa yayyafita. Sunraba dare daiyayen sa suna ta hira, kafin kowaya fada makwancinsa. Al-ameen baisamibarcin ba domin da xarar ya runtsaido. Mama yake hangiwa tsaye tamadubinmotarsa kamar marainiya. Bayason ganinta a wannan yanayinkuma ya kasasauya wani tunanin. Tabbas yasan,tana cikin damuwa, ya kan jikwallah sun kawo masa dauki cikinidanuwansa. Washegari tare daDadynsa suka wuce.Abuja inda suka hadu da sauranlikitocin guda biyu abokan tafiyasa,a harabarwani hotel inda su sauran likitocinsuka kwana. Daga can sukadunguma filinjirgin inda aka gama tantance su.Karfe sha biyu daidai jirginsu, yatashi ya nausaRasha. A wannan rana mama tawuni add'ar Allah ya saukar matada su al-ameenlfya. Sannu a hankali kuazarin ta yadawo jikinta, ta maida hankalintaakan karatun jarabwa kamar yaddaya umarceta. Satin da ya zagayosuka fara cinkwakwa, jarabawa a aikace, watau(pratical). Wasa-wasa sun kwashekwanakiashirin da bakwai suna jarabawa,daga nan suka shiga shirye-shiryeyaye su tareda abada kyaututtuka. A wannanrana makarantar. Babu masakatsinke dajama'a. Mama ta sha mamaki data ga Mami a cikin tawagarbakinta. Ta kwasoda gudu ta xube ta gaishe ta. Ta sahannu ta dago ta, ta rungume,Allah sarki sakeena. Al-ameen yacein gaisheki da kyau, kuma in gayamiki Congratulation!Ta sadda kai tana murmushi, Abbaya ce baki amsawa? Taruga BayanUmma taboye, kowa na mata dariya. Tajatawagar ta xuwa babban dakintaron, ta nemamasu kujerun xama, wuri daya,mai daukar bidiyon da suka zo shiyana ta daukarkai da kawowarsu da na sauranjama'a. Ba'a jima ba, shirye-shiryesu kakankama. Dalibai sahu-sahu,yarurruka kasar nan nata fitowasuna nuna al- adunsu. Bayan angama shkawata aka fara gabatar dajawabai. A ciki har da na tshuwar (Headgirl). Mama ta turance baki dakalamaimasu dadi da ma'ana. Daga bisanita mika dan kwalin ta ga sabuwarshugabar'yan mata wacce ta gaje ta. Badakyaututtuka suka biyo baya.Sakeena UwaisMalami tasha kira, don karbarkyauttuttuka inda tayi nsa dagafannoni daban-daban na darussan aji da gasa kalauku da ta shiga, musammandebate a sci.Bayan an kammala, shugabarmkrnta ta sallami baki, sai daukarhotuna ya balle. Kowa ya mikakyautarsa, sai dauke su hoto. Abbada Umma suka bata, mami tata dauko nata xungureriyar tace amadadin Al-ameen ne, ta batakyautar, dominshi ya umarce ta da ta kawo. Anyimusu hoto, mai bidiyo na dauka.Duk yayyintasun sami halarta, banda soja, yanabakin aiki, amma matarsa tazo, dadansumalami. Ali da sa'aeed duk sunsami halarta kuma kowa yaxo daabin mikawa.Daga nan suka baje wa ni fili, sukaci abinci yayin da sauran 'yanmakaranta basu bar mama sukuniba, kowa yana xuwa suyi hotuna daita har da wasu bakin dabata taba gani ba, kawai ta burgesu ne suka kirata yin hoto. Basubar makrntaba, sai bayan la'asar, kayan mamatuli a bayan motaci. Tana farinciki,sai daitana jinsa kalilan ne idan ta hangataron nan babu liktanta. Ammaalhmdlh! Dagayau maraici ya kare, xa su ke jinjuna a waya. Abinda ke kara matakuzari kenantare da kosawa su isa gida. Kaitsaye direban Mami wucewa yayimdon yamma tayi sosai. Gida fah yacika makil! Ana sha'ani, wannantaro bai tashi ba, sai daabdul- rahman ya gabatr da xancenauransa da yarinyar da yake nemaa cankaduna. Kuma iyayenta sun bukacidaya turo magabatan sa. Farin cikiya karalullube kowa, saboda haka washegari, bayan kowa ya kama hanyargida. Ubandawki da 'yan uwansa suka shiryaranar da za suje kai gaisuwa. Ba abar Mama afandagori ba, kamar yadda tayi waAl- ameen alkawari. Kwanan ma yazama dole ne, saboda dare yayi,amma ko baraka bata tsaya jira ba,tabi yayanta minna,duk da cewar Anty Amina ta sotfya da ita abuja, sai dai sabodatshon cikinAunty Rabi, kowa yafi bada karfinda ta fi minna kawai. Sun iso lfya,ita kantaAunty Rabi tana ta murnar xuwanMama. A wannan ranar bayansallah isha'i sunabaje a falo, suna kallon kaset dinbidiyo da aka yi bikin makrnta.Aunty Rabi na tasanti tana fadin, gaskiyya kallo yawuce ni. Suna tayi mata dariya,lokci guda waya ta dauki ruri.Falon yayi tsit! Gaba daya hankulansu suka koma wayar.Kafin kowa ya motsa, ameera taruga wajen ta dauka Hello! Ta fadada karfi,yayin da ddynta ke kokarin tashi.Daga bangaren aka amsa, hello myfriend! Ameera,Ya Al-ameen ne, Kawai tasai ta saki kan wayar tana fadin,Hah! AuntyYayane; walhi yaya ne! BAKIN CIKI 1***10 Wannan soyayya ta su Al- ameen dasakeenar sa ko a film ba'a taba nuna irinta ba. Sannua hankali bikin abdulrahman yana ta kara matsowa, a'yan tsakanin ne jarabwar su Mama ta fito. Allah daikon sa sakamakon ta yayi kyau matuka, domin tanadaya daga cikin ajin farko. Tsalle da murna wajen Mama abin ba'a cewa komai, ba ita kadai ba, kowa yataya ta murna musamman dan gaban goshin nata,daga can yake gaya mata a halin yanxun yana tare daabokan karatunsa, suna liyafar taya ta murna. Donhaka kowannen su dai tayi magana da shi, tayi masagodiya. Babu bata lokacu Abba ya fara bincikar mata makaranta a zariya, amma aka ce ba'a fara siyar daform ba tukunna, jin haka yasa hankalin Al-ameen yatashi, sam baya so Abba yayi wahalar karatun mamakuma, ai cewa akayi a gidan sa xatayi karatunta. Nantake ya kira wayar gidansu, ya kuma yi sa'a dadinsana gida, saboda haka ya marairaice ya bayyana masalarsa, Dady yace, wai me ke damun ka neAminu? Haba Aminullah! Menene a ciki, idan ta farakaratun? Yace, ni dai Dady nafi so ta fara bayan aure,kamar yadda aka shirya tun farko. Yace, wanan yarorigimarka tayi yawa, saboda Allah ya kake so inyi?Kaje wajen Abban, kui magana. Kai tsaye ya bashi amsa, ba xan iya ba, gaskiyya sai dai ka hk, bakasan nauyin da nake ji na uban dawaki ba. Sabodahaka ba inda xani, wannan karon dole ka hkr. Kuma niban ga wani abin xafi ba, idan sakeena ta fara karatuyanxi. Cewa xatayi ta fasa auranka? Kamar zaiyikuka yake fadin, ba haka bane, Dadyi amma ina tsoron mata a jami'a, yace, ban son shirmen ka, kayarda Da Allah shi daya ne mai xartar da komai,sannan ka rike sakeena da xuciya daya, na tabbataba xa ta ci amanar ka ba. Ya numfasa yace, shikenanDady, na gode. Sukayi sallama ya aje waya. Dukjawabin da dady yayi masa, hanlainsa bai kwanta ba, don haka yake sake kiran waya gidan Yaya Abdul.Mama ce kuma ta dauka. Bayan sun gaisa, ya faratambayarta, yaya maganar makaranta? Tace, tananan, form din ne har yanxun ba su saki ba, yace,saboda Allah menene na wahalar da Abba, yanayawon neman makai makaranta? Hakki na ne sakeena, don Allah ki taimake ni, ki gaya wa Abba yabari in dawo, bayan auranmu, sai ki tsundumamakaranta. Tayi 'yar dariya tace na tsunduma kamarwani kogi? To menene idan na fara yanxu? Gaskiyyaban so my princess, pls ki rushe maganar nan sai nadawo. Ta yaya? Ki na cewa sai na dawo. Babu mai tilasta miki, tace wa xan gayawa? To sai dai in gaywaAunty Rabi, tunda ka nace da alama kana da watamanufa. Yayi murmushi yace, manufar kenan gudadaya, xallar kishinki, bana so wani ya san cewa bakida aure, ya lallabo yace xai miki magana. Aikomuryarki yaji, wlh ya cuce ni. Ta kama baki tanamasa dariya, a gaisheka. Dariya kike yi? Dagaskenakeyi, kina da kyau sakeena, ba karamin jarumi bane xai kalle ki ya dauke kai. So pls kic gaba daxama gida har na dawo, in maida ki tawa, ni kadai, aikin gane? Tace, ba dole ba, ya na iya da Maigida? Yafara dariya yana fadin iye! Dan sake fadi inko? Tace,Maigida takobi. Kaina xai fashe uwargida, in dainafadi? Yace, a'a ci gaba madam. Idan kan nawa ya fashe, kin san yadda xakiyi. Tace ya xan yi? Hakanan xa'a sha bikin. Kina fa dada tunxura ni. Ji nakenakfi kowa awajen nan. Tace, sa ranka a inuwaAmeer da Ameera suna tafe.... Me kikace? Me nacekuwa? Don Allah ki maimiata. Allah na manta. Yamarairaice, gaskiyya ba haka akeyi ba, ba haka akeyi ba sakeena. Ai dai banji ba sai ki maimaita ko? Tanata masa dariya tace, sai da safe. Yace, a'a rufeidonki. Kin rufe? Ta rufe tana fadin, uhm. Yace, kingansu? Su wa? Ameer da ameera. Suna tsakiyar mu.Ameer ya cire min hula ya sanya a kansa. KingaAmeera? Wayyo, kamar ku daya my princess, shagwaban ta kawai takeyi a ajiki na. Oh ma Godmwhat a lovely family. I lobe U sakeena, I really meantit. Murya sanyaye ta amsa, me too dokta. Tayi saurita kife wayar ta ruga dakin ta, tayi sufa bisa shimfida,ta datse ciki ta rasa duniyar da xa ta sa ranta tajisanyi. Haka ta raba dare tana juyi, bata san lokacin da barawon ya sace ta ba. Kamar yadda ya tsaramata haka ta aikta, domin bata bata lokci ba, ta samiAunty Rabi ta gaya mata, abinda dokta ke bukta. Taxura mata ido jim, kafin tace, wannan dan nawa yafiye rikici wlh, menene banbancin fara karatunkiyanxun da kuma lokacin da ya bukta? Kar fa yayi miki sakiyar da ba ruwa, ki shiga gidan yayi mirsisi!Da saurinta tambaya, kamar yaya aunty? Tace, ayiauran ya ce bai san maganar karatu ba. Tayimumushi da bai kai ciki ba tace, Haba anti kamarwani jahili, ai dokta baiyi xubin irin wadannan mutanenba. Tace, oh haka ne? Idonki ya rufe kina son sa ko? Ai shikenan, ni 'yar sako ce kuma ko an tambaye nishawara ba xance a'a ba. Tace, kinyi daidai antina,kin kuma san Yaya na ji dake, idan kika ce eh dinnan, babu sauyi. Tace, banson zakin baki, inda yakexuwa neman 'yan matansa sani zakiyi? Ya ya mutsfuska tace, wannan kuma sharrin kine. Ta dada mata duka. Ai gaskiyya ne anti, dan Abba sadauki ne,bawan Allah bai yi xubin shaidanu ba. Ke da kanki, kikace idab bashi ba, sai rijiya. Tace, a'a sai masai barijiya ba, meye ajikin Yayan naki da za'a fada rijiya? Ta gwalalo mata idanuwa tace, ayi kurumaunty, kar ayi 'yan tone-tone, don ni har na hango ki agidan Zoo! Tace, kan biki! Lallai yarinyar na ki gagadon barcina, to ko ke din suke kwakwaxo a kanki,ma zaki gwada min? Ta kece da daroya tana fadin, aidama ni ban fadi ba. Aunty ke ce xaki raina min yaya, alhalin koda mai kwado, ya dara gaya. Tace, naji saikije wajen kwadon ki gaya masa da kan ki, a kyalegaya agefe. Ta rungumo ta, ayya my Aunty ba ma'yar haka dake surukuta ta kaina! My lovely wife! Tatabe baki tace, haka naji masu kyau ke da Al-ameendin naki hakane? Tace ban so surutu, sai in fasa ta kara kankakme ta, yauwa my swthrt, ke kadai ce harabada. Tace, ko baki fadi ba. Haka ta lallaba ta sukasasanta, don ta san halin Aunty Rabo, da wasa xatace ba xatayi abu ba, amma sai sai ki sha mamaki,taki ai watarwar da gaske. Ba yaya Abdulkareemakadai, su Abba kan su sun sha mamaki da wannan sako da yazo kunnuwansu, sai dai Abba baiyi jayayyaba, du da yana shakku cikin ransa, yana jin kamar Al-ameen ba zai bar ta yin karatun bane. To amma idanya dubi iyayensa, sai yayi saurin kauda wannantunanin. Yanxun bikin abdulrahman shi suka gaba,sun kyale fafutukar makarantar mama. Shi dai dadi bai san yadda akayi ba kawai an masa ne makarantarce bata samu ba, sai wata shekara. Tun sati biyun sasuka wuce aka fara gabatar da shirye-shiryen biki tahanyar kai kayan lefe kaduna. Tun daga lokacin sumama babu xama, kusan kullum fita sukeyi xuwakasuwa, domin yawancin abubuwan bukata, daga nan minnar xa su taho da su. Satin daya shigo shine yakama kwana shida biki, don haka a gobe su mama damutan gidan za su wuce Fandagori. A daran ranarraba dare sukayi suna hira da Al-ameen, saboda xasukwana biyu basu motsin juna ba. Washegari dasassafe yaske bugowa. Sai da kalamansa suka sa Mama kuka, don kalamai ne masu ratsa xuciya, suhana ta sukuni, shi ya sa bakinta gum! Tana tunanitare da kewar Doktan ta, ji take kmar tace su sauketa koma gida. Ta dai ya daurewa sannu a hankali tatattaro nutsuwarta wuri daya, ta dauki dangana. Sunisa kuma, ganin Ummanta ya debe mata kewar masoyinta. Bayan sun ci abinci, sunyi sallolin su,sannan suka ci gaba da tattaunawa akan shirye-shiryen biki. Karfe biyar dai-dai lokacin ne rana tayisanyi. Mama ta sheko wanka tayi shafe- shafe, bayaga hoda bata karawa fuskar ta komai ba, ta daukowata atamafa 'yar ingila ruwan bula ta sanya, ta daura dan kwalin ta, ta ziro bakaken takalma, ta yafo bakingale ta rataya jaka. Duk wannan shirin na tafiya wajenBaraka ne, wai nan ma ba kwalliyya tayi ba, kawaiyanayin jikinta ne baya boye kyan da kaya ke mata.Ta sallami Umma ta kama hannun Ameera suka fitotare A kofar gida suka ci karo da Ameer, yanaganin gari shi ma yace zaije. Tace yaje ya fadi a gida,don kar a neme shi. Daga nan ya kwaso takalman sa.Ya sheka a guje cikin 'yan dakikai ya fito suka wuce.Suna gaba tana biye da su, suna xuba mata labari,iya ko jinsu bata yi, don tayi nisa a tunanin Doktan ta, kalamansa ke shiga suna fita a kunnuwanta, "kwanakigoma banji muryarki ba sakeena? Ai yayi yawa, kitaimake ni kar ki sa asiri na ya tonu a makarantarnan. Xauntuwa xanyi cikin aji in kasa gane komai".Idanuwan ta suka tara kwalla, tayi sauri ta shanye su,tana fada aranta, ba xan xauna ba, ana gama biki xan koma...... Sannu 'yam mata! Muryar ta fito. Samaribiyu ke xaune bisa benci a kaofar wani katon shagodaf da bakin titi. Daya fai sol! Ga dogon hanci damatsakaitan idanuwa, duk da cewa a xaune yake, kana kallon sa zaka gane dogon gaske ne. Gashinkansa kuwa mai santsin gaske ne, har yana nannadewa duk da cewa bai da yawa akansa, watauyayi aski. Kwalli ram! Ya xauna a idanuwan kamarmace. Ga kuma alamar gashin baki baki wulik! Akwance, guda kuwa wankan tarwada ne kuma zamansa kusa da na farkon, ya dushe gaba daya kyan sa.Gaba dayansu, ta san su, amma tuni suka bace a kwakwalwarta, domin shekaru masu yawa rabon ta dasu. Sannan ko a wancan lokacin babu wata alakantsakanin su. Shi yasa a yanxu take masu kallonmamaki, yayin da farin yake kara fadada murmushinsa, sannu ko? Ya sake fadi. Wani guntun tsaki tayi,ta wuce abinta, sukayi sa'a babu wata mota mai xuwa, don haka ta rike hannun yaran suka tsallakatitin. Ka gani ko? Na gaya maka karka yi matamagana, ba zata saurare ka ba. Yayi murmushi yace,ko bata suarare ni ba, dole ne ma ta so ni, domin irinwadannan su ne ke nema kuma ban taba daga ido nadubi yarinya nace ina son ta ba, tayi min kallon banza ta xubar ba. Yace yau ka samu, saboda haka dukabinda kake takamar ka na dashi, yau ka hangowacce ta fi ka, kar ka kuma ka mance, bikinta sauran'yan watanni suka rage, mijin da xa ta auran ma bashianan kasar, kaga kuwa yafi ka komai. Ya ja dogontsaki, aikin banxa, to meye ruwa na dashi? Kasan Allah yarinyar nan sai dai in ban so ta bi ra'ayi na ba,cikin dan kankanin lokaci zan birkita ta, ko? Wlh, kajina ranste, yace hakan dai babu kyau, tunda na gayamaka bikinta ya kusa, sai ka hkr. Yace, kai ba xanhkr ba, yanxu ma na fara sonta. Yana dariya yace,sai ka shirya yaki da manyan kasa, na lura har yanxu ba ka hankaltu ba. Yace, bar maganar nan tun kafinran ka ya baci, don Uban ka! Yace, nayi shiru. Zai fimaka kyau. Ya tashi daga kantar shagon sa ya komaciki ya xauna a kujera. Bai kara tankawa na wajen ba,haka shi ma bai sake cewa da shi komai ba. Yayin daita ma mama ke tafe tana sakin tsaki kamar tsaka. Ranta bace tayi sallama gidan su baraka. Barakar ketsakar gida tana wanke- wanken yamma. Tayi tsallesama ta runtuma a guje suka runguma juna. Inna taleko daga daki da sauri tana tambaya lfya? Sai tagansu rungume da juna, tayi dan tsaki tace, Ammadai Allah ya shirya ku, kunji yadda gabana ya fadi? Suka nufo gunta suna dariya, wayyo Inna, kinsankwana biyu ba'a hudu ba. Tace, ku rika nutsuwa,girma kuke karawa. Mama tace, to Inna. Suka shigedaki, suka gaisa da Inna, sannan suka dawo indaBaraka ke wanke wanke ta baro su Ameera wajenInna. Ta kawo wa Mama kujera ta xauna tana wankewa. Mama na mata dauraya. Ina mutuminki?Tayi dan murmushi tace, karki sani kuka don Allah,yau da kyar zan iya barci baraka. Ko? Kuna da abindariya ke da likitanki nan, tace, baiki tausayinmukenan? Tace shagwabar kawai ke damunku, shi yamarairaice, ke kin marairaice,, to wa zai rarrashi wani? Da kan mu muke rarrashin junanmu. To yaza'ayi, ke kuwa soyayya. Tace, baku da laifi, in gayamiki nima na kamu. Ta mika mata hannu, ban mukashe, don Allah, a ina yake? Suka tafa suna dariya kafin tace, danKagara, wani dan aiki ya kawo shi na garin, na yiniguda, in gaya miki ashe rabo na ne. Muhammadsunan sa, yana aiki a sakateriyar nan ta kagara. Tajuya idanuwa tace, ba shakka ta muhammad. Allah yatabbatar da lkhairi. Tace, amin. Suka kara tafawa, ai zaki ganshi, dan kyakkyawa shi ga addini. Tace, baikai Aminu na ba dai. Ta tabe baki tace, naki kikasani, ni kuma nawa na sani. Kowa da gwaninsa.Tace, gaskiyarki, kuturu ma sarki ne a gidan sa. Shikika raina ma wayau? Tace, ba haka bane wlh, aimisali ne kawai. Tace, na gane kowa jin kamsa yakeyi a inda yake takama? Mama ta gyara zamatace, har kin tuna min, wai yahse wannan me masunansa? Wannan da aka jefe babansa wajenkwartanci? Tace oh! Kina nufin Dan liti? Yauwa shimyaushe ya dawo gain? Tace, ai ya jima zai kai satibiyu. Ta tabe baki, na gaua bude wani shago ne? Kai mutane ba su da tunani, menen na barin Dan liti yaxauna garin nan har da ba shi hayar katon shago?Tace, manyan gari ma basu kore shi, wai zai koreshi? Wai kin san ma wani abu? Yanxun nana xan wuce,wai sannu 'yan mata yace dani. Tace, haka yake,anyi gadon banza ido a mata. Shi jinsa yake mai kyau, marasa tunani na binsa yana lalata su. Kingashekarunsa shida rabonsa da garin nan, amma yanadawowa 'yan mata na masa layi, yana tijara su. Takaici ya ishi mama tace, kwadayi, ba an ga ya dawo daabin duniya ba? Ai mata mun shiga ciki, kwadayi kekai mu ya baro mu. Allah ya shiryemu, tace ameen dai. To wai shi da yayi miki magana menene nufinsa? Ido waje tace oho! Shi ya sani, ke da baki wajen, idankin tanka, nima na tanka masa. Allah ya isa ma nayimasa, daya katse min tunanin dokta na. Suka tafa,Baraka ta mike ta dauki kwandon kayan ta shige dashi kicin. Mama ta dauki tsintsiya ta sa ruwa ta kora wurin, ta share tas! Suka koma dakin Baraka. Hirar takoma can tare da tsara shagalin biki. Gab da akekiran magriba. Mama ta baro gidan Baraka tayo matarakiya, suna rike da hannauen yaran har bakin titi.Anan Baraka ta tsaya tace, to sai na zo goben ko? Tace, ina jira, don Allah ki zo da wuri. ISA, lah! Kinga mutumin naki da zai rufe shago, ya hango ki ya fasa.Kar ki bi ta wajen sake hanya. Kinsan Allah bai isaba, bazan dauki nisa saboda shi ba, idan ya matsamin sai ya sha mamaki, don xan yi masa wnkinbabban bargo, kafin nan bar garin nan. Ina son kimatar likita, amma ki tsaya bata lokacinki wajen danliti asara ce, ki wuce kawai, shi ya fi. Allah kokawata? Don dai ba ke yake wa magana ba, shi yasahaushin bai damunki. Tayi 'yar dariya, haka ne, ammaina rokon ki, karki kula shi, ba don ni ba sabodaDokta. An gama, kinsan wani abu? Cewa yayi idanwani yaji murya ta kawai, ya cuce shi, abinda na tuna kenan. Saboda haka kwalelensa, ba zaiji ba. Suyi 'yardariya. Kuje, yanxun xa'a kira sallah, sai goben. Allahya kaimu. Ta sallamu su ameer, ta tsaya sukatsallaha, sannan ta juya ta koma. Kai tsaye mama tazao zata wuce. Dan liti bai daddara ba, ya sake yimata magana, 'yan mata an dawo? Ko kallo bai isheta ba, wannan karon, ya daga murya ya sake fadin,Haba 'yammata ai rika sauraran masoyi mana, don ba'a san inda rana zata fadi ba! Kai, Dan liti yayi sa'atayi alkwarin ba zai ji muryarta ba, amma da yajiamsar da ba zai sake marmamrin kula ta ba. Dawannan haushin ta iso gida. Suka yi alwala da yaran sukayi sallah. Dare ya raba barci, yaki zama cikinidanuwan ta saboda zafi biyu suka hade mata, gakewar muryar sanyin ranta, ga kuma takaicin rashinba Danliti amsa, har yanxun yana mata kaikayi axuciya. Idan ta tuna kalaman sa na karshe, ta kanjikamar zata mutu. Wai ba 'a son inda rana zata fadi ba? Ta kan kuta, ta shanye hwayen idanuwanta. Hakata wayi gari da ramar rashin barci, shi ya sa take jinkasala. Xuwan Baraka ya sa ta gyagije ta mike sosai,suna ta aiki. Ba'a jima ba, ango ya iso. Gida ya karagauraye wa da shewa da guda. Bayan sallar la'asarmutanen Abuja suka iso. Sannu a hankali gida ya cika da 'yan biki na nesa da kusa. Tundaga lokacinake ta dora tukunya ana saukewa.... Ranar juma'a akwai dinner a kd. Don hakaango ya kwashi su mama da baraka tare da su danDanlami ya wuce da su. Mama kam sai da mucetsarki ta tabbata ga Allah gwanin halitta, ka ranste daAllah itace amaryar. Tana gefen Yayanta, ya na ji daita. Samari kowa idonsa na kanta. Cikin abokansa kuwa babu wanda bai taya ba, amma ya ce mus ansanya mata ranar 'yar watanni suka rage bikinta.Kash! Duk wanda yaji sai ya numfasa. Lallai Al-ameen gaskiyya, sai ma yanxu take kara jinjinwatunanisa. Bata gama shan mamaki ba, bayansundawo daga diner, misalin goma na dare, suna sashin baki a gidan ango, inda aka xubawa amarya kayandakinta. Suna tare da Baraka hirar dinner kawai sukeyi. Dan lami ya yi sallam ya shigo yace wa mamayaya Ali na kiranta. Tace lfya? Yace kalau, yana canbaya. Ya fice abinsa. Ta dubi Baraka tace, kinji watasabuwa kuma. Tace, wata tsohuwa dai, ai kun jima da Yaya Ali. Abin ne ta motsa, kin san gyambo ne, tace,Allah ya ba shi sauki. Ameen dai. Ta figi gyale ta yafata same shi a bayan gida yana xaune bisa dakalinsokawe da fara'arta ta tayi sallama, ya amsa. Ganinfusakar ta sake ya sa shi ma jin sanyi cikin ransa,tace wai kana kirana? Yace eh ina kuma fatan xaki saurare ni, ta kara matsowa tana fadin me hana yaAli? Meya faru? Ya mike daga inda yake yace ga gurixauna, tace a'a yay Ali kayi xamanka kawai, no kixauna ai ni nace ko? Ta xauna tana murmushi sannanta dube shi suka hada ido, ya akayi? Yace babukomai Mama, kawai so nake muyi hira. Ta sunkuyar da kai tare da numfasawa. Yace nasan tuni kin mantada ni cikin ranki, amma ni na kasa mama, waccesahwara xaki bani? Ta dago kai ta sake dubansa,tace me xaisa na manta da kai Ya Ali? Karfa kamanta jininmu daya, dubi fuskokinmu kamar mu daya,don me xan manta da mutum kamar ka? Ashe lallai xan iya mantawa da su Ya abdulkadeer. Ya saukenumafshi yace, haka ne, amma kin san ina miki waniso na daban ko? Sao dai ke kinyi nisa da soyayyarwani, har kun kusa aure. Ba wai ina masa ynaka bayabane, so nake ki gane har abada ni mai sonki ne, bakuma xan taba fidda rai da ke ba, sai ranar da na ga an shafa fatihar auranki. Xanyi farinciki, idan har zakiyarda mu yi hira koda labarin Al-ameen zaki rika bani,wlh xan saurareki. Ta runtse ido, tausayin Ya Ali yaryfeta, sai dai runtse idanuwan da tayi bata ganinhotunan kowa face na Al- ameen dinta. Tayi sauri tabude, idanuwanta suka kada, a sanyaye take cewa, kayi hkr Ya Alli, komai mukaddari ne daga Allah. Kayiaddu'ar Ubangiji yayi maka sauyi na alkhairi. Sannankuma ina so ka sani, ban taba kin ka cikin raina ba,kuma ba xan taba kinka ba, shi aure nufi ne na Allah.Shi ne yake shirya abinsa yadda yaso. Ina fatan kafahimce ni? Ya gyara tasyauwa yana kallonta, yace, na fahimce ki mama, na gode da gudunmawarki. Toamma bana so kana damuwa. Yayi dan murmushi, nadaina kanwata. To kai sai yaushe zaka yi auran? Sairanar da na daina ganin Mama a matsayin budurwa.Ta kalle shi tana 'yar dariya, ka tsufa Ya Ali, ka fagirmi ya Abdulrahma. Kana so a fara maka kiran gwauro ko? Hakan bai dameni ba. Ni ya dameni, aceyayana gwauro. Yayi dariya, nace ki bari na tabbatarna rasa wacce nake so, sai in rufe ido in kwaso kowace ce inyi maneji. A'a yayana, tsakani da Allahzaka aureta, ai sunnan ba'ayin ta da maneji. Iba dace,ibada kuwa akwai hakkoki cikinta. Gaskiyane, amma kin san shan kojo kwanciyar rai. Kuma kowane soyana da mizaninsa a xuciya, ni na san babu macenda xan so tamkar yadda na ke sonki. Ya Ali kenan,ka bar maganr nan don Allah, na yi karya ne? Banfada ba. Bari na shiga ciki, kin gaji da surutu na ko?Ta kada kai, a'a wlh kawai barci na ji ya soma kama ni. Kindai gajin kena. Eh, toh da xak duba agogonkakila ka ganr dare yayo. Ya duba agogon ya dubeta,sha daya da rabi ne kawai. Tayi sauri ta mike, wuu! Aikuwa na kawai bane, dare yayi yaya. Kai kankaidanka ganni da wni a wannan lokacin, dole ka koranigida. Uhm hakane, amma banda Al-ameen, don ban isa na rabaki da shi ba, do ne? A matsayinka nayayana, idan bayi dai-dai ba, dole ka hukunta ni kotare da wa nake. Yayi dan murmushi, to na gode. Saiwani lokacin kenan? Uhm..... Sai da safe. Allah yakamu lfya, Ameen. Ya wuce ba tare da sake waigowaba. Shi kuwa kallonta yake tayi har kule ya sauke numfashi, ya koma inda ta tashi ya xauna, shiru jimsannan ya kada kai cike da damuwa. Damuwar mamaba a kan tausayin Ya Ali kawai ta tsaya ba. Ji takekamar tayi abinda ba dai-dai ba ga Al-ameen. Shi yasa xuciyarta ta rasa sukuni ta rika korafo wajenBaraka. Allah ya sani ba tadi tayi da Ya Ali ba, illa ta saurare shi ne kawai don ta kwantar masa da hankali.Yaushe rabon da yayi mata magana irin wannan?Tabbas ta gane yana cikin matsala, dalilinsa da ya sakenan ta tsaya ta saurari kalaman bakinsa, wadandatake ganin amayo su xasusa ya sami sukuni aransa.To ita gashi ta shiga matsalar, gani take tamkar taci amanar doktanta. Ta runtse ido hotunan sa sukabayyana gareta, yana ta cuba murmushi muryarsa nafadin.. Shema Alqali "Manufar kenan guda daya, zallar kishinki.Bana so wani ya san cewa baki da aure, ya lallaboyace xai miki magana, ai ko muryarki yaji, ya cucuniwlh." A bayyane take magana batare da sani ba, kayihkr dokta, Allah bada wata manufa nayi ba. Barakadake kallonta, ta sa hannu ta bubbuga ta. Ta mike firgigi dafe da kirji, Innalillahi wa inna ilahir raji'un!Baraka tace, wlh xaki xautu! Sambatu kikeyi, idanbaki sani ba, ki sani yanxu. Ta numfasa tace, barakaDokta na baya so kowa ya ji muryata. Har 'ya uwanki?To kunyi karya, dole aji muryarki, musammamn su YaAli, domin dan uwanki ne, kuma tare ya ganku. Shima ba irinsu yake nufi ba, karki maida kankimahaukaciya mana. Ta koma ta kwanta shiru,idanuwanta suka kawo kwalla. Kada ki shiga rudun daxai dagula lissafinki, a aikin baxa har karshenrayuwarki, ba xaki daina magana da Yaya Ali ba, Al-ameen ba zai hana ba, don ya san dolenkine. Dama kin kwanta kinyi barci da ya fiye miki alkhairi. Ta maida kai bisa filo taja mayafi abinta. Mama ta saukenumafshi, ta gyara kwanciya bata san lokacin dabarci ya sace ta ba. Tun safe suke shirin tarbar 'yandaurin aure, karfe daya dai-dai kafar gidan ango babumasaka tsinke da motoci, bayan anyi sallah. Abokan ango tare da angon kansa suka jagoranci tawagarxuwa gidan iyayen amarya inda aka daura auranFadila ta ma mallakar Abdulrahman halas malak!Daga cam liyafar cin abincin rana akayi ta maza zalla.Komai ya ji. Masha Allah! Babu bata lokaci motocindaukar amarya suka koma, yayinn da Mama da Baraka suka koma motar Abba. Anata kirana sallarmagriba, amare suka suka Fandagori, kebabban wurida aka gyara musu cana aka sauke baki. Washe garisuka sha gagarumar walimar da aka jima ba 'yikamarta ba a Fandagori. Xuwa la'asar baki suka komakd, aka bar amarya da lainta. Mama da baraka ke tare da ita, suna ta tslkanarta, karfe biyar da rabi ango yashigo, saboda haka suka fito suka basu wuri. Daganan Baraka tayi sallama da kowa, ta kwasokayayyakinta. Mama ta daukar mata wasu suka kamohanya, tana yi mata rakiya sun atafe suna hirar susuka doso shagon Danliti. Da saurinsa ya fito ya xauna, yana jiran karasowar su, suna xuwa kuwa yatanka, 'ya mata ran gari! Ko kuna jin gaisuwa? Su kaba banxa ajiyarsa, suka wuce. Sun dan jima bakin titi,suna sallama kafin Baraka ta tsallaka, ta kamahanyar gida. Mama ta juyo ta dawo, 'yan mata ji manadon Allah! Dan liti baiyi xuciya ba, ta kyale shi, ta wuce. Kawai ganinsa tayi ya sha gabanta, haba 'yanmata, tunshekanjiya na ke gaishe ki, me yasa bazakiamsa min ba? Bakin ciki ya turniketa, kamar ta kurmaihu bata san lokacin da ta amsa masa ba cikinxafinta. Tace, wai dole ne? Ko ka ganayi kama dashirginka? Yace Ya salam! Maida wukar 'yan mata, ba fada bane, A zato na so bai taba zama laifi ba.Taja dogon tsaki ta wuce shi. Ya daga murya ya sakefadin, a daina fada da masoyi, don ba 'a san inda ranaxata fadi ba! Taf! Yayi biyu kenan. Kamar xata daure,amma ta kasa, cak!!!! Ta ja ta tsaya, ta juyo ta dubeshi har ya koma maxaunin sa, kusa da bokinsa, na rannan. Ta tako a nutse taxo gefensa, ta tsaya sukakarewa juna kallo. Yayi dan murmushi yace, ko ke fa?Ai idan kace so an gama magana 'yan mata. Ta gyaratsayuea fuska daure, " wai ba kai bane danliti? Ni ne.Dan wajen buzu mai shayi ko? Ya hadiyemurmushinsa, kwarai nine. Ta kara kankance idanuwa, ta cigaba, wanda yaje kwartanci din nan akakama shi, ya ci dan banxan duka, wuya ta kashe shi,ko bashi bane? Wani irin kallo yake mata, bai iyacewa komai ba, ta kara karkacewa tace, ai kodamuke yara ba mu da wayau sosai, tarihin bai bacemana ba na munana ayyukansa, muna ganinsu cikin idanuwan mu. Hijira a gudu bayan 'yan shekrau adawo, ba shi xai goge rubutun ba. In bnda abinDanlita, ai bindin rakumi yayi nesa da kasa, kumagaskiyar hausawa da suke cwa kwarya bai kwarya.Dube ni da kyau, kai kanka ka sanni ba abokiyarhadin ka bace. Don Allah a rika nutsuwa, ana tunanin abinda ya dace. Taja tsaki ta wuce su, suna kallonta.Baby wanda ya motsa. Sun fi sakwan uku bayantafiyarta. Babu wanda ya tanka baokin yace, kaga irintako? Sai da nagaya maka wannan yarinyar ba xatasaurare ka ba, gashi ka jawo ta zagi baba.Idanuwansa sukayi ja! Yace, ta kuma debo ruwan dafa kanta ba. Xan nuna mata tabbas ni dan gidanbuxu mai shayi ne. Ai ni dama irin wadannan 'yan jinkan nake nema, inyi maganinsu. A'a dan liti baka dagaskiyya. Tun farko na gaya maka yarinyar nan an samata rana, bikin ta ma ya matso. In banda iskanci irinnaka, menen na yi mata magana? Mu da muke gari ma, bamu ce xamu neme ta ba sai kai da ka dawokwanan nan? Mu ma ai mun sa cewa tana da kyau,amma mu ka basar. Dahskiyara da tace kwarya tabikwarya. To wannan karon xa ta hau akushi, kuma taxauna daram dam!!! Yace, wlh kayi karya. Billahillazi,yarinyar na sai ta dauki cikina kuma.... Ya tsohe masa baki. Babu ruwana danliti, idan ka jawo bala'inda yafi karfinka. Ka ga muna xaman lfya, ba uwa bauba a garin nan, gara ni bani da tabo... Amma kai kana ganin abnda ya faru zamangarin nan ya ggareka , yanxu ka samu ka dawo harankarbe ka , don Allah kayi kokari ka zauna damutane lfy. "Ai ba saboda Allah bane da shiri na,nadawo, shi yasa kaji bakin kowa gum! Sai itace maibakin rashin kunya. To zanyi maganinta , wadanda ma suka fita taurin kai, na gama da su balle ita.Kasan Allah yarinyar nan sai ta raina kanta ..." Danliti! Karka fara wannan danyen aikin , ina ba kashawa. Kasan tana da yaya babban soja ko? Wlh yakwashe ka ya kai bariki, kai kanka idan aka aje kagaban mirrow baza ka shaida kanka ba".. Ya ja dogon tsaki, "Aikin banza, kai ka ke tunanin soja, sojanbanza. Sojan wofi" da kwalli kake takama Dan liti,gashi nan kuma a idon ka ban ga yayi tasiri ba, bansoka matsa da yawa Dan Liti, watakil rabon whla kejanka" Ayuba na ce ba ruwan ka, nkna sha alwashinzanyi maganin yarinyar nan. Kasa ido za ka ga abinda zai faru"... Ya zura masa eyes yana mmakin sa, dazaiji shawarar sa daya kyale yarinyar nan tunda Harda Allah ba ajin sa bace, idan aka bi salsala. Ammashi Dan Liti ko ajikin sa, watakil ajali ke kiransa,kamar yadda ya faru da tsohonsa... BAKIN CIKI 1***11 Washegari anti amina da anti rabi suka shiryatafiya. Tun dare mama ta hada kayanta tace ita mazata bi su,fasa karin kwanakin da tace zata yi.Gabadaya suka rufe ta da tsokana wai sbda alamin zatakoma.Tace eh sbda shi din ne haramun ne? Ita kadaita san abinda ke damunta. Duk da ta ba danliti amsa,ji take kamar amsar tayi kadan ko alama batason ganinsa balle tahi munanan kalaman bakinsa,shiyasa ta zabi data koma minna tayi zamanta canhar lokacin da alamin zai dawo. Allah da ikonsakuma,anti amina ta kafe tare zasu tafi wannan karon.Gaskia hankalin ta zai fi nutsuwa a minna sbda tana gani bebi alamin tana renon sa yana mata dariya idanta kira shi dokta.Ita kanta anti rabi bata so hakanba,sai dai ba yadda ta iya dole mama ta bi anti aminata nace.Suna ta zuba kayan su a mota.Yara damanya na taya su,bayan sun kare suka kara sallamada kowa duka suka yo musu rakiya har da marya da ango.Mama ta shiga bayan mota ita da malami.Yayaali ya tsaya jikin tagar ya zuro mata ido "wai damadake za'a wuce? Tace eh mana."Na zaci zaki yiwaumma kwana biyu".Tayi murmushi,naso hakan ammaai zan dawo,yaushe kenan? Ni ma sai inzo mugaisa.Tayi er dariya,gaskiya ba zance ga lokacin ba,watakila ma sai alamin ya dawo,"Ke don Allah,kusan wata uku kenan ashe zaki iya tafiya ki barumma tsawon wannan lokacin? Tace ba haka bane Sai ga yaya soja ya fito tare daabba,shi yakatse musu zancen.Abba ya leko,toauta na a kula dakai kin ji? Tace to abba",yayanyace "abba har wanirarrashinta kake yi,jaririya ce? Yaceitace mana,damaina son gaya maka ka dainarankwasar min ita'.Yawaigo gidan bayan yanafadin,rankw ashi abba?Irin wannan?Abba ya bude murfin motaryace,"auta nafito! Fito ki bi abdulkareem. Tafito dage da kai har dakukan shagwaba,masu dariyanayi.Shi ma ya fito dasauri,sorry abba,sorry! Ya kamakunnuwansa yarike,"na rantse ba zan sake ba" tacuno baki tamakale kafada,ni ba zan bi suba.Yaya yace,"za ki tsallen kwado awajen nan,I'm telln you,ki shigamotamu tafi!Ta kara turo bakin,abbayace 'yi hakuri komaki kyale shi".Har ta tura kai zatashige ta sakedagowa ta dubi umman ta tsayekofar gida tanadariya,ta ruga wajenta ta rungumeta,umma zan dawonan ba da dadewa ba.tace wuce kutafi". To Allah ya tsare. Ta saketa,ta kwaso sauri bata san yaddaakeyi ta dawo ta bangaran inda yayaali yake tsayeba,kawai ganinsu tayi daf dajuna,ta bi shi da kallokafin tace,ba zan dade ba,zandawo." Jikinsa yayi mugun mutuwa yace,adawo lafiya"'amin".Ta bude mota ta shiga yataimaka ya rufe kofaridanuwansa na kallonta,Ta sunkuyarda kai,ita kantabata san abinda ya kashe mata jikiba,sannan batasan me take tunani ba,Ji tayi motana tafiya ta dagoda sauri tana daga wa kowa hannuhar suka bace.Ta maida kanta jikinmota ta jawo malami tarungume.suna isowa daidai shagondanliti,daga muryayayi yace "Allah ya kiyaye hanya!Ta ballo masaharara,yaya nta na fadin,"amin""amin".Tana harararsayana mata murmushi har da dagamata gira,ta sakidogon tsaki,"ke da wa? Anti aminata tambaya,tace mantuwanayi.Yayanta yace 'ba zan koma ba! tacenima bance ba yaya ai ba waniabun damuwa bane namanta". Suka fada titi,komadamuwar ne ba zankoma ba lazy girl"tace "lazy soja"ya kyalkyale dadariya yana kallon motarabdulkareem tana bin su abaya yace,ni ko? Za ki shiga guardroom yarinya,jikin ki zai gayamiki".Suka kalli juna ita da malamisukatintsire da dariya haka suka cigabada tafiya. Har suka iso minna anan suka tsyasuka karayiwa juna sallama sannanabdulkareem ya daukihanyar unguwar su,su kuma sukacigaba da tafiya.Sun isa abj lafia,sojoji biyu kegadin gidan suka budemusu get. Bayan sun yi sallolinsukowa yaci abindayake sha'awar ci daga nan mamada anti amina suka shiga gyaregyaren wuri.Karfe tara na darelokacin neda mama ta gama shirin barcibayan wankan datayi.Suna kwance da malami wanilittafin labarin yaratake karanta masa,anti amina tashiga dakin tace,gadoktan ki can akan layi dama yasan yau zaki dawo?Ido waje ta kada kai tace a'a kilasun yi waya da anti rabi ne ta gayamasa,ba mamaki je ki dauka.Tasauko kayan barci ne jikin ta rigada wando ta rugafalon kasa ta dauki kan wayar dakeaje gefe,tayimasa sallama,ya amsa muryarsa nabayyanar dafarin cikin zuciyarsa.Watau abj kikagudo ko?me kikenufi da kika baro dokta acan?'Yardariya tayi tace,shi ma yaji yaddanake ji.Baki da hujja yarinya kikomagun sa kafin mami taci ki tara.Zankoma yallabai,toya karatu,ya rasha?To ba laofoamma rasha kin sansai maneji da nake yi,zuciyata nagun ki myprincess.Tana murmushi nima inatuhumar kadokta,waya gaya maka ina nan?Yace kawai na kira ne inji ko suanti sun dawo,inyi musu barka dadawowa.Sai take gaya min kemakina abj,ta dannumfasa tace ta kyauta.Ko?Allah,dama ina tatunanin ina zan ji ka?Allah sarkisakeenta,to ya biki? Tace anyi an gama lafiya amarya na can tare daangonta.da kyau,saura namu ko? Tayi murmushi batace komai ba,ba zaki amsa min ba? Me zan ce? Bayankasan hakan?yace to Allah ya nuna mana,ki karahakuri na kusan dawowa kin ji? Idanuwanta suka kawokwalla.Na kosa dokta,baki kai ni ba sakeena,ni kadai na san yadda nake ji,kin san irin son da nake miki kekanki kin san ina wahala anan tsawon watannin danayi ban ganki ba sakeena yasa idanuwa na sunmakance alhali lafiyar su lau,dul abinda na kalla bayagamsar dani my princess hakuri kawai nake yi. Tagoge kwallan bisa kuncinta,ta numfasa,no sakeena,pls kar ki gigita ni,stop crying,please!M uryana rawa tace dole in yi hawaye dokta,domin na fi kafuskantar kalubale shiyasa na kosa ka dawo ayi takare,Yace kalubale? Wane iri sakeena ta?kowa zuwayake nema na,kare da doki ma,shiyasa na gudo abjdon inyi musu nisa.Yayi hucin zafi,ya fahimci ta shiga damuwa,kar ki saurare su sakeena kullum ki rikakallon zoben alkawarin mu sannan kar ki manta akwairanar auran mu a kanki. Nauyi ne babba a kan ki myprincess pls,kar wani kalubale yasa ki qi saukewa,kitaimake ni dom girman Allah". Ta kara goge hawaye,ka daina roko na doktadomin kai ma kasan cewa ban iya rayuwa da kowaface kai,idan kana roko na sai in ga kamar baka yardadani bane.Da sauri ya amsa na yarda dake sakeenakema in har kin amince da magana ta to ki sharehawayenki ki daina kuka zuciyata ta daina konewa. Ta share fuska tare da kokarin tsaida hawayenta,nadaina dokta,yace good girl! To bani labari me kikashirya a bikin mu? Tace me zan shirya baka nan? Nikuwa kinga list din nan anan rubuce,karanto min inji?Da farko akwai immunization day,wasu manyamanyan allurai ne na tanadar don amarya.....Dariyarta ta katse shi shima ya fara dariyar,ki tsaya kiji mana!me zan ji?Wannan shirin naka almara ce kamasake.Na riga na gama shiri na ba zan sake ba,yarinyaallura biyu da safe,biyu da rana,biyu da daddare,shidakenan.Sosai ma,duk a jiki na,ah to,sa wasa kiga aiki.Ta cigaba da dariya hankalinsa na kara kwanciya,kokari nsa ta manta da waccan maganarshiyasa ya dage da bata dariya har dare ya fara nisabasu sani ba,ai kuwa yayi nasara don ko data je takwanta bata yi tunanin komai ba,tace labarin dayarika bata har tayi barci mai rai da koshi ne. Kwanabiyu cif!yau zuwanta abj kuma ko a daren yau alameen ya kira sun sha hira tana ta kewar bebialameen ta kwanta barci,sosai take son ganinsashiyasa ta kwaso hotunansu ta tsibe tana kallo hakata bata lokaci tana kallon doktan ta sannan tasumbace shi,ta tattara hotuna ta maida cikinjakarta,ta dawo ta kwanta ta zurawa malami ido amma a zahiri ba shi take kallo ba,wani tunanin candaban take yi,bata san lokacin da barci ya sace ta ba Tsintar kanta tayi tare da danliti bisa benci akofar shagonsa cikin wani irin nishadi na banmamaki.Wani abu suke ci wanda bata tantance komenen ba.Ta sanya masa a baki ya cinye,shi ma yadauko yasa mata?Ta sake daukowa ta kai masa bakishi ma ya kara mika mata sai ta hade da yatsun sa ta cije,ya rika yarfawa yana fadin,"wash! Sakeena! Wlhda zafi! Ita kuwa dariya take yi har da kama ciki,yakawo mata duka ta tashi da gudu ta mika hanyargida,tana gudu tana waigensa tare dayi masadariya.shi kuwa kwala mata kira yake mai karfi yanaamsa kuwwa "sakeena! sakeena!! sakeena!!! Ta yunkura ta tashi zaune dafe da kirji tana fadin,innalillahi wa inna ilaihir rajiun! sharkaf tayi da zufa kumatana ta numfarfashi tamkar wacce ta sha gudunfamfalaki. Ta lalubi fitilar tebur ta kunna ta cigaba dazare ido tana dube dube,mamaki ya isheta tanatambayar kanta 'me ya hada ta da danliti? Barcin da bata sake komawa ba kenan har gab da asuba alokacin ne wani sabon barci ya dauketa,ji tayi ana tabubbuga ta,ta bude ido a natse ta dubi mai tashi Malami ne a tsaye yana mata dariya,gari yawaye anti ki tashi mu yi sallah.Ta tashi da sauri tadubi agogo karfe shida daidai,ta duro ta fada bayi tayoalwala tayi sallah,wani abinda ke daure mata kai shafta mance da mafarkinta,a zahiri ta san tayi mafarkiamma ta kasa tuna irinsa. Haka ta wuni tunani babu kuzari a jikinta kuma ta kasa gayawa kowa. Hattaalamin da bata iya boye masa duk wata damuwartayau ta kasa gaya masa mafarkinta mai ban mamakiballe ya taya ta addua.Dare yayi sosai lokacin dabarci ya sake dauketa kamar jiya haka ta sakeganinta da danliti. Babu bambanci da mafarkin jiya,ta farka a firgice hankalinta ya tashi,gaba daya kanta yayamutse tana jin muryarsa yana kiran sunanta cikinkunnuwanta,shiya ta zuwa yatsunta,ta tashi ta runtseido tamau!Tana fadin inna lillahi wa inna ilaihir rajiun!Sannu a hankali ta daina jin kiran. Ta makure a gadota rasa abinda ke mata dadi a duniya,gab da asuba wani barcin ya sake sace ta,yadda take zaune amakure gefen gado.Malami ke tashinta ta bude ido tadube shi,yace a zaune kika kwana anti? Da kyar tatashi sosai ta zauna,wuyanta yayi mugun rikewa,yakage,ta kasa motsa shi,tace ya aka yi na tashizaune?Yace oho nima ynzu na tashi na ganki a zaune. Ta jujjuya wuyanta tace,wash! wuya na ya rikemalami ban iya motsa shi.yace in kira momi? Tace aa kyaleta, yanxu zai warware in na tashi,yana tsaye yana kallonta tana ta juya wuyan har tasamu ya saki, ka yi alwala ne? Ya ce aa . To jekayimana ka fito, ya wuce ya yayo, ya dawo itama dashiga toilet, ta kama ruwa tafara alwala, Sakeena! Tajian kira ta. Ta waigo da sauri, bata ga kowa b, tayi jim, a tsaye sannan ta ci gaba da alwala ta kare ta fito taysallah. Wannan yinin tayi tunanin Dan Liti, gaba 1mind dinta, ta koma fandogari. Har Anti Amina ta lurabatab cikin sukuni. Yau da wuri Al- Ameen ya kirawaya 8:30 ma bata gama yi b, tana daki ta idar dasallar isha. Malami ya shigo ya gaya mata yaya Al Ameen ya kira, takalleshi up n down tace kace masaina zuwa.. Ya juya ya fice, shi kansa da yake yaro,yaji mamaki , don bai saba gani b, Da taji waya harrige rige sukeyi wajen rcvng. Tay guntun tsaki ta tasorai bace ta sauko falon suna ta hira da malami yanabashi daria. Tayi tsaye, tana kallon sa, kafin yace gata. Ya miqa mata , ta amsa ba fara'a, tace hello.Yace Amincin Allah ya tabbata gare ki my princess...Kai ma hak. Yau kuma yanga kike ji, kika barni damamaki? Ko amarci ne ya fara tun yanxu? Tayatsuna face tace " sallah na ke," Oho yau na bugoda wuri ko? Na kosa inji ki ne my wife.. Tayi far da eyez tace ka kyautah wa kanka...... Banda ke? Watakila, banson gulma. To yakike? Kalau, aa ba kalau b, kamar sakeenata batacikin walwala, waya taba min ke? Wa zaitabani kuwa? To ai ban saba jin ki haka b my princess ko bakida lfyne? Lfy lau nake. Ina shakku gaskia, karki boye minsakeena, gaya mi meke damunki? Ta danyi shiru, hawaye suka cika eyez dinta,murya na rawa Lnibansani ba Dr. Kayimin pryr raina yana baci nekawai"jikinsa yay sanyi karki damu mama in shaAllah zan miki, kinsan Dan Adam ajjizi ne, 9 yake baicika 10 b, dole wata rana kaji ba daidai b. Haka lyftake,so karki damu, ok? Nagode, ki manta kawai. Kinsa wani abu? Kishin kishin naji wai skul dinnansuna son rike ni, kamar yaya? Wai in zauna anan inyimasu aiki.... Banjin zan iya ko da sunyi man tayin.Don me? Ke kingoyi baya ke nan. Baci gaba bane? Niban ga wani abu a cikin sa b.... Ni nagani, wayau nekawai suke mana , a haifi mutum a kasar sa, yayi girma ya gama whlar studyng a kasarsa, tashi 1 watakasar ta gwada masa money ya bar kasar sa. Alhalinal umar sa na matukar buqatar gudunmuwarsa. Ni banda sha'awar wannan, na fi so inyiwa kasa ta bauta, badon kudi b sakeena , sai don tai mako ga masubukata kin gane????? Uhm.... Uhm?? Haba sakina ta, na ce ki sakiranki, ko naji dadi, kina so in shiga damuwa ne? Tayihamma,gaba 1 taji slp ya rufe mata eyez, yayi yardariya ya ce, wannan uwar hamma, ai sai ki cinye ni,barci kike ji? Wlh kuwa gaba 1 eyez dina sun rufe,. Aikuwa ya kamata ki kwanta kiyi slp, in kyale ki ko? Tadan nunfasa, kuma bana son kwanciyar. No pls kijeki kwanta, Allah na yafe, ok? Sai 2mrw zankira inAllah ya yarda, sai da 2mrw ko? Shi ke nan. Ki fa yibarcin, kar ki tsaya tinkng komai. Ta amsa,to. Gudgirl I lov U my prncess. A hnkli ta ce Me too... YaceSo much? Tace So much! Murmushin sa ya kari yace to ayi slp lfy. To. Ta fadi tare da aje kan wayar ta jimatsaye tana tunanin iska, ta tako ta dawo daki 9pmdaidai. Malami har yayi slp. Bata sauya komai jikin taba ta kwnta,shirun da tayi, bawai Al amin take tnkba , fandagori kawai take tink,can mind dinta ta koma,tana matukar son ganin Dan liti. Yayin da shima al amin yake zaune bisa bed yana tinkn yanayn sakinarsa take ayau,don hka ya roki Allah daya yaye mataabinda ke bata mata rai. Dukkansu sun raba darebasuyi slp b... Yau mafarkin mama ya sauya salo,domin a yau kiran da ya kwala mata yasa ta tsayacak,! Tana kallon sa, tafiya zakiyi ki barni??? Ta kada Kai.. Ya ware hnds dinsa yace, Kizo nan don Allah. 2acigaba da kallonsa bata motsa b, kizo mana nace,! Taruntumo da gudu ta rungume sa, ta fasa kuka, ya riqeta tamau! Yna fadin, ko ke fa? To kidaina cryng, donbanga dalilin yin sa ba... Ya dago fuskarta yana sharemata hawayen, ya isa haka, ki daina bata hawayen ki? Kuka take yi sosai, tana kwance rashe rashe bisagadon, ta jima tana kuka kafin ta yunkura ta tashizaune,taja jikinta,ta jingina da akanta kan gado tacigaba da tsiyayar hawaye ana sharewa. Bata sakekomawa barci ba har aka kira asalatu. Ta sauka tafada bayi tayo alwala ta bada faralo,ta zauna shiru bisa sallaya. Zuciyarta tana azalzala mata son ganinDan liti...... Muryar malami taji yana fadin, har kinkinyi sallah ne anti? Shine baki tashe ni ba? Tadanruntse ido, ta bude,yi hkri malami,na manta ne. Je kayo alwala,. Ya wuce bayi yayi alwala ya fito yayisallah. Yana idarwa, wanka yaje yayo yayi shirin skul. Bisa gadonsa ya koma ya kwnat.jim yayi shiru cankuma ya dago kai yace anti kifa tashe ni karki manta.Tace bazan manta ba,ya koma ya kwanta.ya bartazaune bisa sallaya. Anti Amina ce ta shigo,karfebakwai da rabi wai barci ne ya dauke ku? KaiMalami!... Ta bubbuga shi,yayin da mama tay firgigi ta bude ido, skul din fa? Ka kwanta kana ta slp?? Yasauko a firgice yace , nace anti ta tashe ni fa! NAGA ALAMA BAZAKU IYA KARANTA WANNAN BAKIN CIKIN BA, gara kawai a samu wani book, INA jiran ra'ayin ku, masu so a cigaba suyi COMMENTS masu son sabon littafi suyi LIKE. BAKIN CIKI 1***12 Tace, Ita ma aunty ai ta bingire, dube ta aza zaune take yinsa. Ta so kayi breakfast dadin kana jiranka. Ta juya inda Mama ke xaune tana famanxuba mika, Yayan ki zai fita ne, ki fito ku gaisa. Tace,Gani nan. Suka fice da Malami, ita kuwa mama bayita shiga ta wanko Fuska ta fito. Suna bisa tebur ta same su fuska ba walwala, ta ja kujera ta xauna, inakwana yaya? Yace kalau, ya lazu Doktan ki?Murmushin bai kai ciki ba tace, ai ni ban shi ba Yaya.Yace a Yau kuma? Zamuyi waya ai, zan gaya masaabinda kikace. Tayi shiru Aunty amina tace, me yasami idanuwanki? Kamar sun kumbura? Ai ba sa min ciwo, tace, to meyasa? Da alama dai sun kumbura.Ta murje idon. Yayanta na cewa, ke me zai dameki?Ita da take tare da lazy Dr. Suka fara dariya, ita kuwayake takeyi. Ta sa abincin, sai juya masa cokalitakeyi, ta kasa ci, da alama tana son tayi matamagana ne. Amma ta kasa, aunty amina ta kare mata kallo, tace wai menene? Ta dago ido ta dubeta, tadubi yayanta, jim kafin tace, Fandagori nake sonxuwa. Fandagori? Me zakayi? Yayan ta ya tambaya.Idanuwan ta suka yi rau- rau! Da kwalla tace, ina sonxuwa ne kawai. Ya xura mata ido yace, xo nan bebi.Ta taso a hankali ta zo gaban sa ta tsaya. Ya kamo hannnayenta biyu yace, me zaki yi a can? Bayan yaukwanan mu bakwai da dawowa? Tace Umma na keson gani. Ya dubi Aunty amina, yace kinji shagwabarbanza! Ke kadai ke da Umman nan ne wai? To ba zaiki ba ki ba, nan zaki zauna sai karshen wata. Ta karamurtuke fuska. Don Allah yaya kayi hkr ka bari in tafi. Ni wlh ko a motar haya xan iya tafiya, ba sai direbaya kaini ba. Yace, motar haya? Baki a tunaninki bebi,banso in sake jin wannan maganar, karshen wata inada hutu zamu tafi tare. Is dat clear? Ya fadi tare damatse yatsunta da karfi. Tayi tayi ta kwace amma takasa. Ya kara girgiza ya, ya kara fadin Is dat clear? Ta kara cunno baki ta kauda kai. Ya saki hannun yace je ki ci abinci, ta juya da gudu ta haye sama.Aunty amina ta kwala mata kira, Mama! Ya dagamata hannu, a kyaleta! Iya shege takeji kwana biyu,ko baki lura ba? Tace haka ne fa, ni ma ban ganemata ba kwana biyu. Ya dubi malami yace, lazy man ayi sauri mana. Yace na gama Dadi. Mu tafi kenan?Ya ce eh. Suka bar tebur. Madam ta kwaso masajakar sa da hularsa. Malami ya goya, ta sa jakar suka fito tayi musu rakiya xuwa mota. Sai da suka fita,ta dawo cikin gida. Kai tsaye wajen mama ta nufa,tana xaune bakin gado ta kumbura suntum! Idanuwan ta sun kada jajur! Ta kare mata kallo, sannan taxauna gefenta, wai Mama me yake damunki ne? Komunyi miki laifi ne? Ta kada kai. To me zai sa ki tashihankalinki haka? Wajen Umma nake son inje. Ai bahana ki akayi ba, tunda yace ki bari karshen wata kutafi, sai kiyi hakr xuwa tym din. Tayi shiru ba tace komi ba. Ta rungumo kafadarta, wannan abu na banimamaki, kamar yau kika fara xuwa garin nan? Dabakinki fa kika ce kin fasa kara kwanankin da kikacexakiki, balle ace matsa miki akayi. Tace sai da na zokuma naji bana son zaman. To kiyi hkr, tundaYayanki yace ba xaki motar haya ba. Shikenan, yauwa autan Umma. Ni bari in je inyi wanka, in dankwanta kafin rana tayi. Tace to, auntyn ta bar dakin takoma nata. Ta aiwatar da duk abinda take son yidaganan tabi lfyr hafo. Bata jima ba, ta sunkuci jakarhannu ta rataya ta yafa mayafi ta debo takalman tarike a hannu ta sadado ta sauko kasa. Shigar ta falon ke da wuya, wayar Al-amen ta shigo falon, gabanta yayanke ya fadi, ta tsaya cak! Tana zare idanuwan.Tsoron ta Allah, tsoronta kar karar wayar ta tashi antyamina. Saboda haka tayi azama ta nufi wajen wayar,ta daga kan taaje gefe, ba tare da tayi magana ba,balle ta san waye akan layi. Ta dan kara tsayawa, jim shiru bata jin wani motsi ba, tayi hamdala ga Allah. Taaje takalmanta ta xura tayi waje abinta. Babufargaban komai ta doshi gate har tana gaida masugadi. Suka amsa tare da fadin a dawo lfya. Taceameen. Tayi waje cikin sauri ta bar sashin unguwar tafito a sarari a inda ta samu shatan tashi ta kai ta tasha. Tayi muguwar sa'a fasinja daya akejira motarta tashi xuwa Minna. Inda daga can zata sami MotarFandagori. Sha biyun Rana Aunty amina ta farkabarcinta, ta sauko falon kasa, tin daga nan ta faraganin abinda bata sa ba ba, kayan abinci na aje bisatebur yadda ta barsu. Mama ta bata kwashe ta gyara wurin ba. Cikin ranta take fadin, lallai yau Mama tsiyatakeji. Haushi ya isheta ta nemi kujera tsakar falo taxauna ta shiga kwala mata kira. Shiru bata amsa ba.Mamaki ya isheta, t yunkura zata tashi idanunwantasuka kai bisa waya, Ah ji wani sabon iya shege. Sumama! Ta nufi kan wayar ta dauka ta mayar yadda take. Tana jan tsaki. Ta hawo saman ta fada dakinmama cikin zafinta. Ganin babu kowa a dakin yasatayi turus! Cikin sanyin murya take kiranta, mama! Kokina toilet ne? Shiru? Wai malam yaci shirwa. Tabude bayin vata ciki. Hankalinta ya tashi ta sauko dasauri tana kiran Mama! Har waje. Daya daga cikin masu gadin yake gaya mata ai ta jima ta da fita.Al'amarin ya daure mata kai. Ta dawo falo..... Tana mamakin mama. Karar waya yadawomata da hankalinta, ta tashi taje ta dauka, hello! Muryar aunty Rabi taji ta amsa. Hello aunty amina,Rabi ce, tace nagane ai ya yara? Lfya lau wlh. Waime ya smu wayar ku ne? Al- ameen ya kirani, wai tunsafe yake neman layin, amma yana engage. Tace, uhm.... Ke dai bari, ina nan ina ganin abin mamaki.Kamar yaya? Tace, Mama ce daxun da safen tacewaYayanta ita gida zata koma, yace ta bari karshenwata ya kaita. Nima na rarrasheta, har fa ta amince,wai kuma na tashi barci yanzun, bata ba dalilinta cikingidan nan. Sannan ina zaton ita ta cire mana kan waya ta aje gefe. Cikin al-ajabi tace, to saboda me? Oho! Kuma ba ayi mata komai ba? Wai zai yi mataRabi? Ko da ma anyi matan ai be kamata tayi hakanba ko? Tace gaskiya ne ka, ah to, ita da yayanta ne.Ni ba babu ruwan. Tace, amma ai mama bata dawannan halin, me yasa za tafar shi yanxun? Wlh bakiji ba duk Al-ameen ya damu, nace masa ya barizanyi tryn inji. Tace watakila don taga kowa na rawarjiki ne da ita, shi yasa take son ta lallace. Zata kuwayiwa kanta sakiyar da ba ruwa, idan ta bari yaron nanya kubce mata. Aunty Rabi ta numfasa tace, to yanxumenene abinyi? Tace, yayan nata zan kira Yanxun in gaya masa ta gudu, Allah ya sawwake. To ameen. Taaje waya, sannan ta sake dauka ta lallatsa lambobinmaigidan na Ofis, jimawa kadan ya dauka, ta zayyanemasa kaf, abinda ke faruwa. Nan take haushi ya rufeshi. Ya mike cikin fushi ya fito daga Ofis, ya fadamota bai zame ko ina ba sai tasha, jami'an union ya samu ya bayyana masu kamaninnta, nan take sukabashi tabbacin ta zo tashar ta shiga motar xuwaMinna tun safe. Ran maza ya kara baci kwarai. Yafada motar sa yana tambayar kansa, dama mama taiya irin iskancin nan? Lallai zasu gauraya, zatayabawa aya zakinta... Karfe uku da rabi mota ta aje taabakin titi, ta fito ta gangagro saitin shagon danliti, saidai shagon a rufe yake. Babu kowa wajen. Ta tsayatana kallon kofar shagon kafin ta wuce, tana tafe tanawaige ko zata ga Danliti ya dawo, amma har ta dainahango shagon. Babu alamun kowa. Taci gaba da tafiya ranta bace na rashin ganin Danliti, xuciyartacike da tambayoyi, tana hasashen menenemusababbin rashin xuwan Dan liti shago? Tun dagakofar gida yara ke kwala ihun mama oyoyo! Shi yasaUmma ta fito har kofar sassan dauke da mamaki bisafuskar ta. Suna hada ido tace ke kuma dga ina haka? Ta kwaso da sauri ta rungume ta, Umma na! Tayisauri ta dago ta, ta xura mata ido, meya faru ne? Mekuwa Umma? Na dawo ne kawai. Ta wuce uwar tabiyo bayanta, bata yarda da ita ba. Cikin falo yara sunrufeta, tace, kuyi hkr ban siyo muku komai ba, gakudin nan kuje ku siyo biskit. Ta dauko Naira Hamsin ta basu., duk suka watse da murna. Har yanxunUmma kallonta takeyi, tayi dan murmushi tace, saikallona kike yi Umma? Tace dole in kalle ki, kin shgokamar an koro ki. Ni bawanda ya koroni, ke nake tamafarki Umma, nace gaskiyya ni xan dawo. To inajakar kayanki? Tana can, kamar yaya? Yaya ne yace baxan taho ba, ni kuma na silalo na gudo. Ta daukisalati ta sauke, kika yi me? Kanki na lfya kuwa?Mama ki gaya min gaskiyya dawa kuka yi fada? Taceumma ni ina fada ne? Da wan xanyi kuwa? Umma kiyarda da ni, wurinki nazo. Ba zan taba yarda dake baMama har sai Yayanki ya zo naji ta bakinsa. Kuma wlh naji akasin abinda kika fadam sai na bata miki raifiye da zatonki, kinji nagaya miki. Na yarda, shikenan,Ina abbana? Ya tafi kd, tayi 'yar dariya, Allah sarki inaango da amarya? Yau kwanan su uku da komawa.Kije ki zubo abinci ko sai kinyi sallah? Tace bari infara cin abincin, yunwa nakeji. Ta tashi ta shiga ta xubo abincin ta dauko ruwa ta dawo falon ta xauna.Bata wani ci sosai ba, saboda cikinta ya cushe dayunwa, don ko karin safe batayi ba, bayan ta gamatayi sallolinta tayi wanka, cikin kayayyakinta, dakegida ta dauko tasa. Ta fito tace zata shiga sasa tagaishe su, daga nan zata wajen Baraka. Umma tace daga xuwanki? Ba inda zakije sai Yayanki ya zo najidalilin dawowarki gida. Ta ya mutsa fuska, tace kaiUmma! Barakara kamar wata bare, kuma wlh damada xan tafi bamu sallama ba, na wuce, hkr zanje nabata. Tace, tazo nemanki kinbi 'yan abuja, amma bainda zaki, kinji na gaya miki. Ta bata rai sosai. Ta jefar da gyele bisa kujera ta koma dakinta. Ummatace, in kinso kiyi bindiga, ba fushi ba. Ta shige natadakin. Jimawa kadan mama ta fito cikin sanda ta lekafalon, daga nan tana jiyi sautin Umma tana karatunQur'ani. Tayo sanda takalmin ta a hannu, ta daukigyalan tayi waje. Bata shiga sassan ba, kai tsaye waje tayi, sauri take kar wani ya ganta. Yaran natakaratu ta gaida Malam ta fice. Ga ta nan ga ta nan harkofan shagon Dan-liti, farin ciki ya lullubeta da tahango shi a bude. Sai dai kash! Tana isowa ta iskeayuba ne a cki. Tayi masa sallama, cike da mamakiyake kallonta har ya kasa amswa, gaba daya tsigar jikinsa ta tashi. Ya xura mata ido kafin yace, sannuko? Me za abaki? Tace ba komai, don Allah ko danlitina nan? Ya kara matsowa ido waje yace, a'a bayanan. Tayi dan shiru jim, kafin tace yayi nisa ne, eh to,kano ya tafi siyo kaya, amma watakila xuwa anjimako gobe ya dawo. Ta numfasa cikin rashin jin dadi, tace, shikenan nagode. Zan dawo xuwa goben. Ya nadan murmushi yace Allah ya kaimu. Ta wuce ta komagida. Ayuba bai gasgankanta idonsa ba, sai da ya fitoya bi bayanta da kallo. Ya dora hannu bisa kai yace,na shiga uku, amma Dan liti anyi mugun dan iska! Baikoma cikin shagon bisa benci ya xauna yana jimami! Mama kuwa tana tafe har tuntube tayi saboda takaicinrashin ganin Danliti. Ta shige gida can sassan sukawunanta. Hajiya Gaje tace, a'a saukar yaushe? Tace daxun nazo. Lfya dai ko? Tace kalau. To yamutan Abuja? Suna lfya, ina su Dan lami? Ko sunsami makarantar? Tace ai kuwa makrnta ta samu, shekaran jiya ya tafi, ana can sakkwato. Allah yataimaka. Amin. Umma tayi sallam sassan suka amsata dubi Mama tace, Abbanki ya dawo yana kira, tamike tana fadin to. Hajiya tace, ashe autan Umma andawo? Tace eh wai hankalin ta ne ya dawo gida.Sukayi 'yar dariya, Haj. Gaje tace, ah shagwaba! Sai da auran yazo ake kwa xucin gida? Kina wasa neyarinya. Suka fice suna dariya. Abban yana falo azaune, ta shigo da fara'arta, Allah ya taimaki maimartaba! Yace zo nan. Ta matso jiki babu kwari tazauna akasa gefensa. Mama me ya faru kika baroAbuja ko jakar kayanki baki dauko ba? Tayi kasa da kai tace, Allah abba babu abinda ya faru, cewa nayizan dawo wajen Umma, shine yaya ya hana, ni kumana gudo. Ya xura mata ido, yace, me ya sameki? Kina ma gani kamar ba laifi kika aikata ba? Haka kawaiki kamo hanya ki taho ke kadai, ba tare da saninkowa ba, idan wani abu ya faru dake, ya kike so mutane suyi? Wannan rashin hankali ne, irin wandaban taba sanin ki da shi ba. Ina fatan kuma daga shiba zaki sake ba? Ina fatan kinji da kyau? Ta kara kasa daidon tace, yi hkr Abba Insha Allah ba zan sake. Yanumfasa yace yanxun saboda Allah kinsan awane halisuke? Zaki gamu da Yayanki ai, kala bazan ce masaba, yayi miki duk abinda yayi niyya. Umma tace ni faabin daure min kai yakeyi. Wai mama ta gudo? Ta kuta tana zuba mata harara. Abba yace, tunda daiAllah yasa ta ido lfya, mungode masa, sauran magankuma sai yayanki yazo. Idanuwanta suka kwalla tana,duban abba tace, Allah abba bada gangan nayi ba,kullum mafarkin gida nakeyi, shine nace ni dai zandawo in ganku. Yace, to kin ganmu ko shi kenan? Tace ka gaya wa yaya idan yazo kar yace zai bigeni.Umma ta karbe, ai ko shi bai ce ba, ni zan sashi.Kuma tunda abin naki ya zama tsiya anan din zaki tazama, na ga inda zaki samu ki dauki wayar. Karyartsiya kikeyi! Ta turo baki tayi shiru. Abba kuwa 'yardariya yayi yace, dama kinyi shiru da bakini, da kanta zaki ji tana neman hanyar komawa. Ba kuma zatanba, yauwa! Ki ma sani. Ta shiga murza ido ko alamarbacin rai bata ji ba, tayi shiru tana sauraren suna tazazzaga mata tsiya. Ita bama wannan ce matsalartaba, kusan ma da za'ace ba zata koma din ba, ita adadinta. Damuwar ta daya, tayi tozali da Danliti ko hankalinta ya kwanta. Domin ko a daren yau ma takuma yin mafarkinsa irin na jiya. Ya kira ta amsakiransa har taje gunsa. Da wannan azalzalar songanin Danlitin ta wayi gari. Allah-Allah takeyi, abba yabar gidan, ta sulale taje ta duba ya dawo. Kafin lokcinfitar sa tayi har tayo wanka ta chaba ado. Yayan kuwa sammako ya bugo mata, karfe tara dai-dai yanaparkin kafar gidan. Ya bude ya but, ya kwasokayanta, da ganin yaddayake ya wurgo jakar kasa zaitabbatar da afusace yake kalla ya iso wajen dasurinsa yana masa sannu da xuwa, ya amsa, kalla yakwashe kayan ya shige da su cikin gida. Yaya abdulqadeer ya biyo bayansa, sallamar sa hade takeda kwala wa mama kira, Ina bebi? Abba da Ummasuka fito falon. Yaya Babba sammako kayo haka?Abba ya tambaya, yace ina fatan Bebi nan na. Yace ,ta iso tun jiya, zauna mana! Yace ina take tukunna?Umma tace tana dakinta tana jinka. Ya wuce dakin abba ya bishi. Mama na makure karshen gado, kaitsaye ita ya dosa, kafarsa daya ya dora bisa gadonya mika hannu zai janyota. Abba ya riko shi yanafadin, yi hkr Yaya babba ka dubeni ka saurareni. Yadubi abba ransa bace yace, abba yarinyar nan tana dahankali kuwa? Ban iya barci ba fa saboda bacin ran abin da tayi min jiya! Tana nufin tayi girman da ba zaa gayamata taji ba? Saboda muna wasa da ita? AbbayaCe, Allah ya huci zuciyar Soja. Zauna kaji, zaunanace ko? Ya zauna yana kallonta xuciyarsa natafasa. Umma tace, wlh da ka kyale shi ya tattabajikinta ko hankalinta ya zl jikinta. Abba yace ya dai karya ta kike so, kinsan irin dukan da zai yi mata?Yadda ya hassalo din nan? Ya juya kan Yaya yacigaba. Dubani nan Babban Yaya, kayi hkr don girmanAllah, ni kaina na san Mama bata kyauta ba, kumatun jiya na nuna mata kuskuranta. Ni tunani na ma kowani abu ne ya faru tsakaninta da maidakinka. Kayi hrk babban Yaya da yardar Allah ba zata sake ba.Idan kuwa har ta sake, duk hukuncin da ka yankemata kayi daidai. Ke kuma bashi hkr, maras kunyakawai. Tuni hwaye ke ta kwaranya bisa kuncinta,murya na rawa tace kayi hkr yaya don Allah. Ya ballomata harara yace, ga komatsanki can na kwaso miki, idan na sake ganin kafar ki cikin gida na, sai na karyaki. Kuma daga yau mun bata, kar sake min magana! Abba,Yace Allah ya huci xuciyar Soja, ai ba zatasake ba. Ta ma sake! Ta rarrafo da sauri, ta rungumebayansa, Allah yaya bazan sake ba kayi hkr. Abbayace, Allah sarki tsaknin babban Yayya da bebinsa, ai ba ajin kansu. Ko? Zuciyarsa ta fara sauka, sannua hankali ya huce, ya jawo ta gefensa ya zura mataido, ban sanki da rashin ji haka ba Bebi na, sabodahaka kar ki kara idan ba ki so mu bata. Ina fatan kinjini? Kwallan ta suka wuce da gude, tace Allah ba zansake ba Yaya. Ya share mata hwayen, ya wuce, shikenan, ki zauna wajen Umma, shi kuma lazy Dr.Din me zan gaya masa? Tun jiya yake damun mu.Tace ai zan dawo. Haka xan gaya masa? Ta amsa daka, yace an gama. Ya dubi Abba yacigaba, munshirya abba, Umma ki yi hkr idan ta kara guard roomxan sata. Tace yayi kyau. Abba yace, Allah ya so ki 'yar nema, da kin jigata. Suka fara dariya, yace dukda haka sai na dan tabata. Ya duma mata dundutsakar baya, ta fasa kukan shagwaba, tana susarbaya. Ya mike yana dariyan mugunta, yayin da takefadin wayyo Allahna. Ka dai jibgeta da wayau, injiAbba, yace ladan sammakon da nayi, ta hana min xuwa ofis. Suka koma falo suka gaisa. Karin safekawai yayi a gurguje ya shiga sauran sassan ya gaidakawunansa, ya fito ya sake dibar hanya. Yau maAbba kd ya sake tafiya bin wata kwangila da yakenema. Bayan sun gama ayyukan gidan. Ummakwanciya tayi, ba dadewa barci ya kwasheta. Nan da nan Mama ta kwashi takalma da gyale tai waje ta nufishagon danliti, amma kash! Ayuba ta sake samu.Dan liti bai dawo ba kamar zatayi kuka, ta tsayadauke da tagumi..... Ayuba yace, karki damu xuwaanjima, ninasan bazai wuce yau ba. Tanumfasa muryasanyayetac e, zanzo anjiman, Allah ya sayadawo lokacin.Yace, amin ta juya ta fito ta danjima a tsaye batasan abinda ke mata dadi ba.Salalau- salalau ta komagida, ta fada dakinta, ta kwantaranta na mata daci kamar tayitsuntsuwa tabi shi kanon. Ta juyanan, tajuya can duk inda ya jefa idonta,shi take gani yamiko hannayensa yana murmushi.Yana fadin zomana! Jikin ta gaba daya ya hauciwo, zazzabi naneman rufeta. Har cikinkasusuwanta take jin ciwontamkar mai sanyin kashi. Karfehudu bayan tayi sallar la'arsar tasake sabon wanka ta sauya kayatacewaUmma zata wajen Baraka. Ummabatayi musu ba,saboda sun warware matsalaryayanta. Cike da farinciki ta bar gidan kuma xuciyarta najaddada matatabas taga Danliti. Wayyo Allah! Ranta ne kawai kesaka mata haka, saboda ta zaku tagashi, ayuba, ne cikin shagon ahain yanxun kam ya rasa kalmar dazai gaya mata. Ta zura masa ido,tace, kodai guduyakeyi idan ya hango? Ya kada kaiyace, wlh baidawo ba ne Mama. Ashe kasansuna na nan? Yayidan murmushi yace, haba kamarwani bako a garin?Asalin sunanki sakeena, ko banfada daidai ba? Fuska sake taamsa, haka yake, amma abokin kayacika yawo, dama haya yakedadewa. Yace, kin sansha'anin kasuwa, watakila ma bakano kadi ya tsayaba. A fada nan ne, a fada can ananeman halali. Tacegaskiyya ne. Barin in tsallakawajen kawata, may bekafin in fito. Allah ya taimakeni yadawo. Yace, Allah yasa. Kin damuda yawa, neman me kike masa ne?Ta gyara tsayuwa tace, a'a tsakanida shi ne, so kake kaji? Ya kada kai yana 'yardariya yace, wane niinji sirrin ku? Sai dai in ce Allah yadawo miki da shilfya. Tace amin, barin in je indawo. To shikenan. Tabar wajen ta tsallaka titi. Al'amrinkara daurewa Ayua kai yakeyi, yama rasa yadda zai fassara shi.Kamardaga sama wata mota (ToyotaCarina) tayi fakin akofar shagon, me ayuba zai gani?Mutumin na sa nea ckinta. Yayi azama ya fito dashgo, yayin da shi maDan liti? Yace, siyo ta nayi. Motar?Ya tambayadauke da mamaki. Yace, eh mana.Ya bashi hannu suka tafa, ka tsulana tsiya mutumin na a bayankasa, ya akayi? Yace yadda akayikenan? Kasan itamota akwai kara aji, shi yasa nashiyo, kada yarinyarnan ta dauke ni wani gara. Yacekai! Don Ubanka dalabari, shigo dai daga ciki! Yayi dangutun tsaki, tanata xuwa nemana nakoa? Ya sakibaki ya na son kallonsa, ka ma sanikenan? Ahaf! Kana wasa danine.... Ya wuce ya bude but, yasake juyo wa ya kalleshi, ka na nan tsaye? Ga kaya kazoka taya ni cirewamana. Ya tako a hankali ya tsayagabansa, kana bantsoro Danliti. Wlh kabi a hankaliMalam mu kwashikaya in ka na kwasa! Mts.. Ya jatsaki ya shigo fito da kaya yanashigewa da su shago. Ayuba natayashi har suka kwashe. Tsakar shagonya baza 'yartabarma ya zauna. Ayuba na bisakujera, kofin ruwaguda ya shanye, ya aje kofinsannan ya dubi Ayuba,duk kayi wani la'asar, kai banza newlh, yace ai doleabin nake da ban tsoro. Tsoro?Tsoron me xanji? In gaya makayadda kasan Tv haka ake nuna minitaakofar shagon nan. Sakeena a tafinhannu na take,sai yadda naga dama da ita. Yacigaba da kada kofardamarsa. Ayuba yace, xan bakashawara mutumi na,tunda ka nace, ka matsa sai da kabirkita hankalinyarinyar nan, kuyi aure kawai kahuta da kwashe- kwashe. Sakeenakarshe ce wajen kyau, ni ban mataba sanin haka ta hadu ba, sai danatsu anan tanamin magana. Kaga idanuwan takamar madara!Mts.... Ya dan kada kai. Yaci gaba,yarinyar nan inaiya ma cewa idan ka aure ka hutamutumi nan. Adage yake kallon sa tsawon lokacinkafin yace, aure? Wa zai aureta? Kana hauka ne? Idan na aure ta,insiyo mata kima? Yadda tageni,haka kowa sai yazage ta a garin nan. A'a danliti! Karika sayan tsoronAllah a ranka... Ya daga masahannu, ya isa hakaAyuba! Naga alama kai ma sai nasaan daure minbakinka, kar kaje kana min shegensurutu a gari. Domin daddawa bazata gayawa manda baki ba. Saidai ni bana zurfi shige-shige irinnaka. Shi yasa nakeba ka shawara ka aureta. Malamba ruwanka! Ni banshakkar Uban kowa, irin ta irin tamasu taurin kai biyuna baro da ciki a garinsu. Daya akano, daya a zariya.Zaman da nayi a can kafin in dawonan. Ido waje yace, iye! Kwarai!Me zai danne ni? Kila ma yanxuduk sun haihu, wa ya sani? Ayubaya kara la'asaryana kallon yadda yake kadakafarsa, ko ajikinsa.Wata 'yar fulani ta leko tana fadin,hannun ku dai! Adama fura? Dan liti yace, dama tahamsin. Ta sauketa shiga damun fura. Dan liti yafito ya zauna bisa benci yana hirada 'yar fulani ya bar Ayuba. AwadayaMama tayi a daddafe wajenBaraka, duk hankalin tayana can tunanin ko Danliti ya iso? Suka fito tare zasu wuce Baraka tace, Yau ba zakishiga wajenkishiyar taki bane? Ta ya mutsafuska, tace, kullumnazo sai na shiga wajenta? TaceHala Dokta yayi laifi ne, ni nagako maganarsa baki min ba. Tace ninadaina yayinsa. Tayi 'yar dariya tacemama kenan.Ashe Dr, zaiyi laifi har adainayayinsa? Dakata, kina nufin kin warwareranar da akasanya miki? Tabbas haka ne,domin hankali na ya fikwanciya da kai.Yayi wani saurayinmurmushi cikinnishadi, nagode sakeena, kin cetorayuwa ta, ban sanirin godiyar da xan miki ba. Dadiya rufe ta, ta rausayakai, nima na gode, kin gode? Menayi na godiya? Dole ka godewa wame sonka. Ya kara jingina da motayaxura mata ido, kamar na sace kisakeena, kalaman kina gigitani, gashi banzo miki dakomai ba, balle inbaki tukwici. Ta kada kai tanamurmushi, ban sankomai naka. Ba kiso nake na, al bahaka bane nufiba, so na gaskiyya baya bukatarkudi. Allah ko? Eh mana. Kin finigaskiyya. Amma duk da hakayakamata ace na zo miki da waniabu, hausawasunce yaba kyauta tukuici. Kar ki jikomai kyauta saikin ture sakeena, tunda kika zabeni. Tace gaba damurmushi tana fadin, to Allahyasa. Awa daya da rabisuna tare, sannan sukayi sallama,ya wuce, ta shigo cikin gidan.Umma na kwance bisa doguwarkujera afalon, ta shigo simi-simi zatawucem umma tace zonan Mama! Ta dawo gunta zaunabisa kafet. Ummata tashi zaune ta dube ta tsaff!Kafin tace, ke da akece kije ki gaya masa an sanya mikirana, me ya kaikidadewa. Ta sunkuyar da kai, batatanka ba, ban gane miki ba Mama,kina so a zage mu a garin nan ne? Bikinki fah saura wata uku ko kinmanta ne? To muba kananan mutane bane, ko kingaya msa ko bakigaya masa ba, ba zaki kara fita ba! Kinji na gayamiki! Ba zaki kawo mana sakarciba, dan na lura taketaken ki kenan. Idan kuma ba hakaba, abbanki zai maida ki minna koabuja, tashi ki ban wuri! Ta mikeda kyar fuska kumbure, ta wucedaki. Umma ta bitada kallo ganin yanayim fuskarta yasa ta kama bakicike da mamaki. Ta jima zaunesannan ta tashi tarufe ko ina ta kashe fitulu ta samiabba a daki. Waikasan yarinyar nan sai yanxun tashigo? Ni fah ban gane sauyinyanayin ta ba, ina mata fada tanabatarai, yace ai na leka ta falon bakina hango su sunawasu dararraku, ni ban ganewanene ba, amma yayishigarsa tsaf harda motarsa. Kajiba? Allah ya sagobe da kanka zaka fita ka bashilabarinta. Ai kamarkin shiga raina, kwanciyar nan danayi abinda nake ta tunani kenan,karta hadu da romon baka, yajikirtatunani nta. Ya kamata ka hanzartayin wani abu. Yazama dole kar girma na ya fadi.Haka suka kwan daabin cikin xukatansu. Ita kuwaMama ba nantunaninta yake ba, hankalintakwance tayi barci cikinshaukin son dan Liti. Da safe Abbaya xaunar da ita yayi matanasihohi tare da jan hankali, akankuskuranda take neman aikatawa. Har yayi,ya gama batacekala ba. Abinda bai sani ba, shinebabu kalma dayada ta shga kanta, domin kuwa tananan akan bakanta,duk ta inda za'a bullo mata. Danliti ne, ba sauyi.Bayan sun gama ayyunkan su, tayiwanka Umma tayi barci ta sadadata fice kamar jiya. A shago ta samiDanliti, koda ganinta, sai yai tsayea kofa, bakinsahar kunne ya mike, ah! Sanyinraina kamar kinsantsundum nake cikin tunaninki. Tatsaya rungume dahannaye ta zuba masa ido. Tace,hum! Haka naji.Baki yarda ba kenan? Dubi lissafinda nakeyi dole na aje shi don banafahimta. Tayi dan murmushi, to yaka kwana? Ya amsa barcin nan baiyidadi basakeena, ko'ina najefa ido ke nakegani, kamar zanzautu nake gaya miki. Tayi dariyafasa min kai. Saiga Ayuba ya shigo, manya manyainji kanana! Tadubi Danliti tace, ka yarda mugaisa? Ku gaisa sanyin raina badamuwa. Ayuba ya saki baki au saima kayarda zamu gaisa? To matar kace?Ya kada kai,wane ni? Tafara dariya tana fadinkadai ina kwana?Yace baxan amsa ba. Dan liti yaceto idan bazakaamsa ba, ka fita ka bamu guri,yace ai ko baka ce ba.Ya juya ya fice mama na dariya,tace wlh baka da dama korarsa makayi? Ah to yadawo ne? Ta kadakai a'a, yace to shigo daga cikimana kya ta tsayuwaanan, tace wlh karka damu datsayuwata. Yadan batarai me yasa? Tace dan Allah karkabata ranka, yasaki fuska nima na hkr banso natakura ki. Ammadole kici wani cikin shagon nan,me xan miko miki? Ta kada kaidon girman Allah ka barshi. Yaceanan nezamuyi fada idan har baki sa minalbarka ba. Me zanbaki? Ta sa hannu cikin wani katontire ya dauki mintguda daya tace, na dauka Allah yakawo kasuwa. Yazura mata ido kawai, bai ce kalaba. Tayi murmushi tabare mint din ta ajefa baki, kaganinama sha. Yace yanxun duk girmanshagon nan ki rasa abinda zakidauka, sai banzan sweet. Ta rufebaki tana dariyakafin tace, baka gane manufa ta bakenan. Na daukisweet ne saboda mahimmancinkalmar, kai sweetheart dina ne, dole in sweet ashagonka. Yayi 'yardariya yace, shagon mu zakice. Toshagon mu. Yauwa yanxu najimagana. To ki kara sweet dinmana, tunda ita kika fiso, zan karabari sai zan tafi.Yace nabari sakeena ta. Sun jimasuna hira, sai datakin taci tashin mama daga barci,sannan tace masazata koma gida. Ya dauki leda yacika mata da kayanzaki, ya bata. Ta sa hannu ta amsatana ta xuba godiya. Ya dago kantaya fito, barin in dan taka miki.Tace ka barwa shagon wa? Bayanka kori Ayuba? Aiko bakin kwata na rakaki ko? Ta fito waje tana dariya, kawai saiga Barakata tsallako titi. Ido sukayi da junabakinta har kunne,ta bar Dan liti tsaye tayi gunta,kawata! Ta tsaya tanamata duban da yafi gaban mamaki? Tace ban ganeba? Kamar yaya? Daga shagonDanliti naga kin fito,eh menene? A tunani na kodasiyayya ce, ajinki ya wuce ki yi ta ashagon Danliti. Amma sai nagakamarkun fito tare kina dariya. Ko idonane? Tace kemuguwar 'yar sa ido ce wlh, bamaganar sa ido bane,wai da gaske daga shagon kika fito?Daga can nake.Amma dai siyayya kikayi? Barakake kika haifeni ne? Wannan irin tambayoyi, me yadame kine? Ta fizge ledarhannunta, ta duba idan sweet kikeso ai gara kitsallaka shagon Okundiri ki siya, yafiye miki mutunci.Arnan? A waje na Okundiri ya fiDanliti mutunci. Tagyara fuska tace, ni kuma wajenabai fishi ba. Fadazamuyi Mama? Yaushe kika faragood time daDanliti? Ban sani ba, ta nuna tace,kina nufin yayi nasara kanki? Baikamata ba, domin a iya sanina, bayaudara Dr. Kike ba. Yaushe kikacanza? Ban sani baBaraka. Haba mama, ai ko laifi Dr.Yayi miki bagirmanki bane ki huce haushinkiwajen Danliti. Kigayawa manya mana ayi masafada. To Ummamtsw..... Ta fige ledar ta, ta dawotana kara zuba tsaki. Baraka kuwatsaki tayi musamman da tagaMama ta sake komawa wajen Danliti. Allah kadaiyasan me sukace. Ta dai ga Mamata wuce, tanadariya. Gabanta ya kara faduwa, tadafe kirji tanaInnalillahi wa Inna ilaihi raju'un!Wlh sai Umma tajimaganar nan...... KARSHE SAI MUN HADU A NA BIYU So Ko Kauna? Go to Home BAKIN CIKI (TRUE LIFE STORY) 2***1 Ta wuce inda aka aiketa kamar zata tashi sama sbda saurin ta dawo gida.Ta zube wa inna cefane,ko zama bata yi ba ta fara fadin "inna mama na cikin hankalinta kuwa? Tace,me tayi? "Kin san danliti ya dawo....""Danliti?" Waye shi? Dan gidan buzu mai shayi fa inna."Oho ,ina jin ki me yayi? Lokacin da aka yi bikin yaya Abdulrahman danliti yaga mama ya nuna yana son ta wlh a lokacin ko kallonsa bata yi amma ban san yadda aka yi ya shawo kanta ba,ynzun nan na gamu da ita Ta fito shagonsa leda cike da kayan sweet." Inna ta dafe kirji ido waje,mama fa kika ce? Wlh inna ni kaina mamaki ya kusa kashe ni.Danliti dan iska!"Inna tace,mun shiga uku ni saude wai! Ban ga ta zama ba dole in bincika na tabbata gidansu ba'a sa ni ba! Kai mama kamar mai hankali,me zai tsone mata ido a wajen yaron nan?Kai Allah ka shirya mana yara.Bari babanki ya shigo Insha Allahu yau din nan za ni gidan gara a yiwa tufkar hanci,kar ya kai mu ya baro!" Ya kamata inna,ni ina ganin ma kamar fada suka yi da Al-ameen don tun dawowar ta bata so ayi maganar sa."To ba sai ta fadi ba,ko yayyinta sun isa su kira shi su sasanta su balle ga iyayensa a gari."Ni ma dai hakan na gaya mata. Tace min babu ruwa na" "ita mama din ta fadi hakan? "Ko yanzu ta maimaita min kiris ya rage mu yi fada a titi,inna ta kuta,ta numfasa,kai jama'a yara halin su sai su,Ita fa ta kawo shi ba dole aka yi mata ba?Ta zabga tagumi bakin tana maimaita salatin Manzo,Da azahar mahaifin baraka ya shigo gida,inna saude ta maida masa halin da ake ciki.Nan da nan ya bata umarnin taje ta bincika,ai bata bata lokaci ba,cikin tsakar ranar nan ta kama hanya ta nufi gidan uban dawaki.Umma na daki tare da abban shi ma shigowarsa kenan gidan aka gabatar masa da abincin sa yana ci.-Inna ta shiga suka gaisa sannan suka koma dakin umman.Bayan sun gaisa da en hirarrakin zumunci kafin tace.magana ce tafe dani yaya amma ki duba ko alhaji ya gama cin abincinsa zan so in fade ta a gabansa."Nan take jikinta ya mutu,tace me ya faru saude?"To magana ce data shafi mama na rashin jindadi shiayasa nace ba zan bari ta kwana ba dole in zo in bincika,sai dai alhaji shi yafi dacewa ya sani,tunda nayi sa'a yana nan.Tayi dan tagumi......Subhanalillahi!Bari in yi masa magana.Ta mike jiki a salube ta shiga dakin abba ta iske ya kammala tace,wai magana ce tafe da saude idan ka gama ka taso muje,To muje gani nan".Ta gyara zama ta maida musu abinda baraka ta gaya mata umma ta shiga tafa hannu,abba kuwa sai daya mike."Kar dai ace shi ne yazo jiya da daddare?Lallai biri yayi kama da mutum,ina maman take? Umma ta dube shi ido taf da kwalla,tana daki. Kira min ita!Ta mike ta fita,har suka dawo tare babu wanda ya tanka sbda tsabar mutuwar jinin jikinta,a darare ta karaso dakin tana fadin,inna sannu da zuwa."Ta zuba mata ido,ke ma sannu."Ta gaishe da abba da umma na mata kallon mamaki,ta dube shi suka hada ido,tace abba ga-ni" yace,wanene yazo gun ki jiya?Ta sunkuyar da kai,tayi shiru,ya daka mata tsawa,ko baki ji ne?Nace waya zo gun ki jiya? Tana rawar lebe tace dan- liti?"Kin kuwa san ko waye danliti a garin nan? Tayi shiru,mama ni kike so ki mayar tsohon bnza,ki tozarta?jiya me na gaya miki?To ni ba hayaniya na kira ki mu yi ba domin a iya sani na ke mai hankali ce,kin san abinda ya dace,kin fi kowa sanin cewa saura 'yan watanni suka rage bikin ki.Sannan idan kika nutsu kika yi tunani ba mutuncin mu bane daga ke har mu ace an gan ki,kina karakaina a shagon wani ma,balle danliti sbda haka nake umurtar ki daga rana mai kamar ta yau,bana son in sake jin wani labari makamancin wannan!Ina fatan kin fahimce ni?Ta kara sunkuyar da kai yayin da idanuwanta suka fara tsiyayar ruwan hawaye,umma ta muskuta ta karbe "kin bani mamaki ba kadan ba mama,wai ma in tambaye ki,me kike nufi da bin sa har shagonsa? Shiru babu amasa,umma ta cigaba,wannan katon sakarci da me yayi kama? A zaton ki abin birgewa ne yadda 'yan mata ke tsayuwa kofar shagon samari suna amsar abin hannun su?Ban taba zaton hakan zai fito daga gareki ba mama kuma mun saurara miki ne kawai sbda wannan shine karo na farko da irin haka ta faru!" Inna tace,kin ga gidan nan da dukkan jama'ar gidan dake cikin sa ana ganin girma da mutuncin su musamman mahaifnki,don girman Allah kar ki bari wani ya rusa wannan ginin,ya hure miki kunne ya kai ki ya baro,kin ji mam? Ta goge kwalla bata ce uffan ba,abba yace,to mun ci mun rufe anan bana son ki sake aikata wani abinda zai sa ayi miki zama irin wannan,kin ji ni? Ta amsa da kai tana goge kwalla.umma tace tashi maza muje ki dauko min ledar kayan da aka ce ya baki,a iya sani na dai baki da yunwar su,maza tashi muje!Ta mike da kyar umma ta tasa ta suka je dakin ta dauko ledar.Umma ta fizge cikin zafi tace,Allah yasa in sake gani ko ji sai kin sha mamaki!" Ta fice ta bar dakin,ta bar mama cikin tashin hankalin da bata taba jin irinsa ba,har inna ta gama zamanta ta bar gidan mama na aikin kuka a daki domin dai tamkar sun kara debo soyayyar danliti ne sun kara antayawa cikin zuciyarta.Ita wannan ranar da suke kwakwazon an sanya mata ta jima da manta saurayin ma balle ranar,ba shi a idon ta ko birnin zuciyarta.Al'amarin ya daurewa iyayenta kai,shin wai me mama take nufi da kukan ta? Tambayar zukatan su kawai suke yi amma basu da tabbacin amsa.Karfe takwas da rabi cif! Lokaci ne da motar danliti ke fakin a kofar gidan uban dawaki,kai tsaya ya aiko yaro a kira masa mama,abba na nan a falo yana gadin zuwansa don haka yace da yaron yaje yace tana zuwa. Umma ta fito masa da kullin ledar kayan kwalamar da ya ba mama Abba ya karba ya bi bayan yaro kamar jiya,yau ma yana harde jikin motarsa yana kada mukullai sai dai yau kananan kaya ke jikinsa,gaba daya ya firgita kofar gidan da kamshin turare.Yana hango uban dawaki tilasa ya gyara tsayuwa yana 'yan kame kamen gulma ko kafin ya karaso ya tsugunna yana fadin,sannu alhaji,yace yauwa sannu,ya sake fadin ina wuni? Lafiya kalau,mike abin ka,magana zamu yi,ya mike a hankali yana sunkuyar da kai kamar muminin gaske.Abba yace magana guda daya ce nake so zan gaya maka danliti,'ya ta sakeena na riga nayi mata miji,tuni aka sa musu rana har ma lokacin ya kusan zuwa da yardar Allah sbda haka ina rokon ka da girman Allah kayi hakuri ka nemi wata,daga yau kar ka sake zuwa gun mama don tana da miji,ina fatan ka ji ni? Ya dan yi shiru jim kafin yace naji alhaji amma nima ina roqon arziki ka bar ni in rinka zuwa muna gaisawa,tnda ba'a daura ba.Wlh..."Abba ya katse shi,ba zai yiwu ba danliti domin koda babu alkawarin wani akan mama kai kanka ka sani zai yi wuya ka sami auranta,sanin kanka ne kaf garin nan babu wanda ya san tushenka,kaje kayi tunani mana.Ya saki baki yana kallon abba ran sa a bace,abba ya mika masa keda yace ungo nan,yasa hannu ya karba kafin ya cigaba da fadin,abubuwan daka bata ne dazu tunda ba auranka zata yi ba bai kamata ta amshi kayan ka ba.Don Allah kayi hakuri ka nemi daidai kai,sai da safe.Ya juya ya shige gida abinsa ya bar danliti a tsaye. )Ya kara harde kafafuwansa yana irin murmushin mugunta,sannan yace ko banzo ba ita zata zo wajena,koda kuwa kasheta zaku yi ta dawo.Dama ai zuwan nawa na hure kunne ne ba wai neman nake da gaske ba."Yayi er budurwar dariya ya bude motar sa ya shiga ya sake fadin,sai ni dan gidan buzu mai shayi taba ni kaga tsiya da bala'I!Ya ba mota wuta yaja ya bar harabar gidan hankalinsa kwance.Sabanin mama da take ji kamar ta saci jiki cikin daren nan taje wajen danliti shiyasa tayi ta leken falo,amma kash!Abba da umma sun ki tashi har dare yayi sosai suna tattauna zancenta.Daren nan bata yi barcin kirki ba sbda bakin cikin an hana ta fita ganin danliti.Gari ya waye ko alama umma ta ki sakar mata fuska,sam abin bai dameta ba Allah- Allah take yi kowa ya kama gabansa,itama ta samu ta sulale,ai kuwa abba na fita karfe goma umma ta gama abnda take yi,ta dare gado kamar yadda ta saba barcin safe,mama ta gama caba kwalliyarta ta sadada ta bar gidan.Ta kwarara sallama kofar shagon danliti,ya taso cike da fara'a yana amsawa kafin yace,a zatona ke ma zaki juya min baya ne,har na fara shiga damuwa,jiya sam ban yi barci ba.Ta dube shi cike da tausayi tace nima haka danliti ko gyangyadi ban runtsa ba,me zai sa na juya maka baya alhalin na san cewa nima zan cutu? Ya zura mata ido a marairece yace,abbanki ya nuna baya so na ban san yadda zanyi da rayuwata ba sakeena,kar ki bari ciwon zuciya ya kama ni.Kwalla suka taru cikin idanuwanta tace ka daina fadar wannan maganar don Allah,in ka ga na rabu da kai to sai dai su kashe ni in daina numfashi,zuciya ta kai take so kuma bana ra'ayin auran kowa face kai." Kwalla suka zubo bisa kuncinta.Da sauri ya tauko sabuwar t鐭泂hu kware ta ya yago ya miko mata,"share hawayenki, ki daina kuka.Na yarda dake sakeena,amma mece ce mafitar mu? Ta dan kada kai tace, "zanyi tunani,ka ban dan lokaci kadan,zan samo mana mafita.'ya daga kanta ya fito ya gyara zaman benci.Yace zauna kiji Ta zauna gefe shi ma ya zauna ya fuskanceta sosai yace,me zai hana ba zaki gaya musu ni kike so ynzu ba?Ta daga ido ta dube shi,jim,amma ba tace komai ba,yace "kar kiji tsoron komai kai tsaye ki gaya musu ke kin sauya ra'ayi ni kike so,za'a yi miki tilas ne?Dole a baki wanda kike so,don babu wanda zai zauna miki da shi,idan kuma kina son in rasa raina ne shikke nan........Ta kada kai tace,"nace ka daina fadar rasa rai danliti idan ka mutu nima mutuwar zan yi.Ka kwantar da hankalinka insha Allahu a yau zan gaya musu na sami sauyi wanda hankalina yafi kwanciya."Ya dafe kirji,ya lumshe ido yace,kin sa naji sanyi cikin raina sakeena.Ya bude ido ya bi ta da kallo ya cigaba,idan kika yi min haka kin gama min komai sarauniya ta,ba zan cika baki ba sai mun yi aure zaki ga tsantsar son da nake miki,bana jin akwai wata 'ya mace a fadin duniyar nana da zata sami irin gatan da zan nuna miki." Tayi dan murmushi tace,Allah ya nuna mana,yace amin.Ya dan gyara zama ya sake gadin,"wai sakeena kin san cewa kin fi kowa kyau a duniyar nan?Ta saki baki,ido waje tace,duk duniya? Wlh duk duniya babu mace mai kyau irin naki,ta kada kai tana murmushi tace,"ka daina fasa min kai danliti,ni na san ban kai ka ba,ya washe baki ya nuna kansa ya9e "ni kuma? A'a ni dai kike son ki fasawa kan,ina ni ina ke? kin gan ki kuwa?kin ga wannan dan bakin naki dagwas ba karamin kashe min jiki yake ba."Ta sunkuyar da kai tana 'yar dariya ya bita da kallo yana shafo habarsa."Mama!" Muryar kawai taji anyi mata wani gigitaccen kira,gaba dayan su suka kalli mai magana,ta bi shi da kallo babu tsoro ko wata fargaba tace,ah! yaya ali! saukar yaushe?"Ya kara tsuke fusk,yace me kike yi anan?"Tace me kuwa?Ba komai,taso muje gida,kaje ina zuwa,"ina wasa dake ne? nace ki taso mu wuce." "Ta dubi danliti suka hada ido yace,tashi ku tafi sai wani lokaci ko?Ta dan numfasa ta mike ta wuce,yaya alin dake tsaye,ya bi ta da sauri ya sameta,"mama,wai mafarki nake yi ko kuwa gaske ne?Ta yamutsa fuska "da aka yi me?" Zaune na gan ki kofar shago kina hira da wani...." 'Wani? Ba ka ma san danliti ba?"Shut up don Allah!waye danliti kike gaya min magana ba dadin ji?Hauka kika yi?Ina mutunci ga'ya mace tana hira da maza a kofar shago gaban jama'a? Ban san ki da wannan ba,yaushe kika canza mama? Ta ballo masa harara ta ja dogon tsaki ta kwahsi sauri ta wuce shi,shi ma ya biyo ta yana fadin,ban gane nufin ki ba?"Ta juyo ta dube shi tace,wai menene yaya ali?"Shi kike so?" 'Ai kaji,menene na sake tambaya? ya kara cika da mamaki,'Ban fa gane shi ki ke so ba mama.Ina Al-Ameen din?" Ido jajur! Ta dube shi,"kai ka san wannan sunan,don girman Allah ka kyale ni da tambayoyin nan." "Ba zan kyale ki ba Mama,hasali ma sai na gaya wasu Abba.Wannan ai zubar da mutunci ne da cin amana!Me ya tsone miki ido a wajen Dan-Liti?Ke ma kin shiga sahun 'yan matan da yake ruda da kyan sa ne?Kai na ya daure Mama.Allah yasa abinda na ke gani da ji ba gaskiya bane." Da gaske ne yaya Ali! Kuma ko baka gayawa su Abba ba,ni da kaina zan gaya musu."Ta zura da gudu ta bar shi tsaye, shakare da mamakinta.Kafin ya iso gida kansa,ya kusa fashewa sbd tunani da al'ajabi.Rokon Allah kawai yake yi Allah yasa mafarki yake yi. Kai tsaye sasan su Mama ya zarce.Suna tsakar falo umma ta tirke ta da tambaya,"Idan biki gaya min inda kika je ba sai na sumar dake yau a gidan nan!"Yayi sallama.Umma bata iya amsawa ba,sbd bacin ran da take tare dashi.Ya-ce,'yanzu na koro ta daga shagon Dan-Lati suna zaune bisa benci suna hira Umma.Yaushe Mama ta sauya haka? Tuni Umma ke sallallami,ta dafe kirji ta-ce "shagon Dan-Lati ki ka koma Mama? Mu kike so ki zubarwa mutunci a garin nan? Ai kuwa baki isa ba,ba ki isa ba Mama!'Ji ka ke tim! Ta rufe ta da duka ta ko'ina.kafin yaya Ali ya kawo mata dauki,ta sha dan banzan duka.Kukan ta ya watsu cikin sassa,matan gidan da kananan yara suka sheko don ganin meke faruwa?Al'amarin ya daure masu kai,ganin Mama na birgima tsakar falo tana ture hannayen Yaya Ali dake kokarin rarrashinta BAKIN CIKI 2***2(TRUE LIFE STORY) Wa ya mutu Ali? "suka tambaya,yayin da umma ta fito daga daki dauke da wayar rediyo kafin su yi aune,ta fara tsula mata.Haba gaba daya matan suka cafke hannun Umma, 'Hajiya Halima! Lafiya wannan abu haka?Me ta yi da zafi irin wannan duka?" Umma na haki tace wai yarinyar nan ita ce zata siyar mana da mutunci? Ta rasa wanda zata tsaya da shi, sai Dan-Liti? "Dan-Liti? Waye Dan- Liti?"Dan gidan Buzu mai shayi mana! Yau kwana uku kenan muna fama da ita ta rabu da yaron nan,ta ki! Jiya yazo kofar gidan nan.Alhaji da kansa ya same shi ya gaya masa tana da rana a kanta.shine don dibar albarka ta bi shi shagon sa,yanzu Ali ya ganta ya koro ta! Wace irin tijara ce wannan sbd Allah! Tuni suke kallon juna suna tafa hannu,hajiya hajo tace "danliti kuma?Waye bai san tarihin su ba a garin nan?Yaron da tun tasowar sa garin nan basu da aiki sai bata 'ya'yan mutane koda baki da wayau sosai ai kin yi dan hankalin da zaki gane buzu mai shayi kasurgumin kwarto ne,shi kuwa danliti kananan yara sau nawa ana kama shi dasu?Ko kin mance ranar da dubu ta cika suka ci shegen duka.Danliti ya sha da kyar shi kuwa buzu ya shura barzahi?Me ya dawo da shi kike kwadayi da har idon ki ya rufe kika kasa duban kazantar dake tare dashi?Hajiya Gaje tace "duk ba ma wannan ba kina nufin zaki fasa auran Al-ameen ne?Umma tace,karya take yi sai dai bayan ran mu,bari kuma alhajin ya dawo,yau din nan zai maida ta minna tnda zaman naki anan abinda ya haifar kenan!Ta tashi da gudu ta fada dakinta har da danna sakata ta bar su nan suna maida yadda aka yi. Shi dai yaya ali tunda ya sunkuci jakar sa ya fada dakin mahaifiyarsa bai sake kyakkyawan motsi ba sai tsabar tunani.Muryar mahaifiyarsa yaji a kansa tana fadin,"kai kuma yaushe ka shigo garin?"Firgigi ya dube ta na'am!"Ta zura masa ido,nace yaushe kazo?Ya sauke gwauron numfashi yace,"zuwa na kenan inna".ciwon daya sami mama,ai ya same ni domin jinin mu daya......"Gafara can sakarai kai ka san wannan,da su ma sun san cewa jinin ku daya ba'a hana ka auranta ba ai sbda haka ban ga dalilin dogon tunanin da kake yi ba,don daga ita har iyayenta basu san ka na yi ba!Gara tun wuri ka halkantu ka gane cewar alhakinku ne ya kamasu!Idan ba haka ba,ina mama,ina danliti? Marasa asali da tushe ga tarin abin gori da na kunya a jikin sa?"Ya dafe goshi idanuwansa suka kara kadawa,yayi hucin zafi ya dubeta,"duk wannan maganar bata taso ba inna abinda nake so ki gane shine muddin mutuncin mama ya zube,to martabar gidan nan gaba daya ta fadi,ashe kuwa dole in damu tnda nima dan gidan nan ne,ga shi kuma mama ta dauko hanyar bada mana kasa a ido. Tace can dai zata badawa iyayenta masu kwadayi,ban sa aka ba balle ya dameni wahalar banza kake yi dama ruwa da abinci ka samu ka ci,daya fiye maka wannan sakarcin!Ya sake dafe goshi yana kada kai,me yasa innar sa baza ta gane ba?Takaici ya kara kama shi ya sunkuci jakarsa ya koma dakinsu.Haj Gaje ta shigo saboda gulma ta cigaba,sharri kala kala suka yi ta jifar uban dawaki da su.La'asar sakaliya abba ya dawo gida ya iske idanuwan umma sun jirkita jajur!Ga kumburi sun yi,ko bai tambaya ba ya tabbatar akwai abinda ke damun ta,don haka ya kasa cin abincin data kawo masa,ya zura mata ido yace kamar akwai abinda ke damunki sadiya? Tace akwai matsala alhaji amma ka ci abincin sai mu san abin yi."Fuska ki ta bayyana tashin hankali dake tare da ke ban jin abincin nan zai iya wuce min ba tare da naji damuwae ki ba.Gaya min uwargida,ni kadai gareki wanda zai saurari kukan ki."Ta dan yi murmushi karfin hali tace mama zata siyar da mutuncin mu a garin nan gara ka dauketa ka maida minna ko abj ta zauna can har zuwa lokacin bikinta."Gaban sa ya fadi yace,me tayi?Bata daina zuwa shagon yaron nan ba,yau ali da kan sa ya koro ta tana zaune bisa benci suna hira,benci fa a kofar shagon bakin titi?Kamar mama yadda muke a garin nan take zama tare da danliti?Ta goge kwalla,ina zan sa BAKIN CIKI Alh,anya kuwa mama ce ke aikata wannan abu?Hankalin alh yayi mummunan tashi ya fuskanci umma da kyau ya sanyaya murya yace,ki daina zubda mata hawaye halima ke mahaifyarta ce,sai abin ya kara wargaje mata......" "Ba yin kai na bane alhaji,hawayen ke tilasta wa kansa zubowa."Yace duk da haka ki rinka daurewa kina mata addu'a,insha Allahu gobe zan maidata minna ko ta ki ko ta so dole ta zauna.Ni abinda ban gane ba shine,tana nufin ta fasa auran Al-ameen ne?Idan wani abu yayi mata ai sai tayi bayani,ba wai ta nemi ta maida mutane sakarkaru ba!Ina take ne?"Tace tana daki a kulle tun safe daya koro ta,haushi yasa nayi mata duka har ynzu bata fito ba."Ya mike cikin fushi ya nufi dakin ya buga da karfi yana fadin,"tashi ki bude kofar nan!"Tana budewa ya cafko hannunta ya jawo ta zuwa falonsa,hakan ya sanya mama cigaba da tsiyayar hawaye,ya cillata tsakar dakin ta zube gefen ummanta.Ya zura mata ido yace,"ashe wani lokaci zai zo da zamu ce ki bar abu ki ki bari mama?Kin dai san maganara auren ki da al-ameen ko?To ynzu nake so ki gaya min manufarki ta bin danliti shagonsa.Gaya min inji tun kafin mu tara 'yan kallo!Tayi kasa da kai kukan ta ya karu.Abba ya daka mata tsawa,"kuka na tambaye ki? Ki gaya min dalilin bin sakaran yaron nan nace?Ta cigaba da share kwalla tana mutsu mutsun rashin gaskia,leben ta na makyarkyata tace,"shi....shi na ke......na..na...ke so ab...."Umma ce ra doke ta da bayan hannu tace rufe mana baki mara kunya!"Ta dubi abba dake tsaye sake da baki tace,"ka ji ko?Ni na san take-taken ta kenan!"Ya matso ya cafki kunnenta cikin tsawa yake magana."Idan barci kike yi to ki farka ki bude kunnuwanki da kyau ki saurare ni! Ni ba tsohon banza bane,in har kin ga ki auri yaron nan,tabbaci hakika ni uwaisu na mutu an binne ni cikin kabari na! Ya girgiza kunnen kamar zai tuge shi,kin ji ni! Wannan itace magana ta karshe da zanyi akan danliti kuma gobe ki shirya kayanki zan maida ki minna!"Ya shirga mata dundu tare da fadin,"tashi ki bani wuri!Ai bata iya tashi ba nan ta baje ruf da ciki sbda tsananin zafin dundun da yayi mata abnda bata saba ba,sai ta ji shi har cikin kayan cikinta sun dau zafi ba kadan ba,Ta fasa kara mai shiga zuciya tace wayyo Allah na shiga uku! Na shiga uku! Yaya ali ya mike a firgice,gabansa ya yanke ya fadi ya fito da sauri yana tsinkayar kukan mama,ya nufi sasa.Umman ke fadin,'ba ki shiga uku ba mama sai nan gaba muddin baki dauki nashihar da muke yi miki ba!"Hannu biyu yaya ali yasa ya ciccibe ta ya mikar da ita,zafin duka da tsananin BAKIN CIKI dake dankare cikin ran ta yasa ta kwakume.Yaya ali bakin gado ya zaunar da ita ya dago fuskar ta hannu biyu yake share hawayenta,yayin da nasa kwallan ke neman sauka,yace "haba mama ki yiwa kan ki fada mana!"Murya na rawa tace,me nayi masu yaya ali!Sbda Allah me nayi?"Me kika yi? ynzu a wajen ki wannan ba laifi bane?Haba mama!Ba haka kike ba,kin sauya da yawa kar dadin bakin danliti yasa hankalin ki ya gushe,laifin me al- ameen yayi miki kike so ki yi masa wannan sakayyar?A zato na koda babu Al-ameen nine mutum na farko daya kamata ki fara kawowa ran ki don na dade ina yawo da ciwon son ki mama.Ki tausaya mana me zai sa ki canza kyawawan halayen ki? Ya Girgiza kunnen kamar zai tuge shi. Kin ji ni! Wannan itace maagana ta karshe da xanyi akan Dan-liti, kuma gobe ki shirya kayan ki, zan maida ki bani wuri. Ai bata iya tashi ba, nan ta baje ruf da ciki, saboda tsanannin xafin dundun da yayi mata. Abinda bata saba ba, sai taji shi cikin kayan cikinta sun dau xafi ba kadan ba. Ta fasa kara mai shiga xuciya. Tace wayyo Allah na shiga uku! Na shiga Uku! Yaya Ali ya mike a afirgice, gabansa ya yanke ya fadi, ya fito da sauri yana tsinkayar kukan mama, ya nufi sasan. Umma ke fadin baki shiga uku ba Mama, sai nan gaba muddin baki dauki nasihar da mukeyi ba miki ba! Hannu biyu Ya Ali ya sa ya ciccibeta ya mikar da ita, xafin duka da tsananin BAKIN CIKI da ke dankare cikin ranta ya sa ta kwakume Ya Ali. Bakin gado ya xaunar da ita ya dago fuskar ta hannu biyu yake share hawayen ta, yayin da nasa kwallan ke neman sauka. Yace, haba mama kiyi wa kanki fada mna! Murya na rawa tace, me nayi musu Ya Ali? Saboda Allah me na yi? Me kikayi? Yanxu a wajenki wannan ba laifi bane? Haba mama! Ba haka kike ba, kin sauya da yawa kar dadin bakin Danliti ysa hankalinki ya gushe. Laifin me Al- ameen yayi miki, kike son ki masa wannan sakayyar? A xato na koda babu a alameen, ni ne mutum na farko daya kamata ki fara dawowa ranki, don na dade ina yawo da ciwon sonki Mama, ki tausaya mana, zai sa ki canja halayenki? Ta xuba masa kwala- kwalan idanuwanta da suka kara fitowa waje jajur! Tace, Yaya Ali ina ganin girman ka, ka kyale ni da wadannan surutan, don ba xa suyi tasiri ba. Ni nace ina so Al-ameen, yanxun kuma bana son shi Danlilti nake so. Ra'aryi nane, ba sai a kyale ni ba, ko akwai wanda zai zauna min da shi? Ya bita da kallo, ta sa aya kafin yace, ki daina tunanin wannan ra'ayin na ki mai yuwuwa ne, kin dauko katon aikin da xai rushe martabar gidan nan a idon jama'a. Idan baki son Al- ameen, ki musanya da ni Mama, zai fi miki kyau a bisa shirmen da kie sonyi. Ta runtse ido tace, yaya Ali je ka kawai! Ba ki son gaskiyya? Ta kauda kai kwalla na tsiyaya. Ya sanya murya yace, xan bar ki ki kwanta kiyi tunani sosai, cikin kan ki. Ina rokon ki girma da Allah, ki manta da kudirin da kika dauko. Bata tanka ba, haka bata dube shi ba yace, A bakin tofa ya tsaya ya kare mata kallo kafin ya sake fadin, bana so ana taba jikin ki mama, tamkar ni ake tabawa nakeji. Pls ki sauya tunaninki. Haushi ya kara kuma ta, ta juya masa baya. Ya fice yana kara waigen ta. A daren nan daga ita har Yaya Ali babu wanda ya iya cin abincin balle barci. Tunanin Mama shine xata ga yadda za'ayi a raba ta da garin nan. Cikn xuciyar ta tasha alwashin ko sun maida ta, zata dawo, dole su gaji su kyale ta da wanda take so. Dalilin da yasa ke nan, yau kwata-kwata taki bude kofar ta, kowa yayi bugu, iyayinsa har kawunninta, sai dai kalaman bakin su suka kare. Amma mama taki bude kofarta. Duk wanda ka duba ransa bace yake, musamman Abba, fuska kamar gobara ya dubi Umma yace, dauko min tabarya! Ta mike a salube ta shiga kicin ta dauko masa tabarya, ta mika masa. Alh basiru yayi caraf! Ya karba. Yace karka balle kofar nan yaya, asara biyu xa'ayi..... Yace yarinyar nan dole ta bar garin nan, ba xata xauna tana jawo min xagi ba, ana kallo na tsahon banza, bansan abinda nake yi ba! Buge min kofar nan, ko ka ba ni da kaina, in sauketa! Kowa yayi cirko-cirko. Alh. Basiru ya kai wa kofa duka da tabarya, sai ga sallamar Yaya abdul- kareem. Basu gama amswa ba, yaci gaba da tambaya, lfya? Me ya faru da kofar? Abba yace, nayi farin cikin xuwanka, don ni ma a yau nayi niyyar tafiya gunka. Me ya faru abba? Umma ya naga kamar kina kuka? Yace, mama ce.... Me ya sameta? Ya kwashe kaf halin da suke ciki ya gaya masa. Kai! Bai gaskanta kunnuwansa ba, shi yasa yace, abba ban yarda da wannan maganar ba, ya kamata asake bincikawa. Abba ya xuba masa ido jajur! Yace, wannan maganar ni Uwaisu nake gaya maka ita. Abdul kareem kasan kuwa ba za ayiwa mama kage ba, domin ni na haifeta. Saboda haka gidan ka xata xauna can har xuwa lokacin bikinta! Yace, ya xama wajibi, don ganin nan da kuka yi min xuwa nayi in tafi da ita dama. Al'ameen ya damu kwarai har yana ganin kamar wani abu ne ya faru da ita ake boye masa. Wlh jiya ya turo mahaifiyarsa da yamma wai ta zo ta bincika masa lfiyar mama, shine nace shi kwantar da hankalinsu Insha Allah da kaina xanje in dawo da ita. Wannan al'amari ya daure min kai. Yaushe mama ta canza haka? Kawu Basiru yave xancan banza takeyi, tunda ita ta kawo Al'ameen har aka sanya musu rana, bata isa tace ta canza shi ba! Wannan karya take yi. Haushi ya kara kure yayanta, ya mike ya suer tabarya ya kaiwwa kofar duka sau biyu kofar ta balle, bata a dakin. Ya nufi kofar bayi ya murda can ma garkamen yake, bai tsaya wata-wata ba, ya maka mata tabarya. Bugu daya kofar ta wangem, sai ga mama jikin bango ta fita hayyacinta saboda tsabar kuka. Al'amarin tamakar mafarki yayana yake gani. Ya xura mata ido, yace hauka kikayi mama! Me Al-ameem yayi miki? Iye? Yayi miki laifi ne da ba zaki fada ba! Sannan ki rasa wanda zaki bi, sai dan liti! Kinji abinda nace? Kin yi karya ki xuabar mana da mutunci a garin nan! Zo mu wuce, ban son jin komai daga gareki! Ta sulale kasa hannaye biyu bisa kanta, ta kara fasa kuka mai tsananin gaske. Matan gidan suka kutso kai cikin bayain suka tarairayo ta, suka fito da ita dakin. Yaya yana fadin ko mutuwa zakiyi yau, sai na tafi dake mu je can idan Al- ameen ya kira waya, in tambayehsi a gabanki, muji abinda ya hadaku! Amma yaro na sonki yana tattalinki. Iyayeynsa na ririta ki, tashi guda kice ba kiyi da shi, aikin san wannan karya kikeyi. Ina kayan ta suke umma? Hada mata si don baxan bata lokaci ba! Gaba daya suka yanyame ta da fada kowa na fadin albarkacin bakinsa, su Umma na hada mata kaya. Su Hajiya Hajjo na rarrashi ta suna bata baki tare da gyara mata jiki da fuska. Yaya Ali kuwa yana xaune gefe rayuwa tayi masa bakikkirin! Ana janta, tana togewa suka saka ta gabn motar yayanta. Ya jefa jakar ta gidan baya, daga nan yayi sallama ransa bace, ya ja motar yayi gaba da mama. Dole ne ya saurar daidai shagon Danliti, domin akan mahada shagon yake. Tsayuwar su wajen, ya jawo hankalin Danliti xuwa garesu. Ya xuba wa Mama idanuwan sa suka sha kwalli rangadau! Haka ita take kallonsa kwalla fal! Suna neman sauka. Ya daga kanka ta fito kofar shagon, irin duban da yake mata ya bayyanar da damuwarsa karara bisa fuskarsa. Tausayinsa ya lullubeta, nan da nan hawayen suka fara bulbula. Yayanta bai kula ba, kokarin sa, duk motocin da suka kawo, suka wuce shima ya samu ya haura. Yawanci duk manyan motoci ne, kamar yadda akansan babban titi ne, wanda ya mike ya tafi har lagos. Suna tsagaitawa ya cilla tasa motar ba tare da ya fahimci Danliti da mama sun ruga sun gama magana da idanuwansu ba. Kawai ji yayi ta kara gocewa da kuka mai karfi. Ya dan dubeta, ya kada kai. Yace, Al'amarin ki na bani mamaki, look kina jina? Saurare ni muyi magana ta fahimta. In tambayeki xaki bani amsa? Hankalinta sam ba awajen sa yake ba, balle ta saurare shi. Fuskar Danliti take gani, irin yadda ya shifa damuwa yana neman xubar da hawayensa, shi ya kara dagula mata lissafinta. Yace, saboda Allah zaki gaya min Al- ameen yayi miki da zaki juya masa baya? Tayi shiru, danliti na cigaba da yawo a idonta. Yace, kin kuwa san tun ranar da kika dawo garin nan. Al-ameen ya rasa nutsuwarsa? Ban iya kirga yawon wayoyinsa ba, tunaninsa kina cikin wani matsanancin hali ne aka boye masa. Kar ki saki reshe ki kama ganye Mama, domin kowa yasan Danliti lalata rayuwar ki kawai zai yi, ya kai ki ya baro ki tashar danasani. Ki ga ya min idan Al- ameen yayi miki laifi ne, ni da kaina xan masa magana in ja masa kunne. Kinji? Bai yi aune ba yaga ta balle murfin motar ta dire waje. Ta mulmula cikin ciyayi. Cikn tashin hankali ya take birki.... Allah yasa ba babu mota a bayansa, yayi fakin gefen titi, ya fito. Can ya hange ta tana kokarin tashi, amma ta kasa, kafin ya gangara wajen 'yan tsirarrun jama'ar wajen sunyi caa! Kanta. Suka ciccibota, suna sallalami tare da mamakin yadda aka yi abin ya faru. Gaba daya gwiwowin ta sunyi mugun kurjewa ta xura da gudu amma bata je ko'ina ba mutane suka cafke masa ita. BAKIN CIKI yasa ya dauke da wani mahaukacin mari daya tilasta mata xubewa kasa. Wani dan dattijo cikinsu ya kama shi. Yace, haba malam yaya haka kuma? Baka ganin kaddarar da ta sameta? Da ta mutu fa? Ku rinka kulawa da murafen mota mana don gudun irin hakan! Idanuwan sa ajuye yake magana, kyaleni da yarinyar nan baba! Da kanta ta bude murfin ta fito! Iskanci ne kawai, dama kin mutu, mu huta da wannan BAKIN CIKIN da kike son jefa mu! Saboda haka xan koma in gayawa abba kin bude mota ki diro, ni kuma ba xan tafi dake ba, ki xauna kiyi duk abinda kika ga dama agarin nan, tunda lalacewa kika xaba. Allah ya shirye ki! Ya shura takalmansa ya koma mota ya tayar yayi kwana ya koma gida ya bar Mama anan tana faman kuka, jama'ar dake wajen suna mamakin wannan abu har sun kasa fassara shi. Dan dattijon nan shi ya riko ta hankali suna tafe tana bashi labarin wai auran dole ake son yi mata. Kwarai kansa ya daure jin cewar ita 'yar gidan Uban dawaki ce, don haka ya tasa ta har gidan. Amma me? Suna xuwa kofar shagon Danliti ta xarce can tayi xamanta bisa benci. Dan liti ya fito aguje da ayuba, mamaki ya rufe ayuba, shi kuwa dan gogan munafuncin ne yasa gaba, sai yazo ya narke a gabanta. Yace, saboda me sakina, kinaso ki rasa ranki ne? Tace gara in mutu da su raba ni da kai, ya dubi Ayuba a gigice. Yace, kawo min mukullin mota ayuba! Ya shige shagon da surinsa, shi kuma ya juyo gunta ya marairaice yake fadin, aure na Allah ne sakeena, ina so ki yarda da wannan. Duk iya son da muke juna idan Allah bai nufi auran mu ba, babu yadda xamuyi. Don me xaki nemi halaka kanki? Bata bashi amsa ba. Ayuba ya mika masa mukulan. Bai jira tace wani abu ba, ya kamo hanninta taso muje asibiti asa miki magani. Dattijon nan ya bisu da kallo, duk tausayi ya rufeshi. Rashin sani kenan, ya fi dare duhu, domin shi gani yake irin haka ke jefa yara yawon banza.. BAKIN CIKI 2***3 (TRUE LIFE STORY) Wasu iyayeyn na da ra'ayin rikau, idan kuma ka bibibya kwadayi ne, wata kila wancan yafi wannan kudi ne? Sai dai kuma ai uban dawaki mutumin kwarai ne, me xai sa ya aikata haka akan yarsa? Duk da cewar dan dattijon nan talaka ne, ya doshi gidan uban dawaki, don ya bashi shawara. Fuskar Umma a sharkaf da hawaye take muryar ta har rawa takeyi, bai kamata ka baro ta can ba abdul... Yaya xanyi umma? Kona cusata cikin, sake fitowa xatayi. Mama ba zata mutu a hannu na ba, umma ta tafi inda take son xuwa, kanta tayi mawa. Fatana kwai Allah ya yaye mata abinda ke damunta. Kuyi hkr ku kyaleta anan domin ina mai tabbatar muku xata xauna can ba dawowa xatayi ba. BAKIN CIKI ya hana abba magana, sai A. Adamu ya iya fadin, gaskiya, gara ta xauna a cigaba da yi mata nasiha watakila a dace. Kuyi hkr Yaya mu dauki wannan a matsayi kaddara. Kai abdul idan ka koma Al-ameen ya kira ka kwantar masa da hankali ka... In ce masa me kawu? Gaskiyya xan gaya masa shi ma ya hkr da ita tunda ba ita kadai bace 'ya mace. Allah xai bashi wata. Ko kuwa? Abba ya dube shi, sai yanxun ya iya cewa, karka gaya masa haka abdul, da yardar Allah sai inda karfina ya kare akan mama. Indai ni na haifeta kuma ni ne xan daura mata aure Insha Allahu shine xai aureta. Kawai ka bashi hkr kayi masa wannan bayanin da naga ya maka yanxun. Ya dafe goshi yayi huci zafi kafin ya dubi Umma. Yace ki share hawayenki, umma ki yi mata addu'a Allah ya shiryata. Ni xan koma sai yadda ta kama. Basu amsa ba, ya mike kawu Basir da Adamu suka yo masa rakiya kuma suna gaya masa kalaman da suka dace ya gayawa Al- ameen. Da dan dattijon nan sukayi kicibis yana sallam cikin xaure suka amsa nan take. Yace baka shaida ni ba ko yaro? Nine wanda yaga lokacin da yarinyar gidan nan ta bude murfin mota ta fito, tayi min bayani ita 'yar mai girma Uban dawaki ce, shine nace ai mai martaba yana da saukin kai xan xo in bashi shawara game da auran dole, yayan ya dube shi da kyau. Yace hakan ta gaya maka? Yace, kwarai hakan ta fada. Yace to tayi maka karya, kawu ka na iya yi masa bayani, don na tabbata abba baxai iya fitowa ba ahalin da yake ciki. Alh. Basiru yace yanxun ina take? Yace tana can ta tsaya wani shago har sun tafi, zai kaita asibiti. Suka dubi juna, yaya yace, kunji ko? Mama ta tafi, bata jin kira saidai addu'ar Allah ya shiryata. Ni na tafi. Ya fice ya barsu nan tsaye. Alh. Basiru ya dubi tsoho yace mun gode baba, amma kayi hkr, bazaka ji komai daga gareni ba, saboda ban sami izinin yin hakan ba. Maganata gaskiyya da nake so ka gane shine karya yarinyar ke maka, tare da shegantaka irin ta yaran yanxun. Mun gode da kulawarka. Tsoho yace, shikenan nima na gode, amma don girman Allah abi a hankali asamu a sulhunta. A. Basiru yace ba komi baba mun gode. Sukayi sallama ya shige gida. Tsho ya kama gabansa cike da wasi-wasi cikin ransa. Falon Uban dawaki A. Basiru ya koma ya xayyane masa labarin da tsho yaxo da shi, da kuma shawarwarin da ya bayar. Abba bai iya cewa komai ba saboda tsabar bacin rai. Sun jima suna tausar xuciyar Abba sannan suka koma sasan su, inda matan suke xaune dirshan suna xuba gulmace gulmace. Suna zagin mama da iyayenta. Basu hanasu ba, hasalima zama sukayi suka dora xancan babu dadin ji, ita kuwa baiwar Allah mama, tana tare da Danliti cikin mota, bayan fitowarsu asibiti, yana ta faman rarrashinta, don ta daina kuka ta kwantar da hankalinta, da kyar ya samu ta nutsu ta daina xubda hawayen. Yayi fakin kofar shagon sa ya juyo ya fuskance ta. Yanxun ya xamuyi mu fuskanci juna abba ya gane cewar idan ba mu auri juna ba, komai zai iya faruwa da mu? Tace, ai ga misali nan na fara nuna masu kuma ba xan fasa ba, ina nan akan baka na. Ya marairaice yace wannan misalin bana son irinsa sakeena, don bana son na rasaki. Gaba ki daya kin fita kamanninki kin kuwa ci abinci yau? Ta kada kai, abinci ba xai iya wuce min ba Dan liti ina cikin wannan masifar meye illar ka? Da abba xai ce samm baka dace dani ba? Ya lumshe ido, ya bude kafin yace, saboda suna ganin ni bako ne, bani da kowa agarin nan..... Ta katse shi, hakan shine xai nuna daga sama ka fado? Wannan ba hujja bace Danliti, son rai ne kawai irin na iyaye ni kuwa ba xan yarda ba, sai dai muyi ta ba juna wahala. Ya ja gwauron numfashi ya sauke, ya lalubo yatsun ta ya runtse su cikin nasa, ya xuba mata ido yace, nasan ki na sona sakeena, amma ki daina damuwa ko sun hana ki xuwa wajena, sannan ki daina wasa da rayuwarki, don tana da muhimmanci aguna. Abu da gaba, ki daina zama da yunwa, ita ma zata iya illata minke. Yaunxu abinda nake so dake, ki zo muje shago in hada miki tea ki sha, sannan kije gida ko sun zage ki, kar ki ce dasu komai, don kar su sami damar dukanki. Kinji bebi na? Ta amsa da ka. Tace, yauwa mai kyau, to dan kalle ni mana, ta dube shi suka yiwa juna xuru, jim kafin ta kauda kai, tana dan murmushi, shima murmushin yayi yana mata kllon kwadayi, ya ja yatsunta xuwa bakinsa ya sumbata. (kuji dan iska). Ta kwace da sauri ta kara sadda kai. Yace, bebi na kenan, sarkin kunya. To muje ko? Zaki iya sauka ko in zo in fito dake? Ta balle murfin batare da tace wani abu ba ta fito, shima yayo waje yana kallon yadda take dingisawa har cikon shagon sa. Ya ba za mata tabarma ta zauna. Ayuba na mata sannu. Akwai wani labule jikin wata kwana a shagon, sai alokacin ta gane daki ne. Cikinsa Dan liti ya shiga ya fito da filas da kofi da cokali ya aje gabanta. Yace ga ruwan zafi, ki daga idonki, ki duba duk irin madarar da kike so, ki zaba na dauko miki. Tana murmushi tace, kai wacce iri kake sha? Yace ai bana shan madara a tea, ganye kawai nake sha. Kinsan buzaye ai? Tayi dariya tace, ba'a raba su da jiko. Yace shayi dai. Ta ciga da dariya tana fadin, to shayi, wai menene sirrin shayin nan ne? Yace xan gaya miki amma da farko wacce madara kika zaba, in dauko miki? Na kowa ki sawa cikinki abinci. Tace, bani peak ta ruwa. Ya mike ya dauko hade da katon bread ya hada mata tea mai kauri, domin duka ya juye peak din. Tana sha, suna hira ya gaya mata ire-iren shayin su. Bayan ta kammala, ya matsa gareta yace, yanxun ya kamata ki koma gida kiyi barci, ki huta kinji? Karki damu ko an hana ki xuwa nan, wane tym zamu hadu. Ke dai kiyi addu'ar fatan samun nasara. Tace, Insha Allahu zanyi. Yana murmushi ya mika baki ya sumbaci kuncinta. Ta sunkuyar da kai tana murza yatsunta. Ya zura mata ido, gaba daya jikinsa yai la'asar, sannan ya dago habarta, suka dubi juna, yace I love U! Tace me too, yace, to ki tashi kije gidan, zaki iya ko? Tace xan iya. Ta yunkura ya taimaka mata mikewa suka fito tare ta sallami Ayuba, ya dan taka mata kadan ya dawo, yana zuwa ya kwashe da dariya, ya mikawa Ayuba hannu suka tafa. Ayuba yace, baka da kyau dan iska. Yace raina kama gayya! Gaskiyya ta gurzu, na tausaya mata wlh. Shegiya akwai taushin fata, baka ji ba kamar auduga, duk ta susuta ni. Ya zura masa ido yace, tunda kuka shiga, na karance ka, shi ya gaba na yayi ta faduwa, kar ka sata labulan nan. Yace, ko na sata ba zata hani ba, nake gaya maka kuma babu abinda zai faru dani. Kawai dai ban yi niyya bane yanxu, ni nasan abinda nake hari. Yace a dai rika tuna Allah Danliti, shagalinka yayi yawa kuma ina ma kwadayin cin ubanta nakeyi, ai har uanxun duniya bata fara zaginta ba. Kaga da sauran mutuncinta. Ya bishi da kallo, bai ce komai ba, yayi tsaki ya tashi ya koma shago abinsa. Tana tafe tana dingishi, ta iso gida, kanta tsaye bata fargabar komai ta fada zaure, kicibus suka yi da Ya Ali sabe da jakar sa zai bar garin. Ko kallon sa batayi ba ta wuce, ya biyota yana kiranta bata waigo ba, balle ta amsa, ta shiga sasan su har falo yana binta. Su abba na kallon ikon Allah, domin dai Mama bata saurara ba, cikin dakinta ta shige. Ya Ali na shigowa ya gansu, ya ja birki amma ransa na son ya shiga wajen mama, yayi magana da ita, abba ya dube shi. Yace, Ali ka daina wahalar da kanka abanza, mama bata bukatar komai sai addu'a. Saboda haka ka kama hanyarka ka koma bakin aikinka. To amma, kayi hkr Abba, don girman Allah karku daketa, kamar yadda kace nayi mata addu'a kuma kuyi mata addu'ar. Yace, na yarda da kai Ali, amma ban yarda auran kowa ba, sai wanda na aminta da shi. Zan gani idan ita zata daura wa kanta aure ko mune? Yace, haka ne Abba don Allah ina rokon 2mins in ishiga in dayi mata nasiha, koda bazata saurere ni. Ya suke numfashi yace, shiga Ali, Allah ya sa taji abinda zaka gaya mata. Ya aje jaka ya wuce cikin dakin. Tana kwance niyyar barci ma takeyi, kamar yadda Danliti ya umarceta. Yana shigowa ta runtse ido ta juya baya, ya tsya kanta yace, komai zakiyi, dole in gaya miki gaskiyya, tunda kunnuwanki naji..... Fadan hakan yasa tai sauri ta toshe kunnuwan nata da yatsunta. Yace aikin banza kike yi Mama, kuma rayuwar ki na cikin hatsari, muddin baki daina jefa su abba cikin BAKIN CIKI ba. Menene anfani abinda kika aikata yanxu? Ki kashe kanki a banza da wofi, ba asarar Danliti bane, don na tabbata duk tsananin son da yake mi, ba zai hallaka kansa ya biki ba. Ki nutsu kiyi tunani. Akwai abinda magabatan mu ke hangowa kan wannan ra'ayin naki. Ni zan koma kuma ina fatan zanji canji daga gareki? Ya juya ya fice bata re da ta daga kai ta dube shi ba. Wani dogon tsaki ta raka shi da shi, wanda ya tilasta masa juyowa ya dubeta ji, sannan ya karasa ficewa. Ya dauki jakarsa ya kara yiwa su Abba sallama, ya bar gidan ciki da Al'ajabin maras misaltuwa a zuciyarsa. Bayan tafiyarsa, su Umma suka shigo gunta ta tana kudundune ta dunkule wuri daya, ko 'ina jikinta ciwo. Umma ta zauna gefen gadon shi kuma Abba n atsaye kanta, yace Mama barazanar kashe kanki ba zai sauya abinda ke cikin raina ba, idan ma baki sani ba, ki sani gara ki mutu da mutunci na ya xube a idon duniya. Saboda haka fadowar ki a mota bata girgiza ni ba balle ta cire daidai da kwayar zarra na alkawarin da na daukarwa Al- ameen da iyayensa. Mu zuba ni dake, duk wani matakin rashin kunyar da kika hau, ni na fi ki hawa matakin karshe! Ya juya ya bar dakin. Umma ta kura mata ido, hawaye suka cika idanuwanta, tace Mama zaki iya tashi ki saurare ni? Ta shiru bata motsa ba, ta sake fadin, idan har ni na haifeki kuma na isa dake, to ki tashi zaune ki fuskance ni. Ta jima kafin ta yunkura ta tashi fuskar ta sharkaf da hawaye, kamanninta sun sauya, saboda fitinar da ta daukarwa kanta a tunanin iyayenta. Umma ta zura mata ido, kafin tace, nasiha xan miki, idan kiji ki dauka wahala ta kare miki, idan kuma kince ba haka ba to rayuwa zata cigaba da yi miki kunci, domin Allah ne ya wajabta miki yi mana biyayya, muddin ba mu sa ba masa. Ban jin akwai wani dalili ko hujja da xaki gayawa ubangiji da ace kin mutu sakamon bude murfin motar da kikayi, ki fado lasa. Wannan ya nuna muraran kin kashe kanki ne da gan-gan. Ma'ana kin mutu kafira. Me zai jawo miki wannan masifar da hankalinki da komai? Ko kuwa kina so ki nuna mana kin fi karfin mu cikin dan kankanin lokcine ne? Kina nufin mu sanya miki ido ki zubar da mutuncin ki da mu a garin nan? Ban taba tunanin Mama, ke din nan zaki zama kaza kici share baki a game da irin so da Kaunar da Al-ameen da iyayensa syka nuna miki. Haka kuma ban taba mafarkin ke din nan zaki iya hango wani da namiji ya rufe miki ido har kice kin fo sonsa akan Al-ameen. Kina nufin daman can yaudara sa kike yi ba tsakani da Allah kike sonsa ba? Har yanxun mafarki nakeyi Mama, don ba gaskanya abinda yake shirin fitowa daga gareki nake ba. Ki yiwa girman Allah kir ki bari wannan magana ta zama gaskiyya, ba ke kadai za'a zaga ba har damu iyayenki. Na mu ma zai fi yawa saboda mune muka isa dake. Yanxun abinda na rokonki shine, ki share hawayen ki ki gaya min, laifin me Al- ameen yayi miki kike son ki katse masa rayuwa? Gaya min daga ni sai ke ce a dakin nan kuma share hwayenki, muddin shi ne baida gaskiyya. Ta shre hawayneta wasu suka xubo mata, kalaman ummanta masu taushi ne dashiga xuciya, amma kash Danliti ya riga ya gama da ruhinta. Allah ya bashi sa'a ya kamata ahannu, idanuwanta ba sa ganin kowa sai shi, kunnuwanta ba sa sauraron kowa face kalaman yaudarsa da izgilanci. Dalilin da yasa kenan kalma daya bata tasiri a hrt dinta, a duk tsahon jawabin da Umma tayi, da ka dubi fuskarta, zaka gane bata yarda bane kawai. Murya cunkushe tace, ni babu abinda Al'ameen yayi min Umma, kawai raina yafi kwanciya da Danliti kuma shi nake so na aura. Haushi kamar ya kashe Umma ta mike tsaye. Tace, to baki isa ba! Mu dan Liti baiyi mana ba, idan kina da wasu iyayen da za su dauta miki auran to bismillah! Ya ci gaba da fadin, ai kuwa bata isa ba, ni zanje in dauko ta kuma dole ta auri wannan yaron tunda itace tace tana so tun farko! Yace, Yaya duk yadda kake tunanin al'amarin nan ya wuce nan, amma ka gwada ka gani, kilan kai tafi jin tsoronka, sai dai kafin nan xance Al-ameen din ya kira ka, kuyi magana, don ni gaskiyya ban san me xance masa ba. Yace ba wani abu xan rarrasheshi, ya kwantar da hankalinsa, kaima yaunxun nan ka kama hanya kaje ka yiwa Hajiyansa bayani, kace kar su damu ba wata matsala bace babba. Ya numfasa ya amsa da to kawai. Lallai babban yaya yana dau kara abin wasa ne. Suna aje waya Aunty amina ta nufo shi, me ya faru ne wai? Nan take ya labarta mata abinda ke faruwa. Tun kafin ya kare idanunwanta ke waje, wai kana nufin Mama ta fasa auran Dr? Yace gara da kikace wai, don bata ida ba. Ni xan je na dauko ta, cikin gidan nan zata zauna sai ya dawo. Ta kada kai cikin damuwa, tace amma mama ta ban mamaki, me Dr? Yayi mata? Babu abinda yayi mata, wani ta hango saboda rashin hankali irin naku na mata da butulci! Tace wlh na yadda sai dai matsalar banyi zaton haka ba daga wajen Mama ba ganin yadda take nunwa Dr. So mai tsanani, duk yaudara ce, kai gani kuma a zahiri ai ta nuna. Amma ai tayi kuskure ni zan gyara mata zama, don bata isa ta zubda mana mutunci ba! Tace gaskiyya ne. Allah yasa ta gane. Ya wuce tebur don cin abinci. Shi kuwa abdulkareem, bai sami zaman cin abincin ba gidansu Al-ameen ya nufa ba tare daya san wane irin bayani xai iya yi masu ba, don hankalinsu ya kwanta. A haka ya isa gidan. Nan da nan aka tarbe shi da girmamawa da abubuwan kusa da baka, marafa baya gari, saboda haka mami ce ke tare da shi, ina fatan dai kaci abinci? Yayi dan yake yace, Alhmdlh Hajiya, nagode. Tace amma dai ko Juice kasha ko? Haba, kamar wani bako? Yanata murmushin rashin nayi, yana kallo ta xuba masa ta mika masa, Ungo sha don Allah. Kuma maimakon kazo min da surukartwa, yau in riketa cikin gidan nan sai tayi min sati. Ya aje kofin lemo ya kara gyara zama, Yace Hajiya, hkr na zo in baki, domin ban sami dawowa da Mama ba,... Saboda me? Kodai maganar Al-ameen gaskiyya ce, sakeena na cikin wani hali? Bata da lfya ko? Ya karkada kai.... Tace karka bote min komai Baban ameer, duk tsananin da sakeena ke ciki, nasan yadda xan rarrashi Al-ameen don hankalinsa ya kwanta. Gaya min me ya faru da ita? Jikinsa ya kara sanyi, cikin taushin murya, yace Matsala ce babba Hajiya, wacce ni kaina ban da ita ba, sai da naje daxun. Ashe tun komawar ta gida, wani yaro ya hure mata kunne, shi ya hana ta dawowa. Su abba na ta fama da ita kuma suna kan kokarin su don ganin raba ta da shi. Na yi nayi ta biyo ni, taki hajiya, shine Abba yace in zo in baku hkr kafin yazo. Insha Allahu za'ayi maganin abin. Gaba daya hankulan mu atashe suke, al'amarin yana daure mana kai. Idanuwanta xuru akansa, hannunta bisa kunci. Tace, wyyo Allah! Wayyo Allah! Me xanji yau mai kama da almara? Ta goce da sallalami, yanxun baban ameera kana nufin sakeena tace amanar Al-ameen kenan? Idanuwanta suka cika da kwalla, yayi da yaya Abdul ya kara kasa da kansa. Yace, kiyi hkr Hajiya, a gaskiyya ban san yadda xan fassara wannan al'amarin ba, amma abinda nake so ki gane Abba ba xao rungume hannayensa ya sanya mata ido ba. Haka muma 'yan uwanta. Muddin kuwa tana son albarka dole tabi umarnin mahaifinta. Shi yasa ya fara turo ni kafin ya zo da kansa ya ga alhaji. Haka kuma ku rarrashi Al-ameen ya kwnatar da hankalinsa komai zai daidaita cikin hukuncin Allah da yardarsa. Ta cire tagumi. Tace, a gaskiyya ba zan iya fuskantar Al-ameen da wannan maganar ba, in katsa masa karatu. Na san ya damu kwarai ya san halin da sakeena ke ciki, amma ba xan iya gaya masa wannan mummunan labarin ba, kuma na rokr ku don Allah ku kyaleshi kawai. Gara abar shi cikin duhun da agaya masa sakeena ta sauke alkawarin da ta daukara masa. Na tabbata komai nasa zai tsaya jarabawar su gab take da xuwa. Ni da kaina xan iya xuwa na roketa, ta tausaya wa Al-ameen karta kashe masa zuciya. Kwalla masu zafi suka xubo bisa kuncinta bata re da saninta ba. Hankalin Abdul ya kara tashi, BAKIN CIKI ya dada lulluba shi. Don girman Allah Hajia karki xubda hawayenki akan maganar nan. Da yardar Allah komai zai gyaru. Kamar yadda kika ce kar agaya masa ba, ba za'a gaya masa ba. Gara ace masa bata da lfiya ne, xuwa lokacin da xa'a shawo kanta. Ta goge kwallah, tace ina ganin hakan zai fi sauki iyaka dai yayi tunanin jikinta, mu kuma nan mu rinka gaya masa tana samun sauki. Yace, to shkienan, Allah yasa mudace. Don girman Allah hajiya kuyi hkr, sakarci ne kawai irin na yara. Tace, ya za muyi baban ameer? Dole mu rungumi kaddara. Ya mike babu isasshen laka a jikinsa, yayi mata sallama ya fice, batare da hajiyar ta kara ko motsi ba. Wucewar awa daya da rabi tana zaune xuciyarta cike da sake-sake iri-iri. Ji take kamar a mafarki abdul yaxo mata da wannan mummunan labari, wanda take ganin zai iya salwantar fa rayuwar dant tilon danta da takeji da shi. Duk fadin duniyar nan bata hada shi da kowa. Yaya marafa zaiji, idan wannan labari yake kunnen sa? Tabbas xai fita shga damuwa, domin yafi ta sanya Al-ameen ransa, ko alama baya son yaga ya nemi abu. Waya ta dau ruri a falon, ita ta katse tunaninta tare da haddasa mata faduwar gaba mai tsanani. Ta mika hannu ta dauka ba tare da tayi hasashen mai kiran ba. Tayi sallama cikin raunin murya. A raunane taji muryar Al- ameen ya amsa mata kafin yaci gaba da cewa, mami na, ashe sakeen ba ta da lfiya shine aka boye min? Ni ban ma yarda bata da lfiya bane Mami, kawai ku gaya min idan mutuwa tayi, xan hana Allah ikonsa ne? Ai nasan yafi ni sonta, kuma ta shi ce ban isa in hana shi amsat kayansa ba.... Tace saurareni Al-ameen, kar hankalinka ya gushe.idan baka yarda ba da maganar yayun sakeena ba, ai ni mahaifiyar kace, ba xan rufe maka komai ba, ka yarda ko baka yarda ba? Murya na rawa ya amsa, Na yarda mami, tace to sakeena bata mutu ba, rashin lfya ce ta sameta aka maida ta gida. Bana so ka damu da yawa, domin sosai take samun sauki, gobe ma xan sake xuwa in dubo ta, kaji? Ya numfasa yace, amma Mami me yasa za'a ajiyeta gida? Akaita asibiti mana, ko can xariya xanyi magana da abokina, na tabbata xai kula da ita tamkar ni. Pls mamy ki basu shawara idan kinje goben. Tace ba ciwon asibiti bane, shedanu ne suka tabata, kuma su iyayen nata suna tsye neman magani. Kai ma kasan xa su xauna ba. Ni dai rokona gareka shine ka nutsu ka kwantar da hankalinka, ka fuskanci jarabawar ki mai xuwa. Ka zama mai imani da Allah, shi xai sa ya karbi addu'ar ka idan kayi mata. Ka jini? Ya goge kwalla, yace naji mami don Allah idan kinje ki dafa kanta ki karanta mata ayatul kursiyu, falaki da nasi. Idan har gane ki ko da baxa ta iya miki magana ba, ki gaya mata Al- ameen dinta na gasheta, kuma xan ciga ba da yi mata addu'a har xuwa lokacin da xanji muryar ta a waya. Idanunwanta suka tara kwalla. Tace, Insha Allahu xan gaya mata, tare da dukkan abinda kace, muddin kayi min alkawarin zaka kwantar da hankalinka. Da sauri ya amsa, Allah nai miki alkawari mami, kinsan bani da wani buri daya wuce in faranta maku rai. Tace, Allah yasa dalilin alkawarin da kayi min Ubangiji ya yayewa sakeena abinda ya sameta! Yace, ameen Mami na! Dadina bai dawo ba ko? Bai dawo ba sai zuwa jibi. Yace Allah ya dawo da shi lfya. Ta amsa da ameen. Yace ki gayawa su iya su taya mu da addu'a, Allah ya taimake mu. Tace, xan gaya musu. Al-ameen, karka damu kaji? Murya raunane ya amsa, to mami sai kinsake jina. Bata iya kara komai ba ta aje wayar, domin muryarsa kawai ta isa jefa mutun cikin damuwa. Taci gaba da xama dauke da tagumi tunani na cin xuciyarta fiye da tunanin mai kallonta. Haka al-amarin yake wajen Al-ameen, domin dai rayuwa tayi masa tsauri kuma hasashen rashin lfiyar Mam yafi koma zama cikin ransa. Ba don yayi wa mamy alkawari ba, da babu makwa zai iya baro abinda yakeyi ya dawo ya ganewa idon sa Mama, tana cikin mummunan hali. Kafin kace kwabo, kowa ya fahimci samun sauyin sa, domin ya yamutse ya wayi garim duk kuzarin da nutsuwar sa basu jikinsa. Yana zaune addu'a yana tafe addu'a, haka acikin aji, hankalinsa yafi rinjayea ga addu'o'in da yakewa mama cikin ransa. 12pm washegari lokacin ne motar Mami ke fakin kofar gidan Uban dawaki. Yayin da mama ke kwance rankas ciwon jiki, sakamakon fadowar da tayi daga mota. Can da nan bata iya motsawa, Baraka ke tare da ita tana zazzaga mata nasihohi, duk da ta san bata sauraron ta, sai dai ya zama wajibi gareta, ta kara gaya mata gaskiyya. Mami tayo sallama falon ta shigo, gaban Umma ya yanke ya fadi. Ta amsa tana fitowa daga dakinta. Yake baki kawai takeyi, amma zuciyarta ta shake take da takaici tare da BAKIN CIKI mai tarin yawa. Ga wata kunya da ta yo wa idanuwanta dirar mikiya, mai alaka da ciwon dundumi. Sannu da xuwa Hajiya! Ta amsa mata da fara'ar karfin hali. Ta nuna mata kujera ta xauna, tana kara yi mata sannu da xuwa. Sannan ta debo mata abubuwan sanyi masu ruwa. Ruwan ta fara xuba mata, ta mika mata ta sha. Suka gaisa cikin girmama juna. Ta kara gyara xama, tace, sai kika ganni da rana tsaka ko? Fuska kunshe da tashin hankali. Tace ke dai bari, nasan kin sami sako maras dadin ji. Ta kada kai dauke da damuwa. Tace naji sakon da ya hani barci jiya, wanda ya sanya ni rama kafin safiya. Ina jajantawa shi kansa Al-ameen da ya sallama rayuwarsa kaf kan sakeena. Nayi kuka da wadannan idanuwan nawa, don na tabbatar da amsata ba alkhairi bace a gareni, domin komai zai iya faruwa ga tilon da na, farin ciki na kuma sanyi idona. Shi ya sa nace xama bai ganni ba, tilas inxo in rarrashi sakeena, ta tausaya min kar in rasa Al-ameen. Wadannan kalami sosai suka sanya hawayen Umma suka tsinke nan take, ta rasa me zata ce wa Mami ta sanyaya mata rai? Dole tayi kuma domin dai bata da kwakkwarar mafada, mama na nan akan bakanta babu sauyi. Da kunnunwata ta, taji lokacin da take gaywa Baraka tabbas zata iya kashe kanta, saboda Danliti. Mami ta cigaba da fadin ki daina kuka Hajiya, Baban ameer ya gaya min tashin hankalin da kuke ciki, kukan bashi da alfanu....... HAUSA BAKIN CIKI 2***4(TRUE LIFE STORY) umma ta hare kwalla ta katse ta Tabbas mama bata da lafia ciwon daya kamata mai tsanani ne maganin Allah, dole kuwa in yi kuka , don mama ta dasa mana BAKIN CIKIN da ban taba tunani ko mafarkin irinsa ba daga ni har Abban ta mu na cikin rudu tare da mamakin yadda wannan alamari ya kasanze haka, hakuri zakuyi hajia sannan ku taya mu addua mama kam ko ta so ko taki doke ta auri Alamin, tunda zabin ta ne na farko bamu muka cusa mata shi ba. Hasali ma bamu san lokacin da suka hadu ba. tsabat rashin kunya ce irin t yayan zamani da rashin sanin mutuncin mutane. saboda. haja hajia karki damu kuma dabarar da kikayi wa alamin tayi daidai sai dai akwai sauran rina akaba domin fadar kalmar ciwon ma ba zai bar shi yayi sukuni ba. Tace zaifi sauki akan a gaya masa gaskiar magana ni na dauki dawainiyar kwantar masa da hankali kullun ya kira waya. Tace to shikenan Allah yasa mu dace ta ce ina sakinar take mu gaisa Ta mike tana fadin Taso muje in kaiki kwance ma take bata iya tashi. Ah me ya faru? ina fatan ba dukanta kukayi ba, ta ce Baban Amira bai gaya maki bude mota tayi ta diro kasa ba? ido waje ta dafe kirji ta diro daga mota? tace ya wuce wai! zo muje ki ganta ta tashi dauke da mamakin tana fadin naga abinda ya ishe ni ni yasu, sakina da gaske take bata son Alamin. suka cusa kai dakin, baraka dake zaune bakin gado ta mike tana gaishe su. umma ta nuna wa mami wurin zama a bakin gadon tace zauyna hajia kinga idanuwan maras kunya ta juya kan mama taci gaba ga hajia nan tazo da kanta inkinga dama ki bude ido ta kudundune kai cikin pilli mami ta dube su tace ku bamu wuri hajia ita baraka suka bar dakin mami ta karasa matsowa tasa hannu ta birkito ta kuka taga tanayi tasa hannu biyu ta tallafo kuncin ta ta sanyaya murya tace sakina dan dubeni kinji? ta dago idanuwa jajur ta dube ta hawaye suka wuce bisa kuncinta. mami ta kara goge su . ta ce na san ba'a siyan so mama da yau nayi cinikin sa ko nawa ne na siya wa alamin, koda zai kasance zani daya zai rage min a fadin duniya. amma kash hakan ba zai taba yuwuwa ba, sai nayi imanin ko dan yaya ne kin san mahimamcin rike alqawari me yasa kika dauki alqawarin da ba zaki iya cikawa ba? me yasa kika yaudari shi kika bari tsananin son ki ya zauna a zuciyarsa? kina so ki kashe shi ne sakina? ki tausaya min ana gaya masa sakon nan zuciyar sa zata iya bugawa ya mutu mama. shi kenan na rasa shi kuma ban da wani alamin na sonki mama sai dai ayi zancen dan adam ssaboda haka ki gaya mani abubuwan da yake miki wadanda baki so har suka sanya ki tunanin fasa aurensa. wallahi nayi maki alqawarin zan masa fada tare da lallashi in kuma. gargade shi kinji? gaya man matsalarki da alamin. hawaye suka ci gaba da ambaliya bisa fuskar mama domin ko sunan alamin bata son ana ambatowa tsawon lokaci bata tanka ba sai kwarara ruwan idonta kamar zai kare mami ta sake fadin da alama alamin dai bai maki komai ba sakina tsuntsun son sa ne kawai ya tashi daga kansa ya koma wa wani ko? ta kara aje ido kasa mami tai wawan ajiyar zuciya idanuwanta suka kawo kwalla baki man halacci ba sakina a iya tunani na mutuwa ce kawai zata raba ki da alamin shi yasa gaba dayan mu muka dora burin mu a kanki. bamu da wami buri face Allah ya nuna mana ranar da zki zama mata danmu sai gashi dare daya kin juya mana baya. A tunani ki kinyi daidai? baki gudun kar amana ta ci ki sakina? kiyi tinani cikin natsuwa duk wanda ya ha'inci wani Allah ba zai kyale shi ba. zan barki kiyi tunani kan magana ta. idan kin canza ra'ayi ki koma minna zuwa gobe Alamin yaji ki hankalinsa ya kwanta kinji? yace in gaishe ki kuma yace inyi maki addu'a. Ta taimaka mata ta kwanta a hankali idanuwanta rufe suke yayin da mami ta dafa kanta tayi mata addu'oi da alamin yace tayi sannan ta kirata ta bude ido. nizan koma sai najiki a minna karki bari shaidan ya rinjayeki ki bar mai tsananin sonki cikin kunan zuciya nakasa zaiyi kinji? ta lumshe idon a natse mami ta wuce ta bar dakin umma ta shiga tare da sallama ta nemi wuri ta zauna yayin da baraka ta fice. ta basu wuri ta saurareki? tace to! bata dai tanka ba sai kuka da zan fito. ma nayi mata addua' kallo na ta dinga yi. da alamun za'a dace tace kwarai da gaske bari in lallaba hajia zan shiga wajen gwaggo sannan mu wuce . to a gaishe ta da kyau Allah ya kiyaye hanya Suka wuce suna fadin"Amin"har kofar gida tayi mata rakiya,motarsu ta daga ita kuma ta dawo gida dakin mama a koma suka taru da baraka suka ci gaba da yi mata nasihohi tana kudundune bata tanka ba,balle su gane me take nufi,Awa guda bayan tafiya mami yaya. Abdul- kadeer ya iso gidan daidai lokacin kuwa Abba ya dawo gidan,yayan tare yake da dakarun sojoji guda uku,duk suka fito,suka toge suna sarawa abba,sannan suka gaishe shi tare da yayan suka rankayo yana ruwan masifa, maganar banza yarinyar nan take yi,mu makace ta kawo shi ko mu muka hadasu wannan ai iskanci ne yanzun nan zan wuce da ita shiya na dauko kuratan nan su yi min gadinta a mota na ga ta inda zata fito,Nonsense kawai" Abba yace kayi daidai domin ni mama ta ginsheni ko ganinta bana sonyi cikin gidan nan,saboda "BAKIN CIKI",abu kamar al'mara yana so ya zama gaske yarinya ta bamu kunya ta zubar mana da mutunci basu ma san sun shigo falon ba sai da umma tace maraba da babban yaya yace sannu umma bamuyi sallama ba ko?raina bace yake ina mama?tana daki ina fatan tafiya kazo yi da ita sosai kuwa umma akwai kurata uku nazo dasu wadanda zasu gyara mata zama muddin tayi yunkurin bata mana lokaci tace yayi kyau wallhi yanzu ma hajiyar al-amin ta bar gidan nan bakaga uwar kunyar da ta lullubeniba na rasa inda zansa kaina Abba yace tazo kikace"tana ma cikin garin nan bata wuce ba"Abba ya nemi waje ya zauna ya kama kai,shi kuwa yaya babba dakin ya nufa kina jina baza ki fito ba"umma tace da wace kafar zata fito bayan ta kusan kashe kanta,yace kadan ta gani amma yau sai kin bar garin nan ko za ki mutu!Useless girl!kina nufin ki zubar mana da mutunci ko,baki. Kai wannan matsayinba,I swear,kin ji na rantse"yasa hannu ya fisgo ta da karfin sa yana fadin"stand up my friend"ta tsandara kara mai garfin gaske saboda gaba gabobain ta suka amsa suka kaiwa kwakwalwar ta zuwa falon dole gabobin suka loma aiki ashe dama wuri suka samu. Ya dankwafar da ita bisa kujera tace wayyo na shiga uku yace"No lokacin bai zoba tukuna sai kin ci gaba da bijire wasu umma I'am telling you! yau abuja zamu wuce ki zauna can, sai lazy doktan ki ya dawo ai ke ki ka zabe shi tun farko so now you have no reason ki ce kin fasa bayan kun kusa aure ya dubi umma yaci gaba karki ji tausayinta ta umma ki fidda ta a ranki har sai tayi biyayya a gareku, Ta kada kai tace tuni mama ta fice min a rai balle tausayinta ko alama babashi cikin raina ka tafi da ita duk abinda ya dace kuyi mata don ta gane kuskuranta yace wannan dole ne Abba bari mu wuce umma ta fara magana bari in hado mata kaya yayin da abba da babban yaya kamar zasu cinye mama a falo kuka take tamkar za a zare mata rayuwa umma ta fito da jakar kayan ta wurga mata gyale bisa jiki,yaya soja ya mike tashi karki bata min lokaci taki mikewa yasa hannu ya maketa sannan ya cafko. ta yana fadin zan iya karya ki u know dat! gara ki shiga hankalinki bai sake taba har kofar gida ita kuwa umma cikin sasa ta shiga ta gayo masu za a wuce da mama don haka suka yo waje ganin yadda za a yi saboda suji dadin karaars wa. A gaban su ya cilla wa kuratan daya zo da su ya ce kusa min ita a mota! kan kace kwabo mama na cikin mota, suka sanya ta tsakiya yayanta na gaba sanda ya jefa jakarta a but yaya ya juya da sauri ya zauna matsayin driver babu bata lokaci ya murza mukulli mota ta tashi ya bar wajen, idanuwan baraka suka cika da kwalla nan da nan ta fasa kuka ta koma cikin gida da gudu. sauran matan na ta fadin Allah ya kiyaye hanya ubangiji yasa a dace. umma ta juya ta shiga gida su suka biyo bayanta . ganin hankalin umma yayi mummunan tashi yasa hajia gaje ta janye hajia hajo cikin gida ta mika hannu suka tafa sannan ta tallafe haba ido waje tace Ashe abin har ya girman haka? wanan sojoji kamar an zo kama gagararren barawo? ta ce ai kamar hakan ne tunda ta gagari iyayenta. zamuga ikon Allah yarinya na neman tayi wa iyayenta bakin cikin daula, sun ga samu zasu ga rashi ai kinga haj halima kamar ranta zai fita sai kace dole suka sake tafawa haj hajo tace Hakki ne nake gaya miki kadan ma suka gani badai danliti ta jajibo masu ba? Allah dai ya kiyaye lalacewa! ta tabe baki Nayaushe kuma? wai ance wa kuturu Allah ya laance ka! shagonsa fa take zuwa tsinancewa ai ba sai an tambaya ba! hajia hajo tace Allah shi kyauta haj gaje ta amsa na gaba domin dai wannan ya riga ya faru anyi abin kunya maga yadda za ayi! sun jima suna yada labaran banza da karairayi kai duniya ina zaki da mu? rayuwa kenan uban dawaki da umma suna kallon ikon Allah suna fama da BAKIN CIKI sai fatan Allah ya musanya masu alkhairi Mama kuwa tun isowarsu Abuja take kudundune cikin daki duk hargagin yaya soja baisa ta dauki lomar abinci tasa wa bakinta ba,al'amari ya daure wa anti amina kai ta zauna ta siga yayyafa mata nasihohi da rarrashi ko Allah yasa ta gane amma ina Alla bai nufa ba tukuna shi kuwa soja babu abinda ya dame shi cewa yayi zai fi kyau da zata bari yunwa ta kasheta a yau hakan kuma shi zai tabbatar masa ta cika mai kunnen kashi,yasa kai ya bar gidan amma kuratan sojojinsa na nan tsare da gidan bayan masu gadi mutun biyu ke nan yanzu sun zama su biyar,kafin yamma mama taci kukan daya fidda ta daga hayyacinta bama ta jin tarin yunwar da ke cikin ta saboda tsananin tashin hankalin da take ciki domin ita kanta ta san ta shigo kurkuku zai yi wuya ta kara ganin dan liti sai dai tunanin ta bai yanke ba duk tsananin da zata shiga baza ta taba auren wani ba dan liti ba. BAKIN CIKI 2***5(TRUE LIFE STORY) Saboda haka taci gaba da zama cikin kunci da yunwa har bayan sallar isha'I yayanta ya shigo gida kamar shi alamin ke kira wayar sa ta hau bugawa falon kai tsaye kan wayar ya nufa ya dauka yayain da malami ya sheko da gudu don yi masa oyoyo.anti Amina ta biyo bayansa daga jin muryar al'ameen kasa yana cikin farin ciki da doki cike da zuciyarsa ina yini yaya,yace lazy dokta ya karatu?"Yana yar dariya ya amsa Alhamdulillahi ai na kira can minna don in tambayi jikin mutunniyar sai aka ce min ta sami sauki harma ka taho da ita, yace haka ne amma kasan yana yin rashin lafiyar sai a hankali cikin dan kankanin lokaci sai ta birkice bari in turo maka ita,koda kaji sauyi daga gare ta kar ka damu haka yanayinta ya sauya,jikin sa yayi mugun sanyi duk a lokaci guda gabansa ya ci gaba da faduwa murya dishe yace to yaya Allah dai ya bata lfy,ya amsa da amin ya aje kan wayar gefe ya amsa gaisuwar iyalinsa sannan ya haye sama ya fada dakin mama yana shiga ta kara kudundinewa cikin bargo yasa hannu ya kwashe bargon ya watsar gefr yace tashi zaune sai ga antin ta shigo ta matsa bisa shimfidar ta birkito ta tana fadin yi mata a hankali ke mama tashi kinji! Ta ciccibo ta ta tashi zaune kamar wacce ta shekara tana ciwo saboda tsabar fita hayyacin da tayi Tausayi ya lullube antyn a hankali tace kinaji na? Ga alamin cen ya kira waya don Allah ki fidda mu kunya ki tashi ki je ki saurare shi badon mu ba sai don girman Alkawarin da kika daukar masa kafin ya tafi tashi kije kudinsa na bin iska kinji? Tamkar antyn na magana da dutse don ko motsi batayi ba sai idanuwa ta ke ambaliyar ruwan hawaye . Haushi da takaici suka rufe yayanta ya daka mata tsawa mai tsanani sai ta zabura bazaki tashi ba? Alamarin ya kara kure su cikin mamaki sukaji wannan kalmar ta fito bakinta Nifa yaya ba zanyi magana da kowa ba Gaba daya suka ware ido baki sake sai dai shi soja baya tsayawa yana kallon raini don haka ya cira hannu ya tsnke ta da wawan marin da yayi sanadiyyar daukewar numfashinta karkaf,ta zube sumammiya ya nuna cikin zafi yace ni zakiyi wa rashin kunya ba na wasa da ke ni zan iya karya ki wallhy anti amina da tuni take kwasar salati tace ai maganar karyawa ta kare tafa suma yallabai yanzu me za a cewa Al'ameen din Yace ta mutu ni tayiwa rashin kunya bata isa ba wallahi!Mtsw"ya ja dogon tsaki ya bar dakin falon ya sauka ya dauki kan wayar ya kanga wa kunnensa hello al'ameen naji na ya amsa ina kinka yaya yace kayi hakuri da mama al'ameen ya katse shi me ya faru yaya ina take yace ta suma al'ameen kayi hakuri da ita domin mama ta riga ta sami matsala....". Ya sauke salati ya katse shi yaya bazan iya hakura da sakeena ba kowane irin hali ta shi ina son ta haka koda kuwa ciwon hauka ne ya kamata,Roko na gare ku shine ku taimake ni ku kai ta asibiti don Allah ko nawane zan kashe yaya please ku taimake ni ya goge hawayen dake zuba bisa kuncinsa yayin da jikin yaya soja yayi mugun la a sar cikin taushin murya yace kar ka damu al'ameen zamu kaita kar ka damu kaji sai da safe. Ko kamin ya gama amsawa ya kife kan wayar al'ameen sai da ya lalubi wuri don baya gani yadda ya kamata sauran abinda ke zuciyar sa kuwa biro na ba zai iya rubuce shi ba domin al'amarin gagarumi ne maras misaltuwa sai dai muce Allah ka kiyashemu sharrin masu sharri amin summa amin Anti amina keta faman neman ran mama shi kuwa yayanta bai sake komawa ta kanta ba dakin sa ya shige don yin abubuwan da yake ganin suna da muhimmanci a gare shi ita kuwa mama zafin. Mari da tsananin yunwa tare da tarin damuwa su suka taru suka jefa ta cikin doguwar suma awa daya da rabi ta kwashe babu motsin rai sannan ta dawo duniya,ta fasa kuka tana fadin wayyo Allah na zan mutu wayyo Allah! wayyo!" Nan da nan hawaye suka tsunkewa anti amina saboda tausayin da ya kamata murya na rawa ta tarairayo ta tana fadin mama ki tausaya wa kanki wannan mugun halin da kika jefa kanki kin kuwa ga yadda kamannin ki suka sauya wane irin masifar so ne wannan na bala'I. Akan da namiji kike wahalar da kanki a banza a wofi ki mutu ya nemi wata ya aura,wannan sakarci ne mama kiyi wa kanki fada tun dare bai miki ba sannan ki sani idan kika ci amanar al'ameen Allah ba zai kyale ki ba,ta fizge jikin ta ta sake faduwa bisa shimfida ta kara fasa kuka, malami ya budo kofa ya shigo cikin sanyin jiki ya karasa gun su yace mami uncle al'ameen ya bugo waya, kafin anti amina tace wani abu tuni mama tayi wuf ta tashi zaune cikin sababi take fadin ba za a zo ba kaje ka gaya masa bazan dauki wayar ba dole ne sai na aure shi nace. Ba zan aure shi ba duk ku taru ku kashe ni kowa ya huta ta sake komawa ta dase ciki anti amina da malami suka saki baki suna kallon ikon Allah. Jimawa kadan ta dube shi tace,Mu je falon." suka fice jiki babu kwari,musamman Malami da sababin ya bashi tsoro ba kadan ba.Anti Amina ta dauki wayar tayi sallama,suka gaisa kafin yace, Ya jikin sakeenar? Ta farfado kuwa? 'Ta farfado Al- Ameen, har ta samu barci. Ya sauke numfashi,'Allah ya kara mata lfy. To amin.yace Anti,don Allah ki taimaka ki tuna wa yaya tafiya asibitin.Ni ina ganin babu abinda zai gagari asibiti koda matsalar junnu din ne, akwai ta su irin gudumawar da zasu iya badawa. Please Anti a kai ta asibitin a gwada." Idanuwan ta suka kara tara kwalla,jin yadda muryar sa ke rawa,ta tabbata hawaye ne ke zuba bisa kuncin sa.Ta numfasa tace "karka damu Al-Ameen,duk wani iya kokari ana yinsa.inshaAllahu Allah zai dube mu ya yaye mata wannan lalura.ka kwantar da hankalinka kaji? Ya amsa,Hankalina ba zai kwanta ba Anti,har sai naji muryar sakeena da bakinta ta gaya min tabbacin samun saukin.Ban san halin da sakeena ke ciki ba Anti,kowa cewa yake tana samun sauki,amma ni ban ji alamun ba a jiki na.zuciya ta tana min sake-sake iri-iri akan sakeena kuma tana nuna min ita acikin mummunan hali.jin muryar ta ne kadai zata warware min rudun dana fada.....Anti Amina ta amshe,komai yayi zafi mgnin sa Allah Dokta.ka tsaya wa addu'a kawai ita ce kadai zata taimake mu.shi kenan Anti,ngd.Idan Allah ya kaimu gobe zan sake kira ko na dace jin muryar ta.Tace To Allah ya yasa a dace.ameen Sukayi sallama ta aje waya ta koma bisa kujera ta kama kai hannu biyu ta matse kwallan ta tace wannan masifa Allah ka yaye mana,muryar mai gidan taji yana fadin kema zai zauna kina bata lokacinki yau mu ma bazamu ci abinci ba ke nan Ta share fuska ta dube shi yallabai ba ka ki kalaman dokta bane su suka kara dafani wallahi ya ya zamuyi da yarinyar nan ne yace oho!ni kizo ki ban abinci ina jin yunwa ta mike ta nufi kicin shi kuma ya wuce ebur yana kiran malami ya sauko da gudu yana amsawa gani dadi kaima yau baza kaci abinci. Bane yace ai na ci dadi to koma daki kayi barci sai da safe,ya juya ya haye saman yayin da anti amina ta fito da jerin kayan abinci bisa tire ta jera bisa tebur sannan ta zuba masa taja kujera ita ma ta zauna yana ci tana maida masa kalaman al'ameen sai da ta kare ya kurbi ruwa ya dube ta, Yace ni kinga duk wannan shiriritar ina yi ne kawai saboda hajiyar sa ta roki a rufe masa amma ni ban ga dalilin yawo da hankali ba yanzu ina fa'idar yin shirun tunda hankalin sa da ake so ya kwanta bai kwanta ba? mama ko zata mutu shi zata aura to me ne ne abin jin tsoron gaya masa matsalar da ake ciki banda shiriritarku ta mata,ta ce ai ba haka bane yallabai kaga kuma shi kansa marafa ya goyi bayan hakan"shi ke nan sai ki yi ta rarrashinta kafin gobe idan ta amince yin maga da shi shi ke nan idan kuma taki kya nemi wata karyar ki shirya masa kinga sharo karya ya same mu ke nan sai abinda Allah yayi ina amfanin sa Ta numfasa tace al'amarin hakuri zamuyi tayi rokona gare ka don Allah ka daina dukanta wallahi taurin kai zai kara mata ido waje yake magana muddin tayi min rashin kunya zan tabbatar da na hukunta ta yadda ya kamata don ni ba sa'an ta bane,you know that so ba zan dauki iskanci ba kina iya hawa sama idan kin kare maganar,tace ran maza ya huce yallabai ba ina nufin wani abu bane yaci gaba da cin abincinsa bai tanka ba ta zura masa ido tana dan murmushi ta san halin yan kayan ta idan kayi magana kaji yayi shiru to kaima ka tsuke dan bakin ka ka kama kanka shi zai fi zama alkairi. Garin Allah ya waye,baya ga sallah babu abinda Mama ta aikata,ta yada kai bisa kafet tayi lamo kamar sumammiya.Gaba daya ta rame,fuskar ta ta tsuke duk ta bushe idanuwanta sun kode sun firfito waje, sbd tsabar kuka.Malami ya fito wanka ya tsugunna gabanta yace "鐭沶a kwana Anti?Tayi banza dashi,ya zura mata ido,Baki da lafiya ne Anti? Tunda ku ka zo da Daddy baki min mgna ba. Ta ballo masa harara,sai na tsinka mka mari ka sake min magana! Ta ja tsaki,ta juya kan ta wani gefen.Haushi ya kama shi,ya tashi ya ci gaba da shirin sa. Wannan karon kam bai gane kan gadon Antinsa ba. Me ke faruwane? Karfe bakwai daidai Anti Amina ta shigo,tana shigowa Mama ta rintse ido. Anti Amina ta dauko bisa kanta,ta dan dafa ta na san ba barci kike yi ba,ki tashi don girman Allah ga Dokta can ya kira. Kamar yadda na gaya miki jiya so yake yaji muryar ki,hankalinsa ya kwanta ko da gaisuwar sa ki amsa,zai ji dadi Mama. BAKIN CIKI 2***6(TRUE LIFE STORY) Ku da baku wurin in kun amsa.To Mama ta amsa. Haushi kamar ya kashe anti Amina.ta mike tsaye tace, kar ki tashi Mamaa,idan kin sake jin nayi mik閾� mgn akan Al-Ameen,duk abinda kika so kiyi min! Mts....... Ta ja tsaki ta wuce. Mama ta rakata da nata dogon tsakin anti amina ta waigo rike da kugu ta zubo mata ido,lallai mama,ni kike yiwa tsaki? Yayi miki kyau! Taja kofa ta fice.kan wayar ta duka rai bace. Tace, hello! Yace hello anti,ta tashi? Bata tashi ba dokta. (nace"dokto ka fiya nace dolene?) "ba matsala,ai barcin ma yana da amfani a gareta.zan sake kira,ngd ant閾�. Cike da tausayinsa ta amsa,kar ka damu sai anjima. To suka aje waya. Ta haye sama shake da haushi,amma bata nuna wa yallabai ba,don ta san ita zai tsatstsage danya. Iyaka tace da shi bata tashi barci ba Wasa wasa mama fa har ta sake kai bayan la'asar batasa kwayar abinci a bakinta ba hankalin anti amina ya tashi kwarai da gaske mama kam bata cikin hayyacinta gaba daya ta galabaita yunwa na neman tayi mata illa koma in ce tayi matan,shiyasa tana jin waya na ta bugawa taki dagawa don tasab mai kiran kuma bata da abinda zata gaya masa a hakikanin gaskiya ma hankalinta yafi rinjaye akan mama dake ta zama da yunwa tun safiyar jiya Tayi fada tayi rarrashi duk a banza misalin karfe biyar ta hada tea ta shigo da shi dakin wai ko Allah ya bata sa'a ta dan kurba me zata gani mama ke ta madedewa tsakar daki wata irin farar kuffa na hauhawa bisa bakin ta,tasaki kofin tea ta tarairayo ta tana sallalami kinga irinta ko mama nayi nayi dake kice abinci kin ki kina so ki kashe kanki a banza a rude ta sake bazamowa falo ta dauki waya ta kira wayar ofishin yaya abdul kadeea ta shaida masa halin da mama ta shiga Amma yanzu za a fara wucewa da ita asibiti nan take ya bata izini yace zai same ta asibitin babu baa lokaci soja daya ya sakata mota anti amina na tare da ita a gidan baya tana shafa mata ruwa a fuska sojan na jan motar an bata gado ga ledar ruwa na aiki a jikinta, wucewa minti talatin yayan ya iso ya same su jugum jugum,suna kallon ta rai bace ya watsa hannaye aljihu yace dama haka take so ba kuma shi zai taimaketa ba muddin tana motsin rai al'ameen ne mijinta so idan ta farfado ki fara gaya mata kafin na dawo zan koma ofis muna da mitin,tace to adawo lafiya ya wuce cikin kuzarinsa kuratan sa na biye da shi har bakin mota suka koma sannan guda ya bude masa ya shiga direban yaja suka wuce,anti amina ta ci gaba da zama dauke da tagumi zuciyar ta na mata saka iri iri haka wayar al'ameen ke ci gaba da bugawa cikin gidan ba a dauka ba malami ya shigo gidan dawo war sa ke nan daga maka ranta,kicin ya wuce kai tsaye saboda yunwa ce ta koro shi ya debo abinci ya zauna ya fara ci waya ta sake daukar ruri ya mike da filet din a hannunsa yana kara lomar shinkafa da salad ya dauki waya baki cike da abinci ya ce hello hello malami al'ameen ne ba kowa ne a gidan yace eh nima yanzu na dawo school mai gadi ya gaya min sun tafi kai anti mama asibiti wai ta suma. Jikin al ameen Ya kara mutuwa ya ce gaskiya Uncle duk ta rame kamar ba ita ba bata magana sai kuka Tunda suka dawo da dadi ba ta ci komai ba ko ni bata. Yi min magana ba sai yau ta ce za ta mare ni idan na sake gaishe ta wane irin ciwo take yi uncle hawaye suka tsunke wa Al Ameen. Bai san lokacin da ya kife kan wayar ba malami yabi ta hannunsa da kallo. Bai gane komai ba dan haka shima ya aje ya dauki abincinsa ya cigaba da ci yayi sallar magariba dadinsa ya shigo yayi masa sannu da zuwa ya amsa ya haye sama ya cire kaki yasa kana nan kaya jaket da wando ya sauko ya shiga kicin ya hada kayan abinci cikin dan matsakaicin kwando ya kira malami yace kai mota ya jirashi can su tafi asibitin,yace dadi yauwa uncle al'ameen ya kira waya dazun me kagaya masa na gaya masa anti ta sume kunje kai ta asibit to ke ka kirani a mota ya dauki kwando yayi waje jim kadan dadinsa ya fito suka tafi har zuwa lokacin mama bata gane kowa yayan ta ya zauna nan zuwa goman dare sannan suka koma gida da malami Anti amina ta kwana tare da ita kiran asubahin farko ta dawo hayyacinta ido ta zurawa anti amina kafin ta fasa kuka anti amina ta matsa gare ta ta dafa ta saman goshinta tace me yasa kike wahalar da kanki bayan ki na sane da cewa aure tsakaninki da al'ameen babu fashi,ta goge hawaye wallahi wallahi anti bazan. Taba cin abinci ba har sai yaya ya maida ni inda ya dauko ni kinji kuma na rantse bazan kaffara ba,baki sake take kallonta tama rasa ta cewa mama ke ci gaba da fadin na gwammace na mutu da a raba ni da dan liti sabo da haka mu zuba nida yaya idan jan idonsa zai sa in daina son dan'liti anti amina tace gadkiya ne kuma yanzu kika tabbatar min kinyi nisa ka kya jin kira To abinda zan gaya miki shine ki guji bacin ran iyaye rayuwa ki ba zatayi kyau ba muddin kika bar mahaifanki da BAKIN CIKI sannan dole ki fuskanci kalubale tunda kika ci amanar dokta bazan rufe miki ba mama koda nan gaba in ta Allah ta kasance zaki tuna dani kice na gaya miki a asibitin nan wallahi yadda kika sanya al'ameen kuka da radadin zuciya kema sai dan liti ya dandana miki fiye da hakan Da namiji ne fa ki bari ya gama shanye romon da yake hange a jikin ki kisha mamaki daidaiku ke da rikon amana su ajiye ki ke kadai suna girmamaki a matsayin matar sunna mai tsananin kamanta gaskiya shi ne zai ce kik zai kara aur amma sauran shagalinsu suke sha a waje su barki hoto a gida balle wannan Dan'liti daya sami shaidar banza don haka kibi a hankali mama so ba hauka bane tace na ji kin fada amman yarda ba dole bane ko ashe kin gane domin ni duk abinda mutun zai fadi akan Dan'liti ina daukar sa a matsayin hassada ina abin hassadar ga Dan'liti koda ban san shiba labarinsa ya gamsar dani kuma na tsane shi idan kin tsane shi ki daina maganar sa don zai sanima in tsane ki Ta ware ido sosai tana kallon ta ban yi mamakin jin kalamanki ba tunda kika iya shafawa idanuwanki toka ba kya ganin mahaifanki ki balle ki saurari nasihohinsu gareki kin ban kunya mama ban taba zaton wata rana mai kamar wannan zata zoba in sha Allahu zan rarrashin dadin malami ya kyale ki duniya ta koya miki hankali,ido cikin ido ta bata amsa zaifi kyau idan kika yimin wannan kokarin haushi yasa anti amina ta mikie ta fito babban falon asibitin tayi zaune har aka kira asalatu tayi alwala tayi sallah ta je ro addu'o'I tare da rokon Allah ya sanya wa al'ameen dangana idan har ya rasa mama Cikin shigar kakinsa tsaf ya shigo asibitin tare da malami shi ma sanye da kayan makaranta kuratan sojoji biyu na take masa baya dauke da kwandon kayan karin kumallon safe a babban falo ya same ta zaune bisa dardumar sallah,malami ya fara isa gun ta ya gaisheta ta amsa sojojin dake biye suka kwashi gaishuwa yayin da ta miki ta tarbi yallabai amma fuskarta babu walwala sannu da zuwa tace dashi ya amsa yauwa ya dai jikin na ta, tana ciki shiga ka ganta ai ta farfado tun asuba,ko?suka jera zuwa dakin tana gaishe shi jin muryarsa yasa mama ta runtse ido ya tsaya kanta yace ki daina matsr ido nasan kina ji na ina fatan amina ta gaya miki sako na saboda haka ina son ki gane wannan sakarcin bazai firgitani ba abinda na sani kawai al'ameen ya dawo a daura maku aure middin kina numfashi sauran shawara ta rage gare ki, Anti amina dake ta kallon ledar ruwa tasa hannu ta dago igiyar tabbas abinda take zato shine din. Ruwan ba a jikin mama yake ba cirewa kikayi mama, ta juya kan yallabai tayi masa kuri ka gani ko ta cire ruwan yaya ya kawo iya wuya kamar ya nannausheta yake. Ji cikin fushi ya juya ya fita anti amina tace da kanki ki ka kama drip din ki ka tuge,sau dubu aka samin sau dubu zan cire me ruwanku dani tunda baku kauna ta tana rufe baki yayan na shigowa da wasu nosis biyu amma abin karin haushin mama taki yarda su mai da mata ledar ruwan nan basu san lokacin da yayanta ya cire hannu ya tsinka mata mari ba,sai da bakinta ya tsatso jini saboda haushi da takaici kafin ayi haka ya bar dakin anti amina ta biyo bayan sa ta bar nosis na rarrashin mama yana shiga mota ita ma ta fada ciki tace kayi wa girman Allah yallabai karkayi fushi ka tsaya ka saurareni kar ki min magana akan wannan wawayar yarinya," I have finish with her, dama munyi waya da abdul- kareem sun ce za su zo harda abdul-rahman so suna zuwa zasu wuce da ita daga can su bata kudin mota ta wuce fandogari zan iya kashe yarinyar nan idan ina ganinta, tace wallahi ni ma shawarar dana ke son in ba ka ke nan idan kaji maganganun da mama ke fadi zaka tabbatar da tayi nisa bata jin kira sai addu'a kawai zamu zauna ne tana bamu wahala koda yaushe mu ma asibiti a aikin banza?ba zai yuwu ba a irin take taken ta tana gab da fara sufa mana zagi ku kyale ta da dan-litin shi ne zai koya mata hankali,yace ai an gama dokta zuwa kice ya sallame ku kawai zan sake kiran abdul- kareem din in ce su dame mi gida ta numfasa don murna kafin tace,"!58,naji dadi yallabai Allah shi taimake ka ita kuma ya shiryar da ita amin ga break fast can kije kici ki kyale ta bari mu kai malami school gada can zan shiga ofis to a dawo lafiya amin,ta fito sannan sojojin suka taso daga. Inda suke tsaye tare da malami suna jiran su babu bata lokaci suka bar harabar asibitin anti amina ta koma ciki tace wa nosis su kyale ta su tafi abinsu guda tace oga zaiyi fada madam idan ya shigo. ni nace ku tafi kawai abin ku ba mu muka kawota ba,kuma mu zamu biya bill ku wuce kwai ba wani abu"nosis suka wuce da mamaki anti amina ta hada abin kari ta hau ci bata sake komawa ta kan mama ba har likita ya shigo misalin takwas da rabi na safiya anti amina ta maida masa bayanini yallabai likita yace a'a baza ayi haka ba nan ya ja kujera yayi ta rarrashin mama,tayi shiru kamar da gaske sauraronsa takeyi da kansa ya nemo jijiya ya maida mata ruwan amman me yana gamawa bai ko bar dakin ba ta sa hannu ta zare ta aje masa robobin sa haushi ya shake likita ya jima yana kallon ta sannan ya dauki (file)din ta yayi rubutu,ya dubi anti amina yace kuna iya tafiya gida madam da alama ba zamu shirya da sakeena ba tace ai dama na gaya maka kayi hakuri dokta kan ta tayi mawa tace ba wani abu shawa ta kawai ia ce ku kyale ta ta auri wanda ta zaba may be rabon wahala ke kiranta,tace sosai kuwa dokta mun gode ji suka yi mama taja wani shegen tsaki duk suka bita da kallo likita yace I'am sorry for yau,a tunaninki kinyi abu Mai kyau ke-nan? NO,ba hk rayuwa take ba. Ya kamata ki rinka kulaw. Ya sa kai ya fice.Nosis din sa suka take masa baya,kowanne su babu wanda bai shak鐭� taikacin Mama ba. Tana hada kaya direba na shigowa, yaya ya turo shi,idan anyi sallamar ya kaisu gida. Shi ke nan kaya sun tsunke karkashin kaba. Ya kwashe kaya,ta dubi Mama tace, ki na iya tasowa muje gida,idan kin so.Ta yunkura ta tashi,Anti Amina bata saurareta ba ta wuce abin ta. Da kyar ta sauko daga gadon,wani mugun jiri yayi tafiyar ruwa da ita,ta koma dabas! Ta zauna.(maganin mara jin magana,yarinyar nan tana ban haush鐭�! Mts!) Tafi minti uku dafe da kai,sannan ta sake mikewa ta daddafa bango ta fito tana layi. Kowa kallon ta yakeyi,musamman Noisis din da komai ya faru a gaban su,ai nan take aka shiga maida labari. A mota ta same su. Anti Amina na gidan baya,duk ta kulle sakatun kofofin biyu,saboda haka dole Mama ta bude murfin gaba ta zauna tare da direba. Ko a cikin gidan ma,babu mai kula wani,hasalima Anti Amina kwanciyar ta tayi tasha barci,bayan ta yi wanka ta sauya kaya.Ita kuwa Mama taci gaba da sanya tsananin kunci cikin ranta,ji take kamar ana hura wa zuciya ta wuta.Tsananin son ganin Dan-Lati da kewarsa suka hana ta sukuni. A yadda jiri ke dibar ta,sau uku tana fitowa waje ta tsaya wai ko zata ga lakwa-lakwa ta sulale ta gudu.Amma ina,ko fuska babu a wajen kuratan nan,balle ta sami hanyar fita.Don haka ta kifa ciki tsakar falo,tayi ta sharara kuka har azahar,bata san lokacin da barcin wuya ya sace ta ba. Anti Amina ta sauko tayi girki ta gama bata farka ba.Dawowar Malami ya kwarara sallama',shi ya tashe ta,tayi doguwar mika tare da hamma mai kunshi da yunwa da wahalar duniya. Ta tashi zaune taja jikin ta,ta zauna ta jingina da kujera,wucewar 'yan mintoci.sannan idanuwan ta suka kwalli agogo.karfe daya hard a rabi. Da kyar ta yunkura ta tashi ta haye sama a wahale,tana shiga dakin ta zube a kasa,sbd babu karfi a jikinta.Malami da ke cire kayan makaranta,ya zubo mata ido.yana so ya gaisheta yana jin tsoran mari. Ya sauya kaya,ya fice daga dakin,wajen Momin sa ya shiga idanuwan sa cike da damuwa. Ya zauna kusa da ita,tana kallon yadda ran sa ke bace,don hk ta rungumo kafadun sa tace, "Yaya dai,yunwa akeji? Ya kada kai yace, Momi Anti fa zaa mutu,ku maida ta asibiti.Allah bata warke ba. Ta zura masa ido,tace,Ba laifin mu bane Malami,a gaban ka ai kana kallo taki yarda asa mata Drip. To ya take so muyi?" Yace, kawai ku kira mata abba yayi mata fada. Wlh bana son Ant閾� ta mutu. Ina son ta Mom鐭�,me yasa take ta wannan ciwon ne? Ta kara rungume shi tace, kowa ma nason Antin ka Malami,kuma babu mai son mutuwar ta,Matsalar taki cin abinci ne,shi yasa ka ganta haka. To sbd me? Tace kaga ka yi shiru da bakin ka,kai yaro ne ba ruwanka da maganar manya.kai da鐭� idan ka yi sallah ka roki Allah ya bata lafiya. Yace, To Momi,tace. Maza kicin ka zuba abincin ka.'ya fice tana kallon sa. Zuwa karfe biyar Mama ta sake fadawa cikin mummunan hali,bata gane kowa. Anti Amina ta rasa inda zata sa ranta,domin ta rasa yadda zata yi da Mama don ta ceto ran ta. Ta sauko falo da nufin kiran wayar ofishin yallabai. Shigowar mota harabar gidan,shi ya dauki hnklnta ta zage labulan taga ta daga.Motar Abdulkareem ke fakin a harabar aje motoci,ta dawo da sauri ta nufi kofa cike da farin ciki da baya misaltuwa. Ta bude kofar tayi waje,farin cikin ta ya karu,ganin har da Abba acikin su. Sannun ku da zuwa! Ta isa wajen tana fadi. Duk suka amsa,sannan suka rankayo cikin gida. Malami ya rugo ya rungume Abba. Bayan gaishe gaishe suka tambayi Mama. Tace,tana daki babu kyan gani,nama fito ne,in kira dadin Malami ko za mu sake komawa asibitin ne,sai gaku. Wlhy Abba taki cin komai tunda suka zo garin. Ban jin tasa ruwa a bakinta,wannan masifa dame tayi kama? Duk suka yi shiru sbd takaici,babu wanda ya tanka har Anti Amina ta mike ta kawo musu abincin da ababen sha. Ruwa kawai suka sha Abba. Ya-ce, muje mu ganta. Duk suka rankaya saman. Yanayin da suka riski Mama,ba karamin daga hankulan su yayi ba. Abba ya zura mata ido,idan da zai hadu da ita a hanya,ba zai shaida ta ba,sbd sauya kamannin da tayi,sbd tsananin son cikawa al-ameen alkawari ko alama bai bar鐭� tausayinta ya rinjaye shi ba. Don hk ya dubi sauran yace,wannan ba shi zaisa mutuncin mu ya zube a idon duniya ba.sbd hk zamu koma da ita asibiti,ta farfado.sannan mu wuce da ita fandogari. Farin ciki na Mama ta mutu a dakin nauran al-ameen wanan shne kwanciyar hnkli na. Ku dauko ta mu tafi. gaskiya ne abba shi kuwa yaya abdul-rahman abin ne ya zame masa banbarakwai don bai taba zaton labarin da yakeji abin ya kai haka ba duk da yana jin zafin abinda mama tayi ,halin da idanuwansa suka gane masa mama a halin yanzu kwarai tausayinta ya kwanta a zuciyar sa shi ne ya fara kai hannu ya ciccubo ta suka taimaka suka sauko da ita kasa kamat matacciya,da kyar likita ya karbe ta sai da yan uwanta suka yita rarrshinsa sannan ya bata gado yayi mata duk abinda ya dace. Acan yaya abdul- kadeer ya same su bayan sallar magariba kafin ayi issha'I suka rankaya gida akabar anti amina tare da ita,kusan kwana sukayi shawarwari akan al'amarin,kwana daya da wuni mama na kwance magashiyan ledar ruwa goma sha tara ta shanye,ana shirin daura mata na ashirin sannan idanuwanta suka fara washewa ta gane inda take hada ido da abba tare da karkaf yan'uwanta bai haifar mata da wata nadama ba illa kuka da ta fasa wai don su tausaya mata babu wanda ya tanka mata wannan itace shawarar da suka yanke babu wanda zai sake bata bakinsa don yi mata fada amma zata sha mamaki ranar da Allah ya yasa al'ameen ya dawo kasar nan,babu wanda yace cikanki har ta gaji da shashekar kukanta. A zaton ta shirun na su alamma ce ta saduda ma'ana sun rasa yadda zasuyi da ita dole suu sa mata ido anti amina ta fara bata ruwan lipton tana kurba da kyar take iya hadiye shi gaba daya Makogwaronta ya farfashe kafin gari ya sake wayewa mama ta samo kanta misalin goma da rabi kawai ganin su tayi sun shigo suna gaya wa anti amina an sallame ta zasu wuce yanzu bata yi mamakin jin haka ba don haka ta amsa da to,Allah kara lafiya ita kuwa yar gigalar murna ce fal cikin ta jin za a wuce da ita fandogari nan da nan suka kwashe kaya,yaya abdul-kadeer ya dauki matarsa,mama kuma tabi ayarin komawa gida a minna suka yada zango suka ci abinci tare da yin sallolin azahar da la'asr in banda su ameera babu wanda mama tayi magana dashi domin anti rabi ma ta sauya fuska al'ameen dintama bai sami kulawa ba suna idar da la'asar yaya abdul-rahman ya jawo matarsa daga inda ya aje ta aka maida jakar mama ciki ita ma ta fito ta shige gidan baya abba na tare da karamin yaya a gaba Shi ya jasu a hankali xuwa fandagori. tun daga kan kwana hankalin mama ya soma kwantawa, domin dai idanuwan ta sun hango wanda take son gani. yana zaune bisa benci a kofar shagonsa, yayi murmushi itama ta sakar masa nata. har motar ta wuce, ba su daina leken juna ba. sai da ta daina hangensa, sannan ta zauna sosai kirjibta nata bugawa, ji take kamar ta balle murfin motar ta fice taje gunsa. ya mikawa ayuba hannu suka tafa. yace baka da kyau! Yace karya kak don ubanka, kalle ni sama da kasa! ba kyawun sura ba, ina nufin.... ya kai masa naushi a kafada, shi ya katse shi. zan ci..... kai! ka kiyaye ni fa wlh! me na gaya maka? yadda suka dauke ya ahaka za su dawo min da ita. wahalar banza sukeyi sakeena mallaka tace. yace ranar da Allah kuma zai kama. ayuba baya wajen, duk ka gama iskancin ka. ya ballo masa harara yace, to ko ka na wajen me zakyi? kai ma ka ji da naka, don ubanka. Menayi? ni nakai ka iskanci a garin nan? dama wane kai, amma sannu a habkali xzaka biyo ni mujera hanya watakila ma ka xarta ni. ya tabe baki yace Allah ya sawwake, kai din ma so nake na janyo ka baya. ka auri yarinyara nan, ka manta da kudinrinka na wulakantata. ya dafa shi yace ka dan kula da shagon, bari na je nemo gasasshiyar kaza. kasan dole anjima ta zo 鎷� ya xuba masa ido kawai, bai ce masa komai ba. yayi dan saurayin murmushin. ya mike ya fada motar sa yayi birnin gwarin tsinke. kai tsaye mama dakinta ta shige. umma bata gasganta idonta ba, irin yanayin da taga mama saboda haka tatashi tabi bayanta. Kallo daya tayi mata taji kanta ya ci gaba da sarawa, wani kululu ya daure xuciyarta, idanuwanta suka tara kwalla, saboda tsabar BAKIN CIKI. Ta jima kafin tace, Mama kina da hankali da tunani kuwa? Ji tayi an dafata ta biyu, muryar Yaya abdul rahma ke fadin, baki da lfya Umma, karki daga hankalinki, abba yace ki fito ki kyale ta. Ya kamo ta suka fito, jiri na dibarta, shi ya sa tace yawuce da ita dakinta. Abba ya taso ya biyo su, yayin da take kwanciya a gado. Gefen gadon ya xauna yace, bai kamata ki bar ciwon ki ya tashi ba halima, kin ji dai abinda Dr. Ya fada, jininki ne ke hawa saboda damuwar da kika sanya a ranki. Ki hrk kawai. Tace, ba alamun yin nadama a wajen Mama, ni kaina, nasan haka,amma shawarar da mu ka yanke da 'yan uwanta shine mu sanya mata ido tayi shirmen ta, sai ranar da Al-ameen ya dawo xata gane mu ma ba muyi nadama ba. Abdul yace saboda haka ki kwantar da hankalinki, ISA sai dai mama ta mutu a dakin Al-ameen, ba zamu ji kunya ba. Su Yaya babba da Iyalnsu duk sunce gaishe ki, sai sun xo. Tace ina amsawa, Allah ya taimake mu, suka amsa ameen. Abba ya dube shi ya cigaba, kai ma ya kamata ka hanxarta wucewa yamma tayi sosai. Umma ta amshe, ba xai bari xuwa gobe ba? Yace, akwai aiki Umma, yanxun nake so na lallaba. Ta dan kada kai. Tace, to Allah ya Tsare agaida min safiyya da kyau. Zata ji, ki daina damuwa Umma, komai xai wuce da yardar Allah. Ta amsa da kai, tana fadin shikenan abdul, Allah yayi maka albarka. Yace amin. Ya wuce cikin hanzari. A tsakar gida ya hadu da su Haj.Hajjo. Ashe da gaske ne kun dawo? Yara ke fada mana yanxun. Yace eh, nima xan wuce kd kenan. Gaba daya suke to Allah ya tsare! Ya amsa yayi gaba abinda, su kuwa ciki suka kutsa kai dakin mama. Kwakwazon surutun su ya sa Abba ya ta so fito. Sannuku da dawowa Yaya. Yace yauwa, ga haliman can a dakin ta. Haj. Hajjo tace, muna nan mun ganin ikon Allah. Mama ta dawo kashi ba rai? Yace haka take so, ai ku daina bata bakinku, kowa ya sa mata ido. Haj. Gaje tace, lallai kam wannan al'amarin sai ido. Allah ya kyauta. Ameen. Suka fice tare suka koma dakin Umma, suka isheta da surutu. Duk iya kokarin mama na son fita a wannan daren abin ya faskara, domin dai Abba ya kasa ya tsare a falo har goman dare ya garkame kofar ya shige dakinsa barcinsa. Allah da ikon sa, abba bai xare mukulin ba, domin bai taba tunanin Mama xata iya aikata wani abu a wannan tym din ba lallai abba bai san Mama ta wuce tunaninsa ba. Yana bada baya, taji motsin rufe kofarsa ta yi wuf ta mike, takalmanta a hannu tare da mayafinta. Tayo sanda ta fito jim, tsakar falon bata ji mtsin kowa ba, sannan ta karasa kofar ta bude ta cikin nutsuwa ta sulale ta fice. Can ma kofar sassan hka ta bude ta, ta wuce zaurukan gidan, ta zare sakatun ta bude ta fita ta maida kofar ta sakaya. In bakayi bani wuri! Ta callah da gudu bata ko jin rashin karfin jikinta, sai da tayi rabin tafiya, sannan ta tsaya ta sa takalmanta ta yafa gyalen tana ta xuba haki, ta dau hanya babu jama'a sosai. Gata nan ga ta nan har kofar shagon dan gogan. Ya tare da dije a kofar shagon bisa banci, ta cukuikuye shi kamar na goye fadi yake, wai dan Ubanki dole ne? Kin fa matsa min da yawa, xan ci ubanki a daren nan, in ga mai kwatar ki! Kawai ganin mama yayi akan su. Ya banbare dije ya ture gefe, bai bata lokacin ya daga kanta ya shige, shagon yana jan tsaki. Mama ta daga itama ta bishi. Dije kuwa mikewa tayi ta kakkabe jikinta ta wuce tana kwafa. Ya hade rai a kujera, bai ko kalle ta ba. Ta matsa gare shi murya sanyaye tace, fushi kayi danliti? Ni ban yi fushi ba sai kai? Ina can naki ci na ki sha saboda kai. Ashe ka na nan ka tare da wata? Dubi yadda na rame na sauya kamanni, saboda tunanin ka Danliti. Bai kamata ka yi min haka ba. Ya dago idanuwansa farare sol! Sunji kwalli ya dubeta, ko mai nai miki ai kekika jawo, kinbi 'yan uwanki ki manta da ni, ba dole in sami wata ba! Tun yaushe kuka shigo garin nan? Nayi ta xuba ido, amma ban ganki ba, me kike tunanin xan dauka? Kafin tace wani abu ya fizgo hannunta xuwa daki, yana kara fadin, idan karya nake yi, xo muje ki gani! Ayuba dake kwance bisa katifa yayi firgigi ya tashi yana kallon ikon Allah. Ledar kaji ya janyo ya xaxxage su. Yace me kika gani nan? Saboda ke na tafi har birnin gwari na siyo miki gashin xamani kajin turawa. Dubi nan juice ne kala-kala har sanyi su ya fita, baki xo ba. Ba dole in yi fushi ba, in saurari mai so na! Ta sauke numfashi, idanuwan ta taf! Da kwallah, ba laifina bane Danliti, baka san irin bakar wahalar da na sha ba, don kawai su dawo da ni. Sau biyu ina kwanciya a ascibiti, dube ni da kyau, kai kanka kasan ba haka nake ba. Amma kayi hkr, tunda kana ganin kamar da gangan nayi, ka hkr? Ya xura mata ido jim, sannan yayi dan murmushi ya ware hannayensa yace, to oyoyo! Ta sa hannaeyanta ta rufe fuska. Yace kunya? Ashe baki so na, lallai na yarda ni kadai nake haukan sonki. Yana rufe baki ta matso da sauri ta rungunme shi. Ayuba, yayi gyaran murya. Mama tayi wuf ta rabu da jikinsa. Ya dubi Ayuba, yace malam ka fita ka bamu wuri! Yace, ai ku ya kamata ku koma daga waje anan nake so mu xauna, fita ka bamu wuri don Allah, shago fah abude yake, ya yankura ya tashi yana fadin, gaskiyya kuyi sauri ku gamacin kazaraku, barci nakeji. Ba ruwanka wannan. Ya fice yana waigen Danliti yana masa ishara da idanuwansa dauke da gargadu, wanda shi kansa ya gane nufinsa, shi yasa yake wani irin mur0ushin na iya shege. Yana fita ya dubi Mama suka hada ido dukkan su sukayi murmushi, sannan ya kamo kafadunta yace, gashi dare yayi, amma dole ki xauna ki cinye kajin nan, domin saboda ke na siyo su. Ba tace komai bam ya xaunar da ita gefen katifa, ya jawo kayan kwalama, ya baje mata kajin, yana bata abaki, tun tana jin kunya har ta saki jikinta, tana amssa sosai tana ci, suka ci suka sha suna hirar bayan rabuwa. Bayan sun kare. Danliti ya dubi agogonsa ya ce shadaya da kwata yanxu, ya kamata kije gida ko? Sai gobe, ina fatan xaki rika cin abinci don ki gyagije kyanki ya dawo kamar da. Kinji ni? Tace, naji kuma xan kiyaye, amma don Allah ka daina bari 'yan mata na xuwa gunka, watarana xamuyi dambe da su wlh, kaji na rantse. Ya kyalkyale da dariya son ransa kafin yace, xaki kuwa sha duka, don dai nasan sunfi karfinki. Wannan jikin naki rugu-rugu babu kwari. Ya fadi yana mammatsa hannayenta da kafafuwanta. Ta yankura ta tashi tana cewa, haka kake gani, ka maida abin wasa, zaka sha mamaki. Shima ya mike ya kamo yatsunta, yace karki damu, ke kadai nake so, ko da damben ya kama kuyi, xan shigar miki balle ma banda lokacinsu. Ke me xai dameki? Tayi murmushi, tace, to shikenan sai da safe. Ya sumbaceta yace, muje na rakaki. Suka fito yana rike da hannunta, tayi wa ayuba sallama suka wuce. A kofar gida suka fuskanci juna, tallafo kuncinta ya xura mata ido, yace karfa ki damu da ganin Dije tare da ni, wlh ba sonta nake ba, kawai ta matsa min ne dole muyi soyayya, amma xan dauki mataki akanta, tinda ta fara bata miki rai. Tayi murmushi, tace, nayarda da kai, ina fatam Allah ya yarda mana, ya bamu nasara abinda muka sa gaba. Da sauri ya amsa amin sakeena. To sai da safe nagode, wannan karon abin ya cigaba akan labbanta ya sumbace ta. Ta juya da sauri, ta tura gida ta shige ta maida sakatu. Danliti ya runtse ido ya jinjina hannayensa, shege ni! Ya juya yana takawa dda+dai kamar wani kasaitaccen basarake. Mama kuwa sanda takeyi, kamar barauniya ta turo kofar fa'aar dshigo ta mayar d hankali ta kuleta, ta fada gado. Tana jan mayafi, taji a; ttay bude kofa, tayi tsaye jim, sannan ya mayar ya rufe. Muryar umma taji tana fadin, menene alh.? Yace kamar motsin naji ana taba mukulli.. Tace Innalillahi an shi ne? Yace amma ban ga kowa ba. Ya dubi agogo, karfe sha biyu saura kwata, dare ma bai yi ba sosai, to Allah yai mana tsari da sharrin masu sharri. Yace amin, je ki kwanta. Cikin fargaba suka bar falon. Mama ta gyara kwanciya tana gyatsar naman kaxa. Dan kanta tace kwanta naman kaza. Tayi tunani Danliti har barci ya kwashe ta, shi take marfi yana sa mata naman kaza abaki. Da safe tayi wanka, duk 'yan ciwukan da suka rage ba su warke ba, ta goga musu mai, ta shafa hoda ta sa atamfah riga da xani, nan da nan ta dan yi fasali, duk da cewa akwai rama sosai a jikinta. Yau kam tayi dan kyan gani, ta fito falo wajen Umma cikin kicin inda take aikace aikacenta, tace sannu Umma ina kwna? Ta juyo da sauri ta dubeta sama da kasa, tace kalau na kwana. Ta kara matsowa tace, bari in gaida Abba, sai in xo in tayaki aikin. Bata amsa ba ta fice, ta bita da kallo sannan ta kada kai tace, Allah ya shirya. Dakin Abban tayi sallama, ya amsa ya bita da kallo, ta karaso gunsa ta tsugunna, ina kwana Abba? Yace Kalau, ta dan dube shi, amma bata kara komai ba, ta mike tayi waje ta koma kicin: Umma me xan tayaki? Tace ban so, koma dakinki kawai. Saboda me Umma? Ai ban isa na fadi ko saboda mene ba, tunda kin xama shafaffiya da mai. Je ki kawai ki sha xamanki. Kai tsaye kuwa ta wuce daki abinta. Tana fadi cikin ranta, kya gama girkawa, mu zo mu jajja (hmmm mama tayi nisa walle). Kan Umma ya sara ganin yadda mama ta wuce ko ajikinta, bata damu ba. Mamaki bai gama kashe Umma ba sai da ta hange ta kicin din tana diban abinda take son ci. Tana kallo ta koma dakinta ta cinye, ta maida kayan kitchen ta fito. Haushi ya kume Umma bata san tym din da tace, Uban wa kika ajewa kayan ya wanke miki? Tabbatacciya! Ta dan bata rai ta juya ta kwaso kayna ta wanke. Karfe 9 abba ya fita harkokinsa. 9:30 mama figi gyale tayi waje, Umma nace na wanka. Ta sha hirarta wajen Danliti har 12pm sannan ta tsallaka ta gangara wajen Baraka. Sosai taga sauyin fuska wajen Inna saude. Sam abin be dame ta ba. Suna kebewa da Baraka tace. Kawata ban gane ba, sai da nayi miki kallon kurulla. Yanxun saboda Allah dawowa kikayi? Tace ga ni kuma kina ganina. Matsala tace, babu ruwan kowa. Mutane masharanta ne kawai, saboda Allah yayi wa Danliti kyau da farin jini, ga shi ya Rufa masa asiri, shi ya sa ake masa hassada.... Ta katse ta, idan hassada ce, ai kuwa kem kinyi masa da. Menen baki fada ba akansa? Tace, Rashin sani ne, duk surutan da akeyi wai dan Iska ne dan guguwa. Dan wata tsiyace, ni har yanxun Danliti bai taba furta min maganar banxa ba balle ya nemi aikata wani shashanci. Rashin fahimta ne kawai yasa ake masa zargi, kisan mutum mai farin jinin 'yammata (Kuji fa wai bai taba mata komai ba?) baki ganin ko mace ce ta fiye samari sai arinka mata wani irin kallo? Baraka ta sauke fuska, tayi guntun tsaki, baki jin kira Mama. Allah ya shirye ki. Ameen, ni bari in koma gida, dama lekowa nayi mu gaisa kisan na dawo. Tabita da kallo, ki na san kin dawo wajenki xano? Menene anfani kawancen mu? Bayan ko na gaya miki gaskiyya bakyaji. Allah ko? To Allah ya bamu alkhairi ki gaida mohd dinki, in yazo. Yaushe xasu kawo gaisuwane? Ko bai shirya aure bane? Wlh ban masa zargin komai ba, amma sonsa bai rufe min ido ba, ina bukatar in gama sanin ko shi waye tunda ba gari daya muke ba. Ta tabe baki, Baraka ke nan, Miss kakale! Ba kakale bane, gaskiyya ce kawai, daga kinta sai bata. Shi ya sa nake nuna mikita, don banson ki bata. Ta mike hannu daya kame da kugu, tace, nagode, ni nayi gida, kar Umma ta neme ni. Tasa kai tafice. Baraka ta biyota, ta sallami Inna ta rako ta iya zaure ta juya. Ta shige gida, tabar mama dauke da mamaki. Tai kwafa tace, kiyi da gwana yarinya. Ta kama hanya ta koma wajen Danliti, wasa-wasa sai da ta bata mini talatin anan, sannan ta karasa gida. Umma na zaune tskar falo ta sha tagumi, ta gaji Mama ta shigo babu ko tsoro ko fargaba tace, sannu da gida Umma. Inna saude na gaisheki. Ta zura mata ido ba tare da cire tagumin ba, jima kafin tace, da izinin wa ki ka bar gidan nan Mama? Ta mimmike kafa sosai akujera. Tace ai kinshifa wanka ne Umma shi yasa banyi miki magana ba. Umma ta numfasa, tayi hucin BAKIN CIKi tace, lallai kin isa mama, duk son danliti ne yasa kika zama maras kunya? To kibi a hankali, duniya zata koya miki hankali, muddin kika dauke ta kika goya. Ta figi gyalenta, ta mike cikin sauri tana fadin, Uhm.....! Ta wuce ta fada dakinta, tayi kwanciyarta. Umma ta kada kai, kwallah suka xubo mata, ta share tace, Allah kana kallo, munyi iya yinmu, amma shiriya na wajenka, kayi mana gaji Ya Allah. Nan Umma taci gaba da zama tana shan BAKIN CIKI tare da takaici mai tarin yawa har aka kira azhar, ta tashi tayi sallah. Abba ya dawo ta labarta masa, hannaye biyi ya kama kai, takaici kamar ya kashe shi, bai niyyara kara yiwa Mama wata magana ba akan Danliti, amma dole tasa ya kira tazo dakinsa ta xauna. Yayi mata kaca-kaca, sannan ya sa mata dokar fita ko'ina, duk da yasan ba dole bane tabi umarninsa. Tabbas hakan ne, yadda Mama ta fito dakin bakin nan nata ya kai wani gari wai shi ZUNTU. Shi kasna ya san rashin kunyta Mama ta kai wani mataki na kololuwa kwatance, ta xauna bakin gadon ta tana fadin a fili, wannan shine bature ke kira Impossible! Tunda kuka hana shi xuwa guna, dole inje gunsa mu ga juna. Ta saki wani lafiyayyen tsaki, ta yada kai bisa filo......... Maganar mama dutse. 7days kenan babu abinda ta fasa, muna iya cewa al'amarin kara haukata yayi. Domin a halin yanxun Mama bata shayi, agaban Umma zata dauki mayafinta, ta fice. Umma na kira, tana fadin tana xuwa yanxu xata dawo. Sau uku Umma na xuwa da kanta kofar shagon Danlinti, tana taso keyarta. Jama'a na kallon su, gwanin ban kunya. Sai da Abba ya hanata xuwa. Yace tasa mata ido, tunda ta zama gagararriya. Wannan abin kunya ya zama abin yayatawa awajen su hajjo, duk inda suka xauna xancan kenan. Babu abinda bai dawowa kunnen Umma ba, sai dai tayi kuka ta share hawayenta ta barwa Allah komai. Mama fa ta gagari kowa, suna ji suna gani mummunan labari na ta yaduwa har gidan Gwaggo Hausi. Daga can labarin ya mika gidan Marafa. Nana take mami ta tsani auran mama da Al-ameen. Shi kuwa Marafa nuna mata yake su daina kama jita-jita. Aure dai nufi ne na Allah, idan sakeena matar Al- ameen ce, bbu makawa xai aureta, idan kuwa ba matar sa bace si barwa Allah yayi masa zabin alkhairi. Duk da haka al'amarin yana jefa Mamai cikin tunani ba kadan ba, kuma da Al-ameen zai ji shawarar ta, da ta umarace shi daya hakura da sakeena, tunda shasahnci tasa gaba. Sallar la'asar ta kammala, amma bata bar sallayar ba, saboda gabatar da lazimi takeyi. Wata tasi tayi fakin kofar gidan, direban ya fito ya bude but, yana fido jakar kaya. Yana rufe but din, idanuwa na suka nuna min Al-ameen a tsaye ya cusa hannu gaban riga ya zaro kudi ya mikawa direban, yace, ka rike chanji. Ya sunkuci jakarsa ya wuce. Direba na xuba gdoiya. Ya tura karamin gate ya shiga, bakin mai gida har kunne ya taso da gudu ya amshi jakar yana fadin Maraba da oga! Fuskarsa babu walwala sosai, yace ya kuke? Lafiya lau oga. Ya shige masa da kaya falo. Al-ameen yayi sallama, muryar sa ta dauki hankalin duk wanda ke cikin gidan. Iya ta riga kowa fitowa, wa nakehi kamar dan Iya? Ya nufo ta fuska sake, ni ne iya, surprise ko? Ya dan rungumo tana fadin, ai kaki koya min turancin nan, da yanxun na gane nufinka. Yana murmushi ya rabu da jikinta, ya dubi Ladi, Hajiya Ladi ina fatan kunje kun duba min jikin sakeena ta? Tace muna dai shirin tafiya da hada tsaraba. Ya ce, baku da tsraaba? Gaskiyya kunyi min babban laifi. Tace, mun san hakan amma tuba muke. Ta ya kuke? Ta amsa lfya lau ya hanya? Yace, Alhmdlh. Yana juyo wa sukayi ido hudu da mami tana masa kallon mamaki. Ya nufe ta da sauri ya rungumeta, Mami na! Idanuwanta suka tara kwalla, ta kasa cewa komai har ya dago ya dubeta, yayi dan murmushi. Yace, nayi muku laifi Mami, kuyi min hkr na kasa daurewa ne. Tace nagode Allah da ya kawo ka lfya. Amma banji dadin xuwanka ba Al-ameen. Yace, na tuba Mami, ki duba halin da nake ciki, kiyi min uzuri. Ta dan kada kai. Tace, muje ciki ka sha ruwa ka yi sallah. Suka wuce yana tambayar Dadinda. Tace, xai dawo anjima daga kd. Yana xama Ladi ta shigo masa da ababen sha masu sanyi. Bayan ya jika makoshi, ya dubi Mami yace, ya jikin sakeena? Na daina kiran waya, don kunnuwa na ba za su jure jin mummunan labari ba, koda yaushe. Dalilin da yasa kenan, nace ya xama wajibi in xo inga halin da take ciki da idanuwa na. Dan hutu muka samu na sati daya, shine na yi anfani da wannan damar. Yaya yanayin jikin nata yake? Ta numfasa sosai kafin tace, jikin ta har yanxun a rikice yake, xan so ace Allah ya saka maka hkr, da dangana akan sakeena, domin kwakwalwarta ta jirkita Al-ameen..... Hauka Mami? Kina nufin sakeena ta haukace? Inna- lillahi wa Inna-illaihiri Raji-un! Idanuwansa suka tara kwalla, ba xan iya hkr da ita ba Mami, ko ba zata taba warkewa ba, sai na aureya. Alkawari ne wannan Insha Allahu ba xan karya wa sakeena ba. Tana ina ne yanxu? Ita ma nata idanuwan suka kawo kwalla. Ta ce, tana Fandagori, kuma ni ma xan so hakan Al-ameen, domin duk abinda kake so, nima shi xuciyata take matukat so da kauna. Amma al-amarin ya sauya salo, ka dauki kaddara kayi hkr da ita, hankalina zaifi kwanciya Al-ameen. Da gudu hawayen sa suka wuce bisa kyakkyawar fuskarsa, ya matso ta a hankali, ya dauko hannayenta biyu ya matse, ya dubeta ido cikin ido. Yace, har abada bana fatan in saba umarnin ku mama, amma ina rokon alfarma ki ban izini in cikawa sakeena alkawarin da daukar mata. Zan tafi samun nutsuwa, idan ina kallonta a matsayin mata ta kowane irin yanayin take. Ina rokon ki Mami ki taimaka min. Ya jingina goshinsa bisa kafadar ta, ya matse hawayensa tare da ajiyar zuciya mai karfin gaske. Haka maminsa ke cikin irin wannan yanain. Ta jima shiru tana tunanin zuci, tana son gaya masa gaskiyya, amma bakinta ba xai iya furtawa ba, saboda tausayin dan tilon dan ta. Ta yi ajiyar zuciya. Tace, nayi maka Umarni akan duk abinda yafi xama alkhairi Al-ameen. Mike ka je kayi sallah kaci abinci. Ya dubeta yana share kwalla. Yace, nagode Mami. Ta danyi murmushin dole. Jeka yi sallah. Ya tashi da sauri ya dauki jakarsa, ya fice. Mami ta raka shi da kallo, hannunta a kunci. Ta nunfasa kafin tace, Allah gamu gareka. Yana shiga, bangarensa ya isa ya yar da jakar hannunsa ya xauna gefen gado Ya kama kai hannayensa 2 yana yiwa Allah tasbihi. Jim kdan ya tura hannu aljihunsa, ya xao wallet dinsa ya bude ya xurawa dan karamin hoton Mama ido, nan da nan hwaye suka goce masa, bai ma san tsaninin kukan da yake ba har da shassheka, kamar xuciyarsa zata tsago kirjinsa. Allah da ikonsa, tamkar mami na da masaniya ta taso ta biyo shi dakin, don ganin a wane yanayin yake? Da sauri ta karaso ta zauna kusa ta shi ta rungumo abinta, idanuwan na tara kwalla. Komai ya sami bawa daga Allah ne Al- ameen, bai kamata ka xauna ka rinka kuka ba! Jin muryarta yasa hankalinsa ya dawo jikinsa, sannu-sannu hawayensa ya tsane. Ya dago ido jajur! Ya dubi Mami, yace mami ki amince min inje in dubo sakeena Yanxun. Ta goge masa guntun kwallan dake bisa kuncinsa. Tace, na baka izini Al- ameen, fargaba na kawai dare. Yace, kar ki damu Mami. Allah xai tsare. Shikenan, Ubangiji Allah ya sa ganinka ya xama waraka gareta, hankalin kowa yakwanta. Yace, Ameen Mami. Tace , To kayi sallah Maza-maza, don Allah kar ka zauna dogon tunani. Yanxun xan fito Insha Allahu. Ta mike ta bar dakin. Al-ameen Ya sauke numfashi, shima ya mike ya fada bayi, nan da nan ya watso ruwa ya dauro alwala ya fito. Bayan yayi sallah ya kimtsa, ya fito Mama ta matsa yaci wani abu, amma bai iya zama ba, gaba daya hankalimsa ya koma Fandogari. Sai dai ya sha Mamaki daya ga Mami ta nace dole ya tafi da direbanya, bai yi musu ba. Kai tsaye ya shiga mota direba ya ja shi suka dauki hanya suka bar Mami cike da damuwa tare da tunanin yaya al'amarin zai kasance idan Mama ta juya wa Al-ameen Baya? BAKIN CIKI 2*** 8 Ba su ido Fandogari ba, sai karfe 8pm, babu bata tym gidan Uban dawaki suka dosa. Ya shige sassan sa tare da sallama. Umma ta amsa ba tare da ankara da mai muryar ba. Sannu Umma. Ta dube shi da kyau, gaban ta yayi mugun faduwa, ta mike tsaye tana fadin, Al- ameen! Saukar yaushe? Yace, yau din nan Umma. Ikon Allah. Sannu da xuwa! Zauna mana, ya zauna yana amsawa. Kafin yace, ina yini Umma? Ta amsa, lfya lau ya karatu? Mun gode Allah, ya jikin sakeena? Tayi dan shiru, kafin tace wani abu. Abba yayi sallama ya shigo, duk suka amsa amsa Abba! Yace, ah! Al-ameen! Saukan yaushe? Yace daxun da la'asar Abba. Ya xauna suka gaisa, sannan ya sake tambayar jikin mama. Abba yace ciwo na nan Al-ameen. Halima kawo masa abinci ya ci, kafin muyi magana. Abba bana jin yunwa, domin na riga na saba da ita, tun tym din na sami labarin tashin hankalin da kuke ciki. Abin daya hana ni jurewa kenan, nace dole in xo inga halin da Mama take ciki. Abba yace, gaskiyya ne. Mama na nan cikin lularar da ta sameta sai dai al'amuran zai ba ka mamaki idan na gaya maka alabari ya sha bambam Al-ameen, nasan an boye maka komai coz of karatunka, amma yanxun dole ka sani, tunda ka zo. Jikinsa ya kara sanyi, yayi xuru yana sauraron abba, al-ameen rayuwa ta sauyawa mama, wanda muke ganin sa tamkar a mafarki, daga ni har 'yan uwanta kaf! Babu wanda ba shi ckin alhinin wannan abu. Balle kuma kai da soyayyah ta hada ka Mama, kuma ita da kanta takwo mana kai cikin gidan nan. Shi yasa nayi rantsuwa, idan mama xata mutu, sai dai ta mutu a dakin ka tunda tun farko ita ta kawo ka. Ashe kuwa babu wani dalili ko uzuuri da xata kawo mana mu saurare ta. Nasan har yanxun kana jina a hagunce ne, baka gane inda na dosa ba. To bari na fito maka a mutum kada ka wahalar da kanka, Magana daya ce, mama ta gano wani kuma idanuwanta sun rufe ta manta cewar tayi xafin farko kuma na karshe a swajena. Ka fahimce ni? Gaba daya kansa ya kunce, daga yadda yayi kuri idanuwan sa kafe yana kallon Abba, suka gane bai fahimci su ba. Saboda haka yace, dole ka shiga rudu fiye da wanda ka shuga a baya, amma ina so ka sani, mu muna tare da kai, ba mu san kowa ba face kai, ba don komai ba sai don tun farko kai tafara kawo mana. Abinda nake son ka gane shi ne, xuwanka ya sanya ni farin ciki. Domin kai kadai nake jira in tabbatar wa Mama cewa lallai ni ba tsohon banxa bane, kuma bana magana 2. Ina mai tabbatar maka ba xaka koma ba sai na daura auranka da sakeena da yardan Allah. Na gama magana ta, ka tashi hankalinka kwance, kashiga wajenta tana nan cikin dakinta. Ya mike ya bar falon. Umma ta dube shi tace, Al-ameen! Murya dishe ya amsa, na'am Umma tace kayi hkr, ka kwantar da hankalinka. Mama bata isa ta xubar mana da mtunci ba. Kai zata aura da yardar Allah, domin da kai ne akayi mata baiko. Tashi ka shiga wajenta ku fahimci juna. Ta mike tabashi guri, don yaji dadin tashi......... Me kunnuwan Al-ameen ke ji yau? Ya runtse ido tamau! Ya girgiza kai wai ko barci yakeyi ne? Abba ya xo masa a mafarki. Ya bude idanuwan ya ware su sosai, tabbas zaune yake cikin falon su Mama. Kenan dagaske ne maganganun da Abba ya gaya masa? Kirjinsa ya soma bugawa ji yake kiris! Yarage ya zare masa rai, saboda wani gagarumin ciwo da yaji cikin xuciyarsa, nan take ya kama shi. Motsin kirki ya kasa yi har Umma ta sake fitowa da nufin dauko wa Abba abincinsa. Ta danyi jim, tana masa kallon tausayi, sannan ta matso tayi kiransa, ya dubeta firgigi idanuwa sun juye jajur! Tace, ka na xaune, baka shiga ba? Tashi ka shiga mana, ka kwantar da hankalinka, komai xai wuce Insha Allah, ya mike a kasale, ya nufi dakin ba tare da yasan me xai je yayi ba. Tana zaune tsakar daki ba ta hade kai da guiwa, tsiyayar hawaye kawai takeyi, domin tana jin duk kalaman da Abba ke fadi. Daf! Da ita ya tsugnna, bai san lokacin da yasa hannu ya dago fuskarta ba. Sukayi wa juna xuru tsawon lokaci kafin yace, kin ganeni sakeena? Al-ameen ne, kin gane ni? Ta kau da kai abinta. Da sauri ya kara juyo da ita, kiyi min magana sakeena ko na sami nutsuwa saboda ke na dawo kasar nan, don na duba jikin ki. Ina can tunani da xulimmi sun addabe ni, idan kin gane ni, ki amsa min, ya jikin ki? Ta watso masa harara, hawaye na kwarara. Tace waya gaya maka banda lfya? Yace, haka kowa ke gaya min tun tym din da na daina jin muryarki a waya, komai nawa ya tsaya sakeena, radadin ciwon daya sameki, ya hanani sukuni. Ina fatan gani na ya zama sanadin samun saukin ki. Ta goge kwalla. Tace duk wanda ya gaya maka banda lfya, ya maka karya, kalau nake, gani kuma kana kallo na xaune, sai dai na tabbata dawowar ka zata iya zame min cuta! Ya kara xura mata ido , kina nufin abinda Abba ya gaya min yanxun gaskiyya ne? Tace ka daina kokwanto. Ya langwabe kai gwanin ban tausayi. Yace dole nai kokwanto sakeena, don nasan akwai alkawarin a tsakanin mu, kuma bana tunanin zaki yaudare ni, wannan ya tabbatar min da tsantsan son da kike min. Ban taba kallonki da xuciya 2 ba sakeena. Shiyasa har halin yanxun da nake magana dake ban yarda kin karya alkawarin mu ba. Ta kalle shi a dage, ta watsar tace, ya kamata ka amince, tunda gashi da bakina ina gaya maka, tsutsun soyayyarka yayi fiffike yayi dogon tashi. Ya dafe kirjinsa a natse idanuwansa tam! Da wahaye, yace, bai tashi ba sakeena, nayi rantsuwa kina so na. Akwai miskhila dai a wani wuri, ki gaya min laifin da nayi miki. Wlh da kaina xan hukunta kaina, koda da jinin jikina ne xuba, idan har zai zama fansar tarin laifin da nayi miki. Gaya min da sauri inji. Ta ya mutsa fuska, hawayen ta ya bushe tace, Al-ameen ka farka daga barcin da kakeyi ka saurareni, ni sakeena na gaya maka a da naso ka, amma yanxun ban son ka, ba kuma zan aure ka ba, idan sama da kasa za su hade! Kaji ni ko? Sai na maimaita? Ya matse ido, kwalla masu zafi suka yo waje da gudu, ya dan kada kai murya shke yace, kin xuba min dafi, kin xuba min dafi sakeena. Baki tunanin amana? Yasa hannu ya kamo yatsunta, ya kura wa zobensa ido, ya ciga, baki kallon zoben alkawarin mu? Me yasa kika mance da dimbin kalaman da kika sha gaya min? Wadanda suka jaddada imani na akan son da kike min? Ta kwace yatsunta a hankali ta zare xoben, ta jefa masa, ga tsiyarka nan, idan shi kake kallo a matsayin alkawari, ni ma cire min nawa ka bani. Yaci gaba da kallonta, kafin ya dauko zoben yace, kiyiwa Girman Allah ki maida zoben nan sakeena.... Bazan karba ba! Idan ma ka aje shi, zan jefa shi masai! Kuma nima dole ka ban nawa! Yace sai dai ki kashe ni, sannan ki zare shi, wannan din ma zan ciga da boye shi, har xuwa tym din zaki sami nutsuwa dakin auranmu. Ta kwada masa harara, sannan tayi wani dan murmushi na kaico, ta kauda fuska, y mika hannu ya kamo habarta, ta sa nata da karfi ta doke nasa, kafin tace, karka sake tabani, idan ba haka ba kuma sai na kurma maka ihun dan iska! Ta mike da sauri ta bar wajen, kai tsaye bayi ta shige, ta maida mukulli ta kulle. Yayin da Al- ameen ke cigaba da kiranta. Ya tashi ya tsaya kofar bayin yana fadin, ki fito ki saurare ni sakeena, ya kamata mu fuskanci juna, mu gane inda matsalar mu take. A zatona har duniya ta nade ba zaki taba juya min baya ba! Tana daga ciki ta amsa, bazan fito ba. Daman kasan inda dare yayi maka, yace ki tuna alkawari sakeena, don Allah karki bari ayi min dariya. Idan na rasaki zan iya rasa komai nawa, ki tausaya min sakeena, kar damuwa ta kasheni. Tace, kan ka akeji! Ni na gama magana da kai. Ko za'a kashe ni ba xan sauya ba, dama ka kama gabanka zai fiye maka alkhairi. Ya tsaya jim, shiru goshin sa jingine da kofar ya rasa inda zai tsoma ransa yaji dadi. A hankali ya soma karannto Innalillahi Wa inna ilaihir Rajiu'un. Ya fi 10mins tsaye. Sannan ya juyo da sauri ya fito yana share fuska da hankaci. Kawai arba yayi da su Abba zaune falon. Ya rage sauri ya nufi gunsu ya tsugunna, abba zan koma. Gab dayan su ido suka xuba masa, jim Abba yace, amma dai ba minna zaka nufa ba yanxu ko? Ya dan kada yace, kuma ka kwantar da hankalinka Insha Allahu Mama matar kace. Kar ma ka bata tym din wajen xuwa goben, kai tsaye ka wuce gida, ka gayawa Marafa ina tafe da kaina, muyi magana. Yace to, Abba na barku lfya. Ya mike ya fice suka raka shi da kallo. Ummma kam bata sami cewa komai ba, saboda tsabar tausayinsa. Yana fitowa Gambo direba ya balle murfin mota ya fito, ya tarbe shi ganin ogansa na ta share fuska, yaya jikin nata? Ya dube shi ido jajur yace ba sauki Gambo. Mu shiga mota, ka maidani gida. Yace yallabai ai dare yayi sosai, nayi zaton gidan gwaggo xamu kwana. Ya miko hannu yace bani keys, kai ka wuce gidan Gwaggon ka kwana! Ya dan sunkuyar da kai, yace yi hkr yallabai Allah ya sauke mu lfya. Shi tuni ya bude gidan gaba ya fada. Gambo ya xauna mazauninsa da sunan Allah ya murza mukulli yaja suka wuce, a tym din agogon motar yana nuna 09:45pm. A daren nan nake son ganin Dady na. Gambo yace Allah ya yarda mana, ita kuma Allah ya bata lfya. Ya kama kai ya runtse ido, ya jingina sosai da kujera yana fadin amin Gambo. Direba na ta tsula gudu cikin dare. Shi kuwa Al-ameen kurwarsa na can cikin tunanin baya. Itin tsantsan son da Mama ke masa, shi yake gani cikin idanuwansa, har xuwa ranar da ya xo sallama da ita a sch, kawai gambo ji yayi Al-ameen na sambatu, sosai kikace kina sona sakeena, dama yaudara ce? Me yasa sakeena? Me yasa? Hnkalin Gambo ya koma gunsa yayi kiransa sau uku, kafin yaji kiran. Ya xuba masa ido yayi da direba ke fadin, kayi hkr yallabai, yace sakeena ta yaudareni Gambo, ta xuba min dafin da xai wuya na sami maganinsa. Xan iya mutuwa Gambo, domin gaba daya na sallama kaina gareta. Ko kasan inda nake da mishkila ka gaya min in gyara? Gaba daya tausayin sa ya lullube gambo, ya kada kai da sauri, yace babu inda kake da mishkila Yallabai, sai dai ko ajizanci na dan adam. Ni kaina ban yarda sakeena bata sonka ba, watakila ciwo ne rudata yace, kai ma ka yarda bata da lfya ko? Amma kowa yace kalau take, ni nasan sakeena bazata ki ni haka kawai ba, zuciya na wasi-wasi. Gambo yace , kar ka damu Yallabai, Allah zai warware komai, sakeena zata zama matarka. Ya sauke numfashi mai karfi yace, wannan shine babban burina a duniya, komai Allah ya bani na gode masa, saura wannan burin ya rage min. Shima zaka sameshi Insha Allahu. Yayi dan shiru, sannan ya kada kai yace, laifi nane, rashin kasancewa ta kusa da sakeena, shi ya jawo shaidani ya shiga tsakanin mu. Lallai mata na da rauni Gambo, ba taba tunanin sakeena zata iya hango wani har ya rikita ta amince dukkan amanar da muka damka ma juna. Al'amarin na daure min kai, na rasa yadda xan fassara shi. Yace, haka ne yallabai, amma idan ka barwa Allah komi na tabbata xai maka zabin alkhairi. Ka sani ko wata jarabawa ce Ubangiji yake yi ma don ya gwada imanin ka. Kar ka damu Yallabai, Allah ba zai hana ka sakeena ba, idan har kayi imani shine mai hanawa da badawa. Ya sake jingina da kujera, ya runtse ido ka fadi gaskiyya Gambo, na gode. Bai sake tankaea ba haka kuma bai daina tunanin xuci ba, ma'ana sakeena bata daina xuwa cikin idanuwan sa dauke da lallausan murmushinta mai sanyaya masa rai, tana tura hularasa gaban goshi bakinta na fadin, so much! Shi ya sa baya aikin komai face ajiya xuciya. Gambo na jinsa tausayinsa nakara zama cikin ransa. Karfe daya dai-dai na dare motarsu na tsayuwa kofar gate din gidansu. Gambo yayi hon, nan da nan Mai gadi ya shaida hon din motar mami ne, ya taso a guje ya bude kofar, motar ta shige kai tsaye kofar shiga ya tsaya. Al-ameen ya fito, sannan ya wuce ma'ajiya motaci. Tun kafin ya kwankwasa, yaji ana kokarin budewa, don haka ya dakata hannayensa biyu cikin aljihu. Marafa ne da kansa ya bude kofar, suka zuba juna ido, daga bisani ne mami ta bayyana wajen har ta riga marafa magana, Al- ameen . Idanuwansa suka yi tam da kwalla, ta yi azama ta jawo shi ciki, daddynsa ya maida kofar ya rufe. Don me ka iyo daren nan Al-ameen? Sai kace babu inda zaka raba ka kwana! Ya zauna dabas! Ya kama hannaye biyu, Marafa ya xauna kusa shi. Ya rungumo kafadunsa, yace baka kyauta min ba Al-ameen, da ka dauko hanya cikin daren nan dan kuskure kadan za'asamu, shikenan ka ajwo mana tashin hankali, karfa ka manta, kai ke nan guda daya muke kallo zukatan mu na wankewa daga radadin rashin da. Ya dube shi ido jajur! Yayin da Mami itama ta xauna daya gefen suka sanya shi tsakiya. Yace, na kosa in ganka Dady, sakon Abba xan gaya maka, yace gobe yana nan tafe maganar aure na sakeena, kafin in koma yake so a daura shi. Mami tace, kun daidaita da sakeenar ne? Ya dan kada kai yace, sakeena ba warke ba Mami, hasalima bata gane ni ba, shiyasa tun farko nace a kaita asibiti, kowa yaki amincea da ni, ga shi nan kwakwalwarta ta tabu. Sakeena ta kasa ganeni Mami, ni kuma bazan fasa auran ta ba, domin shine babban buri na a duniya. Su abba sun goya min baya, kuma ku taimaka min buri na ya cika don girman Allah. Gaba daya ya kara daga musu hankali babu kamar Marafa da ko alama baya kaunar yaga dansa na kukan neman wani abu, shi yasa nan take ya ji ko ana ba maza ha mata, sai Al-ameen ya auri mama. Amma ita Mami bata an ta dosa ba, don haka tace. Al-ameen bania ron hankalin kanan, na ga alama baka yarda Sakeena lfy lau take ba.... Ku kuka gaya min ai Mami... Yanxun kuma ni na gaya maka lfya, kawai cin amanar ka tayi, tunda kaje bata saurare ka ba, kai ma ka manta da ita kawai, ka roki Allah ya musanya maka da mafi alkahiri. Bafa sakeena kadai ce ta yalwatu da dukkan abubuwan da kake so ba. Saboda haka ka kama kanka, ka nutsu ka gane cewa ko an daura auran, ba zaku zauna lfya ba, tunda idon ta ya bude, tana takamar tana da kyau, kowa na kallonta, kajini? Ya girgiza kai, idonsa xuru yana kallonta, tace au baka ji ni ba? Menene nufinka? Marafa ya amshe don Allah, don Annabi ki kyale shi, ba yace Uban dawaki na taf ba? Allah ya kaimu goben lfya, shi aure ai nufi ne na Allah. Yanun kaje ka kwanta mu saurari goben, kaji? Yace naji dady, don Allah ku tayni da addu'a sakeena kadai nake so. Yace na sani, addua kuwa kullum munayi, kayi alwala ka sami koda raka'a 2 ne kafin ka kwanta, na tabbata zaka sami nutsuwa ok? Ya amsa da kai ya dan bubbuga kafadarsa yace, yau dan Dady, Allah ya bamu alkhairi. Bai dai tanka ba, ya mike ya bar falon. Mami ta cire tagumi tace, sai Allah yayi wa yaron nan sakayya! Yadda tai masa haka Allah zai mata. In banda idon Al-ameen ya rufe a kanta, me zaici da ita? Yarinyar da gwaggo tace shagon saurayi take su raba dare suna.... Marafa ya katse ta, don son Annabi, ki bar wannan magana haba. Ki yi masa fatan alkkhairi kawai. Cikin bacin rai ta mike ta koma daki. BAKIN CIKI kamar ya kasheta. Shi kuwa Al-ameen yana can yana nafilfili kamar yadda dadinsa ya umarce shi. Da safe ya fito gaba daya ya zabge, kallo daya za kai masa ka tabbatar da hakan. Gaban mami ya fadi ta kwala wa Ladi kira ta zo a gigice. Tace, to hajiya. Ta juya da sauri ta fice. Mami ta dube shi tace, matso nan kusa da ni. Ya kara matsowa yace, ina kwana? Ta amsa tana shafar kansa. Ina dadina, bai tashi bane? Tace, kwana yayi baiyi barci ba, sai bayan sallahr asuba barcin ya sace shi. Tana rufe baki ladi na sallama da tiran abinci ta dire gabansu. Tace ga shi hajiya dr, Iya tace in gaida ka, yanxun xata shigo. Yace ina amsawa. Ta fita ta bar dakin. Mami ta jawo tiren ta hada masu shayi ta mika masa, ungo nan dan iya. Daute ka sha kaji karfin jikinka. Ya sanya kofi a baki ya kurba kadan. Wlh daci mami ba xan iya sha ba. Tace don me? Ka cigaba da sha za kaji bakin ya washe. Ga kuma farfesun, bude bakin in xuba maka. Ya bude 'yar kular ta debo a cokali ta mika masa, karbi ka gani mana. Ya bude bakin ta xuba masa tace, yauwa ko kai fah? Yanxun idan Abba ya zo maganar auranta kankama, haka za'a ga ango a rame? Dadi ya lullubeshi yayi wani lallausan murmushi yace, mami na rame ko? Kai baka ji ajikin ka ba? Bana so kayi angwanci a rame, don haka ma za ka kama abinci ka ci. Nan da nan ta ga ya gyara zama ya hau shan farfesu yana kurban shayi, kinsan wani abu Mami? Sai ka fadi, shayin nan ya daian min daci. To yi sauri ka shannye. Ya kuraba ya sake kallonta, yanxu Mami idan aka daura auran anan xan barta? Eh mana, ko ba xan iya kula da ita bane? Yayi dan murmushi, a'a mami na, amma ni na fison mu tafi tare can, kin ga kafin mu dawo ta mance da sakaran Yaron da ya hure mata kunne. Ko ma muyi xaman mu can tana karatunta ina aiki na, ko kuwa? Ta dafa kafadarsa, gaskiyya ne, ina goyan bayanka, sai dai in ta haihu ka kawo min maigida ko kishiya. Ya kyalkyale da dariya, kwalla suka cika idanuwan mami ta bisi da kallo tana gyada kai. Yayi gyatsa kafin yace, ina son twins mami, ko? Sai dai an mai son su baya samun su? Da sauki ya katse ta, no duk canfi ne Mami, ni dai ina so kuma Allah xai bani ameer da ameera. Tayi 'yar dariya tace, duk naji, idan ma 'yan hudu ne Allah ya kawo masu albarka, yanxun tunda ka koshi, kaje ka yi wanka kafin dadin ka ya tashi. Xai ji dadi idan ya ga ango shar! Yace haka ne mamina. Ina xuwa, ya tashi da sauri ya fice. Mami ta ta tallafe kunci ta ce nikam tawa.... Nikam tawa ta sameni, ni Ya su, Allah ka duba mana. A bakin kofa suka hadu da iya suka gaisa. Sannan ya wuce bangarens, ya fada bayi ya sheko wanka, ya kimtsa jikinsa da wani lafiyayyen farin boyel mai taushin gaske. Ya fesa turare, ya dawo dakin Mami, ita ma wanka yi ta sauya kaya. Ta dube shi tana fara'a tace, haba yanxu na ga daidai. Ina ganin ma dai daga yau aka angwancin nan. Ya xauna kusa da ita yana dariya. Tsokanata kike sonyi Mami, me kika gani yanxun? Sai ma ranar kenan. Ki gane Mamina, ranar ba zaki shaida ni ba. Ta ware ido tana 'yar dariya zai hana? Sai dai ko amarya ta kasa shaida kai, amma ina mami zata mance da dan tilon dan ta. Dadi ya kara lullube shi, ya rungumo ta yana fadin Allah sarki mamina, Allah ya bar min ke tare da Dady na. Dadin ne kansa ya amsa, amin amin. Ya kara sa shigowa suna masuayar fara'a. Dadyna ya tashi lfya? Na tashi lfy Doktna. Suka gaishe shi cikin annushuwa, duk da bai san sirrin ba, xuciyarsa tayi masa dadi. Don haka ya xauna aka kawo masa abincinsa su ka fara ci tare suna kara kwantar masa da hankalin. Sosai kuwa hankalinsa ya kwanta, yana ganin tamkar an daura auransa da mama, tunda yana da magoya baya ta kowanne bangare BAKIN CIKI 2***9 Abba bai ga ta zama ba, 7:30 suka kama hanyar minna shida Alh. Adamu tare da Umma, domin ita tana bukatar ganin likita. Saboda ha ane aka tafi da Inna saude don ta rinka taimaka mata. Basu iske abdulkareem a gida ba, ya riga ya fita aiki. Hankalin Aunty Rabi ya dugunxuma nan da nan ta dauki waya ta kita wayar ofis dince, Yaya abdul yaji kamar zai mutu, saboda tsabar bacin rai, amma ba yadda zaiyi ya fito saboda tsarin aiki irin na banki. Daga nana aunty amina ta kira, itama ta shaida mata, kafin ayi haka labari ya gauraye ko'ina. Asibiti suka fara aje Umma tare da inna saude. Aunty Rabi itace jagora domin asibitin da banki ke da reg da su ne. Daga can da Abba da alh. Adamu suka dumfari gidan marafa. Da ganin su, gaban Mami ya fadi, fara'ar karfin hali kawai takeyi. Bayan su natsu a falo. Abba ya tambayi marafa? Tace, ai kuwa yayi sammako ya tafi Lafai, don shaidawa mutannan gida maganar daurin auren, shi kuwa ango na san ya ma kai zariya yanxun Insha Allahu. Kasan a can yawancin abokansa suke saboda can yayi krt. Ina fatan lfya? Ya sauke numfashi idanuwan sa suka kara juyewa yace, babu lfya Hjya, Ki Innalillahi Wa inna ilaihir raji'un! Alh. Adamu ya gaya mata. Ya gayara xama, yace hajiya wannnan al'amari babu dadin ji, a takaice dai sakeena ta gudu tun jiya har yanxu ba mu san inda take ba. Tsaye ta mike dafe da kirji, ta yi me? Ta kame a hakan bata iya kara komai ba. Abba yace, nayi iya yina Hajiya, amma mama ta nuna min ta karfina, hanyar da zabarwa kanta ta wuce da sani nan. Kuyi hkr hajiya, ni ban ma san da kalmar da xan gaya maku ba. Ta koma a hankali ta zauna cikin kasala tace, ai shikenan, duk abinda Allah yayi daidai ne, mu mun hkr, Allah ya musanya wa Al- ameen da mafi alkhairi, sukayi ji. Shiru kafin Abba yace mu na nan garin nasan har Alhji ya dawo. Itama hajiya tana nan na kawo ta asibiti tun jiya ciwon ta ya tashi abin sai yadda Allah yayi. Ta maida tagumi tace, dole Umma tayi ciwo, ubangiji Allah ya bata sauki ya kuma shirya mana zuri'a, suka amsa amin. Suka mike sukayi mata sallama suka tafi. Hawaye suka kubcewa mami, hannunta a kunci tace, ta faru ta kare kowa sai ya hkr! Tab, wannan yarinya ta daure min kai. Allah kayiwa Al-ameen sakayya! Iya da ladi suka jiyo hajiya na sambatu, suka fito suka taushi xuciyarta, babu bata tym ta sa driver ya kaita Lafai. Gado aka ba Umma, saboda yanayin jikin nata, yana bukatar kulawar likita sosai domin jininta ya hau, har ya haye yadda ko alama ba 'a so. Anan su abba suka ci gaba da zama har karfe 4. Yaya abdulkrm ya samu ya baro ofis. Kai tsayr asibitin ya nufa a sukwane. Da ka dube shi, kasan ransa a nbace yake, yana ganin Umma kuma al'amarin ya kara gigita shi. Ya dubi Abba ido jajur! Yace, yanxun wane mataki aka dauka? Abba yace, ni na sallama mama, tunda ta iya toazarta ni haka. Na kuma je gidan su Al-ameen, matslar kawai ban same su bam duk sun tafi raba goron gayyata, sai hajiya na samu shaida mata. Alh. Adamu yace amma ni ina ganin zai fi kyau abada cigiyar a gidajen Radio da Tv. Abba ya amshe, da kudin wa? Saceta akayi? Ba xan kara asara ba, yadda ta sa kafa ta bar gidana, ta tozarta ni, ta wulaknata ni, ta nuna min ban isa da ita ba. Wlh ni ma na hkr da ita. Ba xan yi mata baki ba, dan ko bance wani abu, tabbas ita da kanta ta kai kanta mkrntar koyo hankali. Za ku ce na gaya maku. Taje duniya cem ta ishi kowa riga da wando har da mayafin yafawa. Ya abdulkrm ya numfasa, yace ta yiwa knata, Allah ya shiryar da ita, yasa ta gane, suka amsa da amin. Jimawa kadan ya ba Aunty Rabi mukullin mota ta wuce dauko su Ameera daga sch. Kai tsaye ta wuce da su gida. Ta kama hidimar shirya abinci. Tana gamawa ta kwashe gaba daya da yaran suka koma asibiti. Ta iske kofar dkin da Umma take dankam! Da Jam'a, ashe bayan tafiyarta kadan su ya Abdul kadir da abdulrhmn suka iso. Can kuma sai ga dady da mami. Al-ameen ne kadai bai dawo ba. Duk tabisu ta gaida su. Dady kam yama rasa yadda xai fassara al'amarin Allah ya sa bai riga ya yayyada xancen ba ko 'ina, iyakar sa cikin babban gidansu. Allah ya kawo Mami tayi masa birki. Shi kansa yadda yakeji a tym din, idan xa'a gwada jininsa dole ace ya hau, amma daya iso ya dubi halin da iyayen Mama ke ciki sai yaga ashe shi nafila ne, tashin hankali na inda yake. Shi yasa ya nutsu sukayi magana ta fahimta da abba...... Ya Dubi halin da Iyayen Mama ke ciki sai ya ga ashe shi nafila ne, tashin hankali na inda yake. Shi yasa ya nutsu sukayi magana ta fahimta da Abba. Suka dauki komai suka barwa Allah tare da rokon Abba daya amince ya bawa mama wanda ta sake xaba. Abba bai ce komai ba anan. Don baya jin zai iya ba Danliti 'yarsa su hada zuri'a da mutuncin sa da komai a gari. Yanxun tunaninsu dan gogan. Yaya al'amarain zai kasance? Bayan abba ya kauda masa duk wani shakku, ya bashi tabbacin babu wani face shi, shi ya kara karfafa masa gwiuwa har ya sami kafar tafiya gayyato abokan taya shi murnar angwanci? Wannan amsa sai wanda ya gani da idanuwansa. Gab! Da kiran sallah magriba duk suka bar asibitin, aka bar Inna saude ita kadai tare da Umman, wacce har yanxun barci takeyi, domin allurar da akayi mata mai karfi ce sosai, saboda ana son ta samu hutu kwarai da gaske. Su dady na isa gida, kamar tare suke da Al-ameen. Bai fhimci komai a fuskokinsu ba, don basu yarda yaga sauyi ba ya baje a kujera yace, wsh! Ai fah an fara kenanm kinji yadda naga ji Mami? Ta danyi murmushi tace, dan Iya kena, to abinda ya kamata ka hanzarta yin wanke ne, don gab ake da kiran magriba. Haka za'ayi Mami na, dadi ya aka baro mutanan Lafai? Ina fatan zaka jaddada musu su taso da wuri? Wannan ai dole ne, kama san kawunka ba shi da wasa. Yana ta far'a gaskiyya ne ni ma frnds dina ne ce masu kai tsaye su wuce Fandagori, ai gidan Uban dawaki ba boyayye bane, suna tambaya za'a nunna masu. Dadi yace, kayi daidai, yanxun tashi ka shiga wankan nnima shi xanyi aga wanda xai riga fitowa cin abinci. Ya mike xumbur! Yana dariya ni ne xan riga Dadi, to shikenan, mami ki na ji ko? Idan kuma na riga shi bulala tara, tace ni kuma xan cikashe dayar, su zama goma. Na yada. Bai jira komai ba ya kwasa da gudu, ya shige bangarensa. Mami ta bishi da kallo. Dadi ya sa hannu ya cire mata tagumi yace, ke ma tashi ki daina damuwa. Ta sauke numfashi, amma ba tace komai ba, ta yunkura ya taimaka mata ta tashi suka wuce. Kowa ya shige dakinsa. Al- ameen ya fara fitowa falon, ya nufi gefen tebur inda ya hangi ladi na jera abinci. Ya isa wajen yana fadin, angaida Maman abinci. Tayi dan murmushi. Tace ni ma na gaida dr. Yace na kusa dina cin abincinki Ladi, ina ganin daga yau nai masa bye bye. Tayi 'yar dariya, to aci gaba ne dr. Amma ina ganin akwai gobe kafin amaryar ta iso ko? Ya gyada kai, yana dan murmushi, wa ya gaya miki xan dawo ni kadai? Tana 'yar dariya ta amsa, au can xaka zauna? Kafata, kafarta, zata sake magana, ya dakatar da ita, shisshhh... Tayi tsit! Tana kallon sa yana boyewa bayan kujeru. Dadi ya fito mami na biye dashi, madalla, kinga bulala ta hau kan danki, kira shi na tsatstsala masa. Tace, yanxunn nan ma xaka ganshi a sukwane, kwai ganin sa sukayi yana gyara xaman kujera xai xauna. Gaba daya suka kwashe da dariya. Ladi na tasya su sannan ta bar wajen. Dady yace, gaskiyya ba haka ake yi ba, ai dai sai ya bari mu fito tare ko mami? Dariyar Al-ameen ta karu, yayin da Mami ke fadun, kaji wayau! Ta xuba wa kowa abinci yaci, suka kashi suna ta biye masa, suna labarin biki. Bukatarsu ya cika cikinsa, kuma ya ci sosai. Bayan su kammala Dady ne ya fara barin tebur din Al-ameen ya byi shi xasu yi wata magana, nan da nan ya mike ya bi bayansa. Mami ta kwala wa Ladi kira tace ta gyara kan tebur din, ita ma kai tsaye ta wuce, ta iske su xaune bisa kafet. Dayan gefen ta xauna, suka sanya shi tsakiya. Dadi yayi gyarn murya yace, wasu 'yan tamnbayoyi xan yi maka Al- ameen, ina fatan xaka nutsu ka bani amsa shakikiya. Da farko dai shin Al-ameen wa yake badawa, wa yake hanawa? Yace, Allah. To idan ya baka, sannan ya dawo ya karba, me yakamata kayi? Ya amsa, nayi masa gdya, watakila ya musanya min da alkhairi, ko Mami? Tace, Gaskiyya ne! Dadi yace, Madalla, abinda nake ka sanya wa ranka kenan. Idan har ka tabbata tsakanin ka da Allah ka amsa min tambayoyi na. Ka kuma san imani shine cikar dan musulmi, ko ba haka ba? A salube yace, sosai dady. Yauwa, to kayi hkr maganar da xan gaya maka. Nasan ka na son sakeena, sannan kayi imani Allah ne ya hadu ku ya sanya maka sonta, a da mu na ganin kamar itama tana sonka, kamar yarda kake sonta. Amma yanxun ta nuna yaudara ce kawai, saboda haka ka hkr da ita. Kamar yadda kace Allah xai musanya maka alkhairi. Ya dubi Mami, ya juya ya dube shi, Dady ban fahimce ka ba, ai sakeena na so na, xuga ce kawai kuma na tabbata da xarar aka daura auranmu, ni masan yadda xan da hankalinta gareni. Dady ya ka kada kai, maganar ka dawo da hankalinta gareka duk ya kau. Al- ameen sakeena ta gudu tun jiya babu wanda yasan inda take saboda haka nake rokonka arziki da ka kwantar da hankalinka, kayi imani da furucin da kayi daxu, Allah ba xai bari kasha wuya ba. Ya Dubi Mami fuska kunshe da tashin hakali yace mami ban fahimci ta gudu ba? Me dady yake nufi? Tace iyakar kiyayya sakeena ta nuna maka, tunda ta xabi ta dauki akwatinta ta bar gidan iyayen ta ada ace ta aure ka. Ta xabi ta ci mutuncin mahaifanta akan auranka. Wulakanci ya kai makura Al-ameen, ya kamata ka nuna mana ka haihu dan halas, kace kai ma ka hkr da sakeena. Ya xura mata ido, du sun kadu, mami kina nufin an fasa daura auran gobe? Tace abinda Abbanta yayi sammakon xuwa shaida mana kenan, ia ske ba ku nan kun riga kun tafi gayyata, ni na bi dadynka Lafai na dakatar da shi. Kai ma ina so ka dauki waya ka kira abokin ka dr. Lawal ka gaya masa an fasa, don ya gaya wa saura kar su yi wahala. Ya kada kai yace, baxan iya ba mami, na rantse da Allah sakeena na so na, ina xata gudu taje? Ban yarda ba mami sace min ita kayi, don a raba mu.... Rufe min baki! Mami ta daka masa tasawa mai karfi, daga nan ta balle da masifa, kar ka yarda Al-ameen, amma ina son ka sani, babu maganar auranka gobe da sakeena! Idan kuma ka sake tak a wurin nan sai na tsinka mata mari, don ka gane ba wasa muke yi da kai ba! Yaya ana rarrashinka ana numaka gaskiyyar magana ka naso ka akrya ta mu? Sakeenar banxa sakeenan wofi? Ita kadaice mace a duniya? In sake jin xancen ta abakin ka sai na saba maka! Ku ma ka sani, daga daren yau ka fara shiri gobe xuwa jibi xaka koma sch! Kaji ko baka ji ni ba? Ya aje kai kasa. Dadi yasa hannu ya dago fuskarsa. Tuni hawaye suka wanke masa kunci, shi ya fara fadin, me yasa zata gudu ta barni Dady? Ko baxan hkr da ita ba, ai bai kamata ta gudu ba, hatsari ne babba ga diya mace, wa ya san hannu da take yanxun? Mami tayi caraf? Ta cafke, tana hannun wanda take so. Dama ka daina bata hawayenka a banxa. Sannan kama kunnunwanka da kyau ka ji ni, tun daga ranar da ka daina jin muryar sakeena awaya ta daina sonka, ta mance da kai, ta share ka a rayuwarta. Saboda kin da ta ke ma. Sakeena ta diro daga mota, da abin ya zo da karar kwana da yanxun an kusa mata sadakar arba'in. Sakeena tayi kwana da kwanaki tana yajin cin abinci, tayi ta suma ana mata karin ruwa a asibiti. Kai saboda kiyayyar ka, gabada dabi'iun sakeena suka sauya, bata gannin kowa da daraja, nballe ta saurari fada, da iayeynta da 'yanuwanta ke mata ba dare ba rana. A karshe sakeena ta aikata abinda yafi komi muni akan diya mace. Duk saboda bata sonka, ashe ya kamata ka hankalta kasan halin da kake ciki, don kai ba yaro bane, kuma ba alfahari ba, ilimi muhammadiya da boko sai dai a yiwa wani gori ba dai kai ba Al-ameen, duk kuma wanda yayi imani da kaddara, baya tabewa Al-ameen. Ka maida al-amarin ka wajen Allah shi xai maka magani. Ya dube su daidai tamkar karamin yaro, murya na rawa yace, gaskiyya ne Mami, duk abinda ki ka fadi na yarda, kuma na hkr da sakeena, sai dai son ta ba xan iya cire shi cikin raina ba, saboda ba ni na aje shi ba, kuyi hkr, ku yafe ni, idan furuncin danayi ya muku xafi, sannan ina rokon ku don Allah da son Manxonsa, kar ku kullaci sakeena cikin xukatan ku akan wannan maganar. Wlh har yanxu ina ji ajikna sakeenna tawace. Dady ya rungumo kafadunsa yace, shikenan,ya Isa, munji rokonka mun amsa. Zamu cigaba da taya ka addu'. Yanxun abinda nake sonka da shi shine, ka kira Dr. Lawal ka gaya masa, don su sani. Sai dai in baka lambobin ka kira shi dady, bakina ba xai iya furta mummunan labarin nan ba. Ya mike ya jao durowar dadi ya dauki biro da paper ya rubuta ya bashi, ya mike xai fice, ya kusan kaiwa kofa mamy ta kira shi, ya juyo tace kayi nafilfilu cikn dare. Allah zai saurareka, ya nisa kafin yace xanyi mami. Ya sa kai ya fice. Mami ta dubi dady ta hadiye hawayenta, tace gobe in Allah ya kaimu xan koma Lafai wajen baba liman in samo masa ruwan addu'a ya sha ya sami sanyi cikin ransa. Yace hakan ma yayi, Allah ya sa mu dace. Tace amin. Ta jawo wa dady kan waya ya nemi Dr. Lawal, ya sanar masa. Yace an fasa? Subhanallahi? Wannan abu baiyi dadi ba. Don girman Allah dady a samu a daidaita, wlh Al- ameen yana son yarinyar nan ba kadan ba. Ya ce ba sai ka rantse ba Lawal, ni kaina nasan hakan, amma fadan da ya fi karfinka dole ka maida shi wasa. Mu nan muna ta addu'a Allah ya zaba mafi alkhairi. Ya numfasa, yace amin. Ina Dr. Yake? Ai sai da ka neme shi xuwa gobe, yanxun kam babu sukuni yana dakinsa. Yayi dan jim, kafin yace Allah shi kyauta, amma ayi kokari Dadi idan xai yuwu a sasanta. Ba komai mun gode a gaida Iyali. Zasuji, ya aje wayar tare da tsananin mamakin wannan abu? Me ya faru haka da xafi? Haka ya kwana da tambayar kansa, don babu alamar wata mishkila a tattare da soyayyar abokinsa da sakeena, ko daya zo sanar da xancen auran ma babu alamat akwai matsala babba. Labarin barci dai babu shi a wajen Al- ameen kuma xuciyarsa bata daina karyata masa xancan ba. Ko alama ta ki amsar sakon, saboda tsabar shakkun da yake ciki, wai sakeena taci amanarsa? Har 8am yana kan sallaya, ba don wai yana sallah ba, a'a kasala ce ta hana masa tashi. Mami tayi sallama ta shigo da tiran kayan karin safe. Ya xubo mata ido. Mami tayi sallama ta shigo da tiran abinci, ya xubo mata ido, ta aje a agbnsa, ta xauna gefe, sannan yace, ina kwana mami? Lfya lau, ina fatan ba ka tsananta wa kan tunani ba? Ya kada kai, ya xanyi mami? Kin san ba yin kaina bane? Ta dafa shi a sanyaye, kllm ina kara gaya maka Al-ameen, kai kadai ne garemu, kuma ka zama tamkar dubu, ba gare mu kadai ba, gabadaya al'umma za su so rayuwarka ta daure cikin fciki da walwala, saboda muhimmancinta, ina so ka san wani abu yau. Wlh na yi maka rantsuwar da ba kaffara da rayuwarka ta salwanta, gara ni in mutu, don na..... Ya rufe bakinta, a hankali, idanuwansa taf, da hawaye yace, kiyi shiru mamina! Da ni dake zamu rayu da yardar Allah cikin farinciki da kwanciyar hankali. Har ga Allah na hkra da sakeena mami, kawai ciwon fitar son ta ke azabtar da ni. Ka kwantar da hankalinki mamina, a hankali zaki gan ni yadda kike so. Tayi dan murmushi tace, Allah yayi ma albarka! Da sauri ya kwanta a kafadarta yana fadin amin mamina. Zauna da kyau na hada maka brkfst. Kaga masa na sa iya ta shirya maka da sassafe, na san kana so kuma kana kewarta, don ba'a samu a Rasha. Ya bita da kallo dauke da tausayi. Yace nagode mamina, amma tare xamu ci ko? Ta jawo fileta tana fadi ah! Me zai hana? Bari ka gani. Ta loda waina a plate tana xuba miya ya ware ido, yace mami kin cika abincin nan! Ita ma ta ware idon tace injiwa? Ni da kaine fa? Sa hannu ka gani ko asa man shanu? Ya kada kai, a'a kinsa banso kayan karni. Ka bar dadi yaro. Yayi 'yar dariya yace Allah ko? Ta tura masa a baki tace, haba ai ba sai na fadi ba. Dady yai sallama dakin ya karaso da sauri yana cewa iye! Masa kuke ci kuka nuna min 'yan ubanci? Gaskiya ba ha akeyi ba, ai sai ku kira ni ko? Ya tambaya yana kallon al-ameen cikin ido. Ya gayara masa wwuri, yace laifin mami ne, xauna abinka Dadyna. Ya xauna yasa hannu ciki, yace ai mami akwai rowa, Allah dai ya tsaga da rabona. Suna dariya ta bashi amsa, ka san kuwa da na kawai, na aka yi ma. Kaji ko? Tafi son ka akaina. Yayi wuf ya rike hannu da yake kokarin kai loma yace, ba xaka ci ba sai ka fadi! Gaya min, mami ta hau dariya shima ita yake yi. Dady na ga dai da ta rikice kanka. Tace babu wani sai kai, sannan aka sameni, ko ba haka bane mami? Tace ni xaka tambaya? Dady ya karbe yanki wainar daga hannunsa ya tura masa baki, yace cinye dana, ka bani amsa daidai. Bai gama cinyewa ba ya dauko cinyar kaza ya tura msa, ka ra da wannan kayi brush! Duk suka sa dariya, ganin al-ameen na neman kwarewa, kan kace kwabo sun yaudari Al-ameen ya cinye wainar da mami ta zo da ita, domin dai shi suka yi ta turawa da wasa da dariya ya take cikinsa. Bayan sun kare, mami ta dube shi tace yanxun ka tashi ka shiga wanka ka kimtsa, muje asibiti ka gaida Umma.... Umma? Me ya sameta? Tashin hankali ya sa ta sami hawan jini tuntuni, maganar jiya kuma ta kara birkita ta jininta yayi mugun hawa. Tana nan asibitin sun bata gado. Jiyan abba ya taho da ita. Ya marairaice yace, Umma na asibiti tun jiya baku gaya min ba? Ban dadin hakan ba, dady yace kayi hrk, ganin kai ma baka da sukuni ya sa muka kyaleka, kaji da guda 1. Ya mike yace ba sai nayi wanka ba, yanxun xan tafi, idan na dawo nayi, bai saurara ba ya wuce ya jawo dirowa ya dauko key ya fice. Mami ta biyo shi tace Al-ameen, ya tsaya cak! yana dubanta, ta matsi sosai ta dafa shi, ka tafi a hankali, idan kaje kace ina gaishe ta, ni ma xan biyo in na dawo daga Lafai, ya dan lumshi ido, ya bude yace xan kula mami, amma me xaki je yi Lafai? Tace uzurina xai kaini. Allah ya kiyaye hanya, ta amsa amin. Ya daga kai dubi dady dake tsaye yace, sai na dawo dady, to ina jin ma xan sameka asibitin. Yace shikenan sai kazo. Ya juya yayi waje, su iya na kokarin fitowa su gaisa. Amma ina saurin da yakeyi, ya hana su su same shi falon, tuni ya kai ma'ajiyar motocin, ya murza ya bar gidan. Umma na xaune an jera mata filo, ruwan lipton kawai ta iya kurba, ya xuna cikinta. Likitan ne yace ta dan jingina kadan ta huta. Duk 'ya'yan sun kewayeta, abba na xaune gabanta bisa kujera. Gaba daya tausar xuciyarta suke yi don ta fidda abin a aranta. Sallamar al-ameen cikin dakin ita ta dauki hankalin kowa, suka amsa kona masa duban tausayi, ganin yadda ya xabge kamar mai ciwo, wai don ma su mami na yin iya kokarinsa akansa. Ya bisu daidai sukayi musabaha, sannan ya tsugguna gaban Abba suka gaisa. Tuni ganinsa ya sa hawayen Umma suka tsinke, yayi shiru a tsugunne. Abba ya dafa shi, yace sai ka dawo ka sami labari maras dadi? To ina so ka kwantar da hankalinka kayi imani da kaddara, ka sani yau da ace mama na da 'yar uwa xan baka ita, don in nuna maka iya kaunar da muke maka. Mama ta zabi ta wulakanta mu, shi yasa na ke son kowa ya cireta a ransa, mu manta da ita mu kyaleta duniya ta hora ta. Kayi hkr kaji? Ya goge kwalla yace naji abba, kuma nagode akan iya kokarin da kukayi min, amma abba ina rokon ka, don girman Allah ku ya fe mata, sannan ku sanya mata albarka, a auran da xatayi. Duk sukayi shiru, kowa ya xuba masa ido. Tausayin sa na ratsa su, umma ta goge kwalla. Tace Mama ba abar tausayi bace Al- ameen, don haka ka daina rokon ayi mata afuwa laifin data aikata. Ya kata matsowa gaban gadon yace, ba haka bane Umma, ki san sharrin shaidan, sannan xuciya bata da kashi, ba 'a son ran mama zata aikiata wannan abin ba, xuciya ce ta saka mata, na tabbata duk ranar da ta nutsu tayi tunani xata gane lallai bata kyauta ba. Don Allah Umma ko ina nan ko ba nan, idan Mama ta dawo ku amshe ta hannu 2, ku samata albarka. Insha Allahu shaidanin daya rinjaye xuciyarta, xai kyaleta, ta dawo diya ta gari kamar yadda take da. Abba ya kara dafa shi, yace idonka ya riga ya rufe a son mama, shi ya sa baka kallon girman laifin da ta aikata. Ya juya ya dube shi, ba haka bane Abba nasan ina son mama kuma har na mutu ba xan daina son ta ba, amma ku yafe mata, don rayuwar ta, tayi kyau nan gaba, ba farin cikin mu bane ace mama ta lalace tabi duniya, tunda gaba dayan mu nan, muna son ta. Kun yafe mata ko Umma? Tace kayi hkr Al- ameen ba xan iya cewa komai ba tukunna, ya abdulqadeer yace, ko mu bamu goyi bayan su Umma suyi afuwa gareta ba, har sai ta sauya zabin da tayi da. Tunda tace ba kai ba, to ka kawo wani dan mutunci tamkar kai, amma ba Dan liti ba. Wanna itace shawarar da muka yanke. Yana rufe baki dadi ya turo kofar ya shigo tare da gaishe-gaishe. Ya dubi al-ameen yace, dr na jiranka. Da mamai ya dube shi, dr. Lawal? Yaushe ya zo? Bai dade ba, muna shirin fitowa, sai gashi shine nace ya xauna xan biyo na gaya maka. Ya mike yayi sallama da su ya bar asibitin. Bai sami mami ba, don itama driver ya wuce da ita lfya. Dr. Lawal na babban falon gidansu, ladi sun adana shi da kayan kusa da baka, amma da ka dube shu kasan baya cikin sukuni. Yana shigowa ya mike da sauri ya tarbe shi suka kama juna. Dr. Lafai! Yace banyi xanton xaka xo ba. Dole na xo, wannnan mummanan labari ya hanani barci jiya. Yayi dan yake, kai dai bari, mu xauna aboki na. Suka zauna kujera daya, dr lawal yace, me yayi zafi likita? Idanuwansa suka kada yace, bansan me ke faruwa ba dr sama da sati 4 ina can na daina jin wayar sakeena, aka ce min bata da lfya ne, dalilin da yasa na dawo kenan don hankalina yaki kwanciya ita kawai nake son gani. Ina xuwa na iske labari ya sha bambam, wai sakeena ta sami wani ya hure mata kunne, har ta mance da manyan alkawuran da ta daukat min. Kowa yayi iya kokarinsa wajen nuna mata gaskiyya, amma sam tace ba san wannan ba. Abban ta kuwa ya sha alwashin ni da ta fara kawowa akayi mana baiko, ya sani ba xai daura mata aure da kowa ba, face ni don haka yace ba xan koma sai an daura auran. So da kaunar da nakewa sakeena yasa bana tunanin komai Illa xumudin a daura mana auran, shi yasa koda naje jiya bana nuna maka komai ba.a xato na bai kamata in tona kwanne sirri na sakeena ba, do kar a zage ta matsayin maci amana, ina ganin kamar idan muka kebe matsayin miji da mata, xan iya rinjayar ta. Son da take take min ya sake dawowa xuciyarta. Ashe duk abin da nake zato ya wuce nan dr.lawal kawai na dawo jiyan su dady ke gaya min sakeena ta gudu cikin dare ba a san inda take ba. Al-ameen ya jingina da kujera ya runtse ido sai hawaye shar... Na malala, hankalin dr. Lawal ya kara tashim ya xura masa ido jim sannan ya sauke numfashi ya dafa shi, yace, kana cikin tashin hankali aboki na amma Allah yace duk inda tsanani yakem to tabbas da akwai sauki. Pls ka zama jarumi a cikin jarabawar nan, ka bari hkr ya xama sanadin samun saukin tashin hankalin nan. Ya bude ido taf da kwalla, yace inason sakeena Dr. Kai kasan hakan, yace kwarai da na sani kuma xato na itama tana tsananin sonka. Ya matso shi sosai yace haka ne, wlh sakeena tana sona, to me yasa ta kini tym 1? Yace mata kenan Dr. Lafai. Balle sakeenna na da kyau da xata iya wasa da hankalin kowane da namiji. Watakila kuma wancan yafi ka duk abubuwan da take bukta. Dan wani minister ne a abja? Yace ban nemi sani ba, a yau ne nake jin sunansa bakin yaanta wai shi Danliti, danliti? Daga jin sunan kasan ba wani bane. Da sauri ya amsa ai kuwa wani ne.... (Hahaha Allah sarki lazy Dr.) tunda ya sace min sakeena. Ko da kuwa kwara masai yake yi. Inda ace xan gan shi xan iya durkuwa gwiuwa 2 in roke shi, ya bar min sakeena ta. Wlh itace rayuwata dr. Ya kada kai yace, ka daina fadar haka Dr. Lafao kar fa ka mance wani hani ga Allah baiwa ne, xa iya kasancewa sakeena kyan dan miciji gareta.... Ya dakatar da shi ta hanyar daga masa hannu.... Yace gaya min kowace kalma dr. Amma kar ka aibata min sakeena, ba xan taba ganin farinka ba. Ya xura masa ido, kunshe da mamaki, kafin yace, ba nufi nake nan ba aboki na, ina so ka gane cewar bakomai da kake bane yake kasancewa alkhairi a gareka, shi ya sa kullum ake son bawa ya roki alkhairi wajen Allah. Yace sakeen alkhairi ce gareni, tuni mafarkai na suke nuna min hakan, har xuwa yanxun kuma jiki na yana bani sakeena tawa ce, mishkila aka samu wani wurin, bana so musu da su Dady ne kawai, shi ya sa nake nuna musu na hkr da ita. Yace to idan baka hkr ba, yaya xakayi yi? Tunda batayi da kai? Babu abinda BAKIN CIKI 2***10 Amma nan da iya shkrun da xanyia duniya ba xan daina son ta ba har na koma Ubangiji. Ya xura masa ido, yace Al- ameen kar ka manta akwai gagaruminn aiki gabanka wanda kowa ya xura ido don ganin rawar da xaka taka, kasancewar kai kadai ake tunanin xaka iya taka ta kuma mutanenan arewa suna jiran daya tamakar dubu ya dawo masu da abin alafahrin a duniya baki daya. Ina ka sami nutsiwa ka fuskanci abinda ke gabanka ka tare da jadda imani a cikin ranka, lallai Allah xai iya baka wata. Ina fatan xuwa na ba xai xama abnxa ba ba, kuma addu'ar duk masoyanka a zariya ba zata fadi kasa banxa ba. Kowa yace Allah ya musanya maka da lakhairi, na tabbata Allah xai duba ya kawo sauyi na fadi daidai? Ya numfasa yace ka fadi daidai abokina na, na gode ma kowa bisa addu'ar da suka yi min. Xan koma rasha da yardar Allah cikin yardarsa xan dage na fidda kowa kunya. Sai dai abinda nake so ka sani har in mutu ina son sakeena. Yace tuni na sani, sannan ina da ilimin xuciya daya gareka, duk abinda Allah ya xuba cikin ta, babu me iya dauke shi. Ya koma ya jingina da kujrea, rungume da hannayensa, ya dan numfasa ya kada kai, dr. Lawal ya bubbuga kafadarsa ya sake fadin, ka manta kawai abokina, ya wuce, ya bishi da kallo kawai baice komai ba su dade tare. Dr. Lawal na kara kwantar masa da hanakili tare da nuna masa mahimmancinsa ga al- aumma. Bayan azahar suke asibiti ya gaida Umma, daga can ya wuce zariya, shi kuwa Al- ameen gida ya dawo, don shima ba ya son yana ganin Umma kwance tausayinta yana kara karya masa xuciya. Ya rinka jin kamar su abba ba xa su yafe wa sakeena ba. Wannan shine babban tashin hankalin sa. La'asar ta kawo jiki yana xaune shi kadai bisa gadonsa, tym-tym ya kan dauki hoton da ke bisa kirjinsa ya duba. Hotonsu ne shi da mama wanda sukayi a dakin Mami, xuwan ta farko gidan. Karo barkatai kenan daya daga hoton ya xura masa ido tsawon lokaci, sannan ya mike ya sake kife shi. Ya laluba aljihunsa ya dauko xoben da Mama da dawo masa dashi, ya xare na hannunsa ya hada su waje daya, ya xura masa ido. Sannan ahankali yake wasa da su, ya rike kowanne yana hada su karo. Cikin idanuwansa yake ganin ita ke rike da wanda ya bata, suke karawa juna. Wannan karon da karfinsa ya kara mata, na hannunta ya karye nan da nan ta shagwabe, gaskiya ba hake ake yi ba! Ba haka ake ba Dr. Al- ameen! Al-ameen tsananin kiran ya dawo da shi tunaninsa duniya. A firgice ya dubi Mami dake gabansa xaune. Ba xai iya cewa ga tym da ta shigo ba, don haka yake mata kallon mamaki, haka itama ta xura masa ido mai dauke da questions. Mami! Yaushe kika dawo? Ta sauke numfashi ta kada kai, kafin tace, tsoron na Allah tsorona kar ka xaunce al-ameen ka dawo cikin hankalinka mana! Yai sauri ya runtse ido yana fadin Hasbunnallu wa ni Imal wakil, Allahuma ajirni fi musibati wa akhlifini khairan minha. Ya bnude ido jajur ya dubeta, kiyi hrk mami.... Takatshe shi ba xan bari rayuwar ka ta salwanta ba Al-ameen sai inda karfi na ya kare, Allah na gani yarinyar nan ta xalunce ni. Kafin yace wani abu, ta mike da sauri tai waje, ya bita yana kira, ba su hadu ba sai a dakinta... Mami.... Ta daga masa hannu. Ban son jin komai, ta mika masa wani ruwa da ke hannunta tace shnaye shi ka bani kofi. Yace na menen? Ban son tambaya ni na umarce ka kashanye, ka bani kofin. Ya daga kofin da sunan Allah, ya kafa aabki ya kwankwade. Ta karbi kofin ta aje gefe. Ya sake tambaya mami ruwan me nasha? Tace baba liman ya bani taimako na kawo maka, anjima zaka sake sha, gobe ka kara da safe da yamma. Jibi in Allah ya kaimu lfya za ka koma sch, domin fitar da dadin ka yayi bookin ya je maka, ina fatan kajini? Jikinsa yai sanyi, ya kamo hannnayenta 2 ya ja suka xauna bisa kujera yace Allah sarki mamina. Allah bar min ke. Nagode da karfafa min gwiuwar da kukeyi. Idanuwanta taf da hawaye tace, hankalina bai taba tashi ba irin na yau. Ban taba jin faduwar gaba ba irin ta yaukai da zobuna kake hira kana dariya, Al- ameen ban same xai faru ba nan gaba. Kafadunta 2 ya dafa yace sai alkhairi mamina, kawai xancen xuci ne ya fito fili mami... Tace daga haka sai tabin hakali al- ameen , yayi dan murmushi yace Allah ba xai sa ba mamina, ya san ni kadai ya baki, kuma shi mai tsananin tausayi ne. Allah sa ruwan da kika bani ba wanda xai cire min son sakeena bane. Ta xura masa ido cikin xafi tace, shine Al-ameen Insha Allahu sakeena ba xata zama ajalinka ba, ya numfasa yana murmushi da bai kai ciki ba mami kenan, wa ya gaya miki sakeena xata kashe miki tilon danki? Kuma wa ya gaya miki danki xai ji dadin rayuwa ba tare da soayyar sakeena ciknin xuciyarsa ba? Duka 2 tafiya suke kafada da kafada mami, Allah yayi hukuncinsa, don haka ban ji Baba liman xai iya cirewa. Bayin kaina bane, kiyi hkr mami. Tayi masa xuru duk jikinta ya mutu a hankali ta ce ko bai fita ba xaka ji sanyi cikin ranka. Tunaninn ka xai daidaitu da aikin kwakwalwar ka ta yadda xaka yi mu'amula kamar sauran mutane. Wannan shine farinciknm. Yace, Allah ya taimake ku akan burin ku. Nima ya taimakeni akan nawa..... Tace xamu ci gaba dayi da fada idan har kana gaya min irin wadannan kalaman. Ya kada kai ba xa muyi ba mami. To ka daina. Ya lumshe ido, ya bude yace na daina, Allah yayi maka albarka. Ya dora kansa kafadarta ya amsa da amin. Ta ciga da yi ma nasiha yana sauraronta sai dai can kasar xuciyarsa cike yake da xulumi, Allah ya sa ruwan da mami ta ba shi ya sha ba wanda xai sa ya mance da sakeena bane. Da wannan xulumin ya tafi yin sallah la'asar hankalinsa bai kwanta ba, sai da ya tura yatsansa ya arce makogwaronsa ya kirkiro wa kansa aman dole. Bayan sallar magriba dady ya shigo ya tsare shi yaci abinci. Sannan mami ta debo ruwan addu'arta ta mika masa, ya shanye. Allah Allah yake yi tashi ya koma dakinsa ya jawo aman, amma kmar dady ya sano ya ki barinsa tashi. Yayi ta jansa da hirarrakin duniya, wai don ya rage tunanu. Kafin ya bar wajen ya kwashe awoyi sama da 2 takaice ya ishe shi, don ya tabbata ruwn nan ya gama bin jininsa. Wannan karon bai nemi yin aman ba, gado ya fada ya fara tunanin iska, har bacci ya samuyi, da alama an fara samun nasara. Shi kansa yayi mamakin irin barcin da yayi bugu da kari ya rage jin xugin xuciyarsa ke y, hankali kwance suka yi karin safe. Mami ta kara bulbuo ruwan addu'ar ta a gora, ta mika masa. Ya kwankwada duk ba a son ransa yake sha ba, a yau takardun komawarsa Rasha xasu kammalu, haka dady ya gaya masa. Saboda haka ya umarce shi daya kasance cikin shiri koda yaushe xa'a iya basu tym din tashi. Jikinsa babu kasala ya koma bangarensa ya jwo jakar kayansa yayi ta lda kaya har da wadanda ya dade bai anfani da su ba. Ya wuce dirowar madubinsa ya jawo ya kashe takardun cikin kaf, dinsu ya dauko xai xuba jaka, wata ambula ta fado duk hotuna ciki suka watse bisa kafet daidadi shigowar mami dakin. Ya aje takardun gefen gadon yana amsa sallamarta, sannan ya tsugunna ya kwashe hotunan, akasarinsa duk na mama ne, sai kalilan wanda suke tare. Tayi tsye tana kallon katuwar jakar da yake lodawa kaya, ya akayi mami na? Tace kamar bada jakar nan ka xo ba? Ya mike dauke da hotunan a hannunsa yana amsawa, xan kara wasu kayan ne, shi yasa na sauya jaka. Ya matsya xai cusa hotunan, tayi wuf ta karbe ina xaka da dasu? Ai wadannan hotunan wuta ya kamata ka cinna musu. Wuta mami? Me ya san xan sa wa sakeena wuta? Saboda nan gaba xata xama matar wani, ka ga haramun ne gareka kallon hotonta. Ina fatan ka gamsu? Yayi shiru na 'yan dakikai kafin ya numfsa, ya dubeta idanuwan har sun kada, yace kin fadi gaskiyya mami, amma baxan iya cinna wa jikin sakeena wuta ba, sai dai ina rokonki dan girman Allah ki adana min su har xuwa tym din da xata halasta gareni. Tayi masa xuru tana shakku cikin ranta, addu'ar Baba liman batayi tasiri bane ko kuwa bata fara aiki bane tkunna? Ta kada kai ta dubi hotunan ta sake dubansa, amma shi ya riga ta magana. Mami pls ki ajeye min su inda ba xa su salwanta ba. Ta sauke numfashi, xan boye maka sun tunda kafi son hakan, gwaggo ce ta xo tana daki na. Ya ware ido sosai. Gwaggo? Da sasssafen nan? Dole tayo sammako, hankalinta a tashe yake, ka fito tana daki.Tayi waje da ambulan din a hannunta, shima ya biyo bayanta. Tana xaune a shimfida bisa kafet ya xube gabannta dauke da murmushi, uwargida ran fida, kuma sai ki bugo min sammako kamar ban aika da cefane ba? Duban tausayi take masa, ta dafa kafadarsa tace dole nai sammako, in xo in ga halin da kake ciki. Ina fatan xaka sanya dangana cikin ranka. Ka mance da yarinyar nan, domin dai.... Ya katse ta, ya kamata mu gaisa gwaggo kinxo lfya? Ya tsufa? Tace tsufa na nan kuma lfya lau na xo. Amma me yasa ka katse min magana? Babu komai gani nayi bamu ko gaisa ba, alhalin ya dace na fara gaisheki. Haka ne to ina fatan duk shawarwarin da kowa ke ba, kana ji ka kuma dauka? Ka manta sakeena... Da sauri ya katse gwaggo tuni na hkr da ita, hasalima yau ko geb xan koma sch. Ban xan dalilin katseni ba Al- ameen akwai abinda baka so na fadi. Mami ta amshe, sosai kuwa kina so ya mance da sakeena, kunnunwansa ba sa son ji, shi yasa yake katseki. Tace oho, to wahalar banxa kakeyi, domin dai labari ya tabbata tare da shashashan saurayinta suka tafi, kaga kuwa sai abinda Allah yayi. Gara ka kama kanka ka san inda ke maka ciwo. 'yan mata dai ga su nan birjik duk wacce kace kule xata ce cas. Rayuwa kawai sakeena ta xaba, don na tabbata yaron nan baxai aureta ba, nawa ya lalata, ya watsar tana gani kuma ta bishi, inm banda ita ma, rayuwarka ta sha banban da wacce sakeena ta dauka, kaga kuwa tafiyarka ba xata xama daidai da tata ba. Ka fahimce ni? Wasu kwalla masu xafi suka sauka bisa kuncinsa, hakan ya jawo mamaki ga gwaggo da Mami suka xuba masa ido baki sake. Xugum sukayi, daga bisani mami ta numfasa tace ikon Allah! Gwaggo ta xare tagumi tace, akwai sauran aiki, kuma ina mai tabbatar maka , bata tym dinka kakeyi. Ya jawo hankaci ya share fuska, yace, ko kadan gwaggo, labarin ki tsananin tausayin sakeena ya cusa min, sakeena ba haka take ba, nayi rayuwa da ita sosai na fahimci halayenta, xan iya cewa nafi kowa saninta, na fahimci halinta. ,Zan iya cewa nafi kowa sanin ta hakika ya zalunce ta tunda ya sauyamata rayuwa ya bata tarbiyarta ya gurbata mu'amalarta da iyayenta da yan uwanta ya datse tasananin soyayyar dake tsakaninmu ka ALLAH bazai kyale shi ba ta ko wace hanya ya bi yayi nasa a kanta sai ya ga sakayya,"ya mike da sauri zai bar dakin gwaggo ta kwala masa kira ya tsaya bakin kofa yana goge kwalla tace dawo ka zauna ai ban gama magana da kai ba yana daga tsaye gaskiya gwaggo kunnuwa na ba za Su iya sauraron irin wadannan labarurrukan akan sakeena ba,tausayin ta bazai barni sukuni ba gara a bar ni cikin bakin duhu ina laluben inda ALLAH zai sake hada fuskokin mu har ta zama mata a gare ni," jikin gwaggo yayi mugun sanyi tace dawo zauna nan ya dawo ya zauna gefenta ya hade kai da guiwa ta dafa kansa tace idan nayi kuskure kayi min afuwa amma ba laifi na bane ka sani ko wace uwa tana kishin danta kuma abinda ya faru da kai dole mai kaunarka yayi bakin ciki balle mu da muka fi kowa kusa da kai, na san kana son sakeena sai dai ba na son idon ka ya rufe ka kasa ganin aika aikar da ta aikata a garemu, ya cire kai ya dube ta ni kuwa hakan na fi so gwaggo domin na yi imanin ba yin kanta bane sace min ita akayi hure mata kunne akayi da kalmomin shaidan addu'a zatayi maganin abin, da zaki taimake ni da ita ma zan fi farin ciki akan wadannan labaran da ki ke son bani," gwaggo " mami ta karbe za a yi maka in dai addu'a ce ka samu tashi kaje kaci gaba da shirinka bai tofa komai ba ya yunkura ya bar dakin,kamar daman can ya kosa ya barshi,"gwaggo ta dubi mami hankali tashe tace bai kamata ku kyale yaron nan ya koma haka kawai ba tare da wani taimako ba tace tun jiya na je lafai na samo masa wajan baba liman wai nan yama sha ruwan addu'ar ke nan tafdijan ki na kallo fa ko laifinta baya son a fadi wannan so yayi yawa gara ma da auran bai yuwu ba da muna kallo zai zama mijin ta ce,abin haushi nama na jan kare, mami tace me ki ka gani gwaggo?ALLAH dai ya zaba alkairi abin cewa ke nan anan gwaggo ta wuni, Shi kuwa Alameen a dakinsa ya wuni don baya son ana daga masa hankali da labaran sakkena kazantar da baka gani ba tsafta ce,kai a yadda yake jin mama cikin ransa koda ya ga kazantar da idanuwansa zuciyarsa ba za ta amince masa ba bai fito ba sai da gwaggo zata koma suka yi sallama daga nan dakin iya ya shige ya kudundune kamar maraya sama da awa guda tana tausar zuciyar sa da kalamai masu dadi,ya kuwa ji dadin cikin ransa saboda kalaman iya sunfi rinjaye ga. Bashi tabbacin idan sakeena matarsa ce duk rintsi duk wuya sai ya aure ta karfe shidda dai dai dady ya dawo masa da takardun tafiyarsa sun kammalu kuma gobe da yardar ALLAH sha biyu ranan zasu tashi don haka yana gama cin abincin dare mami ta ba shi ruwan addu'a ya kwankwada kai tsaye asibiti ya wuce don yin sallama dasu abba,kowa yayi masa nasiha kuma sun jaddada masa ya maida hankalinsa akan anibda ya kaishi kar ya tsaya bata lokacinsa. Akan tunanin iska wanda ba zai fisheshi ba,sai dai abin yana basu mamaki yadda lafuzzan alameen ke nuni da tsantsan son mama a zuciyarsa. Wanda ko alama na bayyana har yanzu bai yarda sakeena. Taci amanarsa ba, akwai mishkila wani wuri shiyasa yake ta rokansu dasu taya shi addu'a ALLAH yasa wata rana sakeena ra zama mata a gare shi,gaba daya ya kwabe masu guiwa har suka yi masa alkawarin yin yafiya a gareta idan har ta dawo ta nemi gafara,kowa ya dubi alameen sai ya ji tarin kwalla cikin iadanuwansa lokacin da yake barin asibitin yana gugar fuska shi kansa yaya soja a yau zuciyarsa ta karaya,tausayi ya kwarara cikin jikinsa ya nemi haddasa masa abin mamaki domin kwalla ya ji tam da idanuwansa suna zubowa da saurinsa ya bar wajan bai gama ganin wucewar alameen ba AKIN CIKI 2*** 11 Karfe 8am suka dauki hanyar abj tare da mami. Hankalinsu bai gama tashi ba, sai da tym ya cika aka kira passengers. Al- ameen ya rungume su, idanuwan sa cike da hawaye, bakinsa na son yin magana amma kasa, haka su ma Allah ya doro masu nauyin baki, kallon juna sukeyi. Da sauri ya juya ya wuce, yana goge fuska da hankici. Shi yasa suke tafe cikin mota kowa shiru. Mami dauke da taguminta. Tunaninta yay rayuwar dan nata xata kasance a kasar da babu wanda ya damu da wani balle ya sami wata kulawa ta musamman. Dadi yayi tana share hawaye ya dan dube ta, kada kai. Amma bai iya cewa komai ba don ya san mami tana mukatar zubda hawaye ko ta ji dadi cikin ranta, amma da ya ga abin yaki karewa, dole ya tanka, ina ganin bai dace ki ci gaba da bata ranki ba, wanda kika yi ai ya isa, ko sai ya jefa ki wani hali ni in rasa da wanda xanji? Ta goge kwalla, tace Alh. Ba haka bane ganin Al-ameen na da abin fadi, amma yakasa ya wuce da damuwar cikin ransa? Wa zai gaya mawa a can? Kai tsaye ya bata amsa, Allah zai gaya mawa, kin kuwa san ya fini, ya fiki, yafi duk wanda kike tunani zai ba Al-ameen wanni taimako, saboda haka ki bar shi da buwayin sarki, shine xai masa dukkan gudunmawa. Ta zare tagumi ta numfasa, haka ne, Allah ya taimake shi, to amin kuma na tabbatar zai taimakeni shin, tunda kika furta, addu'ar uwar yankan wuka ne, don haka ki kwantar da hankalinki. Ina fatan kin ji ni. Tace, naji alh. Allah ya shige mana gaba, yace amin. Daga nan Mami ta saki jikinta suka ci gaba da hira. Suna shigowa gari, asibiti suka wuce gano jikin Umma. Alhmdlh, Umma na samun sauki, watakila ma xuwa gobe a sallameta. Ba su iske yaya abdulkadeer da Abdul- rahman ba, duk sun koma a wannan yammacin. Sun dan jima asibitin, sannan suka dawo gida. Mami ta dukufa rokon Allah cikin sallolinta, Allah ya sanyaya wa Al-ameen xuciyarsa, ya cire masa wannan makahon so sa ya ke wa Mama. Haka ta kwana tunaninsa har barci tayi mafarkinsa xaune yana wasa da xobunan guda 2. Shiyasa da ta fara tayi ta da na sanin da ta raba shi da zobunan kafin ya tafi. Suna karin safe karfe 8:30, waya ta dauki kuka, mami ta baro tebur ta zo duka tayi sallama. Muryar dan lelenta taji ya amsa. Farin ciki ya lallube ta tace, Allah sarki Dr. An sauka lfya? Yace lfya lau Mami, ina dadina? Ga shi nan, ya taso ya ji kaini, ina fatan ba matsala? Babu mami, na ma iske time table din jarabawar mu ya fito, karatu kawai xa mu fuskanta, ni da abokan karatuna. Dadi ya tsaya wajen tana fadin, kai naji dadi sosai, to Allah ya baku sa'a baki daya. Ga dadinka. Ya ce, to nagode Mami. Dadi ya amsa suka gaisa. Dady time table ya fito a taya mu addu'a. Yace kullum a cikinta muke, amma xa mu kara kaimi. Ubangiji Allah ya taimako. Yace amin. To xan wuce cikin sch, sai kun sake jina. Yace, yayi kyau, all d bst! Cike da fara'a ya amsa. Nagode Dadina. Ya aje waya ya dubi mami yace hankalinki ya kwanta? Bakinta har kunne ta amsa. Kai bari Allah ya kara masa hkr. Yace amin, muje muci abinci ko? Suka koma tebur. Mami tace abinci hankalinta kwance. Ba Haka al'amarin yake wajensu Umma ba, domin yau sun koma Fandagori sun iske da kuara da suka bari baya. Hankulansu su kara tashi yadda xance ke ta yamadidi a agari. Zagi iri-iri babi irn wanda ba'ayi ba wasu suna ba iyayen Mama laifi, amma da dama sunfi zargin mama akan rashin hankali da ta aikata. Wani abinda yafi daga wa Ubandawaki hankali shine, wai gaba daya gundarin labarin daga bakin 'yan uwansa da matayensu ya fara fitowa. Bayan gaskiyya ga tarin karya da karairayin da suka yiwa labarin kawanya, don haka ya tara su falon sa bayan sallar isha'i. Wannan shine karo na 2 da na tara ku akan wasu maganganu na batanci da suke fitowa daga gareku. A zatona ku masu rufa min asiri ne ko bayan raina a matsayin ku na 'yan uwana da muka fito ciki daya. Amma bansan abinda nayi muku ba kuke min bita da kulli, ko kuma ince kuke farinciki don wannan abin ya sameni. To abinda nake so ku gane shine, da frko dai bamu mukayi kanmu ba. Allah ne yayi mu, mu kuma shi ya rubuta duk abinda zai faru da mu. Babu wanda yasan kaddarar mu2m bnalle ya share masa mummuna kafin tazo. Da anayi da na gogewa Mama, don na duk fadin duniyar babu wanda zai kaini BAKIN CIKI, sai kuwa mahaifyar ta. Idan kuwa hakane, bai kamata ace ku da matayenku, ku dauki wannan al'amarin ya zamar maku abin hira a gari ba. Kaddara na kowa, idan baku duba kusancin mu ba, ya kamata ku duba wannan. Allah yai sani ban zalunci kowa ba cikin ku ba, haka ban xalunci mama ba, kamar yadda kuke yadawa cewar mu ne muka dage sai mai kudi xata aura, alhalin kun san komai a game da alkawarin auran ta da Al-ameen. Kun fi kowa sanin gaskiyya, amma kuka boye ta, saboda son rai to na bar kowa da Allah, yayi min sakayya, Da yardar Allah BAKIN CIKIN Mama bazai kashe mu ba, haka zalika ina mata fatana shiriyar koda yaushe. Mai surutu da dariya kuma Allah ya bashi sa'ar yi. Amma kar ya mance kaddara bata fatan shiryar kowa! Yana sa aya, ya mike ya bar falon ba tare da wani yayi magana ba, ita ma umma tashi tayi ta bi bayansa, yayi sauran ke mazuran rashin gaskiya. Haj. Gaje ta buga tsaki, ta bar falon. Daga bisani Haj. Hajjo ta lallaba ta sulale, Alh. Basiru ya dubi Alh. Adamu. Yace mutane munafukai ne, wai daga dawowarsa, an sami wani kusugurmin ya feshe shi, don neman fada. Alh. Adam yace, wai me akace? Au ya faru ba za'a maida yadda akayi ba? Me za'a baoye bayan ta gudun kowa kuma ya sani tare da shegen yaron nan suka tafi! Ai ko ba 'a fada ba, amsar a bayyane take. Tace, bata so, ba sai a kyale ta ba, ta auri dan iskan da ake ganin ba shi da asali ba, ba ita zata zauna da shi ba? Wahalar tace tunda tasan halinsa. Tace sai shi. Wai kuma mu ake ganin laifin mu, don fin karfi! Mts.... Ya ja tsaki yayi waje abin sa. Alh. Basiru ya mike yana kada kai, shi ma ya fice. Zaman doya da maja yaci gaba da yaduwa cikin gidan, duk da ba gaba daya sukeyi ba, amma babu wata kyakkaywar fahimta atsakninsu. Shi uban dawaki yana ganin ya kamata su ba shi hkr a matsayinsa na babban su, sannan yana gani sun yi masa laifi, don sun bada labarin yadda akayi mama ta gudu, tunda ba su suka xuga ta ba, komai ya kwana gidan sauki saboda haka basu ga dalilin da xai sa Uban dawaki Ya dauki dalan laifi ya dora masu ba har ya rinka jiran kalaman tubansu. Su ma fah yanxun ba yara bane, girman 'ya'yan su ya kai, ya gane shekarun su sun cika daidai matsayin masu 'yanci. Zuwan Ali da Ya saed don duba jikin Umma da kuma jin labarin Mama ko ta bayyana, Al-amarin bai yi musu dadi ba, ganin Yadda iyayen su suka ware ubandawaki suna masa yankar baya. Musamman Ya ali, hankalinsa yayi mummunan tashi, babu bata tym ya gurfana gaban abba yana bashi hkr. Daga bisani Ya saeed ya shigo falon. Ya ali Yayi rantsuwa da ace mama zata dawo ta amince da auransa, maimakon Danliti, a shirye yake a daura masu aure. Ko a gaban iyayen sa haka ya maida zancansa. Haj. Hajjo ta rufe shi da bala'i Allah wadarn wannan so kuwa, tunda yake hana ka kishin kanka. To idan ma mafarki kake yi, ka wanke idon ka, ka saurareni, idan har ni na haifeka, ba xaka auri ragowar Danliti ba. Wannan kalma tayi masa ciwo, bai san tym daya tasshi ya tabbatar wa su Haj. Hajo cewa kashe miciji sukeyi basa sare kansa. Domin ko banza sun kwana da mamakin Ya ali da yayi tafiyarsa, daga magana, shima ya gudun kenan? Ko mene nufinsa? Muna iya cewa matsalarsu ce, ko dama abba ya fadi kaddara na kan kowa....... Inna saude ke xaune gefen gadon tana mata fifita. Kallo daya zakayi mata, ka gane cewa ta jima tana fama da ciwon tsananin damuwa, domin dai ta fyade ta fita kamanninta. Amma hakan bai hana ragargazar shagalin bikin da akeyi cikin gidan ba. Nasan xakuyi mamaki, idan na gaya musu cewar bikin yaya Ali da Ya Sa'ed akeyi. Iyayeyn sun hur masu wuta, tun tym din da suka lura da take taken shi Ya alin, sam hankalinsa ba shi akan abinda zai fishshe shi. Shi yasa suka matsa kwarai da gaske akn ya fiddo matar aure ko su su fidda masa, ya kuwa tabbatar da mahaifiya sa xata ita. Gudun kar ta manna masa alakakai ya sa ya fito da yarinyar da ta dade tana sonsa a birnin gwari. Amina sunanta, kuma makwabtansa ne a gidan daya ke xaune. Sa'ed tuni yake tare da Hassana a kd. A yau ne maza suka daura auran 11am. Daga can suka wuce kd, inda xa'a daura na sa'ed bayan azahar. 8pm wannan rana motocin amare ke shigowa layin gidan angwayensu, haka daidai wannan tym motar Danliti parkn a kofar shagon sa dauke da tasa amaryar. Cike da mamki ayuba ya taso, ya bude kofar yana fadin, wa nake gani kamar amafarki? Wai dama kuna tunanin gida? Dan liti ya fito yayi doguwar miki, yana dariya, yace ah gamu kuma mun dawo, ya juya cikin mota ya cigaba da fadin, ya Gimbiya anan zaki sauko ko na karasa dae gida? Ta kada kai, tace, naji tsoro ya kamani Danliti, bansan yadda xanyi ba? Yayi 'yar dariya. Yace tsoro kuma? To me xa suyi miki? Ta kada kai bari dai na sauka nan, canm ajima na karasa gidan. Ya kace da dariya. Amma ke shirmen ki yayi yawa, to fito ki shiga ciki. Ta ballo murfin ta fito, kai! Anya kuwa Mama ce? Tayi wata shegiyar kiba ta kara ja, ina ganin shi yasa Ayuba ya xura mata ido, tym din da take mika masa gaisuwa. Danliti ya bude but suka ciro manyan jakunkuna guda 2 da kit, sai manya ledoji guda 3. Ayuba ya taimaka suke shige da su cikin shago. Kai tsaye dakinta shige ta xube a katifa. Duk suka biyo bayanta. Danliti ya xauna kusa da ita. Yace kin gaji ko? Tace kai dai bari, kamar in kwanta inyi ta barci wlh. To ki kwanta mana, ai ba kya jin yunwa ko kinaji? Ta kada kai, banji, to ki kwnta ki huta ne, xuwa karfe goma sai in tashe ki, ki koma gida. Haka za'ayi, ta jawo filo ta yada kai, suna kallon juna suna musayar murmushi. Ya lukuce mata hanci, yace baby na kenan. Ta juya gefe tana 'ya dariya. Ya mike ya dubi ayuba yace, to muje dogari. Ya juya yana murmushi, ina tsarabata? Yace yauwa ka tuna min, ya suri jakar leda suka fice da ita. Ya xauna bisa kujera ayuba na kan tabarma, ya zazzzage kayan kedar a gabansa. Gaba daya kayan sawa ne. Na gayu ya siyo masa, ya dube shi suka hada ido, yace ga tsarabar legos nan. Baki sake yace babu wai, har ma ga tsaraba nan duka naka ne. Ya washe baki m amma na gode, watau shi ya sana kunyi jajur abinku, ashe kuna bakin teku. Yace, hutu ba karya bane ayuba, ga kuma lafiyayyar bebi na, nake gaya ma. Yayi shiru yana kallon sa, fuskarsa gaba daya tabayyana babu abinda bai faru ba. Ya numfas duk jikinsa ya mutu yace, bakaji Danliti. Me nayi ma tukunna? Ko kaji surutu ne a gari? Ya gyara zama yace ba'a tonawa Danliti, abinda nake son ka da shi, ku sasanta ka aureta kawai, ka ba masu surutu kunya, donn sunce ba auranta zakayi ba, tayi saki reshe ne, ta kama ganye, ya shafa habarasa yace, ko? To ai ba suyi karya ba, shagali kuma basu ga komai ba daga nan ma illa masha Allah ba za mu daina ba. Ya kada kai yace, meye nawa a ciki? Idan ka huta ko xuwa gobe mayi lissafi. Yace ina fatan akwai kudi sosai, don wanda na tafi da su naci uabansu, ya amsa ciniki na na ba laifi, sati biyu ma da suka wuce na je kno na karo kaya da cinikin yafi haka. Da kyau mutumina, shi yasa nke sonka wlh. Yayi 'yar dariya yana daga kayan da aka kawo masa, ni kuma ina sonka da nutsuwa ba amma kakiji. Ya mike ya nufi daki yana cewa, kai ka fiye surutu, bari in baka wuri. Ya shige dakin ya bar ayuba da kallonsa. Ya kada kai yace aransa, Allah ka shiryemu. Shi kuwa Danliti komawa yayi ya hana mama barcin. Karfe 10 ta dan gota, dan liti ya umarci Mama da ta koma gidan iyayenta, su san ta dawo, dan su san matakin karshe da zau dauka. Watakila hakan su ta cimma ruwa. Watau su amince da auransu cewarsa madugu uban tafiyar. Ya hado mata kayanta taf! Da katuwar jaka, tana xaune tana kallonsa, kafin tace gaskiyya ba xan dauki jakar nan ba, guda uku kawai dauka cikin kit, in tafi dasu. Ido waje ya tambaya, sabda me? Ka sani ko su koroni? Ka bari tukunna mu gani, idan suka kyale ni, sai in dawo in kwashe sauran. Idan basu kyaleki ba fah? Sai na dawo nan ka yanke hukunci duk da zaka yanke. Ya xura mata do, ai iyayenki na san ba su ki karbarki ba, hasalima ai laifin su ne, na tabbata yanxun sun gane kuskurensu, dole su lallabaki. Ta doke kafadarsa tana dariya, har ma kasan dole su lallabani? Kai dai ka yi fatan su amince da auranmu. Yace shikenan, yanxun ki dauki abinda xaki dauka na rakaki, dare nakara yi. Ta bude kit ta xuba kaya kala 3, yasa hannu ya dauko wata 'yar karamar doguwar riga yace..... Yace ba xaki dauki wannan rigar ba? Tace wannan shegiyar rigar? Shegiya? Lallai ba ki san yadda take mi ki kyau bane, a'a ka dai barta anan, sanin kanka ne, su Abba bna za su barni na sanya taba cikin gidansu. An wuce wurin, ki barta kyasa a gidana. Ta yada kai kan kafadarsa tace ashe ka gane. Ya tsikare ta, ta mike xumbur! Ban fa so Danliti banso! Ta figi kit dinta, tayi waje baki a ture. Ya kwaso mata gyale da takalmi ya biyota yana fadin sorry 'yar bebi na! Taja ta tsya tana haraarsa, ya yafa mata gyalen, ya aje takalmin gabanta ya jawo kafufuwanta, sa abinki mu tafi. Ta xura kafar tace wa Ayuba, sai da safe. Yake yayi ya amsa, Allah ya kaimu. Suka fice, Danliti na cewa, har kin tabbatar da xamanki a gidan ne kike ce masa sai da safe? Tace gane min hanya wai, makaho ya so gulma. Ya ci gaba da dariya, suna tafe suna hira. Gab da gidan, ya tsaya sukayi sallama, idan kuma ya gan ta ta dawo shikenan. Y koma ita kuma taci gaba da tafiya hankalinta kwance yake, don bata saka komai illa in su koroto, ta koma inda ta fito. Daga bisani ma wata dabara ta fado mata. Tana dosowa kofar gidan, ta hangi kamar ana hada hadar jama'a, duk da dare ya fara yi, kana iya gane wa ana sha'ani a gidan. Bata yi wa kowa magana ba,a haka suma babu wanda ya shaidata. Sai da ta shige xauran karshe ta aje kit dinta, ta xauna akai ta hade kai da guiwa ta kirkiro kukan dole ta shiga yinsa har da shesheka, sannan hankulan masu wucewa ya fara xuwa gunta kuma, Ya ali shine mutum na farko daya fara dosar ta da tambaya, wai wacece xaune? Gida kike son komawa? A zata son cikin 'yan kawo amare ne, yayi dan murmushi, don ta bashi dariya. Da girmanki da komai kike kauyanci? Dan Allah tashi ki koma cikin gida tun kafain yara su fara miki dariya. Ko an yi miki wani abu ne? Daga ji ta gane mai magana, shi yasa ta dago sosai ta dube shi, kawai batare da tayi magana ba. Gabansa ya tsinke ya fadi xuciyarsa ke ambato sunan, mama? Sannan ya tsugunna gabanta ya furta a hankali, mama! Hawayenta suka kara tsunkewa, ta sadda kai, tana gogewa da bayan hannu. Innalillahi wa Inna illaihir raju'un! Ya waiwaiga babu mai kallonsa yayi sauri ya ja mayafinta ya rufe fuskarta, yace, taso muje, kar ki bari kowa ya ganki. Ya ja hannunta suka sulale dakinsy Danlami. Babu kowa cikinsa, duk suna can wajen fatin da sukeyi da abokansa. Ya xaunar da ita gefen gado ya tsugguna. Yace, yaushe kika dawo mama? Baki na rawa ta amsa, yanxun, idanuwansa suka kawo kwalla a raunane. Yace abinda kikayi kin kyauta kenan mama? Da mtuncin ki da komai? Iyayen mu masu girma da daraja a gurin jama'a, kika tozarta su? Haba mama, kamar baki sami tarbiya ba? Ta goge kwalla. Tace, ba haka bane, Ya ali me yasa zaku rinka ganin laifi na ni kadai? Nace ga wanda nake so, ba sai a ba ni shi ba. Ina ruwan kowa da rashin asalinsa? Ai dai ba daga sama ya fado ba, da uwarsa da ubansa. Yace, Maganar banza ce wannan mama, don na tabbata Daliti bai fi miki iyayenki ba. Kin kuwa san halin da umma ke ciki tun ranar da kika sa kafa kika bar gidan nan? Kin daure min kai, ban taba xataon zaki aikata irin wanan mummuna aiki ba. Tace hakan kadai xai memin mafita kuma akan bakana na dawo ko Danliti, ko su rasa ni baki daya. Ya xura mata ido, yana kada kai. Afuwa ya kamata ki nema ku sulhunta da iyayenki, su sa miki albarka, ko kin ga rayuwa mai kyau da anfani nan gaba. Saboda haka ki xauna anan ki jirani, xan shiga wajensu in kwantar musu da hankali tukina, gaskiyya bana so ayi miki taratsi cikin jama'a, kuma gidan cike yake da baki. Baki? Me akeyi a gidan? Ya amsa, biki na akeyi dana seed. Kana nufin kunyi aure? To Ya xanyi, tunda kinki ni Mama? Akan dole na yi auaran nan, su Baba sun matsa min. Ina muku murna, nima Allah yasa ni a danshinku. Ya xura mata ido gwanin tausayi. Yace, nasan ba xaki ji komai a ranki ba, tunda ba so na kike ba, amma ni har kwanan gobe ina sonki, shi ya sa abinda ke faruwa da ke ya xame min ciwon cikin raina, ki yiwa girman Allah mama ki sanya tunanin ki dawo sak! Yadda kowa ya sanki. Karka damu dani Ya Ali, ko da yaushe ina gaya ma kai dan uwana ne, kauanar mu ta jini ce mai asali. Kwanciyar hnakalina kuwa Danliti ya zama mijina. Ina fatan iyayen Al-ameen sunyi xuciya su fasa? Ko baka ji komai akai ba? Ya xuba mata ido yana mamakinta, ya jima bai amsa ba, kafin yace, Al- ameen ya koma Rasha da ciwon xuciya Mama..... Ta katse shi ido rufe ta dafe kirji. Tace, nagode Allah! Har naji sanyi cikin raina. Ya kada kai yana kallonta. Yace, baki masa adalci ba, baki tsoron amanarsa ta ciki? Akan me? Bafa dole bane na aure shi, ina son kowa ya gane wannan, kawai kaje ka gaya masu na dawo din, kaji me xasu ce? Yace ni ne nayi niyyar yin hakan, ba sai kin bani umarni ba. Yi hkr Yaya, bai tanka ba, ya tashi ya five, ta bi bayansa da kallo tana fadin cikin ranta, je ka dawo, duk na kosa in san babin da nake. Cikin dakin yayi sallama, abba ya amsa masa yana kokarin hadawa Umma shayi ta samu ta dan sha, ya akayi Ali? Ya xauna gefe kusa da shi, yace babu komai abba, wata alfarma naxo nema wajenku. Hankalin abba ya dawo gare shi, yace ina jinka. Allah ya sa batafi karfi na ba. Ya kada kai ya amsa, bata fi ba Abba, duk mai laifi idan ya nemi afuwa, me yakamata ayi masa? Ya dube shi da kyau da mamaki yace, ayi masa afuwar, domin Allah yana son masu yafiya ga bayinsa. Su kuma masu laifin su yi alakwarin ba xasu sake komawa ga wancanm laifin ba. Laifin me kayi? Ya amsa, laifin mai girma ne Abba, a misali Mama ta dawo ta nemi gafara, abba xa ka karbi tubanta? Ba abba kadai ba harda Umma dake kwance ta xubo masa ido, abba ya jima kafin ya numfasa. Yace Bansan dalilin da yasa ka min tambayar nan ba, amma ina so ka sani, mama ta aikata laifi mafi muni a shafin tarihin gidan nan, da mu karbeta da kar mu karbeta, bakin fentin da ta shafa mana yana nan baxai goge ba, ina so ka sani Ali, xaiyi wuya a fadin gari na Mama ta sami wani mijin, face katon daya dauke ta ya boye wani wuri tsowon watanni 3. Abu na karshe da nake so ka snai, shine bai kai kadai ka rokeni ba. Al-ameen ma ya rokar mata gafara kuma nayi masa tare da alakwarin ba xanki karbarta ba. Saboda haka ka kwantar da hankalinka, muddin Mamma ta dawo gidan nan, ba xan ce ta koma ba, haka xalika idan bata sauya ra'ayinta ba, ba xan ce mata a'a ba, Allah na kallo, nayi kokarin na, don nuna mata hanyar kwarai da samun abokin zama na kirki mai kyan asali. Ko duniya ta zageni, alhakin Na suka duka kuma zamuyi shari'a da su gobe kiyama. Kawai ji yayi kwallah na xubo masa, saboda tausayin Abba, yasa hannu ya goge, abba ya riga shi sake magana, ka daina kuka Ali, kaddara ce, tashin hankalina daya, mahaifiyarta da ta kasa samun nutsuwa. Ina jin tsoron kar ciwon xuciya ya kamata kamar yadda likitocin da ke duba ta suke gargadin ta kullum. Dalilin da yasa kenan nake fatan Allah ya sa mama ta dawo, watakila ya zama waraka ga mahaifiyarta. Na tabbata hankalinta xaifi kwanciya idan tana ganin ta koda a dakin auran Danliti ne. Ya Ali ya gyara xama yace, gaskiyya ne abba, kuma naji dadin bayanan ka. Saboda haka ina mai farin cikin shaida maku cewar mama na nan ta dawo. Abba ya xura masa ido. Umma kuwa ciccibawa tayi ta tashi xaune. Ba fahimce ka ba Ali? Inji Abba, yace Mama na nan a cikin gidan nan, idan kun ban izini, zan shigo da ita ta roki gafararku. Suka dubi juna shi da Umma baki sake, tuni hawaye suka tsinke mata, tana kada kai tare da salatin Manzo. Abba ya dube shi yace, je ka ashigo da ita Ali. Har ya mike ya sake komawa ya xauana, yace Abba ina fatan ba xaku daga mata murya ba, kasan gidan na cike yake da baki. Yace Insha Allahu, ba xan daga mata ba. Yace nagde abba. Ya mike ya wuce, abba ya bishi da kallon, sannan ya dubi Umma, ashe haka Ali ke da hankali? Nayi kuskuran hana masa auran Mama tunda farko. Umma ta goge hwaye tace, hakika mama tayi asara masoya 2. Haka Allah ya so, ba mu da abinyi, dai yi masa godiya, abba ya sauke numfashi, sukayi xugum suna sauraron ta yadda mama xata bayyana garesu. Jimawa kadan suka tsinkayi muryar Ya Ali yana fadin ki shigo mana! Na gaya miki komai ya wuce, ki shigo kawai. Make-maken munafurci takeyi ba wai ainihin tsoron bane cikin ranta, da su abba xa suyi kuskuran cewa ta juya, fes! Zata juya babu waiwaye sukayi sallama dakin. Ya ali na dauke da kit dinta. Ta toge bakin kofa, yasa hannun ya janyo ta har gabansu abba dake sake da baki suna kallon abin al-ajabi. Gata abba, umma ga Mama, ku mance da abinda ya faru, ku amince da xabanta, ku sa musu albarka, sai kuka ga Allah ya basu zuri'a abin alfahari. Mama ki durkusa ki roke su gafara. Ko dama a durkushen take kuma tuni hawayen suka tsunke mata, murya na rawa, tace.. BAKIN CIKI 2***12 Abba kuyi hrk, Umma ki yafe min. Abba ya numfasa yana kada kai. Ya ce a rayuwata gaba daya Mama ba tba xataon xaki min irin wannan mugun butulcin ba. Na dauke ki 'yar da na dauki burin duniya na dora a kanki. Kece kika bambamta da kowa cikin xuciyata, kuma na nuna miki dukkan gata amma dare daya, kika numa mana akwai wanda ya fi mu muhimmaci a rayuwarki. Tabbas na yarda da hakan, don a tunani na xan ga kin dawo kin bushe a lalace saboda tunanin kin barmu cin BAKIN CIKI sai gaki Fes! Kinyi kiba. Ban miki baki ba, ba kuma xan miki ba, amma ina mai tabbatar miki in rasa masoyi, kin rasa mai tsanin kaunar ki tsakani da Allah, kuma a yau na kara nadamar hana Ali auaranki tun farko. Maganata karshe itace, tunda kin nace sai Danliti to ki gaya masa ya turo magabatansa, muyi magana, sannan kiyi wa Yayanki Ali godiya, domin yayi miki dukkan taimako. Zaciyarta fara sol! Jin Abba ya ambato Danliti ya turo. Ta kara dukawa tana goge kwalla. Tace, ngde abba, kuma ina kara baku hkr, don Allah ku yafe min. Ta rarrafa gun Umma ta cusa kanta jikinta, umma kiyi hkr! Ta share hwaye tace ai ya wuce Mama, kinci albarkacin al-ameen da ali. Amma gyara kayanka, ai baya zama sauke mu raba ba. Ki bi duniya a sannu, domin ita duniya budurwa ce mai kyale-kyale da yawa, da zarar ka biye mata, to ka bace ka kuma shiga uku ka lalace. Ban da abin kari a gareki, don nasiha anyi miki, amma kin rushe saboda batan basira. Allah ya ganar da ke, ya sa ki a hanya madaidaiciya. Ya ali ya amsa da amin, yayin da mama ke ci gaba da gugar hawaye. Alin ne ya cigaba da cewa, don Allah abba karku nuna kowa ta dawo har tym din bakin nan xasu koma. Ko su Baba a kyale su tukuna. Ke mama ina son ki cigaba da xama cikin dakinku dan Allah, na san xuwa gobe da yamma kowa xai watse, sai a kam magana ta gaba, kinji? Ta amsa da kai, Abba yace shikenan Ali, kana son ka rufawa 'yar uwarka asiri, asirin kuwa da ya riga ya tonu. Yace kayi hkr dai abba, yace babu komai, ta tashi ta koma dakinta, idan tana jin yunwa, akwai abinci, yace xaki ci abinci ne? Ta kada kai, to taso na raka ki dakinki. Umma mun gode, tace Allah yayi albarka, ya amsa da amin. Tare suka mike suka bar dakin. Umma ta tafa hannu tana salati, sannan ta buga tagumi. Yanxun alh. Danliti xata aura? Yace, t ya xamuyi, wa kike ganin xai fito neman auranta, bayan ya san wannan kwamacala? Haka nan xamu hkr da abinda Allah ya kaddaro, yanxun dai bana ce ya turo ba? Sai mu sa ido mu ga wadanda xai turo din. Ta numfasa, tace Allah shi kyauta yace amin. Ke dai ki kwantar da hankalinki, ki daina xa damuwa a ranki don Allah. Tace naji alh. Ya ciga ba hada mata shayin suna tattaunawa. Kamar yadda ake tattaunaea da mama da Ya Ali. Shawarwari kawai yake bata, tana sauraronsa kamar gaske. Har kusan sha daya da rabi suna tare. Dagab bisani yayi mata sallama ya barya cike da farin ciki da baya misaltuwa. Nan da nan ta fada bayi tayi wanka, ta kintsa jikinta ta kwanta. Kewar Danliti ta lullube ta, fadi take cikin ranta, ba dan dare yayi ba da naje yiwa sweety Na albishir. Da kyar barci ya sace ta saboda murna. Washe gari hidima taci gaba, mama na cikin dakin na kulle babu wanda ya san ta dawo, daga Ya Ali sai su Umma. Kuma anyi sa'a taji maganar Ya Ali batayi marmarin fitowa ba, sai shi ne ma ya kan saci jiki ya shiga wajenta, ya ganta yaji dan ji sanyi aransa. Allah sarki! Garin dadi na newa, iska na ta wahalar da mai kayan kara, bayan sallahr la'asar baki suka koma muhallin su aka bar amare da angwayensu. Shi kuwa Ubandawaki 'yan uwansa ya tara falon baki yace, naki ku ne a matsayin ku na kannena na in shaida muku cewar Mama ta dawo daren jiya, kuma har na yanke hukuncin ta gayawa Danlitin ya turo magabatansa, muyi maganar aure. Ban san yadda zaku karbi abin ba, ko da mahimmanci ko ya zama abin dariya a gareku, duk daya ne, ni dai na fita hakkinku. Suka dubi juna cikin sigar tsarguwa, sannan Alh.basir yace, ai shikenan yaya, amma banji dadin yadda kayi mana fassara ba, ya kamata kayi mana uxuri tunda mun ce maganar nan bada wata manufa muka fadeta ba. Amma ace mama ta dawo tun jiya, sai yanxun mukeji? Ba komai. Alh. Adam ya cage, tabbas naga Danliti a shagonsa, sai dain banyi tunani tare suka dawo ba, tunda banji labarin ba a cikin gida. Sai dai Yaya a gaskiyya muna so mu ganar da kai cewa ba farinciki mukeyi da abinda ya sami mama ba, mutuncin gidan nan, ai duk namune, me zai sa muyi murna da rugujewarsa? Abba yace duk naji, magana ta gaskiyya, Allah kadai yasanta, don shine masanin sirrin xukata. Abinda ya sa bau san Mama ta dawo ba, sai yanxun. Ali ne ya fara ganinta kuma ya xo ya sameni guiwa 2 ya roke ni da kyale mama kar in daga murya, saboda baki fa ke cikin gidan nan. Idan sun tafi ayi su wacce xa ayi. To maga ma ta kare, nacewa Danliti ya fito a daura musu auran, su karata. Allah dai ya gani ba da son raina bane. Fuska Ya mutse Alh. Basir ke cewa, Dan liti xata aura? Yace bamu da abinyi, haka Allah ya so, sai dai muyi mata fatan alkhairi. Saboda haka bana son abin yayi tsawo, yana turo sai aure. Ya turowa za'a sa rana kuma ba zata wuce sati 3-4 ba duk abinda Allah ya hore min shi xa'a kai mata. Ita kenan maganara, kowa na iya tafiya harkokinsa, mu saurari xuwan magabatan nasa shikenan, Allah ya nuna mana. Haka suka fadi baki dayansu. Abba ya amsa da amin, suka bar falon ba yabo ba fallasa, cikin xukatansu, ma'ana intayi ruwa rijiya in ba tai ba masai. Suna shuga sasan su, suka bajewa iyalensu babu bata tym suka fara xuba sharhi. Haj. Gake kuwa har da guda. Daga bisani suka baxama sassan Uban dawaki, don gain Mama tare da yiwa Umma murna dawowar Mama fida, amma a zahiri a cikin xukantasu yanayin Maman suke son gani. Suka kwarara sallama, umma ta amsa, sai mukaji daddadan labari! Ina maman? Inji Haj. Hajjo, tana dakinta, gaba daya sukace Allah shi kyauta na gaba. Yanxun da Danliti xa'ayi auran? Tace, nufi ne Allah, duk abinda ya rubuta bamu isa mu goge Ba. Haj. Hajjo tace gaskiyya ba haka muka so ba. Sai dai hkr kwai. Haj. Gaje ta tabe baki tace, ya xama dole, amma a hakikanin gaskiyya mama ta bamu kunya. Ajin ai ba daya bane in banda batan basira. Koda yake ance so mako ne. Allah ya sanya alkhairi. Sukayi dan shiru, kafin suka nufi dakin Mama, ina kike? Kina jin mu amma ba xaki fito ki gaishemu ba? Tana xaune gefen gado, ta fesa ado kyanta ya kara bayanna, banda haka da ibar da ta kara suka kalli juna sabe da haba, kafin Haj. Gaje ta soma xuba, lallai Mama, watau hankalinki a kwnace kika je, ki ka dawo! Wannan kiba haka? To Allah yasa ki sami irin wannan a gidansa. Haj. Hajjo ta amshe amin dai, kin dai riga kinsan halinsa, komai yayi miki sai ki hadiyewa cikinki, kar ki doshi kowa, tunda kin nace shi kike so! Ko kuwa gaje? Tace haka yake yaya, ai kowa ya sayi rariya yasan zata xubda ruwa. Mayafinta dake bisa filo ta figo ta mike tsaye ta xura takalmanta tayo waje tana yafa gyelenta, ta barsu anan sake da baki, suna kallon juna. Ko kinga dibar albarka? Inji Haj. Hajjo, Haj. Gaje tace, mamaki kikeyi Yaya? Karfa ki manta watanni 3 ta shafe a bariki, an kuwa ce xama da madaukin kanwa, shike kawo farin kai. Mu meye namu? Ta malam ai bata wuce amin. Can suka sameta dakin Umma tana neman izinin zuwa wajen Danliti, don ta shaida masa sakon abba, suna isowa, umm ana fadin bance kije ki xauna ba, mutunciki shine ya biyo ki nan kofar gidanku. Saboda haka daga yau kar na sake jin kin koma shagonsa. Tace, to Umma, insha Allah yanxun xan dawo. Ta sa kai ta fice, ba tare da Umma ta kara wani abu ba. Nan su Haj. Hajjo suka xauna suka cigaba da kwasar tsegumi, ita kuwa tana fitowa xauran farko, angwaye ta ci karo dasu, saeed Ya maka mata harara, ya wuce abinsa cikin gida. Ta dubi ya Ali, tace me nayi masa? Yace kin fi kowa sani. Taja dogon tsaki, aikin banxa, to shinme me? Don ya ki min magana? Yace, kin baci da Rashin K mama, me yasa? Da ba haka kike ba. Ta dan tabne baki tace, ni ina da wurin xauwa, ba na fito magana da Ya Saeed bane. Yace amma ba kije kinga amare ba. Xanje ai, so nake in sauke wannan nauyin ko ni,a na kama dahir. Yayi dan murmushi yana kllonta, mama kenan, to a dawo lfya, nasan sakon bai wuce na Danliti ba. Tayi 'yar dariya. Shi ysa nake sonka Yayana, bari dai in dawo amaryarka ka xan fara xuwa na in gani. Ta wuce tana cigaba da dariya, ganin yadda yayi tsaye duk jikinsa ya mutu. Ya bita da kallo, sannan ya kada kai, yace, ni ma ina mutuwar sonki Mama. Ina ma ace hankalinki xai dawo gareni? Ya sauke numfashi ya shige wajen amaryarsa. Bakinta har kunne take sallama kofar shagon, ayuba ta gani xaune ckin shagon ya amsa mata cike da fara'a amaryarmu kenan, ya gajiyar tfya? Tace tabi lfya, ina mutumin? Ya amsa yana ciki tun azahar yake barci saboda ragwanci. Ta fara dariya, lallai kuwa ragwanci, barin inshiga dole ya tashi ya bani goron albshiri. Ta wuce ciki, ayuba na fadin, ya dai kamata ya tashi ko salla ya samuyi. Kan tsaye bisa katifar ta fada, ta dada masa duka cinya, don Allah tashi rago! Ka wani baje kana gugar barci, ni ina can ina tunaninka. Ya bude ido firgigi yana kallon ta jim, sannan yayi dan gajeran tsaki. Yace kash! Wlh ba don ke bace, marin Mutum zanyi. Kin ji dadin barcin kuwa? Tayi far da ido, tace ko? To ka tashi, na tabbata dadin barcin bai kai albishir din baki na ba. Ya xuba mata ido yace fadi ina jinki. Idan kuma bai fi ba, kinsan Allah sai na sanya ki kuka, ai kin san gamuwar mu babu tausayi. Tayi 'yar dariya, tace, haba duk wannan kukan wasa nakeyi, kama daina hura hanci. Yayi murmushi, haka kikace? To shiknen, fadi ina jinki. Ta gyara xama albishirnka? Yamasa goro. Xaka bani Ah! Me xai hana? Ke dai gaya min inji. Abba yace in fada maka ka turo, ranar auren mu za a sanya. Ya xuba mata ido, ya kasa ko motsi, kayi shiru? Ya sa hannu 2 ya mutsutsuke idanuwansa yace, dan Allah karki xalayeni! Ta ware ido, kana nufin baka yarda ba? Gaskiyya ban yarda ba, yaushe Abba xai yarda ya bani ke, bayan ya san bani da kowa a garin nan? Sannan suna min kallon dan... Tayi wuf ta rufe bakinsa, sau nawa xan gaya maka ka daina dorawa kanka maraici? Ina sonka Danliti..... su abba kuma sun amince ka turo asa mana rana da gaske na ke gaya maka maganar nan ba wasa ba da sauri ya figo ta jikinsa yayi wani irin ihu wai shi murna ayuba ya kwaso a guje ya fado dakin ya same si kankame da juna dan haka. Bai tsaya tambayar komai ba ya juya ya fita yana kada kai cikin ransa yana fadin "Danliti akwai dan iska"ya jima bai kyale mama taci gaba dayi masa bayani ba yanzu yaushe. Zaka turo? Ya yunkura ya tashi zaune yace bashine matsalar ba wadanda zan turar sune matsalar ta dan bata fuska tace ai ba za ka rasaba "Danliti ko yan dattijan daku ke gaisawa sun isa su wakilce ka ko kuwa? Ya zura mata ido duk sun juye, yace haka ne sai ki baru in gan su mudaidaita tukunna sannan in gaya miki ranar daza su zo ko" tace shi ke nan bari in kwashe sauran kayana in koma gida ya kara matsarta haba tun yanzu ?" Umma ta ce kar na dade kuma tunda sun amince da kai ai zaka rinka zuwa ne kan ka tsaye,"ya kankameta ya na fadin haka ne amma ban so ki tafi yanzu sonki kawai ke azabtar da ni ina kewarki da yawa jiya da kyar nayi barci kinji yadda ki ke tashin kamshi?gaya min dame dame ki ka shafa in karo miki irinsu?"Bata iya bashi amsa ba don tun tafiyar su yake koya mata irin wannan renon ya gama da rayuwar ta gaba daya kai ALLAH ka raba mu da sharrin masu sharri,magariba ta wuce wadan da sukaje masallaci ma sun koma gida yayin da mama ta fito daga shagon Danliti jaye da katuwar jakar kayanta. -yar tafiya kadan ya taka mata ya dawo abinsa bata sami dan dakon da zai daukar mata kayanba ba don haka da kanta tayi ta ja har gida abba da umma na zaune a falo dauke da bakin ciki maras misaltuwa mama ta turo kofa ta shigo sa sallamar ta dauke da uwar jakar kaya babu wanda ya amsa mata ta wuce ta gabansu ta tsugunna tace sannu abba, wani irin kallo yayi mata mai isar da sakon haushi da takaici kafin yace daa ina kike?ta dan sunkuyar da kai tace naje gaya wa Danliti sakon ka ne ai na gayawa umma kafin na fita ko um..."Ya daka mata tsawa rufe min baki don ALLaH shine zakije ki zauna har bayan magariba kiji tsoran ALLAH mama ki sani cewar mutuncinki ki ke zubarwa wannan uwar jakar da kika shigo da ita tawace tukuna? idanuwanta suka kawo kwalla ta fara rawar murya na...nawa ne.. Kayan da...Danliti ya siya min ne yace to ba a gidan nan ba idan yazo ki maida masa kayansa ya baki can gidan sa,ai kinji ni ko,?ta amsa da kai umma ta cire tagumi ta kare mata kallo sannan tace Alhaji ya kamata a tuhumi yarinyar nan idan idan tabada kanta gareshi kasan istibira'i ya kamata, kafin a daura auransu domin ni banyarda da mama ba a yadda suke tare da yaron nan,ya numfasa ciki da bacin rai yace ki na da gaskiya don ni ma wallhy ina wasi wasi cikin raina ke mama ki gaya min tsakaninki da ALLAH ki fi jin tsoran sa akan komai na duniya ki gaya min gasjiyar abinda ke tsakanin ki da Daliti kar kisa muyi kuskure da gangan idan kin san da wani abu to ki gaya mana mubi tsarin da ALLAH ya shimfida. -sosai ta goce da kuka murya na rawa tace ALLAH abba babu abinda ya shiga tsakanina da shi duk sukayi shiru suna dubanta kamar sun gaskanta ta kamar basu yarda ba amma dolensu yarda tunda basu da wata hujjar kama ta don haka abba ya daka mata tsawa ya isa don ALLAH tana wani bare baki kamar mummuna tashi kiba mu wuri kuma na gaya miki yana zuwa ki maida masa jakar kayansa,ta goge hawaye ta dan sunkuyar da kai tace yace ya gode insha ALLAH zai turo din suka yi banza da ita shiyasa da dago ido ta dube su uwar hararar da ta yi arba da ita tilas tasa tayi saurin maida kanta kasa jim sun kikara cewa komai yasa ta mike simi simi ta janye jakar ta, ta wuce daki bakin nan tamkar na agwagwa kai tsaye bayi tashige tayi wanka ta dauro alwala ta fito ana ta kiran issha'i,don haka tana yin magariba ta dora issha'i bayan ta kammala ta fito neman abinci nan falo sukayi kicibis da yaya ali wai me ki ke nufi baza kizo kiga amarya ba?ta kama kugu hannu biyu tace wannan amarya an damu nazo na ganta hala tafini kyau ne ya kama dariya kafin yace soosai kuwa tafi ki kyau muje ki ganta tace haka yake amma duk kyanta dai ni aka fara so kifin ita saboda haka a daga min kafa inci abinci tukuna"kalamanta sun ruruta wutar zuciyarsa ba kadan ba koda ganin yadda jikinsa ya saki kasan ya fada wani yanayi ya zura mata ido hannayensa rungume a kirjinsa murya sanyaye ace zancan ki dutse yar uwata,. BAKIN CIKI 2***13 hasalima rashinki yasa na aure ta koda yaushe ki kace da ni kule da sauri xan ce cas mama don son ki ya zauna a raina, tayi yar dariya tace yaya ali ke nan kar kasa amaryar ka ta tsane. Ni daga wasa sai ka hau jera zance!ba haks nake nufi ba yaya ali muje kawai naga amarya in na dawo na ci abincin bata jira yace wani abuba ta yi gaba abinta tilas ya biyo bayanta yana kada kai!Amare kam masha ALLAH suna dauke da tasu baiwar da ALLAH yayi masu musamman aminar yaya ali har mama na masa tsiya wai ya kamata ya maida sunan sa aminu dan su kara dacewa da juna kallon ta kawai yake yi cikin ransa shi yasan babu wacce tafi dacewa dashi face ita kanta maman,bata wani dade ba ta dawo sasan su ta dauko leda cike da kayan garar amare bayan ta gama cin abinci ta zauna gaban madubi tayi wa fuskar ta kwaskwarima tayi zaman jiran Danliti har barci ya fara dibarta bataji aiken yaro ba,ta kwana zullumi da juyayin abinda ya hana Danliti zuwa alhalin ya sami izinin yin hakan ko har yanzu bai amince wa ransa bane?ya gudun kar yazo ya fuskanci wulakanci!wannan tambayar taso ta hana ta barci domin ta kai sama da karfe dayan dare bata sami barci ba,Da sassafe ta tashi da ciwon kai wanda ya haddasa mata jiri akai akai duk da haka ko karyawa bata yiba karfe bakwai da rabi tasa kai ta fice babu wanda ya sani ta nufi wajen Danliti dauke da ledar kayan garar amaren da aka bata jiya ita ta tashe shi barci ya tashi a gigice yana tambaya lafiya kika bugo sammako haka?tace nayi zaton zaka zo jiya hira me ya hana ka zuwa. ya ja dogon tsaki ya kauda kai jim sannan ya juyo ya dubeta wai me ke damun kine?ba kinzo nan ba sai bayan magariba kika tafiba?to kuma me zanje in yi maki saboda ALLAH ta zura masa ido ya kare mata kwakwazo nan take idanuwanta suka tara kwalla murya na rawa ta ba haba Danliti laifi ne don ban gan kaba na biyo in duba ko lafiya?ya bita da kallo tana ta gugar kwalla ya kece da dariya kamar mahaukaci hakan yasa ta daina hawaye ta zuba masa ido yayi dariya mai isar sa sannan ya natsu shima ya bita da kallo to meye abin kuka ni ina can ina ta billayin neman mana waliyai ai banga ta zaman fira ba sakeena"nan da nan ta hadiye tashin hankalinta ta fara murmushi duk kin wani daga hankalinki don baki ganni ba jiya kawai " kawai ne? In gaya maka dai dai da sakwan daya bana son zama babu kai,yayi wata budurwar dariya yace ko to na kara baki tukuicin kaina ta kwanto masa tana dariya kasan ALLAH da ciwon kai na tashi ga wani jiri na diba na amma na kasa daurewa na fito ko karyawa banyi ba, yace ai ya bebi na sannu ko ya kamata mu karya ki sha magani bari inzo. Ya fice ya bar ta kwance bisa katifar wucewar minti ashirin ya dawo da soyayyun kwai da naman kaza da doya itama hade da kwai ta hada masu shayi suka batse cikinsu harda ayuba anan ta yada kafada daga fira barci ya kwasheta Danliti ya dawo shago ya zauna tare da ayuba ya zura masa ido yace don ALLAH ka tasheta ta koma gidan su yayi banza dashi ya fito yana zuba fito kamar katon arne. -Ayuba ya kada kai yace karshen alewa kasa Danliti idan an ciza a rinka hurawa ya ballo masa harara ya ce ba ruwanka malam ka kyale ni in ci lokacina ya tabe baki yace na barka zaifi kyau suka yi shiru kowa na harkan gabansa, a gida kuwa tunda suka shafa babu mama a dakin ta suke ta kwasar BAKIN CIKI don sun tabbata tana can shagon Danliti karfe tara uban dawaki ya gama shirin sa zai fita ko karyawa bai yi ba saboda tsabar takaici yasa umma ta fito masa da jakar kayan da mama ta shigo dasu ya sunkuta yayi waje da ita kalla ya tarbe shi da sauri ya amsa ya bude but ya saka Abba yace minna zasu tafi amma zasu tsaya shagon Danliti, kalla yaja mota suka wuce yayi fakin kofar shagon abba ya umarci daya fito masa da jakar nan kai tsaye ya wuce shagon lokacin da su Danliti ke ta harkokinsu yayi tsaye babu sallama har hankulansu suka juyo gareshi Danliti ya matso yana fadin sannu alhaji ina kwana yace nasan mama na nan tare da kai ina take baki sake yace tazo amma ta tafi yayi jim yana kallonsa kafin yace ba shi ya dame ni ba wannan ya rage kuda ubangiji ina fatan. Ta gaya maka yace ta gaya min kokarin da nakeyi ke nan na samu na turo yace kar ka bata lokaci domin na kosa na kauda kazantar da nake gani ya dan sunkuyar da kai yana murmushin izgilanci naji abba in ALLAH ya yarda zuwa anjima ko gobe zan turo yace shike nan ina sauraronka amma ga kayan ka nan ka aje idan ta tare gidanka sai ka bata ba na bukatar komai daga gareka sai sadakin da ALLAH ya wajabta ga jakar nan bai saurari wani abu ba yasa kai ya bar shagon ya fada motarsa kalla ya ja suka dauki hanya Ayuba ya matso gare shi yace, Allah na tabaka dama, don ka gyara kuskuran ka Danliti, kar ka bari ta subuce maka, ka dawo kana cizo yatsa. Ya watsa masa harara yace bana bukatar wa'azinka alaramma karfa ka manta da ni da kai duk daya ne. Na ma dai san abinyi, ayuba ya xuba masa ido ya rasa ta cewa babu abinda ya sami Danliti, yasa hannu ya dauki jaka ya shige da ita. Hannu 2 ya rike kugu, yana kallon mama xucyarsa na masa sake-sake. Kusan 5mins yana tsaye, sannan ta tsugunna ya bubbugata. Ta farka tana yamutsa fuska, menene? Tashi kiji? Ta yunkura ta tashi xaune, yasa hannu ya kara janyo jakarta, don ta ganta sosai. Cike da mamaki tace waya kawo ta? Yace, abbanki mana! Wannan kadai ya tabbatar min baya sona, baya kaunta. Bai dameni ba, amma me yasa zai uzzura min dole sai na turo magabata na yanxu-yanxu? Hankalinta ya tashi, ta matso a hankali ta dafa kafadarsa. Don girman Allah kar hankalinka yatashi Danliti.... Cikin sababi. Yace ki daina gaya min wannan maganar! Kora da hali abba ke min, saboda haka ki hkr, kije su baki wanda suke so! Tashi ki bar dakin nan, kar kuma ki sake xuwa, ni babu ruwana! Ta narke da kuka, murya na rawa tace, karka yi min haka Danliti, ina mai tabbatar maka xan kashe kaina idan ka juya min baya. (Kuji banza mtsw :(). Ya cire hannunta daga jikinsa yace, ni ban aikeki ba ya kamata ki gane ki gane ba dole bane na aureki. Don me xa a daga min hankali akan magabata? Banda su, uban wa xanje na tura idan ban nema ba? Kinga ki tshi kije ki gaya musu na fasa. Ta marairaice kamar ranta xai fita ni ina sonka Danliti ba xan iya rabuwa da kai ba, ai dai ni xa'a daurawa aurenko? Xan gaya musu su kyaleka, sai ka shirya. Shikenan? Ya kara murtue fuska, yana kallonta bai tanka ba. Takara matsarsa sosai taci gaba da fadin, muddin suka ki yarda da uxurinka wlh na yi rantsuwa xasu sha mamaki dan wlh nan xan dawo na tare..... Ok, ki sa a daureni kenan? Tace wa xai daureka? Don Allah ki kyaleni ni bana son surutu, tashi ki tafi kawai, sai na nemeki! Dan..... Ya daga mata hannu, idan baki so raina ya baci to ki tashi kawai ki bar dakin nan! Ta cigaba da share hawaye, ta xura takalmi ta dauki mayafi ta mike xata wuce, amma ta kasa, tayi tsaye tana kallonsa, don Allah kayi hkr Danliti. Ya dago ido ya dubeta, hawaye keta ambaliya, yayi dan jim, kafin yace nayi hkr, amma kije tukunna xan nemeki. Xaka xo gidanmu? Eh xan xo ki share hawayen, ba wani abu. Ta share da sauri ta duro bayansa, Nagode Danliti na! To kayi dan murmushi mana ko naji dadi mana. (mayya :() Ya banbare hannayen ta ya mike tsaye, karki damu da murmushina, muje in rakaki, kafin tace wani abu, ya fice, dole ta biyo bayansa, bakin shagon kawai ya tsaya, yace sai nazo ko? Tace, daga nan xaka tsaya? Xan wuce neman wadanda xan turo din ne. Nan da nan sanyi ya ratsa mata xuciya, baki har kunne. Tace, Allah sarki nawan, to sai mun hadu anjima. Ya daga gira yana fadin, sai mun hadun, yana sakin tsaki. Tana shigowa dakinta, ta shige, motsinta kawai Umma ta jiyo ta biyo ta dakin, tana kokarin cire kaya, don shiga wanka. Umma ta kare mata kallo, ta kada kai, tace don girman Allah mama ki rinka xama a gida. Tunda Danliti na sonki kuma abbanki ya bashi dama ai shi xai biyoki. Kullum inaga ya miki babu mutunci ga 'ya mace ta rinka bin saurayi har makwancinsa. Ko bai aikata miki komai ba jama'a ba za su dube ki da mutunci ba. Me yasa Danlit ya sauya miki tarbiya.? Tayi shiru tana ciccika tana batsewa, Umma tacigaba ni rokonki nakeyi, ki taimakemu ki taimaki kanki, don mu tsira da 'yar martabar da tareg mana a idon jama'a. Kinji? Ta amsa da ka, kafin tace, Umma idan abba ya dawo ki fada masa ya daina matsawa Danliti akan turo magabatansa...... Ta katseta kamar ya? To umma tunda an gayama sa kuma ya amsa xai turo din, ba sai asa masa ido ba? Ta mako mata harara, bangane asa masa ido ba? Shi daman can bai shirya auran ba, ya hanaki sauraron wandan ya shirya? To baku isa ba, mu ba wasa mukeyi ba, tunda ya hure miki kunne dole ya gaugauta turowa, ya raba da mu da bakin ciki da muke gani, kinji nagaya miki. Tayi ta tashi tana fadin, to shikenan ai matsa masa ba shine xaisa ya turo din ba. Me kikace? Ta shige bayi da sauri ta rufe kofa. Mama ni kike wa rashin kunya? Lallai kin rika, kina gab da tsinka min mari akan Danliti. Sallamar da jiyo, shi yasa tayi shiru. Ta mike ta fito tana amsawa. Inna saude ce da Baraka, saude sannunku da xuwa. Duk suka amsa, yayin da Baraka ta tsugunna ta cigaba da gaisawa. Bayan sun nutsa a falon, inna saude tace, tun jiya naso fitowa, wani axababben ciwon kai ya addabeni. Tace ayya ina fatan yayi sauki. A'a da sauki, ina maman? Tana ciki ta shiga wanka.... Wai dama saboda ita kika zo? Ai da kin yi kwanciyar ki kin huta, domin al'amarin Mama ya zama jiki. Tace, ya xama dole in taso yaya. BAKIN CIKI kuwa baya taba zama jiki sai dai imani. Allah dai ya bamu ikon cinye jarabawar, ta nisa tace amin. Tace, yanxun me kuke ciki? Ta fada mata yadda al-amarin yake, ta cire tagumi. Tace haka shi yafi dacewa, in ma banda sakarci ba ita xata taimaka mana ya turo da wurin a huta ba. Tace ina fa, ai ina mai tabbatar miki tafi son shi akan mu. Allah dai shi kyauta. Ta amsa da amin. Suka ci gaba da hira har suka ji motsin fitowar Baraka ta tashi ta shige dakin. Ba suyi wata hirar kirki ba, domin ra'ayinsu yasha bambam yanxun. Duk mai zagin Danliti Mama bata ganinsa da kima haka ta fada ma baraka, shiyasa ta shiga taitayinta, tafito daga dakin tace xata ganin amare. Mama dataga shirinta can ta sameta dakin amaryar Ya Ali, nan suka shantake, sama da 2hrs sai da Inna saude ta shiryo tafiya tasameta can, ita ma bata yi ma Mama maganar komai ba akan abinda ta aikata. Domin a tunaninta babu wata bakuwar kalmar da xa agaya mata wacce bata sani ba. A wannan daren mama tasa ido taga xuwan Danliti shiru kakeji yasa ta jin haushin rashin dawowar abba. Al- amarin nata cizon ta taga ba xata daure ba, karfe goma harta goa, ta fito ta bude kofar ta fice abinta. Ko kafin Umma ta fito taga wanda ya bude kofar mama har ta kai kofar gidan, ganin bata a dakin ya tabbatarma da Umma ita ta fita. Ta nemi kujera ta xauna hannunta a kunci BAKIN CIKI ykamar ya kasheta. Take nan taji xuciyarta na ciwo, wani abu dum! Cikin kanta kamar xai makantar da ita, tasbihi ta shiga jerawa ko ta samu saukin kan. Ita kuwa mama Tunda ta kwashi sauri bata sausauta ba sai da taje shagon mutumin nata ta ja birki. Ayuba na xaune daga ciki, taga kanta ta shiga tare da sallama. Ya amsa mata ta wuce tana fadin sweetyna naciki ne? Da sauri ya amsa mata ai bayana nan bai gaya miki bane? Ta tsaya cak dauke mamaki, ina yaje? Ya amsa gaskiya bai gaya min ba, cewa yayi xaiyi tafiya kawai. Na xaci ya gaya miki daxun. Ta kada kai, bai gaya min ba wlh, amma xai dawo gobe ko? Yace watakila, ta danyi shiru sannan tace to shikenan sai goben. Allah ya kaimu. Taga kanta ta fice, ya bita da kallo. Duk tasuayinta ya lullbe shi, aransa yace Allah ya kubutar dake daga sharrin Danliti. To nima nace AMEEN! Da babbar murya. Tana tafe tana sakar xuci, wai duk fushin ne yasa Danliti yatfi ba sallama? Ina xansa kaina idan kalaman Abba suka korar min Danliti? Bata samo amsa ba taji ann fige mayafinta, 'yammata ji mana! Firgigi ta waigo hankalinta ta dubi gungun samarin da suka kai kusan shida, kowanne su dauke yake da tabar wiwi. Ta dora hannu bisa kai wayyo nashiga uku, duk suka fashe da dariya, ina kika nufa mu rakaki? Ta durkusa kuyi hkr dan Allah, dariya kwai suke kyakyatawa, 2 daga cikinsu suka kawo mata cafka. Ta xabura ta mike, Allah ya taimaketa ta kutsa ta cikinsu ta xura aguje, dawa Allah ya hada su ba da ita ba, ta watsar da takalma, ko daman gyalen yana hannunsu, taci gudun fitar rai, ta rufta cikin gida, yayin da alh. Adamu, ke kokarin rufe gidan, bakara min figita yayi ba, amma yayi axama ya maida kofar ya jefa sakata. Mama kuwa tuni tana sassansu, ta fadi warwas! Tana maida numfashi tamkar xata mutu, Alh. Adamu ya biyota, ya isketa daidai kasa, ya xura mata ido kafin yace, wai daman mama ce kartin Maxan nan suka biyota? Me kike a waje har 11pm? Umma tayo waje tana sallami, ganin mama a kasa yasa ta dafe kirji lfy? Ya dubeta ido waje, yace, yanxun saboda Allah me yarinyar nan take a waje cikn duhu? Kinga kartin da suka biyo sunyi su 10, wannan ai diban albarka ne da iskanci. Jiri ya soma dibar Umma tana fadin me? Innalillahi Wainna ilaihir raju'un kasan Allah, Alh. Adamu har na rufe kofa naji motsin fitarta, xaune nake kawai narasa inda xansa kaina dan BAKIN CIKI! Ban san yadda mama ta maida rayuwarta ba......... Tana rufe baki, tayi kasa da dafe kirji, saboda ciwon da yake tsananin yi mata. A hankali hawayenta ke fita tana fadin, BAKIN CIKIN ki zai kashe ni Mama.... Alh. Adamu ya daga murya yana masifa, kin shiga 3 mama! Kin maida kanki 'yar iska da karfi da yaji, to ki bi a hankali, muddin kika bari BAKIN CIKI ya kashe mahaifanki, kin buga babbar asara, tashi ki ba mutane wuri, kafin in taka ruwan cikinki. Ta yunkura ta tashi da kyar, amma ta kasa mikewa tsaye, a duddauke ta shige falo a tym din har mutanen gidan sun fara taruwa, don ji me ya faru, Alh Adamu ke daga murya cikin dare? Nan take ya maida yadda akayi har ya dora karya, wai kartin har sun turmusheta, tsawat da yayi masu, yasa suka gudu. Kowa tafa hannu yakeyi yana salati, kusan 12am suna xuba magana. Sannan kowa ya koma sasansu, aka bar Umma kwance da ciwon abubuwa barkatai. Ya ali ne kadai bai tanka ba, don BAKIN CIKIN sa na gaske ne, tamkar yadda UMMa takeji cikin xuciyarta. Dakin amaryarsa ya koma yana kuka da hawayensa. Amina tayi rarrashinsa tana nuna masa addu'a Mama tafi bukata ba kuka ba. Mts!.... Amina ba zata gane ba, BAKIN CIKIN dake cin angonta ba xai iya jurewa ba, tilas sai ya matse shi. Hasalima ba zai iya zama yana kallon irin wadannan abubuwan ba, gara ya koma bakin aiki ko ya kauracewa idanuwansa ganin abinda ya fi komai daga masa ciwon xuciya. Saboda haka yacewa amina ta shirya kayansu gobe zasu koma birnin gwari da yardar Allah. Al'amarin ya daure mata kai, kuma tayi tambayoyin da bata sami amsarsu ba. Washe gari da suke shirin tafiya, taji fashin baki na bakin Haj. Hajjo. Eh lallai biri yayi kama da mutum. Nan take kumallon mata ya taso mata, ya dasa mata kyamar Mama cikin ranta har tafi Ya ali kosawa su bar garin. 12pm kuwa ya samo shatan mota suka damki hanya. Mama bata ma san anayi ba, tana can tana murkususun ciwon ciki ita kadai a daki. Don ko daya shigo yin sallama da umma bai shiga wajenta ba. Sai wajen azahar barci mai nauyi gaske ya dauke ta. Haka ita ma Umma ke ta gyangyadin takaici bisa kujera. Rabonta da abincin kirki tun jiya da daddare motsi taji a falo ana shigowa da kaya, ta taso da sauri ta leko falon. Kalla ta gani da tsirin kwalaye ya aje gefe yana gaisheta. Ta amsa da fara'a ta karfin hali. Bai karasa ficewa ba, abba ya kawo ka falon tilas ya rabe gefe ya bashi wuri ya shigo, sannan ya fice. Alhajin yana fadin, agaida Iyali, yace xasu ji. Kallo daya yayi wa Umma gabansa ya fadi, ya amsa sannu da xuwan da tayi masa. Ya xauna falo. Yayi da ta shiga kitchen dauko masa ruwa ta kawo masa ta xauna gefe tana kara masa sannu da xuwa. Bayan yasha ruwa ya numfasa. Tace an dawo lfy? Ya amsa lfya lau, duk suna gaisheki, ni ne har abuja, daga can na xarce kd yau da safe. Tace, wai kunsha hanya, ina fatan duk lfya ka baro su? Yace kalau, amma sai naga kamar kin rame, ina fatan ba ciwo ne ya tashi ba? Ta kada kai. Kai dai bari Alhaji, ciwo na ba zai taba warkewa ba, idan ban ga yarinyar nan dakin miji ba. Kaci abinci tukunna, kaji abinda ya faru jiya. Yayi dan shiru har ta mike xata dauko abinci kafi, yace ki gaya min kawai Halima, nasan babu bacin ran da xanji wanda ya wuce na baya. Ta dawo ta xauna ta fede masa abinda ya faru. Ya kada kai. Yace ya rage nata, ba burinta ta fita duk tym da ta ga dama ba? Jikinta xai gaya mata, xata gane akwai wadanda suka fita iskannci. Yanxun tana ina? Tana daki, ni yau ko kalarta ban gani ba. Bata xo ta gaisheki ba ke nan? Tace ni a suwa? Bana ma bukatar gaisuwarta, amma tun jiyan na gaya mata idan na mutu, ta sani BAKIN CIKIN tane ya kasheni. Yace, ba xaki mutu ba Halima da Yarda Allah mama ba zata salwantar min da rayuwarki ba. Karki manta, su hudu kika haifa, kuma Allah ya albarkace su dubi tsibin kwalayen nan, duk sakonki ne, kowa na da sa nau'in tsarabar, zabi kalar abubuwan da kika fiso. Bayan haka, jibi asabar duk zasu hadu anan, don su share mana hawayen kukan da Mama ta samu. Don kuwa zau tsaya tsayin daka dole Danliti ya turo wakilnsa a daura masu aure a cikin satin nan. Saboda haka ki kwantar da hankalinki, ki na dasauran 'yal3an da suke bukatar ki kusa da su a koda yaushe. Kinji ni da kyau? Ta goge 'yar kwallan da suka xubo mata, tace naji alhji, Allah yayi musu albarka baki dayansu. Yayi murmushi yana fadin, amin kina iya dauko abincin yanxun. Ta tashi da saurinta, ta wuce, ya raka da ido tausayinta ya kwarara cikn ransa. Ya numfasa yace, mun gode maka Allah da wannan jarabci. Ta fito masa da abin, ya gaugauta ci, domin gab ake da kiran la'asar. Ya kammalawa kuwa tym yayi, ya mike yana fadin, ki shiga ki tasheta tayi sallah. Ta amsa da to, ya wuce dakinsa. Umma ta kwashe kayan ta maida kicin, sannan ta nufi dakin Mama, don tashinta. Tana kife ruf da ciki, Umma ta dada mata duka ta tashi a firgice. Umma ta xura mata ido, tace, in kin ga dama ki tashi kiyi sallah! Tayi waje ta bata wuri. Da kyar ta mike zaune, kanta ya sara mata, ta dafe shi hannu biyu, gaba daya miyan bakinta ya kafe. Makoshin ta ya bushe. Tana daga xaune, amma jiri ne ke dibar ta.... Idanuwanta na ganin duhu, don haka ta runtse su tamau! Tana maida numfashi, ta wuce minti sama da goma ahaka, sannan ta iya tashi a daddafe ta shiga bayin. Tunaninta kawai tayi wanka ko tafi jin dadin jikinta. Nan da nan ta kwashi ruwa a bokiti ta fara wanka. Kamshin sabulun( Joy) Ya gauraye bayin, ba xato ba tsammani taji xuciyarta ta tsani kamshin, kan ka ce kwabo ta goce da amai. Ta kwarara mai isarta, wai don ma babu komi cikin nata. Tana gamawa ta dauki bojitin ta juye ruwan ajikinta, tun daga kai. Ta jefar da shi ta yayo xani ta daura, ta banko kofa ta dawo daki, ta bar bayin face face da amai. Ruf da ciki ta sake fadwa gado fadi take, wash! Wayyo Allah xan mutu! Tun daga tym din al'amura suka kwance mata, ta rasa kanta ta rasa meke damunta tana rashin son abinci da yawan tashin xuciya, ga wani cikin safe da jiri wani tym din jikinta yayi xafi, don kansa kuma ya sauka ba tare da tasha magani ba. Duk ba wannan bace babbar Matsalarta ba, Ina Danliti ya shiga kwana 2 babu labarinsa? Me kuma yake nufi da tafiyarsa? Duk da cewar tasan dole ya dawo, idanuwanta da xuciyarta sun gaza jure rashin sa na 'yan kwanakin 2. Shi yasa koda yaushe tana kunshe a dakin matsalolinta masu yawa na neman xautar da ita. Umma da kanta bata gane kanta ba, musamman rashin xuwanta neman abinda xat ci. Amma yawan xaman daki umma ta jingina da rashin ganin Danliti da ta rataywa xuciyarta, balle ayi maganar jingina shi da wanccan Matsalar. Ta kan kada kai, tace, kaico! Abincin wani, gubar wani! Allah ka raba mu da muguwar kaddara... A yau asabar ake sa ran xuwan yayyin Mamma, ga shi babu magana mai kwari ko kuma muce uban gayyar baya gari, shi da kansa abba xaune yake shiru dakin ta same shi, ta xauna gefensa tace, kana xaune baka shiga wanka ba? Yayi gajeran tsaki, yace maganar nan ke damuna, da yarinyar nan xata gane da ta amince cewar Dalinti ba xai turo kowa ba. Banda aikin rashin gaskiyya, menene na kama hanya kabar gari, kai da aka ba damar ka aiko a baka mallakar abinda kake so. Wane bata tym xakayi saboda Allah? Ta numfasa, tace yaushe xata fusknaci hakan yadda ta makance gaba daya, bata ganin kowa sai shi? Ai na gaya maka ko abinci bata ci, duk ta fige saboda bala'i, ni yaran nan ma dasu wahala suke nake tausayawa ba su gama warware gajiyar biki ba, ga aikinsa mai dan banxan wahala, da da halin da xa'a ce da su dakata, wlh da ance suyi xamansu. Ya gyara xama kyale su suzo ko hira mukayi, ai maji dadi, ko ba haka ba? Haka ne, Allah ya kawo su lfya. Amin ke ki kira min Mama ta zo yaushe, dan liti xai dawo? Ta mike ta nufi daki Mama ta tura kofa kakarin amai ya fara dibar hankalinta, cikin fargaba ta nufi kofar bayin ta murda ta bude, Mama! Tana durkushe kame da ciki, kamar xata mutu. Kan Umma ya kara daurewa, domin bata taba ganin Mama na kwarara amai haka ba. Ko rashin lfya takeyi, bata amai, sai dai xafin xaxxabi. Don haka ta nufe da sauri ta dafe ta, me xan gani haka Mama, baki da lfya ne ko yaya ne? Bata iya amsa mata ba, tana tsaye kame da haba, tagama kakarinta, ta kuskure baki hade da fuska, tayo waje abinta, ba tare da kula Umma ba. Bisa gado ta fada ta datse ciki tana numfarfashi. Umma ta biyo a fusace tasa hannu ta birkito ta, ba kyajin ina magana ne? Nace lfya kike sheka amai? Ido jajur! Cike da kwalla tace, cikina ke min ciwo, tun yaushe? Yau 3days. Ta jawo ta waje cikin haske sosai, ta kama hannayenta ta dudduba, sannan ta gwale idanuwanta, ta duba cikinsu, a tsorace ta tambayeta ke, kina yi al'ada kuwa? Tayi shiru tana xaxxare ido, baki na rawa tace, nima ban sani ba Umma. Ba ki sani ba? Ke xaki gaya min ko sai na farfasa bakinki? Ta goce da kuka, don ita ma ta kideme, ta mance rabonta da a'alada. Umma ta xura mata ido, jinin ta na kara hauhawa, da sauri ta wuce ta bar mama tsaye. Dakin abba ta koma ta xauna, ta rike kai tana maida salati. Me akayi? Tace alh. Magana takare ka dauki mama ka kaita asibiti ayi mata gwajegwaje! Gabansa ya fadi gwajegwaje? Name kuma? Na komai Alh. Ina shiga na sameta tana sheka amai a bayi, wai cikinta ke ciwo, amma alamu a bayyane sun nuna Mama juna 2 gareta........ Tsaye ya mike tare da fadin me? Hawaye suka kara tsunke mata, ya koma a hankali ya xauna bakin sa na karanto salatin Manxon rahma. Gaba dayansu tsit! Sukayi tsawon lokaci sai Umma ke shatatar hawaye, baiyi aune ba kawai ya ga ta dungura ta fadi a sume. Ya xabura ya tarairayota, yana kiran Halima! Halima!! Don girman Allah karki kara min tsahin hankali akan wanda nake ciki, ya jawo goran ruwa ya xuba a hannunsa, ya yarfa mata, ya cigaba da shafa mata ruwan bisa fuska, ahankali har ta dawo hayyacinta. Ta bude ido, jim tana kallonsa, sannan ta sake fashewa da kuka, nan take tausayinta, yasa kwallan Ubandawaki suka fara sauka bisa kuncinsa. BAKIN CIKI kamar ya aika shi barxahu. Kiyi hkr, ki kwantar da hankalin ki Halima, wannan jarabawa daga Allah Ubangiji take, babu wanda ya isa ya kankare mana ita, bana son tsanin damuwar nan da kikeyi, tana jefa ni mummunan matsayi, ko dogara da Allah Halima shine xai magance mana komai. Ta goge hawayenta tayi, iyayinta don ta tashi xaune amma ta kasa. Yace kar ki damu da sai kin tashi yanxu kiyi kwanciyarki ki huta, bari in kwaso magungunan ki in duba wanda ya dace kisha. Ya mike da sauri wani duhu ya rufe masa idanuwansa, bai ganin komai face wasu miliyoyin taurari kanana, tilas ya dawo ya xauna ya fadin Hasbinallahu wa nimal wakil. Yayi ta maxa ya sake mikewa. Umma tace ka xauna Alhaji kar kaje ka fadi ka nakasa. Bai tanka ba, ya fice. Jimawa kadan ya dawo da kwanndon magungunan ta ya xauan yana bincikawa, jikinsa na rawa saboda bacin rai. Sallama sukayi daga falo kuma babu tantama muryar Ya abdurahman ce, abba Ya amsa, ya kara da fadin gamu nan, ku karaso ciki. Ganinsu jugun2, Yaya take ya rasa kuzarinsa. Yaya dai Abba? Jikin nata ne ya tashi? Yace shine abdulrahman, nan da nan ya xube gabanta, da dauko kanta ya dora bisa cinyoyinsa, sannu Umma! Sannu! Ta matse kwalla, ta dube shi, kaxo lfya? Ina safiyya? Ya amsa lfya lau take, tace in gaisheki. Ina amsawa, me yasa baka xo da ita ba? Ya goge mata kwalla, tayi nauyi ne Umma bata jin dadi, idan tayi doguwar tafiya, koda muka koma, bayan daura aure sai da tayi xaxxabi. Ta dan kada kai, tace Allah sarki, Allah ya raba su lfya. Amin. Ya amsa sannan ya dubi Abba suka gaisa. Kafin su kama wata maganar, muryar Manyan yayin ta gauraye cikin falonm. Abba ya gaya musu suna ciki, kowa ya shigo da kuzarinsa, ya ga Umma a kwance sai yayi turus! Bayan sun gaisa tasha magani. Abba ya kwashe abinda ke faruwa kaf, ya gaya musu, kowa yayi shiru, kawunansu sunkuye tsawon tym kafin Ya soja, yace, yanxun Ina Maman take? Oho inji Abba, gaba daya sukace oho? Ta bar gidan nne, Umma tace tsakar gida na barya tsaye, ban sani ba ko ta koma daki ko ta fice don ba sani xamuyi ba. Duk tym din ta so fitarta, ficewa ta takeyi. AKIN CIKI 2***14 Ya soja ya dubi Ya abdulrahman, yace je ka kawo mana ita nan! Ya miki cikin hanxari, ya nufi dakinta, tana kife bisa gado aikin kuka kawai takeyi. Ya sa hannu ya fisgota, ba karamin tsoro ya bata ba, ta kwala ihu, wani BAKIN CIKI ya kara turnuke shi, bai san tymda yasa hannu ya doke bakinta ba, yace rufe mana baki shashasha. Da sauri ta kame baki, wanda take kyautata xaton hakoranta xasu iya xaxxagow idan bata dafe shi ba. Ahaka ya ciga da jan ta har dakin abba. Gaban babban ya direta, ta xube har tana karo da guiwarsa. Ya xuro mata ido kamar zasu fado kasa. Yace matsa kdaga kusa dani, xan iya tokarinki, ki mutu idan baki matsa ba. Ta janye jikinta baya, ahankali hawaye na ambaliya, sunfi minti 5 babu wanda tanka saboda takaici, kafin Ya abdulkrm yace, gaba daya kin rusa rayuwarki Mama kin lalata cikar asalinki da martabar iyayenmu. Yanxu wa ya isa ya kankare bakin fetin da kika shafawa kanki? Wa ai daura miki aure da ciki? Wa kuma xai jagoranci kisan kai? Wannan cikin dole ki haife shi, domin yunkurin xubda shi, ya fi yinsa barna da tarin xunubi. Kin ga tun daga nan idan kinyi tunani cikin hankalinki, xaki gane babu soyayysa tsankaninki da Danliti. Burinsa dama ya ruguxa rayuwarki, burinsa kuma ya cika tare da hadin kanki. Saboda haka dabara ta rage wa mai shiga rijiya, sannan karki xargi Danliti, idan ya tsallake auranki, gaba daya abinda yake bukata ya samu, abinda yai saura shine ki haife masa wannan ckin, in ya ga dama ya karbi dan, idan bai yarda ba ya kyaleki da shi, ku wulaknta. Dama wannan shine karshen son xuciya. Babu uwar kudi balle riba ga mai cinikin son xuciya. Kuma duk wanda ya hau motar kwadayi da son xuciya, babu tantama tashar kunya da nadama xata kaishi ta aje. A koda yaushe karshen danasani, ina fatan wannan xai xama darasi gareki, ki gane cewa abinda Babba ya hango, yaro ko ya hau gwauron dutse ba xai hango ba. Ya goge 'ya kwallan da suka xubo bisa kuncinsa sannan ya sauke numfashi ya dubi sauran, yace yanxun mene abinyi? Abba yace abinyi babu shi abdulkrm, tunda maganar aure ta rushe a halin yanxun. Ya Soja yace duk da haka, dole ya san tana dauke da cikinsa, bayan ta haihu xa a daura musu aure, su tare da yaronsu! Su karata can da abin kunyarsu! Ya abdul rahman ya kara sanyaya muryarsa mai taushi, yace wannan dole ne, amma abu na farko shine, ina xata xauna? Ta kula da kanta? Umma dai ba xata jure ganinta a wannan yanayin ba, ya soja ya gyara zama yace, gaskiya ne, kuma waje na ya kamata ta xauna, sai dai ba xan iya daukarta ba saboda xan iya yi mata dukan mutuwa yadda nake jin na tsani ganinya. So a cikinku, wanda yake ganin xai iya hkr da ita, yana iya tafiya da ita Allah ya shiryeta, mu kuma kullum addu'a muke mata, idan ta dauki wannan mtsayin darasi a gareta, xamu fi kowa farin ciki. Ya Abdulrahman, yace ni xan tafi da ita, no ka bari ni in wuce da ita Minna. In ji Ya abdulkrm. Abba yace ba xata biki ba nan da xata xauna... ban ce mata yin ku za su yadda ta ba amman yau da gobe sai Allah. gara ta zauna anan, domin anan ne suke aikata abin kunyar u kun ga ganinta da juna biyu ba zai girgiza kowa ba sanin cewar daman can sakamkon da zai biyo baya kenan. in ba wani gyaran Allah ba. saboda haka ku kwantar da hankalinku kuci gaba da yi mata addua sannan ku kwantar da hankalinku ku tallafa wa mahaifiyar ku ta kowace fuska don ganin ciwon BAKIN CIKIN bai tagayyara ta ba, dukkan su suka jinjina kai alaman uban dawaki gaskia ne. yaya soja yace da yardar Allah umma ba za ta tagayyara ba, idan mama bata son ki mu bamu da wacce ta fi ki. bamu da wani buri. da ya wuce mu rayu tare da ke. kar bacin ran mama yasa mu dakatar da dukkan farin cikin mu. mu ukkun nan mun ishe ki kallo ki samu sanyi a ranki ko umma? hawaye na suka malalo mata yaya abdul yayi maza ya rungumota ya na share mata hawayen ki daina kuka umma in kina kuka mama ba zata taba ganin haske ba, duk adduar da zamu mata tace ba komai wallahi bana jayayya da ikon Allah amman ku sani BAKIN CIKIN ba zai goge cikin raina ba, domin FARin ciki da bakin ciki duk halitta ce cdaga Allah fata na kawai Allah ya bamu ikon cinye jarabawarnan Allah yayi maku albarka Kowa ya numfasa, yace amin, abba ya dubi mama da hawayenta yaki yankewa yace, ina fatan kin ji abubuwan da 'yan uwanki suka fadi, idan kinyi anfani da su, ki ga daidai, idan kuma kin ce ba haka ba, mu babu abinda xamu iya yi, sai mu kyale ki, ki ci gaba da rayuwar da kika xaba. Ko dama kin riga kin ruguza ta, karashe ne kawai. Allah ya shiryeki, ki na iya bamu wuri mu sha iska, ki jira dawowar Danliti, amma ki sani auran ku ba shi yuwuwa, sai bayan kin haihu. Tashi ki bamu wuri. Ta kara makurewa, kukanta ya karu, duk suka xubo mata ido. Ya soja yace wa yace kiyi kuka? Cewa akayi mun gaji da ganinki, ki koma dakinki. Ta yunkura kamar xata tashi, amma ta kasa, da sauri ta rarrafa jikin Ya abdulrahman, ta kudundune ta rushe da kuka. Nan da nan ta karya masa xuciya, ko dama shi akwai sanyi da saurin jin tausayin mutum. Idanuwansa suka cika taf da kwalla, tun baya son kulata har ya kai hannunsa, bisa knta muryarsa na rawa yake fadin, imani kawai xai sa akalleki Mama, amma ke ba abar tausayi bace, tunda baki tausaywa kanki ba...... Ya soja ya katse shi, pls abdulrahman, fita da ita, Umma tace sai ma ya fita da ita? Gata kenan, ya kyaleta, ta tashi da kanta ta wuce. Ya tarairayo ta suka mike tare, ya janyo ta xuwa dakinta ya xaunar da ita bakin gado. Ya tsugunna gabanta yace, dube ni Mama. Da kyar ta dube shi, hawayen ta na xuba, yace kukanki bai da wani anfani, muddin ba nayin nadama bane. Nadamar ma ta gaskiyya, tsakani da Allah. Saboda haka ina shwaratar ki da ki kama kanki, wannan ya xama na farko kuma na karshe. Ba soyyaya vace wannan, ki dauki jikinki ki ba da ga namiji, daga ranar da ya sanki a waje. Wlh kin gama yawo, duk wulaknci da ya ga dama xaiyi miki, ko da kinyi sa'a ya aureki, abanxa xai rika kallonki, sannan wulakanci ba xai daina shi ba, a karshe ki ga auran ya bantale, tun ba aje koina ba. Kuskure ne, kin riga kin yi Mama, irin wanda bamu taba xato ba, babu yadda xa muyi mu gyara shi, sai dai kiyi tuba wajen Allah, sannan ki nemi afuwarsu Abba, kin jini? Ta xura masa ido, hawaye na ta bulbula ta kasa fadin komai, domin ita kanta bata san ainihin abinda ke damunta ba, cikin ranta agame da samun ciki ba tare da aure ba. Saboda haka, sake fado masa tayi, ta kankame shi, kukan ta kamar xai fasa xuciyarta. Ba karamin rikita shi tayi ba, domin nan take ya goce da kukan shi ma. Da kyar ya banbare ta ya mike da sauri ya bar dakin, ya dawo falo ya cigaba da gugar kwalla, xuciyarsa na masa ciwo. Kai! Sun dandani BAKINCIKI, da akwai yadda xasuyi su goge wa Mama wannan bakin fentin da sun goge mata shi, ko da shi xasu rasa komai nasu. Sai dai kash! Babu hali, shi ya sa ko abinci tsakurarsa sukayi suka ci, ba don yayi musu dadi a baki ba. Haka suka juya bayan sallar la'asar makare da BAKIN CIKIN da baya misaltuwa. Haka zalika sun bar Mama cikin wani yanayi na kunci rayuwa, wanda ya wanxar mata da cututtuka masu dama ajikinta. Kafin yamma ta fadi, kamar ba ita ta dawo Legos dambasheshiya ba. Sati 2 kenan yau babu labarin Danliti, yayin da rashin lfyar mama ke cigaba da yaduwa tamkar yadda labarin samun cikinta ya gama baza gari, ta bakin Hajiya Gaje. Amma don tsabar yaudara su suka matsawa Mazajensu su akan su kai ta asibiti ko ta sami dan taimakon da xai rage mata larurar jikinta. Da kyar abba ya amince. Alh. Basir ya kaita babban asibiti da garin Kagara. Suka ga likita, yayi gwaje gwajen sa ya gano, lalurar shigar ciki ne ke wahalar da ita. Saboda haka ya bata 'yan taimakon da xasu rage abubuwan da take ji a jikinta, sauka dawo gida. Sun wuce kofar shagon Danliti shi kuma yana karasowa wajen. Yayi fakin ya fito tare da yin daguwar mika mai isar da sakon gajiya. Ayuba ya fito ya tarbe shi, sai dai fuskar sa babu fara'a ko alama. Yaya dai mutumina? Naga kamar kana ciwo? Ya numfasa, amma bai tanka ba har suka shige shagon. Ya dube shi da kyau, yace ina magana ka kyaleni, lfya nace? Ya kara sauke numfashi. Yace ina fa lfya, magana ta cika gari..... Ya katseshi Mama na da ciki ko? Gabansa ya fadi ya saki baki yana masa kallon Mamaki, Dan liti ya kece da dariya, kwalla na gangara bisa kuncinsa kafin yace, shiege ni, dan buzu mai shayi. Raina kama gaiyya, ka tabani ka ga tsiya. Watau labari har ya bazu ko? Kaga burina na farko ya cika, amma har yanxun akwai saura, don na san dan xagin kalilan za'ayi mata. Ido jajur! Ayuba yace, kaji tsoron Allah Danliti, ka kyale yarinyar nan haka. Tunda ba xaka aureta ba, ka barta taji da wannan bala'in! Ai ka gama ruguzamata rayuwa, babu sauran wulakanci da yafi wannan..... Ya ja Kujera ya xauna, yace haka kake gani, nasan akwai saura, sai dai ba xan shanye maka dadin labarin ba, idon ka nake son ka gani kamar yadda ka ga wannnan. Ya bishi da kallo, yana kada kai. Murmushin keta Danliti yayi, ya sake fadin, babu wani abu mutumina, kai kanka kasa ramuwar gayya, tafi gayya xafi. Dadin abin a gabanka mama ta xageni, ta xagi Mahaifina, ka manta kawai! Yace wannan ba hujja bace Danliti, ina gaya maka barnar da kakeyi tayi yawa. Allah ba xai kyaleka ba. Ya ja dogon tsaki ya mike tsaye, kai wannan ya dameka, ni yanxun gidan ma xani kuma lfy lau xaka ga na dawo, see you! Ya juya ya daga kanta ya fice abinsa, ayuba ya koma a hankali, ya xauna ya dora tagumin mamaki da takaici. Danliti ya sake gani ya dire masa bakar leda tare da kwalin juice kato bisa kanta. Yace ga sauran kazar da na ci a mota nan, idan ka gama laulayin, ka ci. Ya juya ya wuce mota, yayi tafiya sa ya bar shi da tagumi. Kansa tsaye yayi fakin kofar gidan Uban dawaki, akwai yara gidan suna wasa, don haka bai yi wahalat neman yaro ba, take nan ya aika yana kiran Mama. Yarinyar ta shiga, jim kadan ta fito ta gaya masa tana xuwa. Yana nan jingine da mota yana kada makullai. Abba ya fito. Nan da nan ya tsuguna kai sunkuye, mummunin kare kenan. Yace, ah! Sannu abba, ina yini? Abba ya bishi da kallo, amma kash, ya kasa ganin bakinsa balle ya gaya masa bakaken maganganu. Ya amsa gaisuwasa, sannan yace mike ka biyoni. Ya wuce kofar falon bakinsa, ya murda ta bude suka shiga, xauna, ya nemi waje ya tankwashe kafafuwa. Abba ya xauna ya dube shi da kyau yace, yanxun saboda Allah Danliti abinda kayi, ka kyauta kenan? Me ya sa duk abinda xakuyi baku sa tsoron Allah a xukatanku? Ya xa kace kana son yarinya da aure, sannan ka aikata mata abinda ba shine ba? Danliti ya kara sunkuyar da kai, kamar xai tsaga kafet din falon ya shige don gulma, abba ya ciga da cewa, to ta faru takare, ahalin Yanuxn Mama juna 2 gareta, kaga xancen auranku ya rushe kenan dole tayi zaman istibra'i xuwa tym da xata haihu. Wannan abu ya bani kunya kuma kun xubar min da mutunci da kima a garin nan. Hannaye 2 Danliti ysa ya rufe fuskarsa yayi xugum, ko mtsi ba yayi. Abba ya numfasa ya kada kai ya cigaba, ni bani da abinda da xan iyayi, tunda kaddara ta riga fata, abinda kawai nake soka sni, shari'a ce ta tsara haka, saboda haka dole ku kauracewa juna, don gudun karku kara maida hannun agogo baya. Ina fatan kaji? Sai ka koma jira ranar da xata haifamaka danka, kaga kun sami dan aike, ba sai kun nema ba. Kana iya tfiya, mu jira abinda Allah xaiyi. Shawara da xan baka kawai, ka nemi tuba wajen Allah, domin ka saba masa, ka keta rigar mutuncin yarainya. Shiru yayi ya kasa tashi, abba yace tashi mana, ni nakare magana, ya dago kai da kyar, amma bai kalli fuskar abba ba, cikin sanyin murya yace, abba kayi hkr ka yafe min? Wlh sharrin shaidan ne. Ya goge kwalla, abba na kallonsa kafin yace, haka ne, amma wani tym har da son xuciya. Si yasa nace ka nemi tuba wajen Allah, don ta ni mai sauki ne. Ya kara rankwafawa yace, je ka kawai. Ya tashi simi simi ya fice babu ko waige. Abba ya raka shi da ido, sannan ya numfasa ya kada kai, yace Allah ya shirya mana. Shi kuwa Danliti yana fita yayiwata 'yar girgiza ta jin dadi, ya wuce motarsa cike da farin ciki ya koma shagonsa. Ledar kazar da ya ajewa ayuba suna nan bisa kantar bai taba ba. Wai don ya ba ayuba haushi sai ya dage kantar kayan suka watse kasa. Ayuba ya bishi da kallon kafin ya ce ni baka ban haushi ba don ka xubar kudinka ne, ba nwa ba, gaskiyya ce dai ba xan daina gaya maka ba, watakila ma baiji shi ba, domin bai tsaya ya saurare shi ba, cikin daki ya shigr. Yayi kwance yana tunanin shirinsa na gaba akan mama. Abba kuwa ys jima falon xaune yana tunani rayuwa kawai. Sannan ya mike da kyar ya koma cikin gida, ya maida wa Umma yadda sukayi da Danliti ta kada kai tace , shikenan, Allah yasa ta nutsu ta xauna gidan. Yace amin, amma ina mai tabbatar miki muddin tace ba xata nutsu cikin gida ba, xan bata mamaki, domin, dole ta xaba ko mu ko shi. Umma tace gaskiyya ne, ace wannan abu ya sameka, baka yi nadama, ai kuwa sai a sallama mutum asa masa ido. Allah yasa mu dace. Ya amsa da amin. Tunanin uwar gayyar ba anan yake ba, domin kuwa jin ga Danliti yana kiranta, ya tabbatar mata da cewar ya dawo kuma taso ta ganshi, su Abba suka taka mata birki. Duk da haka taji karfi a jikinta kwarai da gaske, har wasu daga cikin cuttuttukan da ke damunta suka yaye nan take. Sai dai tana ganin babu adalci a hukuncin dasu abba suka yanke. A zaton su zan iya zama tsahon tym banga masoyina ba???????? Ta tabe baki tana daga kwancw tace, ba xan iya ba gaskiyya, sai dai suyi hkr wlh. Ai dai maga juna, ya san halin da nake ciki, ya tausaya min. Ta goge kwalla ta cigaba da sakar xuci. Ana ta sallar magriba, tym ne da ita mama ta sami damar satar jiki ta sulale ta isa shagon danliti. Shi kuma kaida ke xaune cikin shagon. Ayuba ya shiga sallah. Yana ganinta ya dafe kirji ya wani lumshe ido. Yace wayyo Allah na gode maka! Ta daga kanta ta shiga, ta nemi t barma ta zauna, saboda bata jure tsayuwa. Tana xama ta hade kai da guiwa ta fasa kuka ya kare mata kallo, a dage yana dan murmushi, sannan ya taso ya dawo gunta yace haba bebina! Meye abin kuka? Ya xauna gefenta ya rungumota jikinsa, bana son kukan hakan nan....... Ta cira kai da sauri ta dube shi, ba xanyi kuka ba? Ciki fah gareni, kowa ya tsaneni ana ta zagina. Shine xaka ce ba xanyi kuka ba? Yayi dan murmushi yace, bebi kenan, to don kowa ya tsaneki shine me? Bayanni ina son ki kuma ina son ciki na! Kina so yi kukan ne, wata kila kuma na dadi ne yayi miki yawa. Ta mako masa harara tace, jin dadi? A zageni, a tsaneni shine jin dadi? Son ka ne kawai yake sawa bana damuwa, amma kai ina ganin abin baya damunka, daya dame ka, da baka wanke kafarka ka bar garin ba, tsawon sati 2, alhalin an ce ka turo a daura mana aure. Da ka maida hankali ka turo din, ai da duk hakan bata kasance ba, koda cikin xai bayyana adakinka xai fito. Tunda ni ban ma taba nuna wa akwai wani abu tskanin mu ba. Sannann.... Ya da ka mata tsawa, ya ida don Allah! Haba! Wannan maida xancen na menene? Ko kuwa turo ki akayi ki zo ki batan rai? Ko dan kinga ina ta rarrashinki? Babu fah dole, kin ganne? Abban ki cewa yayi ba dole bane ya bani ke, ko bayan kin haihu. So pls ki daina damu na da irin wadannnan surutun banxan, ban son jinsu, idan har kin son mu shirya! Kin gane? Ta xura masa ido hawaye na xuba, ta ma rasa me zata ce? Ayuba yayo sallama ya shigo ya riske su cikin wannan halin. Shi ma yayi tsaye yana kallon su, jim kadan Danliti ya buga tsaki ya tashi ya shige daki ta goge hawayen itama ta tashi ta bishi, ayuba yaa kada kai ya ja kujera ya xauna yana fadin Allah ya kwaci yarinyar nan. Tana shiga ido ya xubo mata. Yace au biyo ni kikayi? To ranki xai baci kuwa, gara ki koma. Ta marairaice tace, kayi hrk Danliti, ba don ranka ya baci bane ya sa na gaya maka abinda ke damuna. A xatona xaka tausaya min a halin da nake ciki. Bani da wani gata wajen iyayena. Tun ranar da na nuna kainake so Danliti, ka tausaya min. Yayi lum da ido ya bude, ya cigaba da kallonta tana tsiyayar hawaye kusan 3mins sannnan ya yafito ta da hannu, yace xo nan! Da sauri ta isa gunsa, ta fada jikinsa ta kara fashe da kuka. A'a, kinga ni fa kukan ne bana so. Yanxu menene damuwarki? Ta goge hawaye, tace kullum in rinka samun kulawarka, hakan shi xai tabbatar min da kana sona kana son abinda ke cikina. Yayi dan murmushin nan nasa, ya kara janyo ta jikinsa, yace, kin samu bebi, karewa ma da kewarki na dawo. Kin ci abinci? Ta kada kai, saboda me? Bana iyawa ne, jikina gaba daya ya canza, sai amai kamar xai kasheni. Yace ayya sorry ko? Amma duk da haka ba za a rasa abinda kike sha-awa ba, gaya min in nemo shi, na kosa in kore kishirwata. Ta mako masa harara, ya kyalkyale da dariya, meye na harara ta? Ko ke ma xaki min BAKIN CIKI ne, irin na 'yan sa ido? Masu shiga tsakanin masoya suna son suga bayansu. Haushi su nake ji wlh. Tace ai ko ni din ma haushin su nake ji, ah haba? Wlh kaji na rantse. Ya cacume ta tana dariya tana fadin, ban da lfya Danliti, bai saurare ta balle ya tuna ya nemo mata abinda take son ci. Karfe 8 ya fito ya barta can kwance tana murkukusun ciwon ciki, ya wuce waje wani mai suyan nama, ya karbi danyan naman da yasa ya aje masa. Ya dawo ya bade shi da magani, ya maida cikin leda ya nade. Yana xaune bakin shgo bisa benci, yana tunanin tafiya yayi wanka ko ya samu yayi sallah. Mama ta fito tana yafa mayafinta, ya bita da kallo yana murmushin keta, ya cikin? Tace yayi sauki ni xan koma gida sai gobe. Haba haka da wuri? Yanxun fa 8 ta wuce? Kar a neme ni ne. Wa xai neme ki? Don Allah xaumna muyi hira, ba wanda xai nemeki, bayan sun san kina nan. Bata da xabi, don haka ta xauna kusa dashi, ya shiga bata labaran banxa. Jimawa kadan wani kare ya xo gilmawa nan take ya hau kiransa, tace me xakayi da kare kake kiransa. Kasan karen okundiri fada gareshi ko? Yace bai sami nama bane don ubansa okundiiri, ya kece da dariya, okundirin ne ubansa? Lallai ka samo shi. Yacee to da waye ubansa? Kinga bude ledar nan nama aciki dauko ki ba shi. Yana magana yana shafar kan karen. Tace, taf ya cafke min hannu? Kai dai ka bashi kai da ka siyo masa,don raka asara. Yace karki bani kunya mana, me xai sa ya cije ki, bayan yasan ke bebina ce, ko kare? Ai ka santa ko? Sweetheart dina ce kar ka cije min ita. Tuni kanta ya fasu, ya jawo leda ya bude ta dauko katon yanka ta mika masa tana fadin, abin har da yaji? Sangarta! Ya kwashe da dariya, yace ina ruwanki? Ke dai mika masa gudan. Ta dauko ta mika masa, ya cafke, Dan liti ya runtse ido yace yes! Ya xarce da dairya. Ta xuba masa ido tace, menene abin dariya har da wani cije labe? Yace ji nayi kamar ya hade da hannunki ya gartse. Takai masa bugu a kirji tace amma kai mugu ne! Yace sosai ma ashe baki sani ba yarinya, to tashi kije gida an gama hirar, kinga karen yayi tafiyarsa. Ka gaida okundiri kaji? Ta ci da kyakyata dariya. Yace, ah! Tashi karki sa yarona ya fito yana fito yana kyakyatawa kamar dolo. Ta shi kije gida sai safe. Don Allah kiyi hkr, so nake nayi wanka inyi sallah. Ta fido lah nima har ka tuna min banyi ko magriba ba. Ta juya da sauri tana cewa, sai da safe! Yace Allah ya kaimu. Ya bita da kallo, yace yarinya kin gama yawo kin shiga 3 kin lalace, ya daga murya ki fa sami abinci ki ci. Ta juyo ta amsa, kar ka damu xanci. Suka ja hankalin mutane, don haka yama didi ya biyo baya, masu tsinuwa nayi, masu addu'ae shiriya nayi. A tsakar gida ta iske su Abba na jiran dawowar ta, shi da su Alh. Basiru. Tana shigowa tasha jinin jikinta, ta shiga bin bango, tana so ta shige falo. Alh. Basiru ya daka mata tsawa, ke dawo nan! Simi simi ta matso gun su ta durkusa guiwa 2, batayi aune ba, taji saukar wani wawan mari. Gaba daya ya ratsa kanta, ya gigita ta, ta dunkule ta fasa kuka. A cikin ba tace ga wanda ya xabga mata wannan marin mai tsanannin xafi ba. Sai dai taji muryar Abba na fadin wannan shine gargadi na karshe da xanyi miki, shi ya sa na tara kowa su xama shaida! Idan har ba xaki bi umarni na, ki xauna a gida ba, to wlh sai dai ki xaba, ko mu ko Danliti! BAKIN CIKIn nan ya ishe mu mama. Gara in sallama ki, in tabbatar da kinfi karfina xaman kanki kikeyi. Saboda haka daga yau kika kara sa kafarki kika fita kikaje gun yaron nan, to kar ki dawo, ki yi zaman ki can wajensa ku sha shagalinku yadda kuke so. Duniya ce Mama, mai dauke da axuxuwa babu adadi! Ina fatan kinji kuma kowa ya shaida! Alh. Basir ya karbe karuwa kike so ki xama ko? To Allah ya baki sa'a, mu dai ba xa mu hana shi ba, duk ranar da koreki. Alh. Adamu yace dama saboda me xamu hana shi? Cikin shege ne fah ajikinki, amma bai sa kinyi nadama ba, to me xai sanya ki kuwa? Karkiji da wai, mun tsame hannun a kanki, haka xuri'ar gidan nan kaf! Kar ki ce kin san daya daga cikinsu, duk ranar da wuya ta koro ki! Ta shi ki bace mana da gani shashasha sakarya. Ta mike da gudu ta fada dakinta, ta dasa kukanta, a fusace abba ya bar wajen kowa ya kama gabanmsa, suka cigaba da yada xancan a sasan su. Daren nan su ma Umma basuyi barci ba, musamman Umma da tabbatar wa kanta ciwon xuciya ya kamata. Da safe ta atashi xuru-xuru baki daya idanuwanta sun xurma, shi kansa Abba ya rame ta maxa kawai yakeyi yana wa Umma fada kar ta salwantar da rayuwarta akan Mama. Ita Mama ba wannan ta aje ranta ba, kawau burinta kasance tare da Danliti, don haka take ganin kowa ya tsangwame ta saboda kiyayya. Kafin safiya ma ta mance duk kalaman su Abba da kawunninta. Allah Allah takyi ta sami saukin laulayin safe dake damunta ta lababa taje ta gano Danlitin ta. Xuwa 12noon ta iya shiga kicin, ta dan tsiyayi ruwan lipton, ta dawo ta shanye. Xufa ta keto mata, danji dadi ajikinta, kana ta shiga bayi tayi wanka da sabulun wanki maras kamshi. Ta kimtsa, tsaf, duk da tayi haske sosai, ta kuma rame kwarai, kana iya gane kyanta na asali mai daukar hankali. Ta koma ta kwanta yana kllon agogo 1:00 ta tashi tayo alwala tayi sallah, ta dauko gyalemnta ta xura takalma ta leko falo bataji motsin kowa ba, ta kwahi sauri ta fice abinta. Yara suna ce mata sai kin dawo aunty Mama! Jin haka yasa Umma yanke sallah, ta fito da sauri ta tambayi yaran ina maman? Sukace yanxun ta fita. Tabi xauran, yaran suka biyota ta tura su tace, ku kira min ita. Yara suka fice da gudu suna kwala mata kira, Aunty Mama, ki zo Umma na kira! Haka suke ta gudu suna fadi har suka isketa, ta dube su tace, sai na ci ubanku in kuna kwala min kira haka! Ni sa'ar kuce don Ubanku? Ku tafi ku ban wuri kafin in fallawa yaro mari! Mts..... Taja tsaki, ta wuce abinta, yara suka dawo a guje suka iske Umma a xaure sukace, wai sai ta ci ubanmu idan muka sake kiranta! Ta dafe kirji tace, ta kyauta, kuje wasan ku. Ta dawo cikin gida a salube tare da mamakin taurin kai irin na Mama, me take nufi kenan? Ta xauna a falo tana juyayi. Da kyar ta sake mikewa ta shiga dakin Abba, ta tashe shi barcin ramakon da yakeyi. Ya farka yana kallonta...... Yace, azahar tayi ko? Tace tayi alhaji. Ya yankura ya tashi yace menene na ganki a salube? Tace tasake fita, wa? Mama mana. Cike da mamaki yace ta fita? Yanxun nan kuwa, kamar fako na takeyi, har yaran nasa su kirata, ta dinga kunduma musu xagi, taki dawowa. Ita Maman ta zage su? Tayi murmushin takaici, tace kana mamaki ne? Bai kamata kayi ba alhji. Ta kuwa tafi kenan, kinsa Allah ba zata dawo ckin gidan nan ba. Kiyi hkr, duk abinda ke ranki na so da kaunar Mama, ki cire ki dangana da ita, nima na hkr da ita. Umma ta fasa kuka, ta tashi da asauri ta bar dakin. Hankalin Abba ya kara tashi, ya taso ya biyota dakinta, tana xaune bakin gado kukan kawai takeyi. Ya tsaya kanta, yace saboda Allah ya kike so nayi Halima? Ta cira kai murya na rawa. Tace har ga Allah ba korar Mama ke sanya ni kuka ba, tausayin rayuwarta ke bani, yadda ta ka sa gane cewar mu ba tsangwamarta mukeyi ba, saboda tana son Danliti. Yanxun shikenan ba xata gane cewar alabarkar mu itace kwanciyar hankalinta ba, duk tsananin son da Danliti ke mata, shikenan ta xabi cigaba da xaman shashanci akan ta nutsu, dn tym kankani a daura masu aure? Wannan rayuawar tana cike da tausayi da ban Mamaki, kamar Ya asirce Mama? Ta kada kai ta ciga, ba haka Mamar mu take ba alhji, ta sauya saboda soyayya, kenan ta fi son shi a kanmu? Ina xan samo amsoshin nan Alhji? Ina xan..... Ya rufe bakin da sauri, ya ace ya isa haka! Kar ki jefa kanki damuwar da xata tada miki ciwo, ki kauda kanki ki akan komai, sannan ki nisanta xuciyarki ga irin wadannan tambayoyin da kike wa kanki. Xaki xautu saboda yarinyar da bata damu da lfyarki ba, xamani ne Allah ya kawo mu da yara ke rufe idanuwan su akan abinda suke so. Suyi ta fada da iyeyensu har xuciyoyin iyayen su fara xargin asirce su akayi. Xan ji dadi da farin ciki idan xa'a ce, duk wannan abubuwan da suke faruwa, ki dauke shi amatsayin mafarki mai wucewa, tamkar baki taba haihuwar wata mai suna sakeena ba. Ta dube shi xai yuwu ko? Mai hana? Idan har zaki dage da adduoi, ubangiji ba xai barki haka ba, ta goge hawayenta ta sauke gwauran numfashi tace, xan yi iya kokarina Alhji. Ya jinjina kai. Yace haka nafiso sadiya, kin san ina jin dadin xama dake, kuma tun ina saurayi ban taba son wat 'ya mace ba sai ke. Ban fatan abinda xai salwantar min da rayuwarki, ya kasance wata kaddara tasa kin fara barina cikin duniyar nan. Kullum nayi sallah, sai na roki Allah ya fara daukar raina saboda ba xan iya ganin gawarki ba halima. Idanuwanta suka kara tara hawaye. Tace ka daina fadar maganar nan Alhji..... Ya katse ta, ni ma ba ason raina na fadi ba, domin sirri nane wanda nake xaton shi kdai ne ban taba gaya miki ba, sai yau, dole ce ta sanyani, don ina son ki sami nutsuwa sadiya. Ta matse ido kwallatana suka kwararo ya mika hannu ya goge mata yace, sha kurkuminki Maman abdul 3, gwarazan samarin nan masu takama da baiwar Allah. Ta numfasa tace, Allah yayi masu albarka baki dayansu. Kina nufin har da sakeena ko? Ta amsa da kai, kafin tace, ai mu na mata fatan shiriya ko? Yace haka ne, toh Allah ya shiryta. Amin ta amsa. Haka yayi ta rarrashinta, ta samu nutsuwa, sannan sukayi sallah suma mika kukan su ga Allah. Na san kilan kuyi musu ko mamaki idan nagaya muku Mama bata dawo gida ba, sai bayan sallar magriba. Abu na farko da ta fara cin karo da shi a kofar sasansu dake kulle, shine akwatin kayanta. Taja cak! Ta tsya ta xura masa ido tsawon tym, kana ta matsa ta tura kofar taji ga,! A kulle. Ta tabe baki tare da jan tsaki, ta figi akwatin ta juya tana fadin a ranta, sai aga na kwana a titi. Kai tsaye Danliti ta dosa, yana xaune kofar shagonsa, inda ta basa. Yana hangota da akwati, ya mike ya shige daga ciki yana gayawa Ayuba ga mutuniyar can tafe da akwati, ko maganarta tace ta tabbata? Ayuba ya murtuke fuska yace ni xaka tambaya? Au haushi kaji? Amma dai kana ji na gaya mata kar ta kuskura ta bari su koreta, don bani da wurin ajeta, ko ban gaya mata ba? Yace oho! Wai kai wani irin banxa ne? Yace Ni banxa bane, ai rainin wayau yasa ka gaya mata hakan. Wa ke jan ragamar rayuawarta, in ba kai ba? Ai sanin bata da xabi shi yasa ka raina mata hankali. To ya isa malam, sai gata tsaye gaban kanta, tana kokarin dagawa, duk suka xubo mata ido, ta karasa shigowa, ido waje ya dubi shirgegen akwatin, ya ce ya dai? Bata saurare shi ba, kofar dakin ta tasarmawa xata shige. Yayi azama ya shawo gabanta, magana fa nake yi, kona kokarin shigewa kamar gidanku? Ta xubo masa ido a marairaice tace, me na gaya maka? Ni kuma me na gaya miki? To yaya xanyi? Ina komawa na iske akwatina akofar gida sun kulle gidansu. Ya gayara tsayuwa, da yake kuma ke sakarya ce sai kaka kamo hanya kika taho baki tsaya kika nemi sulhu ba! Yanxun menene nufinki? Anan xaki xauna? Cikin shago? Lallai kin cika dakikiya, Jaka! Kuka sosai ya kwace mata, ta tsugunna ta rungumi kafafwansa, murya na rawa tana fadin, karkayi min Haka Danliti! Saboda kai suka koreni, ina kake so naje, idan ba nan ba? BAKIN CIKI 2***15 Ayuba ya daga kanta, ya fice hankalinsa tashe, shi kuwa ko gezau beji ba ajikinsa, a dage yake kallonta, tsawan tym sannan ya fizge kafarsa ya kama hanya xai fita, da sauri ta mike ta cukuikuyo rigarsa, fadi take, kayi hrk don girman Allah. Wasu samari 2 suka iso wajen siyen taba sigari, ai sai suka buge da shari'a, kaya-kaya hayaniya har waje Danliti na daga murya shi ba xai aje ta cikin shagonwa ba, ta koma ta nemi sulhu da iayeynta. Kan ka ce kwabo jama'a sun cika makil a gun. Kai Mama ta sha zagi da la'anta, Allah shi kara kwando- kwando. Kalilan ke cewa Allah ya shiryeta, Dan liti ya gacciye banci kofar shagoin ya xauna yace yaga uban da ya tsaya mata agarin nan, wnada xai sashi ya ajeta. Baiwar Allah kuwa na tsugene gaban akwatinta, tana ruasar kuka har karfe 10pm. 'yan ganin kwakwaf suka gaji suka koma gidajen su dauke da labari mai ban al'ajabi. Wasu suna ganin bai kamata Uban dawaki ya koreta ba a matsayin sa na Uba, kuma babban mutum mai sarauta, wasu kuwa suna ganin hakan shine daidai, imna xai sa BAKIN CIKI? Idan bai sallame ta ba, tunda ta tara masa, ya cika masa xuciya, tana neman fashewa ta hallakashi? Ai gara da ya sallamata duniya ta koya mata hankali. Ga darasi na farko nan ta fara gani, duk iskancin Danlitim yace baxai aje taba. Alhalin saboda shi aka koreta. Wannnan ya nuna a fili ita ta nace masa kamar sauran 'yan mata marasa xuciya. Mutane na mamaki abinda Danliti yake da shi wanda yake tsonewa 'yan Mata ido. Su mutu cikin soyayyar sa. In bata ga kyau me yake da shi? Shi babu hali babu kwakkwaran asali. Amma duk wacce ta fada tarkonsa sai gagari iyayenta. Ko don kudi da ya ke kashe mus ne? Shiya sa suka dauki laifi kacokan suka dorawa 'yan Matan masu biye masa don kwadayi da kyalekyalen jikinsa. Wayyi, kai bai san dawan garin ba, dai bai yi tunanin kutsa kansa ciki ba. Tun ciki dare surutai kala- kala suka fara baza gari. Shi kuwa gogan da ya ga kowa ya watse sai ya matso ya xunguri Mama da kafa, ta dago kai da sauri ta dube shi, matso mana nan kiji, ta matsa gareshi, tana hawaye. Ya dubeta da kyau yace, ke banxa ce wlh, shi ya sa kika bani haushi. Nace ba xaki xauna anan ba. In banda hauka irin naki, ya xa'ayi ki xauna tare da mu cikin shago? To ina sane da abinda nakeyi, kin gane? Saboda haka ki koma ki nemi wani wurin ki xauna, ki bani nan da sati xan san abinyi. Murya dushe tace, ni bansan inda xani ba, a'a ko gidan 'yanwanku ba xaki je ba? Ko baku da su ne? Sai dai inje gidan su Baraka, yace ko gidan su Mubarak xaki, sai kinm dawo matsalar kice. Amma ba xaki kwana shagon nan ba. Yauwa, tashi ki sungumi akwatinki, ki wace kar su kulle gidansu. Tace to nagode, sai da safe, Allah ya kaimu 'ya bebine. Muyi fada mu shirya ko? Kar ki damu xan ganki goben. Tayi murmushi, dadi ya rufeta, ta mike tana kara masa godiya, taja akwatinta ta nufi gidansu Baraka. Ya mike janye da benci yana kyalkyala dariya, ya shige shago. Kai mugu dan gidan buzu mai shayi! Yayi wa kansa kirari ya shige daki. Ayuba na kallonsa yana kada kai. Gidan su Bara akulle yake, saboda sha dayan dare tayi ma. Ta shiga bugawa har aka xo aka bude mahaifin Baraka ke tsaye cikin xauran, ya dubeta da kyau yace, Mama ce? Daga ina haka? Ta fara kuka yace shigo shigo ciki! Ta wuce da uban akwati ya maida kofa ya rufe. Tana gaba yana biye da ita yana fadin, subhanalillahi! Dakin Inna saude suka shiga tana tsaye tsakar daki, lfya? Ta xube sharaf! Cikin kuka tace, abba ne ya koreni..... Ina saude ta nemi waje ta xauna, yayin da malam kasim ke fadin, me ya sa Uban dawaki xaiyi hak? Inna saude tace BAKIN CIKIN ta ne ya ishesu. Ace kamar Mama ta gagari kowa duk abinda ya sameta da abinda ake gaya mata ba su isheta nadama ba, idan ba su koreta ba me kike so suyi miki? Ba shashanci kike sha'awar yi ba? To sun baki hanya, meye kuma na kuka? Mal. Kasim yace hakan ba hujja bace, duk abinda xatayi, gara tana gabansu suna tsawata mata, yau da gobe ana hada mata da addu'a, sai Allah ya taimaketa ta gane illar abinda take aikatawa. Saboda haka ta xauna, gobe Allah ya kaimu lfya, xanje in ganshi. Ke kuma je ki kwanta kiyi tunani, meye amfanin lalata rayuwarki da kikeyi? Har jikokinki sai an yi musu gori, wannnan abinda kika aikata! Kina da babban laifi mama, sai kin tuba kin bi Allah kin bi iyayenki sannnan xaki ga daidai a rayuwarki, kinji ni? Ta amsa da kai, yace ta shi ki shiga wajen 'yar uwarji kafin Allah ya kaimu goben. Ta mike simi-simi ta ja akwatinta, inna saude ta xuba mata ido tana mamakinta. Ta kada kai, taca baka ce xata aikata ba, yarinya kyakkyawa, ta lalata rayuwarta. Allah ya shirya mana, yace amin albarkar annabi. Atsakar gida taga Baraka tsaye tana share hwaye, ta matso ta kama mata akwatin suka shiga dakin, kowacce ta nemi wuri ta xauna bakin katifa. Baraka ta dubeta......... Tace anya mama abubuwa da kike yi kanki kalau? Ke bakijin kinya? Baki tunanin gaba daya idanuwan garin nan sun dawo bisa kanki? Baki da martaba da darajar Abba agarin nan? Haba Mama, kamar ba tare muka taso ba? Tarbiyarmu iri daya, nutsuwa da kamun kai, kowa na yabon mu. Mutane na rububin mu, da son hada xuri'a tagari. Ta daga kai sama, idanuwa cike da hawaye ta cigaba, Allah ya isa tsakaninmu da Danliti! Ta dube ta sukayi ma juna xuru kafin Mama tace kar ki sake xagin Danliti Baraka, alhakin sa xai kamaki, laifin mune? Tun tym din da mukace muna son juna, ya kamata su Abba su rungume mu hannu 2 amma suka ki, suka gwammace in kwashe kayana in bishi. A tunanin ki wane sakamako ya kamata su gani? Bayan wannan dake jikina? Baki sake take kallonta, kafin tace, maganar Banza ce, idan duka jina kunnuwa ne xai taba sauraronki ba, wa kika burge don kin aikiata wannnan sakarcin? Shi kansa Danlitin adage yke kallonki. Kin dawo an yi miki afuwa, cikin nman ya bayyana, duk sun hkr, sun shanye, amma ki ntsu xuwa tym din da xaki haihu, a daura maki aure, kar fa ki manta xaman nan naki agida ibadane tunda Allah ya shifida hakan, sai ki ga dalilin xaman, duk xunubunku sun kankare, auran ku yayi karko tare da xuria masu albarka. Ki kwanta kiyi tunani mama, ko asiri Dan liti yayi miki, xakewar taki tayi yawa. Ta sualala kafita ta kwanta, tace, na kwanta shekiya Baraka, sai da safe ko? Ta bita da kallo ta numfasa, tace Allah ya sa ki gane. Amin, ta amsa da gatse ta juya baya abinta. Baraka ta mike ta rufe daki ta dawo ta kwnta. Ta jima bata sami barci ba, saboda juyayin halin da 'yar uwarta ta shiga. Da farar safiya M.kasim ya usa gidan Ubban dawaki yasa aka yi masa sallama da shi, jin cewa shine ke sallam ya sa yace ya shigo cikin gida. Bayan su gaisa. Umma ta fito suka gaisa. Sannan ya maida jawabinsa, a karshe yace, alhaji kar bacin rai yasa ka yanke wannan hukunci, ni ina ganin gara yarinyar nan ta xauna agaban ku, kuna tsawata mata, sai Allah ya taimakemu ya shiryar da ita. Don girman Allah ka yafe mata dawo gida, tunda tayi tunani taxo wajenmu, ta kawo mana kukanta. Abba ya gyara xama yace, a tunanin ka a kashin kanta, ta yanke shawara taje wajen ku? To ba haka xancen yake ba, kila ba xaka sani ba ne, saboda kuan cikin lungu. Amma ni tun jiya na sami labarin wulakancin da yaron nan yayi mata, ya tara mata jama'a, ya tozarta ta, ya kuma ce ba xata xauna masa a shago ba, kaji dalilin nemanku, amma ba nadama tayi ba. Yace, duk da haka ina son ka duba girman da martabar ka agarin nan. Kayi hkri ka amshi rokona, ba don ni ba, sai don girman Allah da darajar iyaye. Ya sunkuar da kai yana kadawa, kafin yace, M.kasim ban ki ta taka ba, amma ba xan iya xama da yarinyar da ban isa in bata umarni ta bi ba. Ta fita tayo shashancinta, ta dawo min gida ta wanke najasa ta kwanta. Mts! Ban jin idanuwana xa su iya jure gainin wannan kaxanta. Gara ta tafu su cikashe. Wlh na hkr da ita, kuma ina rokon Allah ya sanya mana dangani nida Mahaifiyarta, ba kuma xamu gaza ba wajen yi mata addu-ar shiriya. Watakila wata rana taga uwar bari, ta dawo da kanta ta neme mu. Kaga a tym din xan tabbatar da tayi nadama. M. Kasim yayi shiru, jawabin Uban dawaki na cike da tausayi, ya numfasa, yace, na yarda da kai Alh. Sai dai har yanxun ina rokonka, da ka sake bata dama ta karshe, mu gani.idan bata daina ba, to muma sai mu tsame hannayen mu. M. Kasim ya cikwa Abba ido kwarai da gaske, ya jima kafin ya numfasa, yace, shikenan ba komai nagode. Yace nima nagode, Hajiya akara hkr, a bata damar karshe, tace babu komai M. Kasim, Allah saka da alkhairi. Yace amin, barin in koma in turo saude ta dawo ita. Tace to ka tsaya kaga abin kari akawo maka mana, ya mike cike da fara'a, yana fadin alhmdlh, kar ki damu nagode, to nabr ku lfya, Allah ya shige mana gaba, suka amsa amin. Yaka hanya fice. Bayan tafiyarsa kamar da hadin baki, jama'a sukayi ta xuwa suna ba uban dawaki hrk tare da rokonsa ya daure ya maida 'yarda gabasa xai fi kyau agareshi. A cikin su har da abokansa da yaron gidansa, watau kalla. Duk ya karbi rokonsu, kuma yaji dadin kulawar jama'a gareshi tare da tausaya masa akan kaddarar da ta fada wa iyalinsa. Karfe Tara saura, Inna saude ta taso Mama xuwa gida. Bata ma biyo da ita ta shagon Danliti ba, balle ya gansu, haka suka taru da matan gidan kamar zasu cinye ta danya, sannan matza suka shigo suka dasa nasu. A gaban kowa suka tilasta, ta dauki alkawarin ba xata sake xuwa ko ina ba, kidan kuwa ta saba, to a yanke mata hkunci da yafi wannan. Kwana 2 hatsaniyar nan ta kwnata, mama na xaune cikin gida bata fita daidai da tsakar gidan sasansu. Muna iya cewa Danliti bai murda kambunsa bane haka? Saboda haka xuciyar Mama ta sami 'ya nutsuwa. Bata ita kadai ba, su abba ma sun sami 'ya nutsuwa har tana debo 'ya'yan itatuwan da Abba ya ka siyo ta kawo mata, tace ta sha saboda rashin cin abinci da take fama da shi..... ***************** A wannan asabar din ma abdulkrm ya xo daiyalinsa duka. Su ameera nata murnar ganin auntynsum domin sun jima basu ganta ba. Dr. Na ta dabo, yana son ya taka, sai 'yar banxar kuiyam shi ya sa yaki yarda Mama ta daukeshi. Aunty Rabi ta tasa ta da nasihohi, ayoyi, hadisan Manxo SAW akan ta dage ta yaki xuciyarta ta dawo kan kanya, sannan ta nuna mata wannan ba shine soyayya ba, duka saurayin da ya nemi lalacewa da yarinyar da yake so, a hakikanin gaskiyya ba son gaskiyya yake mata ba. Sha'awar sassan jikinta kawai yakeyi. Haka yayanta ta tsatsagge mata gaskiyya, har yayi mata alkawarin idan ta nutsu ta xauna gida kamar yadda aka umarceta, to bayan ta haohu za'ayi bikinta, duk abinda take so, shi xai sayo mata. Mama ta wani kuka tana ba su ameera tausayi. Anann suka kwana, washegari lhadi karfe 12noon suka juya. Su ameera nata tambayar antyn su yaushe xata xo? Tace kar su damu tana nan xuwa nan bada dadewa ba, suna isa gida, yayan ya kira 'yan uwansa, ya labarta musu abinda ya gani game da Mama, idan har ya dore a hakan, alhmdlh! Ana iya cewa an fara samun nasara. Kowa yayi farin ciki jin wannan labarin da fatan Allah ya shige mus gaba. Allah, da ikonsa a yammacin yau din, tun bayan sallar la'asar mama ke cike da kewar Danliti, kafin 5pm ra mance kaf! Da alkawuran da dauka, babu abinda take so face gain Danliti, kewarsa ta gigita kwakwalwarta, ta birkita ta. Kamar an tsikare, kawai ta tashi ta suri gyale da takalmi ta fito kanta tsaye ta fice abinta. Dan gogan ta samun cikin dakin barcinsu, tana shigowa yana xubawa wani kaskon rushi ruwa, ya dago ido ya dubeta, yace ba xan miki sannu da xuwa ba. Ta xaune gefensa tana murmushi, saboda me? Ya xubo mata harara, yace kwanaki nawa rabon ki da nan? Sabo da nayi miki fada ko? Ta rungomoshi tana dariya, ayya nawan ba haka bane, kowa yasa min ido, sai surutai sukeyi kamar ni kadai na fara soyayya agarin nan. Amma kana cikin raina, kaima ka sani, bani da burin da wuce in kasanxe tare da kai, ta bae baki yace tsarani, au baka yarda ba? T yanxun ba ni na xo ba? Dana kiraki ba? Ka kirani? Kamar ya? Ya ture kaskon ba xaki gane. Sai dai na yarda kina sona, tunda kika amsa kiran. Ta xura masa ido tace ngode, tunda kasan hakan, me kake yi da kasko? Ke duk xamanki a dakin nan baki taba ganinsa ba? Da shi fah muke turaren daki. Kai amma wannan bai hadu ba, kauri gare shi, kin kuwa san tsadarsa? Ai ku maza ba gwabe bakin ku ake wajen siyayya? Kabari xan kawo maka mai kyau, idan ka sanya shi sai makwabta sun tambayeka ina ka samo. Ko? To sai kin kawo din. Yanxun mu ake maganar turare, ina kuka kwana da su Abba? Ta tabe baki, me ma? Wai an bashi hkr ya kyaleni, amma idan na sake xuwa nan, dole in tafi. To kice kin karya doka, tunda gaki kin sake xuwa, ni kuma da har nayi cinikin wani gida can bayan tasha, ina fasa kenan? Bakinta har kunne, tace ka fasa kuma? Ai xai mana anfani idan munyi aure ko? Ya shafa kai, gaskiyya ne, xan biya kudin in sa a gyara shi, ai sau muje ma ki ganshi ko? Ya xama dole, yaushe xamu? Duk tym din da kika shirya. Ko yanxumn a shirye nake, mu tafi kenan? Bismillah. Ta sumbace ta yace, amarya ta kenan, maman bebi! Ta rausaya da kai tana dariya. Tare suka fito yana rike da hannunta, har gaban motarsa. Ya bude mata ta shige, ta dawo maxauninsa yaka suka tafi. Gidan ginin kasa ne mai dauke da dakuna 2 kicin da bayi, tsakar gidan turbayar kasa ce, haka ginin babu digon siminti ko kadan, zallar kasar ce kawai, illah iyaka cikin dakunan anyi masu dabe, suna tsaye kafada da kafada, ya dubeta yace, kinga gidan, ina fatan yayi miki? Ta yake baki ta makalo wuyansa tace, ya fiye min kowannne irin gida muddin da kai xan xauna cikinsa. Kar wani abu ya dameka,a hankali na gyara shi, kyau xaiyi fa, yayi dan murmushim ya falla ido sannan yace, toh shikenan, tunda yayi maki, yau din xan nemi dillalin in bashi kudin. Ta kara kankame shi tace, ina tayaka murna. Ya xubo mata ido yace ni xaki taya murna, ko ke xan taya murna, gidan ki ne fa? Tayi dariya sosai. To dukkan mu Congratulations! Ya sumbaci labbata, tace thnk U! Sun jima cikin gidan suna sharholiyar su, ana kiran magriba, suka fito, ya kulle kwadaon gidan suka koma shago, maimako ta koma gida sai ta rashe nan, tana nishadantar da shi, kamar yadda ya bukata, ya siyo mata abubuwan da take so, tace, tayi hani'an, kai barci sace ta mana, ta yada kai bisa filo tai tayi kuwa...... 11pm za su kulle hsago, ayuba yayi juyin duniyan na Danliti ta tashe ta, ta tafi gida amma yaki, ya kuma hana Ayuba ya tasheta. Da ita suka kulle shago, ayuba ya kwana tsakar shagon, shi kuwa dan gogan yana tare da gimbiyar. Tsakar dare ta farka da ganta tare da mutum. Ta tashi xaune ta bubbuga shi ya tashi, menene? Tace dama ban tafi gida ba? Yace ga shi nan kin gani, ai da ka sani ka tasheni Danliti. Yace waya gaya miki ana tashin mai ciki barci? Kiyi kwanciyarki kawai da safe kin koma, Abba xai koro ni Danliti, yace akwai gida na biya kudinsa, baki da haushin wannan. Idan kina kwanciyarki, ki kwanta ida kuma yanxun xaki fita 2am ga hanya nan babu ruwana. Bebi na kawai nake ji. Ta watso masa harara ni banda ni ko? To! Na ga kin wani hakikance ne, meye sabo idan kin kwana anan? In banda gulma! Ta dare ruwan cikinsa ta kai masa duka, ni ce magulmaciya? Kai din fa? Todama mai neman kuka ne aka jefa shi da kashi awaki, sai yaya? Washegari, yadda bata sallaci magriba da isha ba haka batayi asuba ba, karfe 7am ta dauko hanya. Gata nan ga nan har gida, salalau- salalau ta karaso ciki, ta iske duk sammakonta Abba ya riga ta tara jama'am don haka tana xuwa tsakar falo, tayi sanrada. Gwiuwa 2 ta xbe ta fara kuka. Kowa ya saki baki yana kallonta, M.kasin ya fara magana, yanxun saboda Allah Mama duk maganganun da aka gaya miki ta bayan kunnunwaki suka wuce? Ashe haka kike da taurin kai? To mu babu ruwan mu, dama rokonsa mukayi, ya ga girman mu ya hkr, tunda ke baki gani ba. Shikenan ga hanya na, ki bi duk wacce kika xaba. Abu yaya kamari har da kwana? Ke Mama kiji tsoron Allah ki tausayawa iyayenki. Ba xata suka ji tana magana, wlh Baba bada niyyara kwana ba na fita, Danliti ne ya sayi gida, yace muje na gani, mun dawo ina hutawa, ban tym din da barci ya kwasheni ba, abba ya xaburo yana fadin, kunaji Maganar Banxan da take fadi ko? Kun tabbatar da cewa abinda nake fadi gaskiyya ne? To ya isheni haka! Ya isheni haka!! BAKIN CIKI ba xai akshe mu ba. Daga nan ki juya ko koma, idan har ki na son kanki da arxiki, wlh! Wlh!! Babu wanda ya ya sake roko na in kyaleki cikin gidan nan! Duniya ce da fadi, karki saurara wajen bin ta kwararo-kwararo har ki gano iyakar ta! Tashi ki bace min da gani, kafin in kusa kashe ki da duka. Gaba daya falon yayi tsit, sai shasheshekar kukan Mama, jim kadan muryar abba ta kara gauraye falon, kai Jama'a! Ina xan kai takaici da BAKIN CIKI? Me nxan yi wa yarinyar nan a dniya na huce, banda in sallama ta, tamkar ban taba haihuwarta ba? Ki tashi fice min nace, in daina ganinki a gabana..... Ki ta... Kawai sai ya yanke jiki ya fadi, gaba daya suka mike da sallalami sukayi kansa...... Toh masu karatu, wannan fa shine wasa farin girki. Nayi iya kar kokarina ace nayi muku sallama anan. Amma ina abin ya faskara, kuyi min hkr karshen badakalar wannan littafi yana cikin 3, ku biyo ni, kada ku gajiya nayi gaba....................THE END!!! BAKIN CIKI 3***1 Ganin haka yasa Alh Adamu ya figi wayar rediyo ya tsulawa mama "zaki kashe mana shi ne? Ta mike a gigice ta yanka waje a guje shima ya bita da gudun yana fadin fita! Shegiya! Tsinanniya! Yar iska! Idan kin sake dawowa gidan nan sai mun taru mun kasheki! Har suka wuce kofar gida a guje sannan yaja ya tsaya yana haki, yar banzar yarinya gantalalliya maras mutunci! Ya dawo yana ta zage-zage yan kallo suka fara kawo dauki ya fada cikin gidan ya iske umma ma ta sume anata shafa musu ruwa tare da firfita ya kutsa cikin yan gudummawa. Abba kam ya farfado amma umma abin yaci tura don haka gaba 1 aka debesu sai minna inda zasu fi samun kulawa sosai sannan yayansu susan halin da ake ciki. Al*amrin ya daurewa Abdlkrm kai kwarai da gaske sanda ya sami waya a office. Yaushe suka baro fandogarin har wann abin ya faru? Dama mama bakan kawai tayi tana jinsu tana kallonsu a dage? Tirkashi! Ai dole su hakura da mama! Hankulansu bai kama tashi ba saida suka zo asibitin suka ga halin da umma ke ciki. Tun isowarsu take sume Dr yace heart dinta ta riga ta buga saidai suyita addua Allah yasa ta mike. Kowa ka kalla dole ya baka tausayi musammn Abba da yayi wata muguwar rama sbd zullumi. 3 days anata kai kawo akan umma abun yaki dadi abdlkdr yace a basu ita su wuce Abj a daren aka sallamesu suna jira gari ya waye su wuce. Karfe 3 na dare Abba na zaune a gaban gadon yaga umma ta daina jan numfashi a zatonsa ta sami sauki ne don hk yayiwa Allah godia ya leka ya kira nurse yace tazo ta gani ko zasu cire mata tukunyar gas din iska ta huta. Nos ta kalleta da kyau tace tana zuwa cikin sassarfa ta fita ta kira dr suka dawo tare ya gwada ta da kyau ya cire duk injin dake jikinta ya rufeta da mayafi ruf! Gaban Abba ya fadi ya tsurawa dr ido ya juyo ya dubeshi... Alhaji..... Ya katseshi naga ka rufe mata fuska me hakan yake nufi? Ya dafa kafadarsa yace sai hakuri Alh kuyi imani da abnd Allah yayi. Yasa kai ya fice. Abba yayi mutuwar tsaye fadi yake Innalillahi.... .....!!! Nos dinnan ce ta kamashi ta zaunar tana kwantar masa da hnkli saidai zaiyi wuya idan yanajin ta ya dai zauna ya zubawa gawa ido yana tasbihi. A haka ya riki asubahi sannan ya tashi da kyar ya fito masallaci yai salla. Yana fitowa su abdlkdr na fakin har sun fito tafiya ya nufesu da sauri suka yi saurin gaidashi ya jikin ummar? Yace jiki yayi sauki ina fatar zakuyi hakuri ku dauki maraici. Haka Allah yaso.... Ya wuce da sauri yana goge kwalla ya barsu suna kallon juna kamar ba. Ya jima yana kallon gawar umma tamkar a dream sannan suka shigo yaya soja ke kan gaba ya zauna ya bude fuskarta nan da nan abdlkrm ya fice daga dakin yana kwalla da salatin Manzo SAW. Shi kuwa soja zura mata ido yayi baya ko kiftawa ganin haka yasa Abba yaja mayafin ya rufeta sanna ya cira kai ya dubi Abba amma bai iya firta komai ba idanuwansa kamar garwashi. Abba ya dafashi yace ya kamata mu wuce gida kuyi hakuri kaji?. Ya kada kai kwalla suka zuba kuncinsa yasa hannu ya share nan da nan aka fito musu da gawar aka sanya a mota suka tafi. Anti rabi da inna saude suka gigice ta fasa kuka ganin haka suma yaran suka hau kukan. Abba ya rungumesu yana rarrashi yaya soja ya kira waya abj ya shaidawa anti amina. Daga nan ya kira abdrhmn yace su hadu a fandogari nan take suka danko hanya shida ya saeed da matarsa suka biya birnin gwari suka wuce da yaya Ali. Gida ya barke da koke-koke kan kace kwabo rasuwar tayi tambari a gari. Baraka da mahaifinta suka garzayo gidan. Misalin 10am suka iso da gawar kowa sai cewa yake mama ta kashe uwarta! Hnklinta ya kwanta, babu bata lokaci aka shiryata aka fito da ita jama'a kamar kasa suka sallaceta suka kaita makabarta, uban dwk dai karfin hali yake har suka sata a kabari shida yayansa wanka zata fito lokcn danliti ya shigo gidan a sukwane ina kike? ta karasa fitowa da bocket a hannu gani nan wanka nayi. ya matso ta yana fadin kina da lbr kuwa? tace name?kai tsaye yace ummanki fa ta mutu yanzu aka wuce da ita..... ta saki bokiti da kwandon soso ido waje tace gane ba? yace ya hausar baki gane ba? kije kisa riga kije gidan ki gani amma ni tabbs haka naji ana fadin matar uban dawaki. ta rasu ko yana da wata matar bayan ummanku? ta fasa kuka ta ruga daki ta rarumi riga tasa ta fito waje a guje ba takalmi ta kwasa da gudu. tana salati hawaye na kwarara, danliti ya fito ya bita da kallo cikin ransa yana fadin mahaukaciyar banza ta wani kwasa da gudu kamar barinta zasuyi zama a gidan. Shashahsa! yaja tsaki yajawo kofar gidan yasa kwado. ita kuwa taci gudu gidan ma nisa yayi mata tana isowa motarsu Abba na tsayawa. Taja birki tana haki kamar ranta zai fita ga hawaye na kwarara duk suka fito suka zuba mata ido shi kuwa soja yana fitowa ita ya dosa gadan-gadan idanuwansa kawai ta hanga ta soma ja da baya kafin ya karaso don kanta ta juya ta koma inda ta fito. yace dakin tsaya mana in karaso! kiga yanda zan kasheki da sauran kwananki! su M kassim suka rikoshi suna bashi hakuri kwalla taf idonsa yace in banda raini me zatazo nema bayan ta kasheta? tunda wuri ku gaya mata idanta bari na damketa saidai wata ba ita ba! akayi tabashi haquri,yazauna cikin en uwansasunata karban gaisuwa,inna saude da sauran matasun cika falon umma.baraka kuwa hawayenta yaqi yatsaya da zarar ta tuno mama sai taji kamar ta sheqabarzamu da bakin ciki! Gidan dan liti mama takomatana tafe tana kuka anata kallonta tamkar mahaukaciya...tana isowa taga gidan a rufe,tarasameke mata dadi....mutuwar umma ko rashin makulli?tasake bin titi tadawo shago tazauna akan benci kofarashagon dan liti na kallonta bai tanka mata ba.ayubayace kace tashigo ciki mana a ranafa take.......yacekasani ko ranar tafiso?kyaleta tagama juyayin muma haka mukayi muka bari.ayuba yace bakada tausayidan liti,narasa inda imaninka yake,yace to kaki filincigiya da sanarwa mana,sai su nemo makashi.ayubayafita ya lallashi mama tadawo shago tayi kukantaharta gaji,bacci ya dauketa.danliti kuwa yaci gaba dacinikinsa hankalinsa kwance..don yasan yasha gaban kowa babu mai tinkararsa akan wani magana.ammayamanta Allah nanan?kuma yana kallonsa?baikulataba saida yagama cinikinsa,zai kulle shagoyasameta zaune yace kitaso muje in sauqeki indawoyau anan zan kwana,,,,,,tadubeshi ido jazir tace anankuma?nikadai zan kwana kenan?ya qara tsuke fuske yace ke!na aureki ne? ina tambayarki...na aurekine?Daga taimako sai ya zama tsiya?kuma shikenan saiin ringa kwana dake,salon kisa mutane su zageni,acena ajiyeki muna dadiro ko?......takada kai dasauri,tace a'a wlh ba haka nake nufi ba,yi haquri,yacemeyasa kikeson batamin rai?kinga nafasa kaiki tashi mazaa ki kama kanki,ungo makulillin ki wuce.tamarairaice tace kayi haquri katausayamin dan litikaga dare yayi bayan tashan nan yan shayeshayene.wulaqanci zasumin don Allah kayihaquri.......ya zura mata ido fuska daure yacemuminar qarya!da anyi magana ki marairaice,ni tashi muje in ajiyeki indawo!iya mike yayi wajeabinsa,canta sameshi cikin mota ayuba dai bai iyakallontaba saboda tausayi tunda tashiga baitankamataba duk lallashin datake masa kuwa...hakata sauqa tana waigensa yayi ribas ya figi mota yawuce tasa mukullai ta bude kofan tashiga ta kulle da sakatagidan bakikirin tayita laluba tashiga daki talalibo ashana ta kyasta,,,ta hango inda fitilar kwaitake tana kunnawa ko minti goma baiyibayamuta,kalanzir din dake ciki ya qare.........dole takwanta kusa da katifar da danliti yasayo mata.takasabacci tarasa abunda yake damunta...tsorone?fushin da danliti yakeyi ne?ko rasuwar mahaifiyarta?saikusan asuba tasamu bacci mai nauyi yadauketa. kwanaki uku da rasuwar umma.a tsawonkwana ukun nan abba baya barci,daka dubeshi zakagane yana wani boyayyen ciwo dake tsananindamunsa.idanuwansa sun zurma,fuskarsa ta tsukekwarai da gaske,shisa hankula yayansa yaketashe,abincin kirki babu mai cinsa...sallar azahar aka kira kowa ya tashi da nufin yin alwala,akaja sahu nanbisa tabarmi malam qasim ke limanci tunda akafarazaman makoki,,,,,,,,,,,,,,,a raka'an qarshe suka dagojiri yadebi abba ya buga da qasa mutan biyu dakegefen hagu da damansa su suka yanke sallan,sukajanyeshi gefe suna masa firfita har saura suka idar da sallah.yaransa suka rugo gunsa tare da sauranmutane,,,,,masu shafasa ruwa nayi masu firfita nayiharya farfado,sai dai yanayin yanda yafarfado yafirgita kowa,gefen damansa ya shanye,baki yakomagefe,gwanin ban tausayi.labari yashiga cikin gidamata sukayi ta fitowa suna koke koke ganin yanda akadauko abban kaman gawa akasa a mota sukakaman hanyan minna......har akayi bakwai abbanacikin kaka nikayi.dole suka kasu,alh basiru da yaabdul kareem suna tare da abba saura kuma sunawajen karban gaisuwa..kai!sunga tashin hankali,kukadai anyishi babu adadi,da yana magani.daya magance matsalar data sauqa cikin gidan uban dawaki.. Wasawasa abba ya kwashe wata guda ana jelarasibitoci,daga minna aka turasu k.d dagananzariya,akarshe ya abdulqadeer ya daukeshi yadawodashi abuja,sukafara shirin fita egypt cikin sati gudakomai ya kammala,abdurah man da anty amina ne suka tafi dashi saboda yanayin aikin sauran ammashi yaya soja zai biyosu da zarar yasamu umarnidaga ofis. andanga canji a cikin sati biyun dayasamu yana ganin kwararren likita,domin ansamu yanamagana kuma yana amfani da hannunsa kadankadan,kafarce dai bata aiki haryanxu.,...a sati nauku..akabasu sallama tareda magunguna da zai ringaamfani dasu.suna sauqa abuja.ya soja yawuce dashi gida yace anan zai zauna yarinqa samun kulawan dayadace..aka gyara masa daki,,,sannan yayi masarijistan zuwa ganin likita lokaci lokaci,anty aminatasha damarar kulawa dashi cikin hakuri dagirmamawa Dan jikansa kuma malami yana debemasa kewamusamman da yamma zaiturasa akan kekensa sufito shan iska yana zagayawa dashi cikingidan,wataranma harwaje dan yaga gari,,,,kullam daresai sunyi tilawar alqur'ani mai girma sannan sukebacc.haka kusan duk sati yayansa ke zuwa dubashi danasu iyalan.har safiya ta haifi ya mace,abdurahman yaso yasa mata sunan umma,ammaabba yace tunda akwaita yana roqon arziqin asamasasunan mahaifiyarsa watoo sakeena tunda shi yanxubaida mai sunan....abdurahman bai musa masa badukda dai sunan bai kwanta masaba yabi zabin abba,don ya faranta masa rai....komai na abbayadawo qarqashin kulawan yaransa hardagonakinsa,,,bayan wata biyu da haihuwar sakeena. Bayan wata biyu da haihuwar sakeena qarama yaaika da takardar murabus,,,aka nada alh basiru amatsayin uban dawaki.zaman sa yayi masa dadi agidan dansa hankalinsa kwance dukda yana damuwada rashin umma...sai dai imanin dayayi qokarintusawa kansa wajen maida al'amuransa wajen ubangiji.illa iyaka yarakata da addu'a tareda nemawamama shiriya. To komai dai sai Allah yayi hattaasiririn dayayi tasiri ajikin mama da izininsa ne,,,,donya jarabta ta da iyayenta kuma yayi wa danliti daurintalala.saboda fidda tsoron Allah a zuciyarsa. Page 12:mama dai sharholiyanta takeyi dukta mance abubuwan da suka faru..domin ko alama bata ganinkowa a idonta sai danliti.....shine mai sata shine maihanata musamman yanxu data samu lafiya,cikintayashiga wata 6 yana neman 7 batada watamatsala,batada abun dayake daga mata hankali saifushin danliti.shikadai zata gani yanxu tafita hayyacinta...tun mutan gari na suru2 suna zaginta harabun yazama jiki bamai kallonta......sau dayawa zakasameta cikin shago ita ke siyar da kayan shagon saitazauna tun safe har dare suna sakarci kalakala...gidan danliti kuwa yanxu bata tsoronsa dukdare zatabi hanya takoma takwanta,,,shiyasa ma inna saude tadaina bin hanyar haka ma baraka ko saudaya bata bari hanya ta hadasuba. A yan tsakanin ne akasa ranar baraka da Muhd dinta 5mnths. Basu baraka kadai ke gudun mama ba harda Ya Ali shima idan yazo garin bai biyowa ta kofar shagon ya gwammace yayi zagaye ta hanya mai nisa, ya kanyi kuka shi kadai idan ya tuna halin da mama take ciki baida abinyi face addua kullum bata yankewa a bakinsa yakan jima bai shigo garin badon kar ya shiga gida a rinka bashi mummunan lbr masu jirkita masa tunani. Kwanci tashi watan haihuwar Mama ya tsaya ta kumbura dam! kamar ta fashe sbd hawan jini bata sani ba, tunda ba awo take zuwa ba, amma shegen dariya yake mata wai ta dawo alkubus. Ita kadai a daki tsakar dare nakuda kamata ta rasa inda zata tsoma ranta taji dadi tayi nan tayi can tana ambaton Allah tare da tambayar kanta wannan wane irin ciwone kuma? gab da asubah jini ya goce mata idanuwanta suka raina fata fadi take shikenan zan mutu! ta hau kuka tana kiran zan mutu danliti ka taimakeni! garin Allah ya waye 7am danliti baiga tazo shago ba alhalin kullum 6am take zuwa wata zuciar tace yaje ya ganota ya buga mota ya iso gidan ya iske a kulle yayi ta bugu bata bude ba wasu samari suka taimaka masa aka buge kofar ya shiga. a zatonsa ma ta mutu ganin ta shame shame cikin jini saida ya tabata ta motsa tace zan mutu ka taimakeni. cak! ya daukota ya saka a mota sai asibiti take sukace bazasu iya ba ya kaita kagara, nan da nan ya buga mota yazo shago ya kwashi kudi ya wuce yanata zage zage dama haka takeso aci kudina tana jin ciewo tayi zamanta bataje asibiti ba zata farfado ta hadu dani kudin dana kashe saita biya su don ubanta .......ayuba yayi tagumi yana juyayin karfa mamatarasa ranta .yana isa asibiti a ka turata emergencylikita yace tiyata za'a yi mata sunan bukatar jiningaggawa. Babu yanda Danliti ya iya dole yaceagwada nasa jinin a gani ko zaiyi daidai Aka gwadaamma bai yi ba. Mai daukar jinin ke gaya masa akwai wanda ya saba bada jininsa ana biyansa, idan yayarda a kira shi au tsadance ya biya. Ba ason ransaya amince ba nan da nan aka kirashi, suka tsadance,ya biya shi dubu biyu aka diba, ga kuma kudin aikidubu goma sha biyu da dari bakwai da hamsin. Donhaushi kamar yace bashi dasu wannan shiri Maimakon yaci bulus ya dawo yana cacan kudi donneman lafiyarta. Wucewar minti talatin aka fito da itada jariri namiji. Santalele dashi ga kyau ga girma shikansa likitan sai da yaji kamar ace babyn nashi ne.Malaman jinya kuwa kamar su lashe yaron. Ahi kuwaDanliti yake kawai yakeyi cikin dan kankanin lokaci da bai wuce awa daya ba an wawure masa kusandubu sha biyar, bai ma san me zataci ba nan gaba namagungunan. Ya na tsakar wannan tunanin watanurse tazo ta gaya masa akawo kayan da za asawababy kudin aljihunsa kaf sun kare sai da ya komaFandogari rai bace. Ayuba yayita masa dariya yana masa kirari, "angon karni angon karni!!", bai kulashiba ya shiga ciki ya sake lalo wasu kudin ya fito yakoma. A kagaran ya shiga wani shago, ya sayo kayanjarirai kala hudu da rigar sanyi, sai sabulu da Omonwanki ya koma asibiti ya kai musu aka sayaron.Mama tana kwance bata farfado ba tukuna. A ka kawo masa jariri ya karba ya zura masa ido gaban saya fadi. Yace a ransa "kaga shegen yaro kamar mudaya dashi? Maimakon ka kwashi uwarka, sai kadebo ni? Tun yanzu kenan ka nuna min baka dakunya". Ya bawa kansa dariya ya shiga yi kamarsakarai" kwana bakwai mama ta gyagije tare da taimakon nurses da wasu masu jinya saboda karyarda sukayi, wai daga nesa suke kuma iyayensu basason aurensu, shi yasa babu wanda yazo jinyarta.Babynsu sai kara kyau yakeyi, shi ya kara jawo musufarin jini a wajen ma'aikatan asibiti da masu sontaimaka musu. Ranar da ta cika kwana 7,aka sallamesu likita yagindaya mata sharudda banda aikin qarfi,sannan tatabbata tana samun ishashen kayan qarin jini....dantayi saurin maida jikinta.sati daya aka basu su dawoakara duba lafiyarta sukayi sallama da kowa cike dakewa,,,,don anriga ansaba dasu.danliti ya kwashesu a mota suka kama hanya. sunfara tafiya ta kallesa idokode tace haryanxu banji kafadi sunan yaronba,kawaiqarya nayi wa mutane ake kiransa adamu...jitayikawai yamake mata baki..kar insake ji bakinki ya kirawannan sunan.dama na kyaleki ne dan ganinmutane,,don iskanci kirasa sunan da zakisa wa shegen danki sai sunan ubana? Tuni take rungume da baki ido waje takekallonsa,,tace haba danliti!baka tausayina? dana sansunan babanka ne zanfada?wlh zuwa kawai sunanyamin nafada musu shiyasa ranan da kazo da ayubasuke ta kiranka baban adamu... yasake kawo matawani dukan,yace sake fadi kikayi?? wato raini ya shiga tsakaninmu koh? bakisan cewa inajin haushinkiba ko?to kibi a hankali,idan kina neman zaman lafiyadani,,idan nasake jin adamu a bakinki sai na karyakiwlh..... taguma ta doka tana kwalla tana kallonsa,Allahb aka haquri danliti,yaron nan dai dankane,duk sunanda kace akira dashi za'a na kiransa.bannaso na bata maka rai danliti..amma kai abu kadan sai fushi. yacebabu ruwana da sunan yaro,,idan kinso ma kinakiransa BIRI ,duk daya a wajena!tace Allah ya hucizuciyarka,, maganar batakai hakaba,tunda ran talataaka haifishi zamu na kiransa mai kudi...yadan dubetakadan ya kauda kai yarage naki inkinso ma kina kiransa miloniya wannan keya dama..zatayi maganayadaga mata hannu banso jin don Allah kimin shiru.tasunkuyar dakai tana kallon yaron dayake jikintayanata bacci abunsa.har suka iso gida,,basuyi wanimagana ba.ya tsaya kofar gida tafito yatayata kwashekaya..taron mutane nata kallonsu suna mamakin wannan lamari..bai zaunaba yajuya yana kokarin fitatace ya maganar abinci?zan girka ne ko za'a na kawomin na sayarwa? Ya kalleta sama da kasa yace,wai ke me kikadaukeni?baki ganin kudin dana kashe a asibiti? Koshagon kikeso ya rushe na tsugunna? baga saurankayan tea a nanba?ki hada mana kisha! Kedamaba'aso ki nannagi abu mai nauyi.mtsssss..... Yajatsaki yayi waje,,,ta koma gefen katifa tana tabe baki...a ranta tana fadin Allah ya huci zuciyarka.tadangyara waje tamaida kai ta kwanta ba'a jima ba bacciya dauketa... Bayan sallar la'asar kukan yaro yatasheta.ta tashi da sauri tabashi nono da ruwa..nandanan yasake komawa barci.tafito tsakar gida tanahamma tareda mikar yunwa..tayi dan shawaginta a tsakar gida takoma daki..tajanyo ledar kayan tea tazuba a kofi tajanyo fulas zata tsoyayi ruwa taji baburuwan..tasaki tsaki ta nufi kichen babu itace ko dayabare ta daura.haka tadawo tasha tea da ruwansanyi..tasake kwanciya dan babu abunda zatayi harqarfe taran dare bataga danliti ba,,bare tasa ran wani abun sanyawa a baka. Ga yunwa tana sha'awar tacimai dan gishiri...nan take tayafa gyale ta zura silifastadauki jariri taja kofa tayi waje ta lallaba a hankalitayi wajen danliti.....yana ganinta ya daurefuska,,,yayinda ayuba ya taso ya karbi maikudi,,meya kawoki?inji danliti tace naji shiru ne ga yunwa inaji.....ba akwai kayan tea ba?we me kedamunki ne? Murya raunane tace nasha wlh..dama ruwan sanyinasha babu sauran ruwan zafi kuma babu itace...maidan gishiri nake sha'awan ci kodan yayane! Ya gyarazama nifa ba ubanki bane,bakuma mijinkiba bare kinadauramin wannan nauyin,,kingane koh?daga taimakosai ya zama tsiya?ki dauki duk nauyinki ki dauramin? to bafa zai yiyuwa kinjiko?karkisake biyoni shago kicenabaki wani abu...abun da nasamu nabaki basai kinmatsamin ba..karki sake dauko danki kizominnan...idan kunne yaji..... Tace yi haquri,,,yacewaayuba bata danta ta koma.ta karbeshi tajuya zatawuce taji yana fadin bata taliya daya taje tadafa karta cinyeni....ta karba tana murna ya wurga mata nairaashirin tasaya itacen..jikinta na rawa ta dauka hardagodiya ta sabo yaronta takoma gida..sai yanxu matake tunanin a ina zata samo icen dare yayi?ta sauqenumfashi numfashi takoma takwanta dayunwarta.dasafe da kanta taje ta nemo itace,ta tafasa ruwa ta dura a filas,tayi wa danta wanka itamatayi..tahada tea tasha da ragowar biredi. Tayi wanka tayi wanki duka ita kadai,,anjima kumadole ta bararraka taliyan da zataci.ko ta ci gaba dashan shayi...aikin yamata yawa ita daya shisa dakwantawarta zazzabi ya rufeta. Maganar haihuwartakuwa naci gaba da yaduwa a gari,wasu emmata masukarambani haar suna zuwa mata barka.haka tci gaba da manejin rayuwa sai abunda danliti yaga dama yakekawo mata taci,a lokacin da kuma yagadama! .......kwana 7 suka cika tayi masa maganarkomawarsu asibiti,,,kai tsaye yace bai zuwa,Allah daikonsa jikinta ya hade kamar yana samun kyakkyawarkulawa.haka mai kudi yayi bulele dashi alamun ruwan nonon dayake sha yanada kyau...batadai zuwa koina,,,saboda danliti yahana.komaisa oho?shi kadaiyasan dalillin yin hakan. wannan satin shine ake bikin baraka da muhddinta,mama na gida mai kudi goye a bayanta.tunsafebatasa komai a cikintaba,,,har zuwa yanxu da akaidar da sallan la'asar.tagumi hannu bibbiyu tayi tunanitake lafiya meyafaru da danliti baizoba?bata samuamsarba taji tsayuwar motarsa. Farin ciki ya lullubeta ta taso ta tarbesa.babu walwala ya wuceta yashigedaki...t abiyo sa abaya tazauna kusa dashi tanatambaya,,,waya tabamin cweethrt dina?ko fushin netunna jiya? Ya ballo mata harara yace kinason wanimarinko?to kici gaba da tadamin wannanzancen,,tadan kada kai tana murmushi tace sha kuruminka,indai maganar aure ne bazan sakeyimakaba duk lokacin dakaga ya dace saimuyi,,shiyasa bangankaba tunsafe?.......ido zuruyana kallonta bansaniba! tace yi haquri shalele mezanci yau?yace babu,ki tashi kishirya kije gidan bikikici..tace bikinwa? yace ke saboda sakarci ma bakisan ana bikin yar uwarkiba?bikin yarinyar nanakeyi baraka...ta ware ido ta washe baki,bikin barakaakeyi?to ina zan sani ka hanani fita? Yayi matabanzan kallo ai dama ni kike gani na hanaki fita?toubanwa zakiyi a waje?kina samun ci kina samunsha...kinfiso kirinqa yawo kwaroro kwaroro da goyo ana nunaki?to shikenan tunda kinfison hakan gahanya nan,,,,amma kisani kwayar dawa bazan kawomiki gidan nan ba..da sauri ta rungumeshi,Allah sarkidan litina,ba haka bane ,nima bana sha'awarfitan,tunda baka so.yanzu bari in shirya ka saukeni agidan bikin...a razane ya kalleta,wai ke meyasa jaka ce?kawai sai in daukeki a mota in kaiki gidan biki anakallonmu? idan ke mahaukaciya ne nida hankalinanasan abun da nakeyi.... BAKIN CIKI 3***2 Yaja dogon tsaki ya tashi .da sauri yatashi yafitayana fadin sakaryar yarinya kullum sai ta bata wamutum rai!ta taso ta biyo shi tana bashi haquri,baisauraretaba yafada mota abinsa,,,,tadawo tanahawaye tana shirya mai kudi.ta goyashi ta rufa gyaleta kulle gidan...bata zame ko inaba sai gidansu baraka.ana tsaka da biki kallo yadawo kanta....dukyan uwa na kallonta a wulaqance,tana gaishesu sunabasarwa.kai tsaye inda inna saude take ta dosa,takuma zuba mata ido harta qaraso gunta,,,sannu inna!Ta bita da kallo daga ina?tace daga gida,yanxu danlitiyake gayamin ashe auren baraka ake,nace ina nasani! inna saude tace dama ya za'ayi ki sani?ke kokunya bakijiba?kika ratso jama'ar nan da goyo kikashigo?dubeki kamar ankoraki babu mamaki ma bakiciabinciba. Duk baki ya wani bushewa anya kuwamama...baza kiji magana bako?wannan duniyarkagama da iyayenka lafiya ma ya ka qare?belle ke kina kallo mahafiyarki tafadi ta mutu saboda BAKINCIKi,,mahaifinki nacan bisa keken nakasassu.ammaduk wannan baisa kinyi nadama ba mama?ke kuwawata irin iskar duniya ke kwasarki????? A marairaicetake magana inna bai kamata ku ringa ganin laifina bani kadai....ta katseta da sauri rufemin baki sakarya! Da yana son aurenki da tuntuni baizo yayi maganaba?tun yaushe kika haihu?ina lissafi watanki biyarkenan! ya ajiyeki kawai kin biye masa kunawatsewa..wa llahi ki guji makomarki,,ki kuma gujiwalaqancin da namiji.gashinan ai kinfara gani da hakakike?to wlh ki kuka da kanki karma kice kin sanni,,saboda haka juya ki koma inda kika fito! Tace aidama shima dan liti yace inya shirya zaizo yasameku a daura mana aure,ta watso mata harara tajadogon tsaki zata wuce mama tace banga amaryarbainna,ina take?ta juyo tace,suna makwafta itadaqawayenta..tayi tafiyarta sabgoginta.mama ta shigazabga loma,rabonta da abinci da naman kaza harta manta.tayi ta zabga tana zare ido gwanin tausayi.kankace kwabo,ta tada shinkafar nan cikin kwanotatas,ta kora ruwa da kunun aya tayi gyatsa tayihamdala,sannan tajita aduniya.. Tananan tsuru kamarmujiya baraka tashigo cikin gidan,inna ke gayamatamama tazo,,ta zagaya bayan kicin din tasameta zaune tana bawa mai kudi nono,,bakin ciki yaturnuketa kamar ta hadiyi zuciya ta mutu.haka nan tacije ta qarasa gunta fuska daure....amare!injimama,tace mama kenan,ya kike?tace kuma dankowa ya gujeni shine hardake koh baraka?zancenbikinma a bakin danliti nakeji,,,banci arzikin da zakizo kisameni ki gayaminba.ai kinsan inda nake.ta kalletasama da qasa ni bansan inda kikeba,,koda ma nasaniwannan ba gidan zuwana bane..hasalima namantadake.bandan kinxo inna tace kinanan ba wlh bazantaba tunawa dakeba.! mama tace ba laifinkibane,,,,,,,ta rausayar dakai tace thank god da kika gane ba laifina bane.bari inkoma frnds dina na jirana.tajuya dasauri tawuce ko kallon yaron batayiba.mama ta tabebaki tace agayas mai qawaye,zakaran da Allah yasoda cara,ko ana muzuru ga shaho sai yayi.danliti nedai ba a kauna,nikuwa inason kayana,bazan rabudashiba! yawwa! Ta mike ta jefa mai kudi a baya ta goyeshi ta tafi neman inna tasameta tace innazantafi,ta juyo ta dubeta,bangane zaki tafi ba?bakijiabunda nace bane?ko a zatonki wasa nake?nandanan ta kumbura fuska.samu wuri ki zauna kafin nabata miki rai!ta zauna gefen gado tana kunkuni,kowana kallonta,masu taya inna fada nayi........ana sallar magaruba gida ya gwaraye da duhu sai inda aka ajiyefitulun kwai keda haske.mama ta fakaici ido ta sulaleabunta ta kullin wainar ta da miya,duk ta juye su cikinleda.abincin dare ne da aka rabawa kowa tajuye nataa leda,,ta cika wa zaninta iska ta harba gida abinta.Hankalin inna bai dawo garetaba,,sai da za'a wuce da amarya.ta nemi mama sama ko kasa ta rasa.ta dokatagumi tana sanar da Allah da manxonsa kafintace,kai jama'a!wannan yarinyar tayi nisa batajin kira! Allah ka shirya mana ni saude..sauran mutane sukace amin!haka aka wuce da baraka tana kukan BAKINCIKI!da takaicin yar uwarta.ita kuwa mama tana can hankalinta kwance,ta juye wainarta a kwano miyarkuwa taji tantakwashi masu taunuwa,zatafara cikenan danliti yashigo gidan ,ya tokare bakin kofayana kallonta,,,tace saboda me?yace saboda naxokafin magruba naga baki dawoba. Tayi dan murmushidanliti kenan,bikinma badan kaikace najeba maizai kaini?kaga maganar inki dawowa ma baitasoba.yaqaraso yana fadin Allah yasoki,dama bell dina nadawo induba,idan baki dawoba inbiki hargidan indawodake,,sannan inmiki shegen duka! kinganshi ko?, Tace Allah sarki danliti bai kamata kanadukanaba,,,iyakar biyayya inamaka,amma dankuskure kadan sai ka hassala..!ya zauna kan tabarmayace,ke dai kiyi shiru tunda Allah ya kwaceki yau,aiku mata sai da haka,domin kwakwalwar kifi Allah yayimuku. Ta sosa kai tana kallonsa,batace komai.danki yayi barci ne?tace eh! Meye wannan kike ci? tacewaina ce inna ta bani.yajanyo kwanon gabansa yacedama kuwa yunwa nakeji..tace to muci tare mana aitana da dan yawa.yace ni bazanci dakeba miko filet inzuba miki.ta jawo filet din roba ta miqa masa,ya jefamata guda daya..tace guda daya nagani?......a fusace yace wannan wani tambayar banza ce?don kinxo dawaina zanci? shine kike min kurilla?watau nawa nebanza!ga tsiyarki cinye dani kike zancen,,,,ya turamata kwanon.da sauri ta maida masa ta tarairayo shikamar na goye,tayi ta rarrashinsa,sannan ya aminceda cin wainar. Tarinqa bashi a baki,,ya taune qashin ya batse.ita kuwa ko guda dayar bata ciba,bata ma kokwatanta ci ba,don karya ransa ya baci.sai dayagyatse,sannan ya gaya mata bibikon da yake nanemanta...babu musu tabada kai bori ya hau Haka rayuwar mama ta kasance tamkar tadabbobi,,duk inda danliti ya kadata can zatadosa.tsakaninta da Allah kafin maikudi ya shekarabiyu ya zubda mata ciki sau uku kuma kowanne babuwanda batasha wahalar zubansaba.,,duk ta jeme tayiduhu fatar jikinta yafara yaushi saboda wahala da ukuba.(Allah zai i sarmata) ......tabbas hakane,tundamasu ganin rashin jinta ne yajawo mata halin da takeciki sunayi mata addu'a, mussamman abba kullum yadaga hannu samu bashi da abun nema wajen ubangijiface Allah ya dafa masa akan qaddarar data sauqaaka sakeena,wanda hakan shi ke hana yan uwanta zuwa fandogari...amma kannen abba sukanxo abujasu dubashi.haka ya ali musamman yake zuwa damatarsa su duba abba su koma. Shekarunta qarashudewa suke tare da qara dumulmulewar rayuwarmama cikin kunci da talaucin dole...duk yansuturunsu sun mutu,ko da yaushe busu busu zaka gansu,musamman lokacin sanyi.babu manshafawa ,babu sabulun wanka,balle na wanki,sau ukutana zuwa neman taimako wajen inna tanahanata.tace muddin bazata dawo cikin yan uwantatazaunaba,ko kwandala bazata bataba......mama tagammace hakan shiyasa ma tadaina zuwa.wani lokacin tsirara zakaga mai kudi yana yawo sabodarashin sutura.sai makwafta sunga Allah sunga annabizasu kamashi su sanya masa kaya sadaka,anya?kaicon wadanda imani yayi musu karanci! BAYAN SHEKARU GOMA SHA BIYu. Nasan maitausayi da imani zai daura hannu akai yanakururuwa,idan yadubi halin da mama take ciki dayaronta kai duniya!ina zaki damu? shekarunta nahaihuwa talatin da biyu cif cif.amma idan ka dubetazaka rantse da Allah ta zarce hamsin.tsufa ya bayyana kuru kuru a jikinta,badan takai shekaruntsufanba sai don wahala. Sau da yawa tanayin rashinlafea babu kulawar data dace,saboda zata kwantaciwo sai ta kusa sati akwance kafin danliti yakaitaasibiti. koya sayo mata magunguna.muddin kuwahakan ya kasance to tabbaci idan ta warke sai ya kirkiro mata laifin da bai taka kara ya karyaba,don yajibgi kudinsa...a wasu lokuta idan taje rokonsa ayubake tausaya mata ya dauka cikin shagon yabata aranar kuwa zai bita gidan ya narketa yandayaso,dataga hakan ba riba sai ta fara neman wankaua makwafta tana samun abincin da zasuci itada danta. A wannan hali mai kudi yatashi yagamahaifiyarsa cikin ukuba da azabar duka wajenbabansa,wanda shikansa yagane randa yazogidan,sai yaga mahaifiyarsa na kuka.tunyana matamaganar makaranta har yadaina.ya fahimci cewabashida gatan xuwa makaranta kamar sauran yara!!... Daka dubeshi,kaga yaro mai kyau amma babugata.sai dai abun mamaki a game dashi yana danitsuwa kuma a koda yaushe yana taredamahaifiya rsa.,musamman inyaga tana kuka,daya farakawo qarfi sai yafara fita nema,shine yankan ciyawaya siyar,shine neman kwalabe da fasassun robobi da tsofaffun karafuna a bola,yana kaiwa inda akesayarwa,ya siyar ya kawo mata kudin. A haka tasamu da kudin datake wankau tahada,tajajarin AWARa,tana rabin tiya tana sayarwa a zaurengida.a haka take dan saya musu kayan gwanjo masuarha.duk wannan halin da mama take ciki gaba dayajama'a namata kallon rashin biyayyar iyayece ta jawomata hakan.shiyasa kalilan ke tausaya mata.itada gidansu sai gani sai hange,,ko a hanya ba dukkansuke magana da itaba,rayuwa tayiwa mama tsauri dayawa,tsawon shekaru ashe dole tayi tsufan qarfi dayaji........yamma tayi sosai lokacin da mama kezaune gaban kaskon suyar waranta a cikin zaure.yaranata shigowa suna saye naira biyar biyar,goma ashirin,duk yanda takama.muna iya cewa tanaciniki,don bata tabayin kwantaiba.maikudi ya shigosabe da buhun tarkacensa a kafada.kayan jikinsaduku duku,kafa babu takalmi,ta cire kai cike da fara'ata kallesa,yaro dan umma andawo?ya zagaya gefentaya zauna.nadawo umma.tace angaisheka.to kaje kayi wanka kayi sallah,akwai dumamenka yananan atukunya,ka zubo kaci.yace to ya mike ya sungumibuhun kayansa yashige gida.yayi duk abunda taumurcesa.ya zubo tuwunsa yadawo zauren gefentaya zauna. Ta dubesa sai kaki ci saboda riba?kai nalura kafini son kudi,,,,yayi yar dariya yace umma kenan yanxu saboda Allah gabadaya ribar nawakikesamu?tace mungode wa Allah ko nawa ne,ammaai dole aci,dauki guda biyu to,yace barin gama cintuwon tace gama idan kuma ta qare ka huta. Ya sa hannu ya dauki guda biyu ya ajiye a gefe,yaceban nuna miki ciwona ba,wani tsohon kwano ya yankemin gefen kafa!ta kamo qafar cikin sauri da tausayitace wayyo dan umma,sannu,shiyasa na kosaingama tara maka kudin takalma ka sayo,gamacintuwon inbaka naira goma kasayo ja da yalo in rinqa barbada maka yana saurin warkar da ciwosannu.....yace to umma!sukayi shiru yanata cintuwonsa yana gutsurar awaransa,jim kadan yaceumma wai ni bani da wani suna ne sai mai kudi?tayidan murmushi tace kana da shi mana...yace aibantaba jin kin kirani bane,zura masa ido tayi tace sunan kakanka gareka shisa bana kira shima yabitada kallo yace kigayamin inji,gobe idan munhadu daabokina in gayamasa,tace sunanka adamu,ya sakibaki yana murmushi,yace lalle ai sunan tsofi neamma inason sunan.tayi yar dariya tace amma karkabari babanka yaji yasan nafada maka dan baya so,yace saboda me?bashi ya radamin ba?tace shineamma saboda sunan babansa ne baiso ana kira.yatabe baki yayi tsaki,yace bani kudin ja da yalon,tamika masa naira goma yafita yana sude hannu,tabishida kallo ta kada kai,domin ta fahimci bayasonmaganar babansa,,,bai taba yabonsa ba kuma bai damu da al'amuransaba.bai dade ba yadawo damaganin,ya zauna ya kakkabe kasar jikin ciwon,yamika mata kafar tasanya masa garin maganin.nansuka zauna sunata hirrasu har wara ta qare,ya kwasomata kayayyakin yadawo mata dasu gida,yayin da itake zaune tana qirga kudin,gaba daya dari uku tayi ta ware uwar kudi Ta ware uwar kudi,tasamu ribar naira tamanin,ta cirenaira goma tabawa mai kudi tace jeka wurga a cikinasusun takalminka,kayi sauri kayo mana cefane danaira saba'in din,sannan ka auno min wakensuya,rabin tiya mai gwangwani biyu....yace to ya karbikudi yafice,itama ta mike ta ddebi ruwa a bokiti ta dauki sabulunta yankan qusa,da soso tayo wankatafito.injin oil dinta a yar roba,,ta dauko ta shafa tacanxa tsumman zaninta da wankakke, ta hada dawata kodaddiyar t shirt,ta fito tashiga kicin ta doraruwan tuwo. Sallamar mai kudi ta amsa ta leqo dagakofar kicin din jirgi dan umma,shiyasa nake sonka saboda babu wasa,,yana murmushi ya zube matacefane,ta duba komai dai dai yasayo ya laluba aljihuya ciro naira biyar ya miko mata ta me ce ce?yacemai waken suyane yamin ragin naira biyar,ta dafakansa,tace Allah sarki mungode,amma kaima kajekasha minti,,,ya kada kai,umma me zanyi da minti kamar qaramin yaro......ta kece da dariya!iye lalle maikudi angirma ko?to je kasha rake..yace umma ki ajiyeko farin maggi kya saya ko kuma a xuba a asusu...tazura masa ido tadan kada kai jeka tura a asusun,,,yawuce taraka shi da kallo harya fito tana tsaye batamotsaba mezan tayaki umma? tace kaga ka zauna ka huta ai ka sha gararanba dan umma,,,ya kamata kahuta,kaga rauni a qafarka.yace to. Ya jawo tsohuwartabarma ya kakkaba ya shimfida a kofar kicin din,yakwanta.it a kuma tana ta hidimar mada miyar kukakamar yadda yayo mata cefane,. Bayan ta kammala,ta fito da robar gari tanatankadewa tana fadin daga yau ma garin tuwunmu yaqare,,,ya yunqura yatashi,yace ai gara daya qare maumma.nagaji da cin tuwon nan,ta dubeshi da kyautace yaro kenan!har ka mance wata rana ma nemantuwon mike ido rufe? bama samu?kadaina fadar haka komai Allah yabaka kayi masa godiya sai ya qaramaka kaji ko?yace naji umma amma kinsan waniabu?sai ka fadi...yace in Allah yasa natara kudi dayawa zanbaki mamaki.tana dariya tace aidamakasaba bani mamaki yarona.....yace amma baki tabaganin wannanba....kedai kiyimin addu'a Allah yasa intara kaya da yawa,,,tace to Allah yasa dan ummayace ameen..ya koma ya kwanta yayi matashi dahannunsa.yana bata labari tanashan dariya.ta qaregirkinta ana kiran magrub..ta kwashe ta aje gefe gabadayansu sukayi alwala sukayi salla,shiya dauko musuabincin sukaci tare kamar yadda suka saba. Bayan sallar isha'i ta koya masa karatun alqurani kamaryadda suka saba haryakai amma,mai kudi nason yinkrtu amma basu da kudi shiyasa take koya masa dakanta.kullum kafin su kwanta,,,musamman ranakunda babansa bai xoba,,,shiyasa bayason zuwansa.donyasan zuwansa baya haifar da komai sai BAKIN CIKI .A Garesu Kwana uku mama na ririta kudin da ke hannunta dankar dan jarin da take taqama dashi ya qarye,,,gashidan gogan yaqi waiwayarsu balle ya wurga masu nairadarin datake samu tayi awo akai niqa,su sami garintuwo....shikuma mai kudi yana can kasuwa wajen yankyadi da tulin kayansa.. Daya tara buhu buhu,,,kuma Allah da ikonsa wannan karon yasamu manyan kayamusamman karafa,aka auna kayansa sai gashi dakudi naira dari bakwai da hamsin...kai farinciki kamarya kasheshi,,,,nan da nan yafada kasuwa.dafarkoshinkafa yasaya rabin tiya.......ya wuce teburin mainama yasayi na dari da hamsin,ya koma bangaren kayan miya aka hada masa na naira dari,yabadamarkade,,,aka juye masa aleda,,mai gwangwani biyuda maggi mai tauraro dda fari,ya koma ya nemi wajeya nutsu ya qirga ragowar kudinsa naira dari dasaba'in yanade abinsa yamaida aljihu ya kwasocefanensa ya dawo gida. Mama tasaki baki tana kallonsa da ledodi,,,ina kasamo kaya haka? yacedama nagaya miki zanbaki mamaki,kayan da na tarane...ta bude ledodi tana fadin iye! yanxu kayan nanharsun kai haka?yace naira dari bakwai dahamsinfa...kinga harda canjin dari da saba'in nakawomiki ki qara jari,,,,ta saki baki tana kallonsa ya miko mata kudin,,,ta amsa kina ta kallona umma ko bankyautabane?ta janyo shi jikinta da sauri tace a'a danumma..gani nayi ka kwashe kudinka ka kashe,bakasayo wa kanka komaiba,,,,ai da kasayo kodatakalmine,kaga wancan asusun sai kaci gaba da zubamasa abunda yasamu kawai.........yace babu komai umma,nima so nake muci dadi yau,,rabonmu fa dashinkafa tun na sunan maman fati kullum tuwo mukeci,,aiya kamata mu canza,tunda nayi dabara nasamukudin. Tayi dariya tana mamakin mai kudi,,,,sannan tanumfasa,,gaskiyane,Allah yayi maka albarka.ammaduk da haka kadauki saba'in da biyr kasayosilifas,inyaso daga baya sai kasayo dan dari biyu dahamsin din,,,yace umma kibar maganan takalminnan,yanxu kawo talatin nasayo itace,tace to tamiqa masa to maza kaje ka dawo kayi wanka ko?yace toumma.ya fice tana fadin haba ni inacan inata tunaninbanga dan ummaba ashe yanacan yana kashe managara.Allah sarki mai kudina!ta kwashe kaya ta nufikicin ta hura wuta ta daura shinkafa da sauranitacen,,,,yana kawo mata itacen tahadi wani murhun,,,ta kama hidimar miya.shikuma mai kudi yayiwanka ya sauya kaya ya fito ya shimfida tabarma yazauna .ta miqa masa warar data aje masa gudabiyu,ya karba yanaci suna hira abinsu. Kafin kiranmagruba ,gida ya hautsine da qamshin dage dage gashinkafa a gefe,,,,,tuni ta sauketa gwangwani uku ta dafa ta wadace su sosai .kawai tsayuwar mota sukajia qofar gida,mai kudi yayi wuf yatashizaune,,,gabansa ya yanke ya fadi,mama da sauri taleko tace kamar tsayuwar motar babanka?ya qaradaure fuska,,shine man..to menene na bata rai?yayiwuf ya mike ya dauki buta yafada bayi. Ku sakani a addua zan fara exam, tnx. BAKIN CIKI 3****3 Ta bishi da kallo tana kada kai,,,,babu sallama yashigo.bakinta har kunne..sannu da zuwa!ya kalletasama da qasa hannaye cikin aljihu,yace tundagazaure nakejin qamshi,na makwafta ne?ko a nangidan???ta matso shi sosai ganin ba fara'a a fuskarsatace wlh mai kudi ne yasayar da kayansa yayi mana cefane harda nama,shiga ciki barin zubo maka....yawatso mata idanuwa mai kudi?karki mai dani wanisakarai mana.kinfara iskanci kina samo kudi ko?dasauri ta katse shi,,iskanci dan liti?ya daka matatsawa,rufe min baki ko in farfasa miki kai,,,banxakawai ina magana kina so ki qaryatani..ya wuce kicin din a fusace yaje ya duba,,banda ke yar rainin hankalice mai kudi ne zai samo miki kudin uban wannancefane?ina mai kudin?ta durkusa gabansa ido tafhawaye tace na rantse da Allah danliti bangaya makaqaryaba,,anan yayi ta tara kayansa buhu buhu ya fitadasu ya....ya isa haka don Allah! mtss yaja tsaki ya wuceta tsugune. Tsakar gida yatsaya yana dagamurya ina mai kudin?cikin sanda yafito daga bayin,daganinsa dama can kuka yakeyi,,,zonan danuwarka.ya matso gabansa yana kokarin tsugunawayasa hannu ya murde masa kunne miqe tsaye daniska!gidan ubanwa kasamu kudin wannan cefanen? yayi banxa dashi BAKIN CIKI ya hanasa badaamsa...... Kafara sata ko?to saurareni dakyau,,,duk ranarda aka kamakakayi sata daga kai har uwartakamai goya maka baya karku kuskurakuce kunsanni! kajiko?bai tankaba.illa hawayensa da suka qaratsinkewa bace min dagani shegebarawo yaruga bayan kicin yatsuguna yana kuka,mama na tsayeta rasa nayi itama hawayentakeyi,,,,yaja dogon tsaki ya wucedaki.dole ta biyoshi badan rantayasoba sai dan sanin batada yancinrarrashin danta agabandanliti...........yana zaune gefenkatifa tazauna a hankali tace kabanmamaki danliti daka mancezamanka nakeyi a cikin gidannan,,,,ya daga mata hannu bansonjin komai dan Allah.tace to nazubomaka abincin?yace kema kinsan baabincinku naxo ciba..tadannumf asa kanta sunkuye gwanin bantausayi..... ...ankusa idar da sallarmagruba taje kicin ta debo masaabinci cikin langa da nama yakaiyanka hudu,,,,,,ta hado masa dakofin ruwa ta ajiye agabansa.yanaci yana danqara matamaganganu! bai kammala ba maikudi yashigo gidan,,,waye yakemana sanda?ya amsa da kyarnine,,to miye kakeyi wa mutanesanda? yace ba sanda nakeyibamasallaci nadawo!yace sannu dazuwa liman,ya koma can jikin kicinyayi zamansa.ya qare cin abincinsannan ya dubeta baki buqatarkomai tunda danki nakawo miki. Kafin tace wani abu,ya miqe yanashirin barin dakin,ta biyoshi tanahaba danliti!kwana nawa rabondaka waiwayomu?kuma wannan yarshinkafa kwana nawa zata mana?idocikin ido yace bafa dolenabane,,,,ni ba mijinkiba ni baubankibane,ko ban fadaba?.........tayi shiru dan bataso ta qara waniabu dazai jawo mata duka,,,sabodahaka ta kyaleshi,,,yasa kai ya ficebai ko kalli inda mai kudiyakeba.....ta jima tsaye tsakar dakisannan ta fito ta tsugunna gabanmaikudi tadafa kansa kayi haquridan umma!yace wai umma meyasakika auri wannan mutumin?cikinfada take masa magana karka sakemin wannan tambayar idan kanasomu shirya dakai cikin gidan nan.yagoge kwalla da bayan hannu kiyihaquri umma,dole nagayaa mikigaskia natsani wannan mutuminnatsane sa.shiyasa danayi sallahyanxu na roqi Allah ya kasheni danbanaso na girma dashi. Ta xuramasa ido na tsawon lokaci habadan umma karka daga min hankalimana meyayi zafi?yace umma dukabunda baba yake miki ina kallokuma inajin zafi,mesa zaice minbarawo?bayan ni banasata...umma da baba yayi minbaki inzama barawo gara na mutuAllah! tace bazaka mutu ba danumma kuma da yardar Allahbazaka zamo barawo ba.kai yarone shisa kake gani babanka ya cikafada.amma idanka girma zaka ganesauqin kai gareshi.baka ganin harabinci na xuba masa yaci?to aialbarka yasa maka.saboda haka kakwantar da hankalinka komai zaiwuce da yardar Allah kajiko?bariinyi salla inxo muci abincinmu. Ta share masa hawaye ta tashitayo wanka tadauro alwala tayisalla,lokacin ana kiran isha'i,,,,donhaka tadaura gaba daya,,,,shikuwamai kudi yanajin kiran masallaciyatafi bayan ya dawo suka zaunacin abincinsu.tanata lallashinsakafin tasamu hankalinsa ya kwantatadaura masa karatu sukakwanta......yau kwanansa hudu cifdayin rauni a qafarsa yana tafeyana yawon neman robobi dakwalabe amma bayajin dadinjikinsa....wani irin sanyi yakeji gazazzabi na neman kamashi hakayaketa yawo bashi wannan bolabashi wancan,,,,,,har aka kiraazahar,ya nufi wani masallaci danyin sallah.ana idarwa yafito yadaukibuhun kayansa yaci gaba,,,la'asart ayi,,,yanajin qira bai bata lokaciba ya nufi masallaci,,yabada faraliAllah kenan yaro qarami sai kaifinhankali shiyasa yake bawa mutanemamaki harba mai iya daga kaiyayi masa gori. Yana fitowamasallaci gida yadawo sabodazazzabin qaruwa yakeyi,,,mamanata yanka wara tana sawa a cikinruwan gishiri.....yayi sallamayashigo tana amsawa yau da wurihaka dan umma?ya jingina buhunkayansa yadawo kusa da ita yazauna.yace zazzabi nakejiumma..da sauri tajawo shi jikintata cusa hannunta kasan wuyansataji zafi rau..wai wai aikuwa gajikinka yayi zafi maikudi meyasatuntuni baka dawoba? yace inatunanin dan abunda zan samomana ne umma,,,kinga bamudaabinci Ta rungumeshi,sosai ya kwantajikinta,tace Allah sarki yaronakomai ai sai da lafiya.bari inyisauri inje chemist insamo makaparacetamol kasha....kwanta nan kajirani.ta miqe tadauki naira ashirinta yafa mayafi ta wuce.........ka fintadawo ya qarasa yanka mata wararyazuba cikin ruwan gishiri,,,,tazura masa ido maimakon kakwanta mai kudi kaji zafin jikinkakuwa?yace natayaki ne umma kobaki so?tace inaso Allah yamakaalbartka ungo maganin barin debomaka ruwa kasha guda biyu. Tadebo masa ruwa yasha maganin tamatsa masa ya kwanta adaki,,,,amma dayaso yafitar matada kayan suya zaure ya hura matawuta....ai kuwa yana kwanciyabacci ya kwasheshi.harta gama baifarka ba,tazo ta taba jikinsa zafirau.hankalinta ya tashi kwarai dagaske ta zura masa ido sannan taqirga kudin dake gabanta,,,,kawaiabinda yazo ranta shine takaishichemist a hada masa maganinmaleriya .haka kuwa akayi baifarkaba sai da aka kira magrub.kaitsaye alwala yayi yakama hanyazaifice,ina zaka mai kudi?yacemasallaci mana umma!tace kayi agida tunda bakajin dadi.....yacenafiso inje masallaci umma taceadawo lafiya,yawuce yanaamin.yana dawowa tariqehannunsa har chemist aka hadamasa maganin maleriya takashedari uku suka dawo,,,takawo masasauran tuwon datayi da ranasukaci,,,,tabashi magugunayasha,,,yana sallar isha'i wanibaccin yasake kamasa. Cikin dare taji yana ta rawansanyi,,ko ina jikinsa rawayake,takwaso duk tsummanzannuwanta ta rufa masa.amma abanxa haka suka kwana zaunekamar bazaiyi raiba...hankalinmama yatashi kwarai ganin yaumaikudi ko sallah yakasa tashiyayi.don haka tana sallame sallahta figi gyale sai shagon danliti.Ayuba ke alwala kofar shagon bisabenci..ya dubeta afujajan kwalla tafidanta yace lafea sakeena?tacemaikudi baida lafiya ayuba jiyabamuyi bacci ba.danliti yananan? yace yananan baima tashiba.......tawuce ciki tuni hawayenta sukafara zuba tausayi yakama ayubadomin ya hango matawalakanci,,,,danliti na bacci zatatashe shi? haka kawai ma ya akaqare? ya kada kai yarasanayi,,,,yana kwance dai dai akankatifa ta tsugunna ta tanbubbugashi.ya bude ido yamutseya zuba mata ido baitankaba....hakan yabata damarfadin abunda ke tafe da ita. Maikudi babu lafiya kamar zai mutudanliti don Allah kazo ka taimakaakaishi asibiti.....nakaishi kemisanbashi magunguna amma baiyibako barci......ke ya isheni haka!haba!ke sakaryar inace wai?tukunama banhanaki zuwa shagon nanba?kin raina ni koh?har ina bacci kizokitashen...nina samasa ciwon?iye?ina tambayarki? Da gudu hawayenta ke kwarara! takada kai murya na rawa tacebakaga halin dayake ciki banedanliti.don girman Allah kataimakaka kaishi asibiti..wallahi sukenankudadena duk na tattara na kaishichemist Idanuwa sunkafe,,,,,ta yada mayafita doka salati ta tarairayoshi...tanakira amma ya gagaretadagawa,,saboda duk gabobinsa sunmimmike ta koma kicin takandamo ruwa tazo tana shafamasa bakinta na fadin nashiga ukuyau me zangani me kudi? Hawayenta yaci gabada kwararatsawon lokaci batare datasanadadinsaba kawai hango rana tayiyafito ba danliti ba alamansa.tafitokofar daki idanuwanta duk sunkumbure tarasa yanda zatayi taceto rayuar danta mai tsananintausayi nta....batasan lokacin datafada gidan maman fati ba. afiya maman maikudi?ta durqusaa gabanta baki na rawa kitaimakenimaman fati,,,,mai kudi zai mutu!maikudi zaimutu maman fati!meyasameshi? daga zazzabi sai sumayakeyi....kitaimakeni da kudiinkaishi asibiti inmundawo zantayimiki wanki har kudinki yaqare....dan Allah kitaimakenimama n fati. Naje nagayawa babansa yaqizuwa....tausayi yakamata tanumfasa tace nima maigidan bayagari ne maman maikudi.ammabarin dubo miki abundayasamu.tashiga daki tafito mata dakudi yan dari bibbiyu. Ta mikamata ungo nan dubu daya cekawai!nasan bazasu ishekiba ammakiyi kudin mota xuwa kagara sai kinemi taimako.idan kuma babannasa yaga dama yajeshikenan.Allah ya sauwaka. Takoma dakin tasameshi yanananyanda tabarshi...ta sake baxamatasha neman mota suka tsadanceakan dari takwas dan sun tausayamata....tadauko mai motar harkofar gida....sannan tace yashigoyataimaka mata da maralafiyar...yayi sallama yashigodakin.me direba zaigani?dafara ngangara gefen bakin maikudi dasauri ya tabashi ya jujjuya ya dubimama dake tsaye idanu waje. Yace uwargida,ai ina ganin yaronnan babushi!ta qara zaro ido tanafadin a'a malam babu ruwankadashi...kasanya minshi a motakawai tunda nace biyankazanyi....yace uwargida haquri fazakiyi ko kinje asibiti wahalar kawaizakisha dole kidawo dashi,,,dominbabu abunda zasu iya masa...kiyihaquri kawai Allah yajikiansa.yasakai yafice cikin alhiniyaja motansa yakoma tasha. Mama ta zubawa mai kudiido..ahankali ta zube gabansa takamo hannayensa taci gabadakallonsa hawaye na zuba kamarfamfo..shikenan anyi angama?dagazazzabi kwana daya?haka zuciyartataketa wasi wasi.haqiqanin gaskiyakuwa ciwon maikudi tun ranardayaji rauni a bola tetanus yashigeshi.rashin kulawa kuma yakaishi garasa ransa..kokuma mucekwanansa ya qare ya huta dagwagwarmaya. Tamkar a mafarki mama ke ganinabun,,,shiyasa take zaune bataredatasan meya dace tayiba.kawaimurya taji bisa kanta.kitaso mutafiasibitin in ajiyeku sauri nakeyiinada wurin zuwa.!taciree kai tadubeshi ido yayi jawur wasuhawayen suka qara tsunkowa bakina rawa tace yamutu...yacebangane ya mutuba? Mama ta zubawa mai kudi ido..ahankali ta zubegabansa ta kamo hannayensa taci gabada kallonsahawaye na zuba kamar famfo..shikenan anyiangama?daga zazzabi kwana daya?haka zuciyartataketa wasi wasi.haqiqanin gaskiya kuwa ciwonmaikudi tun ranarda yaji rauni a bola tetanus yashige shi.rashin kulawa kuma yakaishi ga rasaransa..kokuma muce kwanansa ya qare ya huta dagwagwarmaya.Kan dole ta tsagaita da kukanta...amma hawayentayaqi yanke.jimawa kadan ayuba yazo tare da abokandanliti mutum hudu,,,,daya daga cikinsune ma yatahoda likkafani.ayuba yayi masa wanka...ya kintsa shisuka nadoshi a tabarma sika fito dashi.kowannensuyayi alwala suka sallaceshi tare da tsirarun mutane masu wucewa, Sannan suka tafi kaishi suna bada baya maman fatita shigo tasami mama tana ta kuka.tazauna tayitararrashinta harta sami yar nutsuwa.ta dauko kudinmaman fati tabata tace nabarmiki mama.nidai fatanakokuma ince roqona gareki shine Allah yasa kiganewannan zama bayida wata fa'ida ga dan musulmi. Tausayi rayuwarki kebani,,,saboda duk wanda yahaihu baikamata yazauna yana aibanta waniba.donyaganshi a wani hali marar kyau.don Allah kirinqa yinaddu'a kina rokon Allah ya kore miki wannanshaidanin daya dabai bayeki miki ziciyarki.saifa kindage kin yaqi zuciyarki sannan Allah zai taimakeki kinji? kiyi haquri ni zankoma Allah yajikansa.....tashare kwalla tace ameen ngd maman fati kumaazanyi addu'a kamar yadda kikace..tace toshikenan.ta taso tabaro gidan cike da tausayinta Suna dawowa maqabarta shago kawai ya wucedasu.yan rakiya kowa ya kama gabansa..ayubayazauna yanata juyayin mutuwan maikudi.shikuwagogan cikin shago yashige ya kwanta.baza ace gaabinda yake tinani ba.domin zuciyar danliti sai Allahkawai.ita kuwa mama zaune take idanuwanta na kallon sama,,,hawaye nata sauqa bisakuncinta.maganganun mai kudi ke yawo cikinranta.kiyi hauri umma"!yazama dole ingayamikigaskia!natsani mutumin nan na tsanesa umma!shiyasa danayi salla yanxu na roqi Allah ya kashenidan banso na girma tare dashi.Tayada kai bisa filo tagoce da kuka,,meyasa ka rokimutuwa maikudi?tayi kukan daya isheta babu mairarrashinta har akayi kiran azhar.sannan ta fito kantasosai yake ciwo haka kuma batajin yunwarcikinta.dukda cewar rabonta da abinci tunjiya.ta zubaruwaa abuta tashiga bayi tadawo tazauna tana alwala.karaf! idanunta suka sauqa akan buhuntarkacen maikudi.buhun yananan inda ya jingineshi.tazubawa wajen ido tana kallon shigowansa da dukkanabunda yamata jiyan kafin yakwanta.nantake kukantayadawo sabo tana alwala tanayi.tashiga sallahhawaye na zuba harta qare.karo na farko da Allah yafara bata ikon daga hannu tayi addu'a.Allah kajiqanadamu!Allah kasanyamin haquri da dangana!Allah kakoremin sheidanin daya dabaibaye zuciyata!Allah kataimakeni!tasauqe hannu tana goge kwalla takomagefen katifa ta zauna BAKIN CIKI 3***4 Kun jini shuru ko wlh sub dina ne yayi expired da kuma exam da nakeyi kuyi hakuri Zamanta keda wuya almajirin maman fatee yayisallama...yashigo dauke da kwano a hannunsa..bayanyayi mata gaisuwa yace wai gashi inji mamanfati.tafito ta dauko kwano a kicin ta juye dafadukanshinkafa da manja da bushassen kifi.kace matangd.yafice yana fadin to.tajima bata iya cin abincin ba daga baya ta daure ta tuttura badan yamata dadinciba.haka takasance cikin kadaici da kewar dantakwana uku batare da danliti ya waiwayetaba...saimaman fati ke aiko mata abinci sau biyuarana..shiyasa dubu dayanta bata tababa.waniabunda ke qara mata qarfin zuciya shine tun mutuwar maikudi takoyi addu'a.kuma bakinta ke maimatakalaman maman fatee Allah ya kore shedanin dayakecikin zuciyarta, Ita kanta batasan lokacin da kalamin kezuwabakintaba.fadi kawai takeyi.amma duk da hakamutuwar maikudi yadasa mata ciwo acikinzuciyarta.wanda yake hana mata duk wani kuzari naaikata wasu aikace aikace kamar yaddatasaba.kullum zaune take shiru.a cikin wannan yanayin danliti ya risketa.yau kwana hudu darasuwar.ta zuba masa ido bata tankaba haryaja yarkujera ya zauna.haka shima yayita kallonta kafin yajadogon tsaki.yace ke!bakiga shigowata bane?tadubeshi ido cikin ido tace me kakeso incemaka? Yace gaskiyane,,,da alama haushi kikeji dankiyamutu.to ai bani na kashekiba.ta kalleshi koba kaibane kaine sila..yace saboda kinkirani banxo akanlokaciba? aiba tsoronki nakejiba.tace nidama bancekaji tsoronaba kadai ji tsoron Allah.kasani duk abundayasamemu nida maikudi alhaki nakanka donkai ka ajiyemu. Yadaga mata hannu tare da tsawa.tsaya anan!yadanjima yana kallonta kafin yace da alama wuyanki yaisa yanka.toki tsaya anan tunkafin in hassala inhadamiki zafi biyu.dan zan iya farfasa bakinki.sannankibar gidannan yanxu domin dai bana uban dawakibane,,na buxu mai shayine.kuma axatona bakida gadonsa ko kina dashi?tayi shiru tana kallonsa.yacigabada fadin duk ranarda kika sake gayamin maganamakamanciyar wannan,zaki fuskanci tashin hankalinda harki mutu baxaki mantaba.ya miqe a fusaceyadaga kujerar dayake kai ya makata da qasa takarairaye.ya dubeta ido waje yace sakamakonki daya da wannan kujerar duk ranar da bakinki yayi gigingayamin maganar banxa.yasa kai yafice tamatsekwalla tarasa abinda ke mata dadi,Kullum kuma a rashin jin dadin take tsawon lokacisati uku itake ciyar da kanta.domin dai danliti yaqiwaiwayarta,,tun wancan xuwanda yayi.yankudinhannunta gaba daya sunqare.saboda warar matadaina.tun rasuwar maikudi kuzarinta ya qare.yaukam tura takai bango rabon mama da abinci tundan saura dumamen taliyar hausar jiya da daddare .la'asarta wuce sosai lokacin tafito baki bususu.dun rabontada wanka kwana biyu kenan.balle wanki tayo alwalaamma sallah ta gagareta a tsare jiri ke dibarta.daalama bayan yunwa dayake damunta akwai rashinlafea a tare da ita.da kyar ta idar da sallah ta raarafa katifa takwanta.bata jimaba baccin wuya yakwasheta..jitayi ana bubbugata tayi firgititi ta tashitabishi da kallo.yana zaune kusa da ita ta tashi tazauna jikin bango.taja doguwar hamma hartanakwalla,,sannan tasake kallonsa sannu da xuwa!yacekema sannu kinajin dadinki la'asar sakaliya kina bacci to gani naxo. Tadubeshi da kyau tace yinme?baki sake yakekallonsa kafin yace kinfi kowa sani .takauda kai shirubata tankaba,karki batamin lokaci inada wajenxuwa.takada kai fuska yamutse batare data kallesabagaskia banda lafiya.danliti kuma yunwa nakeji.rabonada abinci tunjiya. Ya mako mata harara me kike nufi? tayi shiru...ya numfasa yace hu'un!lalle nayi sake dayawa ba laifinki bane.tadago ido takalleshi wannanmatsalark ace.Ita kanta batasan lokacin da kalmar tafitobakintaba..saida gabansa yafadi ya qara zaro idoyace mene?me kikace?ta sunkuyar dakai tayi shiruhawayenta suka fara zuba.yasa hannu yazaretakalminsa ya lafta mata aka.yadaka mata tsawa mekikace?nikike gayawa wannan maganar?yasake lafta mata..iye? To saurareni kiji kinshiga uku kinlalace...zaki ci gaba da dandanan axaba a gidannan.tabbas zan nuna miki nidan gidan buxu mai shayine,,,,kwarton nan daya mutu wajen kwartanci.kinmance ko haryanxu tarihin yananan cikin xuciyarki? (kalman da ya jefa mama cikin halin datake ciki kenan inbaku mantaba)taci gaba da kuka bata tankamasaba, Yasa takalmin ya dago habarta,,sakeena kenan maikyau yar asali jikar asali!yanxu ina asalin da gatanyake?dalili daya yasa nake rangwanta miki sabodakina gamsar dani yayi dan murmushi.yakada kaizandawo anjima zankawo miki abunda xakici kitabbatar da kinyi wanka dan wari kawai kike kinji?ta zuba masa ido bata tankaba ya marmari kumatuntada takalmin yasake fadin kiyi wankafa!kinsan bansonhamami.(dan iska).ya mike ya xura takalminsa zaifice.. Tabishi da kallo DANLITI ya tsaya cak.kafin yajuyoya zuba mata ido.ta goge kwalla murya na rawa tacenaji duk abunda kace,,,amma ina rokon Allah idanxaman da muke banida haqqinka ubangiji Allah yayimin sakayya! ya matso ya wanketa da mari yanunatada yasta nikikewa Allah ya isa?gaskia ne tabbas ba laifinki bane,amma xangyara.yasa kai a fusace yabargidan.mama na xuba kuka abun tausayi.a fusace yaisa shago ya nemi wuri kawai ya zauna yana hucikamar mesa, Ayuba ya xura masa ido tsawon lokaci kafin yacelafiya?ya kada kai ido jawir inafa lafiya...ni sakeenakewa Allah ya isa? lalle nayi sakaci ba kadanba.wanidadi ya ratsa zuciyar ayuba cikeda fara'a yace kayisakaci? Ko kuma tafiya ce tayi tafiya?ko kanatsammanin har abada zaluncika zai dore?towlh ka farka barci kasan yanayin da kake ciki.ko kasanwaccan juma'ar danaje masallaci akan zalunci darashin adalci liman yayi huduba.Anan naji cewa addu'ar wanda aka zalunta tamkaryankan wuqa take.kuma batada hijabi daubangiji.anayinta kai tsaye Allah zai amsa.sabodahaka ka kiyaye danliti.kasani shekarunmu sunyinisa.gaba dayanmu yakamata ace munadaiyali.amma muna zaune cikin shagoana mana kallon yan iska..ya watso masa harara yaja dogon tsaki.kaiwannan yadama.Allah ya isan sakena bai isa yaminkomaiba.kuma kasa ido kayi kallo aure kuma ninahanakayi?ni banda ra'yi inkanadashi ga hanya kajekayi man... Yace baka hananiba.amma bakin halinmu ya hanaabani.kana gani har kauyuka bansamuba sabodakowa kanyabada yarsa zaiyi binciki.danliti yaja tsakikaikaso amaka binciken ni dan uban mutum inya isayaxo yamin maganar banxa.yagani idan banyimaganinsaba dagashi har diyarsa.kuma a zatonka sakeena taci banxa ne? wlh bataciba munanan mutukaraba takalmin kaxa.kahada min lissafi kafabundake hannu zanyi tafiya gobe. Yaja tsaki yatashiyashige dakin baccinsu, Mama kuwa na shimfide gafda magruba. Almajirinmaman fati yshigo da kwanon sameera yace injimaman fatin.ta bude kwanon shaqe yake da tuwonmasara miyann ayayo.jikinta na rawa ta tashi tajuye.ta wanke mata kwanon tabashi tanata zubagodiya.tanemi roba tayanki tuwon ta adana sauran. Ta zauna ta cinye tas.tasha ruwa.zufa yaketo mata tayigodiya ga Allah.abincin ya tsirga mata ta tashi tayisallah.tajira isha'i tayi tarufe ko ina ta kwanta.tunaninmaikudi ya lullube zuciyarta,,,,ba tasan lokacin dabacci ya sace taba.dasafe ragowar tuwon ta dumam,ataci tafito ta nufi neman wankau gun maman fati. Shikuwa danliti a wannan lokacin yadade da barinfandogari.ayuba keta hada hadar shagon kamar yaddayasaba.amma zuciyarsa na cike da mamakin danlitiyadda yakasayin nadamar abubuwan dayakeaikatawa.kuma yana mamakin yanda yakasa rabuuwadashi.alhalin yasan cewa halin abokinsa bamai kyaubane.karfe daya da rabi dai dai wata daf tayiparking bakin titi danliti yafito daga cikinta da alamaragajiye yake.saida ya matso kusa akaganefuskarsa.dukta kumbure.musamman gefen bakinsadana idonsa..mai mota yaja yayi gabaabunsa.shikuma ya qaraso shago yana dingishi, Ayuba a tsorace yake tambaya lafiya danliti?baiamsaba harsai da yakwanta akan katifa.yace wlhyanfashi saida naxo daidai buruku.na iske suntarehanya.in gayamaka dagani sai yar wannan wayan natsira sunkwace mai tsadar.ido waje yace kana nufinsun kwace har motar?yace bar maganan ayuba nikaina bakaga yadda suka maida niba?ai mutanennan yan iskane mutum da kayansa..amma suyitaduka kamar Allah ne ya aikosu...Ayuba ya numfasa yace ai amma gode tunda basuharbekaba basu da imani..sannu!ya nxu me za'a sayomaka kasha?yace barin huta sai inje kemisdakaina.yakwanta a hankali yana fadin wash.ayubayadawo cikin shaghon ya qaleshi harbacciyadaukeshi.akwai alamar tambaya acikin wannan lamari.danliti dazai gane daya saduda...ammakash.bazai ganeba.shikadai yaketa saqe saqensacikin ransa.shikuwa danliti cikin baccinsa yayi mafarkisuna ganawa da bokansa.shiyasa bayan la'asar yanafarkawa yakirasa yana shaida masa abundayafaru.sh ikuma yabashi tabbacin ya kwantar da hankalinsa za'aga motar.sakeena kuwa har abadaragamar rayuwarta na hannunsa. Hankalin danliti yakwanta yaci gabada jinya yanashan magungunandaya amso a chemist,,,haka kumabai waiwayi mamaba.danta masalaifi saita kurxu da yunwatukuna.ganinsa dan abunda yakebata shitaketa ci kodayake yasantanashan wahala sosai.sati biyubabu mota ba labarinta.sabodahaka ya qulla a ransa gobe ya tafiwajen bokansa suyi magana gabada gaba.a wannan daren sunkwanta babu wutan nepa. Can cikindare nefa suka kawo wuta maiqarfin gaske.ba hawa ba sauqakawai shagon danliti yakama dawuta.da kyar sukasha shidaayuba.kowannensu dagashi saikayan jikinsa sai yar wayardanlitidake cikin aljihunrigarsa. itama rabon zaifita daitane.yasa yamanta bai cireba Sunata kururuwa wuta!duk jama'asukayo waje.amma duk iyakokarinsu basu iya kashewutanba.sai da ta cinye tas koallura bata bariba.danliti kamarzaiyi hauka.gaba daya ya gigiceyanata zuba sambatu har gari yawaye.kofar shagon yacika dankamda jama'a anata musu jaje,,,dadama na tambaya yaushema akayimasa fashi?mutane na hasashenhalin danliti ne.ba mamaki danmasifa ta afka masa.domin damaabunda mutum yashuka shizaigirba.komai daren dadewa kuwa Suna zaune jugum danliti yayi baqikamar bashine dan kwalisan nanba.mama ta iso wajen fuskasharkaf da hawaye.tayi tsaye tanakallon yadda wuta ya cinyeshagon..tace nashiga uku danlitigarin yaya wannan abu yafaruhaka?ya kauda kai baitankaba.ayuba ne yabataamsa.Allah ne kadai yasani mudaimuna bacci mukaji numfashinmubaya fita imgaya mudai munbudeido ne munga wuta takoina.sannan kwananmu kegababamuda rabon wahala shisa mukafito Taci gaba da tafa hannu tanasalallami.kafin tace nima inanasani?kawai yanxu nashigamakwafta neman wanki shinesukemin jaje.wai ashe abundayafaru kenan? ni wlh cewa ma naketun maganan fashin nan ne....dasauri danliti yadaka mata tsawa danAllah malama kiwa mutaneshiru...bamu san surutu.ta zubamasa ido tace Allah baka haquridanliti.ayuba sai anjima.Allah yamayar da alheri. Yace ameen.tajuya zata tafi danliti yace dama kikwashe komatsanki kibarmin gidanima ciki zandawo. Tadawo ta tsaya cak,,,ta xubamasa ido a marairaice tace inakakeso naje danliti?yace kekikasani wannan ba damuwatabane,,,kawai abunda nasani inasondaganan xuwa dare kibarmingidana.ta goce da kuka ta dubiayuba ina yakeso inje ayuba?donAllah ka rokeshi ya rufamin asiri.Bansan inda zaniba ayuba....yaceko ma gidan babu komai zanyi masamagana.ta goge kwalla ta wuceabun tausayi danliti yahadafuska.duk irin maganganun dadanliti yake masa babu wadda yayarda da ita..shiyasa ma baitankaba.abinda ya ajewa ransa yaukomai dare sai tabar masa gida Saboda haka yaci gaba dabilayinsa,,,bashi kasan wancanbishiya,bashi kofar shagonmutane.sudin nema masu sayamusu abinci suci tare.abin duniyaya jagulewa danliti.BAKIN CIKIKamar ya kashesa.idan ya dubishagonsa.ya tuna dukiyar dakeciki,zuwa la'asar yaga bazai iyajurewa ba shagon okundiri.yajeyaci bashin kati yasawa wayansayakoma gefe ya kirabokansa.yasanar dashi abunda kefaruwa.sunjima suna adawo ya zauna shiru.a qasanwata bishiya.ayuba yafito dagamasallaci yace danliti kaje kayisallah kaga ko asuba bakayiba.yaceina kai kayi?yace nayi mana yace toAllah ya karba.yace kana nufinbazakayiba kenan?fuska yamutse yaamsa dan Allah ka kyaleni ayuba kakyaleni najida abunda nakeji.ayubaya numfasa na kyaleka tundabakason gaskia.yaja tsaki ya tashiyabar wajen. Karfe takwassuka tafi gidan dan basuda wajenzuwa daya wuce candin.mama nazaune a tsakar gida tana tunaninidan danliti ya koreta ina zata?sallamar ayuba tamaidata cikinhankalinta.tayi wuf tamiqe tanaamsaw.inafata kinhada komatsanki?ayuba ya cafe haba danliti asheduk maganar dana maka bakajibakoh?ina kakeso taje adaran nan? yace bansaniba.duk inda taga damataje gida sayar dashi zanyi. Insakebude wani shagon.ko kuwa inadakadara sai inxauna haka saboda gashafaffiya da mai tana zaune agida?to bazai yiwuba!maza kamahanya kisan nayi a durkusa amma kafin tayimagana ayuba ya rigata kayiwagirman Allah ka kyaleta zuwa gobenida kaina zan nema mata wajenzama ko kuma ka bata izini takoma gidan iyayenta,,yace ninahanata zama gidansu?yace kainemana aikasan yanda zakayi takomagidansu......ya katseshi ya ishekahaka ayuba!ko kuma idan zaka iyakamaidata gidan nasu mana.yakada kai yace kasan bazan iya baneshisa.roqonka nakeyi dan turafatakai bango dazaka fahimcihakan.yaja tsaki ya shige dakiabinsa.ayuba ya dubeta miqesakeena ki gyara wancan dakin kikwanta xuwa safiya.koda zai sayarda gidan nasan abinda zanyi a juya ya bishi dakin itakuma tasaaci bal bal ta share daya dakin tasata baxa keson tabalma.ta kwasotsummokaranta ta kulle tayimatashin kai ta kwanta cike datunani.sha biyun dare ta gotalokacin da danliti ya tsinkayi ayubayanata minshari barcin ramako dagajiya ya saceshi.yayi wuf ya tashiya sulale yabar gidan..kamar yaddabokansa ya umarcesa dayayi amfanida akuya a wannan daren kafin gariya waye yasaida gidan sa yasakebude shago zaiga kudi yana zuwakota ina.kai tsaye kasuwan ya nufadan awakin da sukayi batan kaidare yayi musu basa gane gida cansuke kwana Yana zuwa yasamu qatuwar ciki yaturmusheta tareda matsebakinta.kaya kaya harya biyabukatansa (yayi releasing) farin cikayakamasa ashe banan gixo kesakarba.yayi yayi ya rabu da jikinakuyan nan abu ya gagara..tunyanaiya riqe akuya hartafi qarfinsa tazabura aguje tarinqa wasan kuradashi a cikin kasuwa.duk sauranawakan suka watse.can yasamutadan tsaya.zafi da wuya kamar sukasheshi.idanuwansa suka farahawaye ya lalubo waya yana kukaakuya nayi da nufin yagawabokansa ya nemo masamafita.kamar ansake fincikar akuyata zabura wayarta fadi! shikansabaisan inda tayi ba.kai danliti yagawuyar duniya...kafin asuba yayibusu busu da kura..yafitahayyacinsa HAUSA Novels BOOK BAKIN CIKI 3***5 Gaba daya qarfinsa ya qare.duk inda akuyar tayi canzai nufa.suna manne gagam.inda tayi gudu yatafi dagudun inta tsaya ya tsaya.inta baje a qasa shimahaka zai baje a qasan.akuyar kanta ta galabaita harkukanta baya fita sosai.gari yafara shaa zai wayemasu dawowa daga masallaci suka fara ganin wannan abun al'ajabin.domin dai akuya takawo danliti harbakin titi.mutane sukayo caa dan ganin waye maiwannan aika aikar... Motsinsu ya qara firgitar da akuyar nan.ta zabura tafada titi.dai dai wata tirela takawo kai.Allah yasatashin motan kenan.aikuwa nan take ta hankadasukwalbati...kankace kwabo jama'a ancika danqam akacirosu.mutane nata kallo ikon Allah tare da hasashenwai wanene dubunsa ta cika haka?gari ya waye tangaram,ana zubawa danliti ruwa sannan yafarfado,,aka zuba masa ruwa ya wanke fuskansaqurar data wanke masa fuska ta bude.nantakemutane suka shaidashi.wannan ai danliti ne,,,danliti?kowa ya dauka guri ya dauki sallallami.tafdi! muxuraikawai yakeyi.yana kallon jama'ar dake kansa.yansanda suka iso dan ganin meke faruwa.Cikin masu kallo kuwa harda malam qaseem mijininna saude,,,kowa ya tsaya cirko cirko anrasa yaddaza'ayi dashi.shikuwa nunawa yake abashi ruwa.wanidan cuwa cuwa ya bula pure wata yana tsiyaya masarabi a qasa rabi a baki.can saiga ayuba yafito nemandanliti.don tunda yatashi bacci bai gansba.Tun kafin ya qarasa yasamu labarin,,,don haka yakutso ya ganewa idonsa.tamkar zai suma yakeji,,,yatsugunna gabansa ya ce mezan gani dan liti?meyajawo maka wannan aikin?ya kada kai da kyar yaceayuba wlh bantaba ba.alhakin sakeena neyakamani.nina san alhakintane kawai.don nasan na cutar da ita.kuma inason yau kowa yasani.dukabunda sakeena tayi a garin nan sharrinane,,,,asirinayi mata mugun asiri kuwa..wanda ya dabaibayezuciyar kowa bamai ganin aibuna.balle a tuhumeninasa andaure bakin kowa harda naka ayuba tayandazanci karena ba babbaka.. Dafarko ruwan maniyyi na na bayar aka hada min dawasu ayoyi da garin magani wanda idan na turara shiduk inda sakeena take sai taxo.daganan aka baniwani magani na badeshi da nama da hannunta tabawakare yaci duk wulaqancin dazan mata bazata tabarabuwa daniba.kuma baza taji maganan kowaba sai nawa....nayi haka ne kawai dan inci zaarafin sakeenasaboda walaqancin datayimin.haqiqa na wuce makadida rawa kuma ayuba nagayamin.amma banjiba.sai dayanxu nagane duk masifar data samen sakamakonabunda na aikatane.don Allah kuyafen.ayuba kakiramin sakeena na roqi gafararta.insami sauqin masifar danake ciki!sa'a ce malamina yabani bantababin akuyaba,Labari har gidan ubandawaki...don haka suka garzayoakan idonsu danliti ya qarasa labarinsa.kuma yakemagiya akira mama taxo ta yafe masa.tuni wani danmatashin saurayi wanda shekarunsa baxasu wucesha takwas ba ya sheqa da gudu kiran mama,,,bamama kadaiba hatta malam qaseem ya aika a kira masa inna saude.ayuba yarasa abunyi hawaye kawaike zuba.yayinda samari ke cewa abari su kasheshi! jininka ya hallata danliti ayar Allah ka wulaqanta...yansanda suke bakin qoqarinsu don ganin samari basudauki doka a hannuba, Ana cikin wannan hatsaniya akuya tace ga garinkunan.Allah da ikonsa tana mutuwa jikin danliti yafgitadaga duburar akuyar nan.can saiga mama a guje batako ganin inda take jefa qafarta.tana kawo bakin titiwani mai mashin shima yanaso yaxo yaga taron meake...?yayi awon gaba da ita.duk suka watse bakin titi.dai dai lokacin inna saude nakawo kai itama,,yuuwasu jama'a suka koma inda hatsarin yafaru.kowafadi yake sakeena ce,,,,Allah sarki sakeenance.jinhaka inna saude da sauran yan uwan sukayikanta.asume take sai dai babu alamun wani ciwoajikinta....ruwaa aketa zuba mata yayinda yansanda biyu suka wuce da danliti ofishinsu.daya kuma yatsaya a wajen hadarin daya samu mama... Da akaga tajima bata farfadoba,,,,sai akasakata amota da dansanda daya aka wuce da ita asibitinkagara..suka bar mutanen gari da mamakin wannanabu mai kamada almara.shikuwa ayuba sulalewa yayiyasamu babbar mota ya bisu kudu.dauke da nadamamai tarin yawa.tamkar shiya aikata wannan sabon.a babban asibitin kagara kuwa..tuni anbawa mamagado.kuma su alh basiru sunkira waya abuja.,donbasu wannan labari mai ban al'ajabi...ba abujakadaiba.duk yan uwan mama sunsami labari...innasaude ma bata bata lokaciba...ta garzaya gidanbaraka amma bata samu kowaba duk suntafi aiki...domin tuni baraka ta fadada iliminta a fceminna.kuma tasamu koyarwa a l.e.a tana amsaralbashinta ,Yaranta biyar duk suna makaranta....da albashintatasawa inna waya.sai dai yau wayar bata jikinta baretakira baraka da tambaya tagane makarantar dabaraka take koyarwa...ganin innarta yasa gabantayafadi.kwarai da gaske basu ko gaisaba inna ta sanarda ita halin da ake ciki.jikin baraka yadauki rawa idanunta ya kada tace haba!wannan lamari akwaidaure kai.Allah ya isa tsakaninmu dashitambadadde.kotu ce zata rabamu ina zuwa inna.Ta sheqa ofishin shugaban makarantar ta nemi iziniankawo yar uwarta magashiyan asibiti.take aka bataizinin tafiya.suka rankaya da inna saude.baraka tanakallon mama tafara hawaye saida inna tayitararrashinta.tayi shiru.sunanan zaune jugum jugum hartym din sallah yayi dake ranar juma'a ce.duk maza suka dunguma sallar juma'a.basu wani dade sossaida tafiyaba mama ta bude ido tana kallon silin.innazoki gani ta bude ido inji baraka.ta taso da sauri!ta isawajen gadon mama!duk suka kirata.a hankali ta juyoda fuskarta garesu.ta zura musu ido quri babu koqiftawa.wucewar minti uku kafin tace inna! Jiki na rawa tace naam sakeena!kingane wannan yaruwarki ne?ta zura mata ido tace baraka tace naammama.alhmdulillahi mungode Allah.tasake kalle kalletace inna a ina nake?tace asibiti ne mama,,,,tacemeya sameni?tace babu komai taci gaba da kallonjikinta kaya dukun dukun gata cikin tsumma farce kaman na makaniki takara zare ido taceinna.haukacewa nayi koh?ina abba nah?ina ummanaha?tayu wuf zata sauqo duk suka riqeta hawaye naxuba musu.inna tace kwanta mama ba haukakikayiba.ki nitsu!amma inaso ki nutsu cikin hankalinkizaki iya tuna meke tsakaninki da danliti?Idanuwanta suka qara yo waje tace danliti?ta koma takwanta ta runtse ido tamau! komai yana xuwa matakamar a mafarki.zuciyarta ta soma zarya.kirjinta nabugawa dasauri.kafin su ankara ta dirqo daga gadontafita aguje.fadi take inna lillahi wa inna ilaihiraji'un.suka biyo ta suna kira hankalin mutane yadawo kansu daidai lokacin ya ali yake isowa barandar zuwansafandogari kenan.inna fadi take riqe min ita ali.ai kokafin ta qaraso gunsa ta yanki jiki ta fadi..da gudunsaya qaraso ya ciccibeta.ya riqe hannu biyu tamau! tanaqoqarin kwacewa batare datasan ko a hannunwatakeba.shiko fadi yake nitsu ki saurareni dubeni mama!nace ki nitsu,Nitsu ki sauraren,,,dubeni mama dubeni nace! dakyaryasamu ta nutsu tana kallonsa jikinta yaqara sanyi.tazura masa ido murya na rawa tace yaya ali kana kallonadawo haka?tuni hawaye sukafara zuba masa yacekwantar da hankalinki mama! Abunda Allah yaqaddaro babu wanda ya isa ya hanashi...zomuje ki kwanta ki huta...ta kada kai .nibazan komaba.wajenumma na zani.yace mama umma ta dade da rasuwatace nasani dakinta zanje.ku kira min abbainganshi.yace tuni aka kirashi kinsan yana abuja nesuna hanya insha Allahu.kiyi haquri likita yabakisallama tukun. Ta zube nan tace atafau bazata komaba.inna saude tace a jira su alh sufito sallah asan abinyi.ba'a dadeba suka fito sallah suka iskesu waje..mama nata faman kuka baraka na tayata.babu wanda bai tausaya mata.jin kalamin dake fitowa bakinta.suna kallo ta walakanta haka?duk wanda ta kalla irin tambayar take masa.ganin ta kafe bazata zauna a asibitiba yasa alh basiru yanemi sallama.daga asibiti gidan baraka aka wuce da ita.sukuma sukayi fandogari.nanda nan baraka tasa ruwan xafi a hita.kafin wani lokaci yayi zafi.tare suka shiga bayin ta surka mata.ta zuba mata wani abuta..tace idan tagama na sabulu tayi na tsarki, Wasu hawayen suka qara goce mata ta zurawa baraka ido...na tsani kaina baraka.dan Allah ki gayamin wani irin xama mukayi da danliti?ni bangaskata abunda tunani na ke nuna minba.ta dafata tace mama sanin irin xamanku da danliti bazai haifar miki da komaiba sai bakin ciki..ki dangana da qaddara!sannan kiyiwa Allah godiya daya kubutar dake tsawon shekara goma sha uku kina wahala.ta qara zaro ido sha uku?ashe dagaskene?yaron danake gani nina haifeshi dagaske ne ko baraka?Itama ta goce da kuka tana fadin mama kidaina fadi nace?kiyi wanka ki tsaftace jikinki kiyi sallah kiyiwa Allah godiya.kinji?tafita da sauri ta janyo mata kofar.ta kama kai kuknta ya tsananta.amma tana dirza jikinta da soso da sabulu tayi ta dirza saida sabulu guda ya qara...ruwan zafi ya qare ta bude famfo ruwan sanyi.yi take da soso hakanan.tanayi tana kuka.ta figi buta tayi wankan tsarki...ta sake maida soso dirza takeyi sama da awa daya watsa ruwa kawai sukeji shaaa.kamar ana ruwan sama.inna saude tace babu lafiya wannan wanka.ta tashi tabita bayin.tayi biji biji da wuri inna ta kwace soson ta dauraye mata jikin,ta warware sabon zanin da baraka ta bayar aka rufa mata tace daura muje! Ta xubo mata idanu jajur batace komaiba.inna ta qara fadin ai kinfita mama kin wanke duk wani datti.kisani Allah bazai kamakiba,,,karki matsawa kanki.daura zaninki kiyi alwala muje kiyi sallah.ta goge hawaye tadaura zanin tayi alwala.inna ta kamo hannunta suka fito.tace ga sallaya nan.gamai kifara shafawa ki sanya riga.ga hajjabi kihau sallayar kiyi salla.dakai take amsawa duk abinda inna tace.tahau sallaya tafara sallah.kafin ta idar abincinta dana sha suna gefe.Ta daga hannu sama fiye da minti shabiyr tana addu'a tana kai kukanta ga Allah tareda zuba godiya agaresa.hawayenta bai yankeba saida tasauqe hannuwanta qasa baraka tashigo ta matso mata da abincin.tasa hannu ta share mata hawayen tace ga abincinki nan.ki daure kici.hakan shi zai qara nuna godiyarki ga Allah.tace banajin yunwa baraka.bana sha'awar komai naci kosha..bazan gane menake ciba.tace to zankira miki inna......tace a'a baraka bawai kema baki isa kisani cibane kawai banajin cine..na qosa inshiga dakin umma.na qosa inga abba da yayyina.baraka kigayamin kadan daga labarin al'ameen kozan daina jin kuna cikin raina.Baraka ta qara matsowa ta riqe yatsunta mama ban san komaiba game da al'ameen.tun lokacin daya dawo kika qishi.yanaji yana gani ya haqura da aurenki.ance yasake komawa rasha daganan,bansake jin duriyarsaba.amma nasan kakarsa goggo hassu ta rasu.kamar anbude famfo bisa kuncinta....murya na rawa tace wlh baraka banqishiba...al'ameen kadai nakeso ke kinsani..meyasa baki gayawa su abba ba adaura min aure dashi dan dole ba?tace haka abba yaso amma kika kwashe kayanki kuka gudu da danliti.aka nemeki aka rasa. Ido waje tace nidin baraka?ke kuwa mama..sai da kuka kwashe wata uku baku dawoba.....ta toshe kunnuwanta tana fadin.kidaina gayamin baraka!kidaina!tamiqe da sauri tayi falo..taci gaba da maimaitawa baraka ta biyota su inna suka mike.suka tarbeta...ta zube jikin inna kidaina gayamin kidaina gayamin nace.inna ta rungumota me kike gaya mata baraka?don Allah ki dena daga mata hankali.tace inna ita ta tambayeni labarin al'ameen.inna ta numfasa tace ya isa,duk maganar nan abarta taci abinci? bataciba. Jeki dauko mata ta juya tadauko...su hajiya hajjo ba baka sai kunne.tagumi kawai suka doka suna ganin ikon Allah.addu'a suke kar mama taji magana daya acikin wanda suka yayata.inna ta tasa mata abinci tace ci abinci mu wuce kinga yamma tayi.ki kwantar da hankalinki.irin walaqancin da danliti yagani yau.dakin ganshi ke kanki zaki gane Allah ba axxalumin bawa bane.daure ko cokali uku kici.tasa hannu tdauki cokali tafaraci kamar mecin magani ido na zubar da ruwa. ***page 60:sun iso fandogari.la'asar sakaliya golf din da ta kwasosu ta ajesu kofar gida mama ta balle murfin mota.ta tsaya ta qarewa gidan kallo.wasu abubuwa nadawo wa cikin tunaninta.qarara take ganinta ta kwaso a guje alh adamu ya biyota da bulala a guje.takenan ta zube bisa guiwa.ta qara fasa kuka.ciwo zai kamaki mama wannan kuka yayi yawa kiyi haquri mana Inji hajiya hajjo duk maxan gidan suka fito.suka tarbesu.sukaja mama zuwa cikin gida.sunaa isowa kofar sasansu,,taja ta tsaya tace ku budemin inshiga wajen umma na!hajiya hajjo ta ruga daki ta dauko dan makulli.alh basiru ya amsa da kansa yabude.ta shiga suka take mata baya.ta kalli nan takalli can.harya bude qofar falon yace shigo! yajawo hannunta...ta shiga falon.da gudu ta nufi dakin umma ta murda ya bude.cikin sanda take shigowa.tunaninta ya koma baya lokacin da danliti yake gayamata rasuwar umma.da gudun da tayo zuwa gida.haduwarta da yanuwanta suka hanata shiga.jiri ke dibarta...basu luraba.sai ta zube qasa a sume.take nan tasamu taimako ta farfado.ta fasa kuka tana fadin.umma kiyafemin kiyafemin umma! Kai ya ali bazai iya jure ganin mama ba cikin wannan yanayi.don haka yayi waje yana share kwalla.yana zama ya abdul rahman na sawo kai.ali yace sannu da zuwa yaya!yace wai da gaske ne abinda naji?yace gaskia ne yaya tana cikin dakin umma.yayi azama yatafi dakin tun kafin yaqarasa yakejin kukanta.yadannada gudu ya qaraso tana kife kan cinyan inna saude.kowa kukan yakeyi tamkar yau umma ta rasu.yasa hanna ya dagota.tadago kai ta dubeshi haba tuni ta tashi ta rungumesa..wanisabon kukan ya balle.ai shima baisan lokacin danasa yafara zubaba.tsawon lokaci suka kwashe kafin ya dagota ya share mata hawaye.kidaina kuka haka mama!murya na rawa tace yaya kuna kallo aka maidani haka? kuna kallo aka haukatar ni?aka rabani da gatana? Ya rufe bakinta ya girgixa kai.yace ba haka bane mama munyi iya yinmu.amma bamu nasaraba! sabodaAllah ya nufa sai dan liti.yaxamo jarabci agareki.amma bamu gaxaba wajen yimiki addu'a kuma nayi imanin addu'oin ne suka taimaka wajen kwato ki daga hannun mummunan halin da danliti yajefaki.kiyi haquri kinji?kimaida al'amuranki gurin Allah.kiyi masa godiya daya ku buto dake.share hawayen ya isa haka.yaci gaba da share mata.tace wai yaushe su abba zasu xo? yace munyi waya yace min yataso amma abdulkareem sai gobe.kinsan yabar minna anmaidashi legos,,shekara uku dasuka wuce....tace Allah sarki yaya.tagoge kwallan daya digo mata tace...kowa nananko?yara duk sun girma?yace kowa nanan mama.yara kuwa wadanda kika sanima baxaki ganesuba.naso xuwa da nawa saboda mkrnta gobe weekend direba zai kawosu da mamansu. IN CIKI 3***6 Nagodai da adduar ku, bari na dan taba muku kadan idai kunji shuru to exam ne ya rike ni Kai ya ali bazai iya jure ganin mama ba cikin wannan yanayi.don haka yayi waje yana share kwalla.yana zama ya abdul rahman na sawo kai.ali yace sannu da zuwa yaya!yace wai da gaske ne abinda naji?yace gaskia ne yaya tana cikin dakin umma.yayi azama yatafi dakin tun kafin yaqarasa yakejin kukanta.yadannada gudu ya qaraso tana kife kan cinyan inna saude.kowa kukan yakeyi tamkar yau umma ta rasu.yasa hanna ya dagota.tadago kai ta dubeshi haba tuni ta tashi ta rungumesa..wanisabon kukan ya balle.ai shima baisan lokacin danasa yafara zubaba.tsawon lokaci suka kwashe kafin ya dagota ya share mata hawaye.kidaina kuka haka mama!murya na rawa tace yaya kuna kallo aka maidani haka? kuna kallo aka haukatar ni?aka rabani da gatana? Ya rufe bakinta ya girgixa kai.yace ba haka bane mama munyi iya yinmu.amma bamu nasaraba! sabodaAllah ya nufa sai dan liti.yaxamo jarabci agareki.amma bamu gaxaba wajen yimiki addu'a kuma nayi imanin addu'oin ne suka taimaka wajen kwato ki daga hannun mummunan halin da danliti yajefaki.kiyi haquri kinji?kimaida al'amuranki gurin Allah.kiyi masa godiya daya ku buto dake.share hawayen ya isa haka.yaci gaba da share mata.tace wai yaushe su abba zasu xo? yace munyi waya yace min yataso amma abdulkareem sai gobe.kinsan yabar minna anmaidashi legos,,shekara uku dasuka wuce....tace Allah sarki yaya.tagoge kwallan daya digo mata tace...kowa nananko?yara duk sun girma?yace kowa nanan mama.yara kuwa wadanda kika sanima baxaki ganesuba.naso xuwa da nawa saboda mkrnta gobe weekend direba zai kawosu da mamansu. Su nawa ne yaya?yace su uku nee.harda takwararki..itace tafari.ido waje tace kana nufin sakeena sunan yarka ta farko?ya amsa sosai ma abba ne yace asamata.ta runtse ido abba nah kaxo inganka.hawaye shar bisa kuncinta.ganin yayanta kusa da ita yasa ta saki jiki tarinqa tambayar abubuwan dabata saniba,tare da tambayan yanuwanta da bata gansuba..da yawansu suna skul.danlami kuwa yana aiki a sakkwato harda matarsa da yaransa biyu.daganan suka fara amsa sallamar mutanen gari masu zuwa musu murna da jaje,,,ciki kuwa harda maman fati saida tayi kuka dataga mama acikin danginta.meya fi wannan dadi?tajima tana maida abubuwan data sani game da zaman quncin da mama ta fuskanta.sannantatafi itace baquwa ta farko da mama tayiwa rakiya.don baxata mance gudumawar data bataba.anyi sallar isha su hajiya hajo suka gabatar da abinci.mama na kwance lamo kamar mai bacci gefen yayanta.malami suka gani yayi sallama yashigo yazama qaton saurayi yanata karatunsa a n.d.a kaduna. Su suka biya suka daukeshi.duk suka miqe malami kun iso?yace mun iso kawu.ina anty maman?tana zaune jugum takasa motsi jin cewa abbanta ya iso.idanuwanta tuni suka fara tara kwalla.gabanta na faduwa !malam.ta kirashi.yayindaake nuna masa ita.kai ina baiyarda.duk da yafara manta kamanninta yasan anty maman sa.kyakkyawar gaske ce mai kwarjini wanda yake burge manya da yara.dan takaitaccen tarihin da yaji a mota yasa duk tausayinta yamasa bargo.idonsa ya cika da kwalla.ta mike tana fadin kunxo min da abba na? ya kamo hannunta gasu nan a waje.zo muje ki tarboshi.sukabibayan sauran ayarin dasukayi gaba.suna kawo kai zauren farko ana turasa a keke.anan ta qame suka xubawa juna ido.abbanta ne a keke?duk tsufa ya mamayesa? zuciyarta taci gaba da bugawa shiko tasbihi yakewa ubangiji wanda yayi nufin sake hada fuskarsa da diyarsa.shi sauyin kamanninta bai damesaba ganinta yadanne duk abunda ke cikin xuciyarsa Batasan malami najantaba.ita dai ganinta tayi daf da keken abba.muryarsa dataji ya qirata yasa tayi lau zata xube.amma ina yan uwanta.basu bariba.caraf!suka cafketa.yaya soja ya amshe yasa hannu biyu ya girgizata.mama!ke mama!ya ali ya miqo kofin ruwa.ga ruwa yaya.ya zuba masa a hannu ya shafa mata a fuska.tayi ajiyar xuciya..tafara kuka abbana!da dorata jikinsa ya rungumeta.irin kukan datayi sai da tabawa kowa tsoro.domin ji sukayi dif babu rai.daukarta sukayi cak sukayi cikin gida da ita.babu abunda BAKIN CIKI Baya bayarwa.haka zalika FARIN CIKI!dan saiya gigita mutum take nan har ya iya fadawa wani hali.mama kam farin ciki yasa sai da yan uwanta sukayi da gaske ta farfado.tadawo hayyacinta ta bude ido taganta kwance jikin abba.ta zura masa ido yakada kai yace mama ki taima keni kar farin ciki ysa ki sake jefamu a yanayin da muke sallama dashi Ta hadiye miyau da kyar tace har yanxu cikin BAKIN CIKI nake.abba.na kuma tabbata bazan taba fitaba daga cikinsaba.menayiwa danliti ya lalatamin rayuwa?menayi masa dazaya karya dukkan gabobin tatbiya ta da kima ta da asalina...sannan yawargaza dangantaka ta da iyayena,,,ya rabasu da komai najin dadi...har umma tabar gidan duniya?yaya soja kana kallo duk hakan ta kasance?meyasa baka jefani gadi rum ka rufeba?meyasa baka hadani da sojoji sukayi ta dukana harna mutuba?dukknku kuna nan?kun san wanda nakeso kunsan zabi na,,,amma kuka barshi yatafi maimakon ku tilasta inbishi duk. Yaya soja ya rufe bakinta,,mama ya kamata kiyi shiru haka.zuciyarki zata buga.idan kina fadin irin wadannan kalaman.ni yadda nake gani ma ke baki ga BAKIN CIKI Ba tamkar yadda muka ganshi kiri kiri.amma bamuda maganinsa.kisani duk abubuwan da kika lissafa babu wanda bamu kwatanta akankiba.sai dai abin ya faskara.saboda anriga an mallaki zuciyarki mama.karki danganta laifin akan kowa.don babu wanda yasan gaibu sai Allah.shidin kuwa mukayi ta roko ya warware mana abunda ke boye.agame da lamarinki.ina ganin yakamata ki kalli uzirinmu.kiganecewar munyi iya kokarinmu. Hargashi Allah ya shige mana gaba ya kwato mana ke.ayanzu mukeda damar nunawa danliti cewar lalle ya debo ruwan dafa kansa.dazai kaisa har lahira.ki kuma sa ido kigani. Da sauri tadawo wajensa shima ta rungumeshi murya na rawa take cewa karka barshi da rai yaya!kasa a masa azaba mafi radadi harya mutu.ya lafe kanta a kirjinsa zuciyar maxa ta motsa.idanuwa suka qara jirkita.kawai gani sukayi yasaketa ya miqe cikin hanxari zaiyi waje,,,abba yayi azama yace ku riqo minshi don Allah!su alh basiru suka cafke hannayensa.dawo ciki ka zauna ya qame a tsaye suna ganin yanda jikinsa ke rawa.namansa na girgiza saboda fishi.alh adamu yace alh ne zaiyi magana dakai..abba ya daga murya yace abduqadeer dawonan ka zauna!a hankali fishin yarinqa sauqa sannan su alh basiru suka dawo dashi ya zauna.yayinda mama tasake baro jikin abba tadawo gunsa ta zauna. Abba ya numfasa dukkanmu musulmai ne,,kuma munyi imani!da ko waccw qaddara ce.ina ganin fushin farko banamu bane.kar zuciya tasa mu aikata aikin nadama.yaya soja ya kasheshi babu nadama dan an harbe azzalumi macuci.irin danliti.karka manta muya fesa mana gubar mutuwa.mun shaqa harta shige mana da ginshikin gidan nan abba,!bazamu yafewa danliti ba abba.koza a kasheni saina harbeashi.abba yace kenan bamu godewa ubangiji ba daya nuna mana wannan ranar?wanda yace muyi afuwa a tsakaninmu.domin shi yanason masu yafiya.ko bamuyi fansa a gun danliti ba.nayi rantsuwa Allah bai gama walaqanta shiba.tunda ya walaqanta ayoyin alqur'an.inaso mugane wannan.ba haqqin mama kadai ke wuyansaba. Banajin akwai hukuncin dazamu yankemasa face mu qyaleshi da wanda yabasa ikon aikata wannan aiki akan mama.na tabbata bazai qyaleshiba yaci bulus!ba.ina roqonku da muyi haquri.mu sadauqar da yafiyarmu a matsayin godiya ga Allah daya musanya mana bakin ciki da farin ciki.ina fatan yaya soja zaibi umarni na? jikinsa yayi sanyi yadan kada kai..yace ya wuce abba yayi dan murmushi. Yace nagode! mama zonan...!ta rarrafo ta dawo jikinsa ya jawota. Yace ki nitsu nasan kinrasa komai na tsarin rayuwarki yanda kika shirya....saidai inaso ki gane cewar shirin Allah shine gaba da komai...saboda haka ki rokesa sabon rayuwa mai albarka.muma zamu tayaki zakiga kamar wannan abun bai faruda rayuwarki ba.ki sani har ummanki ta rasu bata taba yi miki baki ba.kullum addu'arta Allah shiyaki.idan zatasa albarka tare takesa muku da sauran yayunki.don haka tsakaninku adda'a ne kawai. Na tabbata hasken addu'arki zaije gareta.harta gane cewa lallai albarkar ta na tare dake kinji mama?ta dubeshi kwalla na zuba tace naji abba.don Allah kayafemin ya goge mata hawaye yace baki min komaiba mamana.ayau nagane baki da laifi ko kankani saboda haka ki saki jikinki.tace nagode abba intambayeka abba?yace tambayeni mamana.ta karya wuya gefe tace al'ameen fa?ya kada kai yace allahu akbar!alkairi Allah yakai mas duk inda yake.haqiqa bantaba ganin tashin hankaliba irin wanda nagani a fuskar al'ameen..saboda rashinki mama kiris yarage ya zautu amma qarfin adda'a ya miqar da imaninsa zuciyarsa ta daidaitu bisa shirin ubangiji.ya rungumi qaddara yawuce da ita rasha.gaskia bansake jin duriyarsa ba haryau din nan danake magana dake...kuma hulda ta yanke tsakaninmu.ni kaina bansan daliliba.watakila iyayensa sun nisancemu don qara nesanta rayuwar dansu ga tinaninki.hasashe nayi amma bansan musabbabinba. BAKIN CIKI 3***7 Tacire kai ta dubesa kwalla na zuba tace tabbas zai iya zama hakan abba!nima nayi alqawarin zanyi masa addu'a Allah qara nesantamu.ya mance ya taba sanina a duniya..ko a hanya kar Allah ya qara hadamu.abba yashafa kanta Allah ya shige miki gaba.yayi miki jagora a sabuwar rayuwar dazaki fuskanta nan gaba.kowa yace ameen yace muyi addu'a.sun raba dare a falo suna hirarrakin duniya abba yace aje a kwanta a huta.mama ta turashi a kekensa zuwa dakinsa wanda tuni anty amina ta dade da gyarawa.suka kamasa yakwanta a gado.sannan sukayi sallama takoma dakin umma!inda anty amina da baraka suke. Kowa ya kwanta barci ya kwasheshi.amma mama ta kasa.kawai tunanin yanda tayi cudanya da danliti take.nan da nan ta ji kyaman kanta ta kamata.tafara sunsuna jikinta.hankalinta tashe batasan lokacin data diro tashige bayiba.ruwan sanyi ne a bokiti da anty amina ta dibo.mama ta duba ba soso ba sabulu.haka nan tahau kwara ruwan sanyi ajikinta.tana dirjewa da hannu hawaye na xuba.ruwan ya qare ta dauki bokoti ta kwarara sauran. Tadauki bokitin takwara sauran ruwan gaba daya.haushin qarewar ruwan yakamata.tasanya kayanta ta figi bokitin da nufin taje tsakar gida ta debo a rijiya.su anty amina da baraka tagani cirko cirko abakin bayin.tawuce abinta ta doshi kofar.yayinda anty ameena kefadin haba mama! ashe bakiyi bacciba?yakamata kimanta komai karki zautu a banxa da wofi.ta zuba mata ido kwalla na xuba wari nake anty ku bakuji?babu wani warin da kike mama!tunaninki yagaya miki qarya.yakamata kisamu bacci ko kwakwalwarki zata huta.ta dubi baraka taga hawaye itama take,,,tace saboda Allah baraka bakiji warin danake ba?sunsuna fa kiji....takara mata hannu a hanci baraka ta goce da kuka ganin haka jikin mama yayi sanyi ta zube qasa dabas takama kai.wayyo Allah na!suka kamota sukayi ta rarrashinta.tadan nutsu.amma barcin da basu komaba kenan gabadayansu Washegari kowa ya hallara da iyalansa.ya abdulkareem da anty rabi kamar su hadiye mama sukeji.sun xubda hawaye saboda murna.ta dubi girman ameer da ameera kawai sai ta kada kai.tana tuna al'ameen shikansa docta yazama saurayi.ta zura masa ido,,,hannayenta bisa kafadunsa ta matse ido.hawaye suka kwararo..jitayiyana share mata hawayen tayi wuf! ta bishi da kallo.bakinta na rawa tace al'ameen momy nagayama inasonka?? ta taba gayamaka? ya juya ya kalli mominsa.yamaidoda kansa gareta ya girgiza kai.bata gaya maka ba?amma momy bata kyautaba.tasanfa yadda nake sonka Allah tasani boyema tayi togayamin kana sona? yadaga kai alamar eh.ta rungumeshi tana fadin nima inasonka dokta. Anty rabi ta taso ta dafata.ta dago kai ta dubeta kwalla na xuba mama!ki kwantar da hankalinki na tabbata Allah baxai barki hakaba.zai musanya miki mafi alheri wata qilama fiye da al'ameen.tayadd a rayuwarki zata daidaita tamkar da. Ta miqe a hankali ta fuskanceta tace hakane.nasan babu abunda zai gagari Allah.amma dokto shine farko shine qarshe.ta wuce ta murda kofar dakinta.ta qare masa kallo inba qarya idonta ke gayamata ba.kamar ta taba ganin al'ameen tsugunne a wajen data qurawa ido.dukda takasa tuna kalaman dayake fadi.idanuwantana nuna mata zubar kwallansa.tayi wuf!ta cafke yatsunta ta runtse su tamau.tana tambayar kanta ina zobe na?ina na ajeshi?ta wuce a hankali bakin gado ta zauna tayi shiru tana tuna kalaman dayake fadi idanunta na zubda hawaye.kai al'amarin mama qara sukurkucewa yake dalilin dayasa abba yace subar garin wataqila tafi samun nutsuwa.nanda nan suka fara shiri.kafin wani lokaci kowa ya kimtsa abba ya sallami en uwa da abokan arziki.su hajiya hajo sunata neman gafara wajen abba da mama.motoci suka kwashesu kowa da iyalansa suka miqe hanya.suka bar danliti hannun hukuma.duk abinda yakamata su masa A kagara suka sauqe baraka tukuna suka dau hanya.minna suka yada zango gidan ya abdulkareem.ko anan dinma al'amarin bai sauyaba.haka suka kwana ba barci a idon mama.washegari suka kimtsa masu tafiya abuja suka dau hanya.ya abdulrahman yayi kaduna da iyalansa da malami.shikuwa abdulkareem jirgin shabiyu sukabi zuwa legos.yan abuja suna dira gida wanka mama tafarayi.wannan wanka yafara damun yan uwanta.su wanka ma kawai suke gani basusan yanda taga dare haka take ganin ranaba!akwai fargaban rashin bacci zai mata illa.idan ba'ayi gaggawar daukan matakiba.towayasani bare ayi mata magani? shiyasa kafin sati ta birkice gaba daya.ga zama shiru ga sunsune sunsunen jikinta.wanka kuwa ba'a maganarsa.saidai in danliti bai fado mataba.nan da nan tafara mura zazzabi mai zafi ya rufeta.hankalinanty amina yatashi.data shigo dakin tasameta nade cikin bargo sanyi na kadata.cikin sassarfa tasamu abba.ta durqusa a hankali tace abba idan ba'a dau matakiba mama zata kashe kanta da yawan wankan nan. Mama zata kashe kanta da yawan wankan nan.gatacan jikn kamar wuta sai rawar sanyi take.yakamata asan abinyi cikin gaggawa.nanda nan ya latsa control din kekensa yawuce ya nufi dakin yana fadin kira yayanta a waya.kuma fa yau dinnan naji yana fadin sun gama magana da yan uwansa egypt zasu wuce da ita asibitin dana kwanta. Su duba lafiyarta! tace nima yagayamin amma duk da haka yakamata afara kaita nan tafara samun taimakon farko.yana kutsa kai dakin yana fadin gaskia ne.kirashi din ki kara gaya masa.ta juya shiya shige dakin yasamu mama sai kyarma take cikin bargo.kwananta biyu a asibiti basu gane ainihin matsalartaba.amma taimakon dasuke bata yataimaka kwarai wajen sanyata bacci.tana samun hutu.duk takardar tafiyarsu masar sun kammala itada yayanta wato soja.a ranar basu kwana ko inaba sai egypt .acan bincike ya tsananta.don babu irin gwaje gwajen da bata samuba.hoton kwakwalwa hiv aids,,ciwon sanyi da sauran ciwuka dakan kama mutum sakamakon shiga wahala mai tsanani.Ba a sameta da wata matsalaba sai hawanjini da rashin bacci.kamar dai yadda likitotin nigeria suka ce amma su abba basu yaddaba dan gani suke kamar hauka mama keda niyyan yi.sai dai Allah da ikonsa likitotin masar suna kokarin shawo kan matsalarta.da magunguna da shawarwari.don cire mata damuwa wanda gabadaya ita ummul aba isin komai.to muma bari mubarta ta huta. A lokacin da mama ke kwasar hutu damagunguna akasar masar.shi danliti yashe yake aofishin yan sanda.yanata hauhawa kamarfarashi.gaba daya fuskarsa ta aune ta kumburasundum.sukansu yan sanda sun gaji da saya masagarin rogo yanasha..babu mai belinsa.tsawon kwana biyar dama ayuba ne yake zaton ziyi belinsa to shimatunda yaga ayar Allah ta sauqa.don haka yayi wakansa alqawarin tuba daga nasa laifukan zinacezinace dayake aikatawa.babbar mota yabi sai indamai yaqare.wajen neman halal.to Allah ya karbitubansa.shikuwa dan goga yarasa tudun dafawa ga ciwo ga masifar yansanda.ranar daya cika kwanashida.sukace zasu sakeshi yatafi yanemilafiyarsa.idan yaga dama ya gyara halayensa ko yacigaba da lalacewarsa..shidai yana kuka yana roqonsusu barshi dare yayi su sakeshi saboda kunya kunjidan iska ashe yanada kunyan?kuma da tsoron kar jama'a suganshi su sake rufar masa da duka,Yansanda suka amince hakan amma baxasu bashiabinciba.h aka yazauna da yunwa har qarfe gomandare.suka tarkata shi suka tura waje.a hankaliyasamu ya sulale yakoma gidansa ya kwana.yanatunan in mafita da da hali gidansa zai sayar a darannan yahada kudinsa yatafi neman magani.sai dai kash takardun sun kone a shago lokacin gobara.meyeabunyi yanxu?bai runtsa ba kamar sauran dararendasika shude.yana wahala da ransa.sai dole yakaudakunya ya nemi wasu takardun yasaida gidan danbashida wata mafita data wuce wannan.idan yanasoya tsira da sauran mutuncinsa duk inda zashi..haka kuwa akayi da sassafe ya lallaba gidan maianguwa.baiko dawo masallaci ba.ya zauna yajirashi.ya gurfana gabansa yayita roqon gafara.sannanya miqa masa kukansa.mai anguwa bai bata lokacibaya amince domin shima zaiyi farin ciki idan danlitiyabar garin fandogari.saboda haka nantake yakawo takarda da biro suka rubuta wani takadda.dakansayanemo shaidu uku sukasa hannu.kuma yasa akanemo dillalai sukayi wa gidan kudi yace shi zai Saya,Gaba daya dubu dari biyu cinikin ya kaya.danliti yasallama ya karbi kudinsa a hannu.kafin qarfe goma nasafiya ya tattara yabar gari.gashi nan gashinan harwani kauye da ke tsakanin zariya zuwa kura jaharkano.da la'asar sakaliya.kofar gidan daya dosa cikeyafe fal!da jama'a anata alwala.a raunane yayi musu sallama.suka amsa ya tambaya..ko lafiya kofar gidanmalam?daya daga ciki yabashi amsa ai malam wa'adiyayi.shirin yimasa sutura ake.danliti ya dora hannuaka yace ciwo yayi? yace to ciwon ajali ne.kwanansabiyu kacal a kwance.ya nemi waje a qasa ya zaunahankalinsa ya qara tashi..wanda ke bashi amsa yamiko masa buta yana fadin hala kaima cikinalmajiransane?yace aytoo harda neman taimakoma.Allah sarki malam Allah jiqansa.yace amin yialwala yanxu za'a fito dashi.jiki babu kwari yafaraalwala.ya na kammalawa ana fito dashi.daganan sukadiba zuwa makabarta..ga kabarin malam an haqa duk abunda ake anyi akasakasa a kabari aka maida qasaakarufe iyalansa nata kuka harda danliti,Daga nan aka dan jira ayi masa addu'a kawai ganingawar malam akayi ta bulloqo waje,subhanallah! mekefaruwa ne? tashin farko jama'ar wajen suka watse.kafainbak iyi kibani waje musamman danliti.daya riga kowaficewa daga wajen.daga bisani liman yasa aka tattaromasa mutane suka dawo.danliti nacan baya yana rarraba idanu.liman yadaga murya yace innalillahiwainna ilaihi rajiun.! jama'a wannan al'amari fa banagudu bane.! wata ayace dake bukatar bincike.matsayin malam agarin nan wannan zai iya zama abin kuka agaremu.domin mu a zahiri munsan malam mai iliminaddini ne,,wanda ya koyar da almajire da yawa.wanda yake wakilta na lokutan danake da uzuri.sai dai ahalin yanxu wannan abun yanuna mana akwaiboyayyen laifi agareshi!ina rokonku dan girman Allahku tsaya muyi masa addu'a.mu roqa masa rahamarubangiji.alfarmar annabi muhammad (s.a.w) Yayi kabbara sau uku jama'a na amsawa.iyalanmalam kuka da firgici yaci qarfinsu labari kuwa tuniyabaza kauye.har wadanda wani uxiri yahanasu xuwasun sheqo aguje.shiyasa makabarta taqara cikamakil.liman ya jagoranci addu'a mai tsawo.sannanaka qara haqa kabari aka sakasa.shikansa liman kuka yake da hawayensa saboda ganin wannantashin hankalin.bayan anmaida qasa an rufe .sukasake tsugunnawa dan nema masa gafara.ai sai gagawa tayo waje.ana salatin annabi da tasbihi daistigifari akasake mai dashi.amma ba'a gama maidaqasar ba gawa tasake bullowa waje.liman ya dubi babban dan malam.ya tambaya!meka sani agame damalam wanda mu bamu sani ba? gashi ubangiji yananuna ishara gamasu yi su tuba su daina.ya gogekwalla yace wlh bansan komaiba,,,bantaba lura dawani aiki na assha atare dashiba.dana sani wlh danafadi sai dai ko aje atambayi mata a gida, LLiman ya numfasa duk guri yayi tsit!kawai sai ganindanliti akayi a gaban liman ya tsugunna Allah gafartamalam ni nasani.na kasance ina daya daga cikinmasu zuwa gun malam.neman taimako akanabubuwan dasuka damemu ko ince nemanduniya.bansan irin shirin dayake wa sauranba amma nida kaina. Nasha kawo ruwan..........ruwan maniyyinayana rubuta ayoyin Allah dashi.yana hadaminmagunguna danake buqata.ina bashi maqudankudade.tahanyar malam mun cutar da bayi Allahwadanda basujiba basu ganiba.ba malam kadai kebuqatar addu'a ba harda ni.Allah gafartawa malam.wuri ya kaure da sallami.wasu sukafarazungurar dan liti suna la'antarsa.liman yatsawatar.yace a saurara.tsarki ya tabbata ga ubangijindukkan halittu.jama'a kunji wannan mummunan tashinhankali?toga aya ta tabbata.ina ganin ta ishemutsoron Allah.ta ishemu mu gane komai ka boye wa mutane bazaka boye wa Allah ba..kuma ko ba dadekoba jima zaka koma gareshi.bamu da abinyi a halinyanxu dan hukunci yakoma gunsa. Ya daga hannunsa sama yaci gaba da fadin yaubangiji muna tawassali da sunayenka guda casa'inda tara,,,ka taimakemu ka amshi wannan bawa nakadan kar warin gawansa yazama guba ga bayinkasalahai!ya Allah ka sauqar da rahamarka cikinkabarinsa badon halinsaba.badon halinmuba.badon ayyukanmu ba sai don monxon mu annabimohammad (s.a.w)suka qarasa tare da muryoyinmutane dake cike maqil.kai tsaye liman yace akamaa maidashi.kankace kwabo ansakasa a rami anrufeakayi zuru! ana jiran ikon Allah.amma tsawon mintocishabiyar. Babu abunda yafaru.aka soma qabbara.liman kuwa fadi yake jama'a muji tsoronAllah.muji tsoron Allah ya al'umman musulmai.kodada nliti yaga haka saiya fakaici idon mutane tuni yasulale ya tsere kar yasha dukan banxa gun wadannanyan kauyen.A gigice yashiga kano cikin dare da kullin kudinsayanufi inda yasaba sauqa,,,,,zuwa safiya yayi amfanida kudinsa danyin wata sana'ar don riqekansa.washegari yashiga kasuwa yin sari wani mutumya bangajeshi ya wuce.saida aka hada masa kayandubu dari da hamsin.ya laluba kudi sukace daukarmu inda ka ajiyemu..nanda nan ya firgice.ya tubekayansa tsundur yana dube dube....ina kudin suke?anan fa na ajiyesu...masu shago sukayi zuru sunakallonsa.am ma dasukaga abin nasa babu hankali aciki sai suka turasa waje.ga ganin wannan mugun nufine yakawo sa Allah yakamashi.yakama haukan qarya.haka masu shagon da jama'ar wajen ketafadi.danliti kuwa ya rinqa bi kwararo kwararo akasuwayanata surutai.fadi yake...wannan bala'in yayiyawa..wata tsiyar ma sai anmutu.lalle lahira dakallo.toni wama zan kalla?aini ne zanxama abinkallo.da dama idan sukaji dariya suke.wasu kuma al'amarin yabasu tausayi.ga mutum har mutum daganiya aje iyali amma ba saiti,Bayan watanni hudu har mutan fandogari sunfaramantawa da abin mamakin daya faru...wanda ya ajetarihi musamman ga yan jarida ta yadda..suka rinqawatsa labaru.cikin shafukansu.na abin al'ajabindayafaru a kauyen dunduta.ba xato ba tsammanikawai sukaga danliti ya keto titi a kafa da rana face face.yayi bakikirin.gashi n kansa cunkus hade daqasumba.harda furfura.dafarko basu shaida shibasaida yayi sawu uku.nanda nan labari yayi tambari harkunnen su abba cewa danliti ya HAUKACE.Allah daikonsa,tunda ya iso fandogari bai qara gaba ba.nanyaketa bilayinsa.qafafu duk sun kumbura.wani lokacinma kasa tafiya yakeyi.kaganshi kwance cikinrana quda na binsa.idanyaji yinwa yayi tabin gungunmutane yana bara.asiya masa abinci.kai jama'a muceALLAHU AKBAR! **A watannan hudu,,ita mama sauyi sosaitasamu.domin tasamu matuqar kulawa a sati ukundatayi a masar.tacci gaba da samun kulawar yanuwanta.suna nuna mata gata fiyeda wanda tasamuada.tadawo sakeenarta.sai dai dan qara manyanta dafuskarta tayi.ayau suke sa ran dawowarta daga umara!inda tasami sati biyu a saudiyya tana ziyararka'aba.tana samun nutsuwa tare da miqa addu'ol daneman buqatu na alheri.sai dai bata sauqa abuja ba alegos ta yada zango.anty rabi dasu ameera sukadaukota a filin jirgi tayi bulbul. Abinta gwaninsha'awa.dokta yafi kowa tsaraba masu tsada.bayan taci abinci ta huta ta kira wayan abba.ya dauka tayimasa sallama kafin yace haba mama na! watau dagaske kike a legos din kika sauqa? tayi murmushitace yi haquri abba.ai bazan dadeba zandawo kwanauku kawai zanyi,Yace sunyi yawa mamana!kiyi kwana biyu na tabbatasun isheki warware gajiya.akwai magana muhimmiyadanake so muyi.tace shikenan abba Insha Allah jibinzanbiyo jirgi inade ya soja baiyi fishiba?yace yayiamma ya huce tunda yayan legos din yabada haquriinkindawo jibin kinqara wanke kanki.ta qara murmusawa tace nima na qosa in ganka abba dukkewarka tadamen.yayi yar dariya,,,mamana kenan tomuna sauraronki jibin.sai munsake waya tace toyanxuma zankira any amina mu gaisa. Toyayikyau.ace ina gaida halima.zangayamata.sukayisallama takashe wayan tasake kiran yayanta.sannan ta kira anty amina duk suka gaisa.tagaya musu inshaAllah jibi zasu iso abuja.daganan kaduna ta bugasuma suka gaisa.bayan tagama wayan duk indatakeson kira ta dubi dokto.dake liqe jikinta.kanatakallona na fiye surutu koh?yayi yar dariya yace nibanceba anty.taja habarsa tace ai nasan bazaka ceba.kai din waya kaika surutu?yaware ido kamarnata yace ni anty?ko a skul gentle man antynmu kecemen saboda banda surutu da yawa.Ta zura masa ido fuskarta cike da murmushi taceuhm.....yabon kai adai rage dokto saboda gobe yacemai zan rage?tace qarya!yadan cunno bakin takamatana dariya.toyi haquri gettlemen ai nima nasan kaigentle ne.akwai wasu cakulate a jakata miqominnaqara maka sunfi ta dazu dadi.yamiqe da gudu yadauko mata bisa madubi.ta bude ta kwasomasa.tadauki daya ta bare tace bude bakin insanyamaka...kunya takamasa.ya tsaya yana kallonta yanamurmushi.lah!kunya?dan kyauye bude mana.yakasabudewa sai rufe fuska yake ba zato tafara fadin bahaka akeyiba...gaskia ba haka akeyiba dokto!ka bude bakin insaka maka.anty rabi ta kyalkyale dadariya.sannan mama tagane tashigo dakin.tadubeta afirgigi.lah anty labe kike mana?ni yasu mezanyi walabe a sha'anin uwada danta?akwai dai son kai danbashi kadai bane dan.amma ankilliceshi shikadaianabasa gara.adai rinqa adalci...... Tayi dariya sosai tace kaji hassada,,bude bakinkamubasu haushi.ya bude tasanya masachocolate.suna ta masa dariya.ta jawosa jikinta tarungume..anty rabi tazauna gefen gadon sukaci gabada hira.da daddare ma bayan cin abinci haka sukataru.a falo suna kallo suna hira.da yayanta.washegari bayan cin abincin rana.suna kebe cikin daki da antyrabi..suna hira.mama tace anty nikuwa tuntuni nakeson tambayanki wani abu amma inajin nauyi.tazubamata ido menene shi? tace don Allah ko kinadatsofaffin hutunan su ameera da al'ameen?tayimurmushi mama kenan!inbanda abinki waya isa yarabaki da al'ameen balle yahanaki ganin hotonsaharda zaki rinqa jin nauyin tambaya?ni wlh bakiji dadindanake jiba innaga yanda kike hira da al'ameen dankisai inrinqa ganin kaman a'ameen dinkine.yanzu zanbinciko miki nasan dai suna nesa cikin tsofaffinalbum. Tayi murmushi to nagode!tamiqe tayita sauqe kaya tazakulo album din tadawo dashi inda mama kezaune.ta miqa mata tace gashi duba,,tafara budewatana kallon tsofaffin hotunansu harta kawo wandaal'ameen yadauka dasu ameera.yana tsakiyarsu duksuna dauke da wadataccen murmushi!gabanta yafadi ta bude ledar ta dauko hoton tazuba masa ido.dagacan tajiyo muryar anty rabi na fadin nidai mamatsorona daya kar ganin hoton nan yasake jefaki waniyanayin da bama fata.kinsan abba bazaiji dadiba.tanumfasa ta dubeta anty rabi nayi rashi tace nasani!nakuma tabbata shima bazai taba mantawa dakeba.tace zai manta idan haryasamu labarin mummunan halindanake ciki......takada kai nikuwa banjin wannanaraina saboda shine mutum na farko dayaqi yardacewar akan ra'ayinki kika canxa.kullum fadi yakeyasan kina sonsa..lalle akwai rashin sani a waniwaje.kowa yayi biris!da zancensa.dan anaganin zautuwar sanki ne.ta gigitashi.kinga kuwa banjinakwai wani abu dazai goge sonki aransa. Ta goge kwallan daya zuba mata.anty rabi tacekingani koh?gaskia bazan baki hoton nanba.kisa inyilaifi gurin kowa.tagoge da sauri tace bawani abu antyrabi kinsan Allah?zuciyata adake take kanal'ameen.kuma nasan narasa sa har abada.kuma nikaina bana fatan mu hadu.ina mai tabbatar miki a gaban ka'aba nayi wannan rokon wajen Allah.fatanaya amshi rokona.saboda haka kar hankalinkiyatashi.donkinga ina hawaye bazan iya hanasuzubowa bane..tunda sun taho sanadin farin ciki.tacegaskia ne.to Allah zaba mafi alheri.taceameen.intambayeki mana...waiya kikaji da akace miki danliti ya haukace?tayi murmushi ta kada kai tacemaizanji kuwa anty?ai qarshen alawa qasa kuma dukwanda yataba qur'ani.bazai shaba anty.Allah yayigaskia dayace qurani nashi ne kuma shi zai bashikariya! kinga kuwa danliti yadebota da zafi.wata qilada haqqina kadai yadauka abin yazo masa da sauqi.Allah ya shiryi zukatanmu baki daya.ta amsa daameen tana mata kallon tausayi,80..... .jirgin safe tabi xuwa abuja tana zaunecikin jirgi tunanin maganan anty rabi kawaitake.tabude jaka ta zaro hoton ta zura masaido,,,salon soyayyar dayake mata take karantowa.tasauqe numfashi cikin ranta tace inasonka al'ameenamma bana fatan sake haduwarmu dakai.tamaida hoton cikin jaka takoma ta jingina da kujera.taci gabadayiwa Allah tasbihi har suka iso abuja.tana fitowaharabar taran fasinjoji ta hangi anty amina a tsaye.Suka rungume juna zuwa inda tayi parking.suka shigemota anty amina tajasu zuwa gida.a guje tashigegidan cikin falo ta iske abba zaune kan kekensa ta zube jikinsa cike da murna..abba nah!mamana kenan! andawo lafiya? ta dago kai tadubeshi lafiya lau.yacenayarda saudi ta amsheki kinga kumatunki kuwa? tayidariya kai abba harda zolaya? yace aiba zolayabacekowa yaganki zai shaida hakan.anty amina tace nimadai haka nagani.tace to ai hakan akeso ko? yace kwarai kuwa bakiji dadin danajiba.toya mutan legos?tace qalau suke suna gaidaku.ina amsawa.anty aminatace nizan haura sama.Anty amina tace ni zan haura sama..duk abindakikeso naci akwai a kicin.tace to anty sai na hayosaman.tajuya ta haye saman tabasu gu su gana.abbayace kije kisamu abunda zakici..tace aibanjin yunwaabba karfe 12 ne yanxu akwai sauran lokaci.yacekodan ruwa mamana.?tayi murmushi ta miqe barin dauko abba..ta ajiye mayafinta tawuce kicin ta zuboabinci filet tanaci suna yan hiransu.tana bashi labarinumara har aka kira azahar.takaishi dakinsa yayisallah.itama taje tayi tasawo tasamesa yana cinabincinsa gefensa ta zauna ta qara yawan abincinsunaci tare abba kace zamuyi magana..amma bakace min komaiba?yace ina sane inasone ki qaranitsuwa.tace a nitse nake abba...kagayamin nimainada nawa maganan.yace toki saurarenidakyau.bayan tafiyarki umara kawunki alh basiru yabugamin waya wai mutane sunata zuwa nemanaurenki... ..aurena?yace wlh kuwa kuma abin mamaki duk yan fandogari ne..bangama nazarin maganarba..saiga wata wayar tasameni aranar dakika sauqalegos,,,ake gayamin ko yar gida zamuyi, Domin yayanki ali yadawo da maganarku tabaya.nace duk sumin uxiri kidawo muji tabakinki..nanda nan fuskarta ta sauya tashin hankaliyabayyana a fuskarta..abba ya zura mata ido kafinyace..yanaga hankalinki yatashi?hawaye suka gocemata tace dole hankalina yatashi abba nah!don ka kawo min maganar dana jingineta a babinrayuwata.....kamar ya mamana? aini addu'ata kenanAllah fidda miki miji nagari kuyi aurenku.hankalinkowa yakwanta..kuma Allah ya amsa ganin gamanema Allah ya turasu..ko baki zabi kowaba inakyautata zaton bazaki qi zaben dan uwankiba.domin aliyu yacika dan halas kuma masoyi na haqiqa. aliyuna daya daga cikin mutanen da bazanmantaba.saboda shine mutum na biyu daya roqe ninayi afuwa a gareki duk ranar da kika dawo gidalokacin dakika bi danliti kuka gudu.al'ameen shine nafarko sai ali.haka bana manta ranar daya kamo hannunki yakawo minke.ya durqusa yanema miki,Kuma ya hana mu daga miki murya saboda baqi cikingidan.aliyu ya jima yana zubda hawayensa akanBAKIN CIKIN Qaddarar data sameki.ba qaramin maisonki bane zai nuna maka irin wannan yardabamamana.a yanxu kinga zahiri ali mai qaunar ki ne.donAllah mamana kar kice bazakiyi aureba! saboda wani dalili nikam ayanxu banida wani buri face nagankidakin mijinki.ta kada kai tana share hawaye wannanbashi ne burinka akaina ba abba,,,tun banda wayaukagayamin burinka akaina amma yarinta yasanamaka musu.na sauya maka tunani.akan dolekadauki zabina.bansani ba wataqila musun dana maka ne yazamemin matsala.abba yanxu nayihankali burinka shine nawa,,,yadda kake sha'awar yamace likita insha Allahu Allah zai nuna maka ni amatsayin likita.kamar yadda kake burin hakan tunasali.da wannan tunanin nadawo umara.kuma itacemaganar danace zamuyi.don Allah abba kagoyamin baya akan rayuwar danake ganin itace zaman lafiyada kwanciyar hankalina,Kuka sosai takeyi hankalin abba yayi mugun tashiyace saurara mamana sanin kanki ne idan na goyamiki baya kikaqi aure,,haqiqa nabi son raina.ni aganina ai auran bazai hanaki karatu ba.idan banmantaba hakan kuka shirya da al'ameen.Allah ne bainufaba inkuwa hakane mezaisa ki fasa mamana?tace abba a fuska faram faram,amma zuciya saiAllah.inada abin gori ajikina wanda yazame mini adolena nesanta kaina da kowa.don tsira damutumcina.abba na tabbata ka gane nufina.dangirman Allah kaban izini nakama karatu.ya kada kaicikin damuwa.mamana ko wani zai miki gori kamar yadda kike hasashe na tabbata aliyu dan uwankibazai miki gori ba.ki sadauqar masa da kanki kamaryadda ya miki halacci lokacin da kowa yakyamaceki.tace zan iya yiwa ya ali komai muddin inadashi har qarshen rayuwata amma bazan iyaaurensaba.tu nda yanada mata.kubashi haquri yaci gaba da juriya da kulawa da iyalinsa yadda yadace.tayunqura ta tashi tayi waje.abba yabita da kallo yanasoyakirata amma ya kasa saboda tausayinta. ana fitowa ta hadu da yayanta yana shigowa.ta rugata rungume shi yace menene? takasabashi amsa yajata suka koma dakin abban yanazaune shiru yana juyayi,,abba meya faru ne? sukazauna kusa da abban yace ba'ayi komaiba akan maganar nan ne dana gaya maka masu sonta daaure.shine tace karatu zatayi amma ban yarda dahujjojintaba.ina ganin aurenta zai zamo mata garkuwaaduk inda zata neman ilimin.yaya soja yace gaskia nesai dai inbata aminceba akwai matsala dan ita bayarinya bace.tasan abinda take hangowa kanta,,,so pls abba..idan bazaka damuba a madadin sauran yanuwana muna roqonka kabar autanmu ta nemiilimi.ahankali zata gane aurenma yanadamuhimmanci.dakanta zata kawo maganar cikin gidannan so please abba!please!!ya tallafe goshi shiru jim!Ya dubesu yace.shikenan Allah yasa hakan shine mafi alheri matsalata kawai bansan mezan cewa aliba.inajin nauyin yaron nan.farin ciki ya mamaye matazuciya.yayin da ya soja ke fadin yayi haquri.Ai ali ya girma babu wannan haukan yarinta a taredashi kamar da.kekuma dole kiyi taka tsan tsan andaishaki kin warke.rayuwa ta zarce duk yadda kikezatonta saboda haka ki kiyaye.tayi murmushin farinciki ta matsa kusa da abba nagode abba,,kuma dayardar Allah zan kiyaye.yadafa kanta yace Allah yayi miki albarka tace amin.yaya nagode.yace inatsarabata?kinje kin rabeta a legos ko?kin kai wa lazydokto.ta rufe baki hannu biyu lah yaya me kake nufi?ya damki bayan wuyanta yace are u askin me? aiangayamin kayan al'ameen yafi tsada da yawa.taceok nasan magulmaciyar ameera ce babbar kwabo batada abokin kishi sai al'ameen.sukayi dariya abbayace umman takice mai gulma?lalle ya ta riqa.tacigaba da dariya tana cewa ni ummata bata kishi dakowa.Allah ya jiqanta amin.anty amina tayi sallama tashigo ta zauna cikinsu abba yace mutuniyarki taqiyarda.yayanta kuma yace abarta tayi karatu.tayi murmushi kayi haquri akan hakan abba Allah saalherine.yace amin haka nake fata.hira ta tsunke ananya soja yaci abinci. BAKIN CIKI 3***8 Ai ali ya girma babu wannan haukan yarinta a taredashi kamar da.kekuma dole kiyi taka tsan tsan andaishaki kin warke.rayuwa ta zarce duk yadda kikezatonta saboda haka ki kiyaye.tayi murmushin farinciki ta matsa kusa da abba nagode abba,,kuma dayardar Allah zan kiyaye.yadafa kanta yace Allah yayi miki albarka tace amin.yaya nagode.yace inatsarabata?kinje kin rabeta a legos ko?kin kai wa lazydokto.ta rufe baki hannu biyu lah yaya me kake nufi?ya damki bayan wuyanta yace are u askin me? aiangayamin kayan al'ameen yafi tsada da yawa.taceok nasan magulmaciyar ameera ce babbar kwabo batada abokin kishi sai al'ameen.sukayi dariya abbayace umman takice mai gulma?lalle ya ta riqa.tacigaba da dariya tana cewa ni ummata bata kishi dakowa.Allah ya jiqanta amin.anty amina tayi sallama tashigo ta zauna cikinsu abba yace mutuniyarki taqiyarda.yayanta kuma yace abarta tayi karatu.tayi murmushi kayi haquri akan hakan abba Allah saalherine.yace amin haka nake fata.hira ta tsunke ananya soja yaci abinci.Basu tashiba sai la'asar kowa yaje sallah.bayan taidar da sallah ta haye gado tasaka (ear piece)tanasauraren karatun qur'ani.wucewar minti talatin tanasaurare dadinsa na ratsata.tashi guda karatun yayanke adalilin kiran daya shigo.ta duba allon wayandan ganin waye sunan ya ali ya bayyana.gabanta yafadi amma ta daure ta danna ok' ta dauka kawaitaci gaba da saurare.da sallama ta fara.ya amsadawata muryar dabata saba jiba.tace yaya ali dangirman Allah......ya katseta da sauri yace karki hadanida Allah ki cuceni mama!meyasa baki tausayina newai?ta numfasa idanu suka kawo kwalla.tace bazaka fahimceni bane ya ali .....yace babu abinda zanfahimta mama,,,ai dama kin dade kina azabtardani.axatona yanxu tunda babu al'ameen zaki iyamaye gurbinsa dani.ashe bazaki iyaba? wannan yanatabbatar min ko alama can zuciyarki bata sonamama.mesa?ta kada kai tace yaya ali ba haka bane nasan ada al'ameen kadai naso amma ayanxu hardakai kashiga raina.saboda halaccin dakamin.wlh dazaniya aure kai zan aura Sai dai bazan iyaba don girman Allah kayi haquri..yayiajiyar zuciya yace mesa mama? kinkuwa san yandatausayinki ya ke bin jinin jikina?bani da wani buri dayawuce kizama matata mama don inshare mikihawaye.kimanta rayuwar wahalar dakika sha canbaya.kiyi tunani zanbaki lokaci karatu kuwa na miki alqawarin ko ina kikeso zakije indai kinxama mataagareni.kai tsaye tace bana buqatar lokaci yaya ali.ainagama yankewa kaina hukunci..kariqe matarka zaifima kyau yaya ali..idan kuwa qari kake sha'awakanemi maras tabo ka aura.tabo? ban fahimceki bamama.tace bazan jure goriba.ka kuwa san yauda gobe sai Allah.ba daga gareka nakejiba ina nufinkishiya da kaidinta.zan iya mutuwa saboda BAKINCIKI.Duk ranar da matarka ta gorantamin.wani abudaga rayuwata.kasani ba ruwan kishiya da asiri idantaso musguna maka zata iya maka sharri zata iyarufe komai ta musguna maka da gangan.Yaja dogon tsaki wannan ne hujjarki mama?ni bankarbetaba dan nasan amina bazatayi mikihakaba.idan kuwa harta kuskura zan nuna matabayan tsananin sonda nake miki zan nuna mata keyar uwata ce ta jini.saboda haka bake zatayi wagoriba ni zatayiwa.tace nagode Allah da bakinka ka furta wannan.ni bazan zama sanadin rabuwarka dayar uwarkaba yara biyar ba wasa bane yaya ali.Allahyamin tsari dashiga wannan tsakanin.kayi haqurikayafemin kullum nayi sallah zanmaka addu'ar fatanalheri yazama sakamakon halaccin dakamin.nagode.jitayi shuuuu!ya kashe wayar karatunda takeji yaci gaba.ta sauqe numfashi bakaiba ya ali ko al'ameen neyadawo yanxu bazan auresaba.ku kyaleni BAKINCIKI Yazamo tarihi a rayuwata.taci gaba da sauraronkaratunta hankalinta na qara kwanciya.da zamandakin ya isheta tafito tasamu anty amina a kicinsukaci gaba da aikin abinci har suka gama aka kira magaruba sukaje sukayi sallah.bayan cin abinci dareda hirarraki kowa yakoma dakinsa.don kwanciya tayizuru tana kallon hoton dake hannunta .Tsawon lokaci ta rufe ido tana kallonsa yana matalabarai ta bude ido a hankali tayi murmushi tana kadakai tamaida hoton cikin jakarta.tagyara kwanciya tayiaddu'oi ba a jima ba bacci yadauketa.bayan kwanabiyu suka samu labarin haihuwar baraka mamatasami zuwa sunan.saboda tasamu takwara harta kwana biyu acanma.inna saude ta matsa tana songaninta don rabonsu da juna tun dawowanta dagamasar.direban dayakawota yasake daukanta sukayifandogari.inna tayi farin cikin ganinta fes kamarbalarabiya yar hutu.daga can tace akaita gida tagaidasu hajiya hajjo.suna gangarowa babban layinsu saiga danliti yana ta hauka afajajan.ya wuce cikin sauriwando a hannu yanata zamulowa tabishi da kallo arazane saidata juya sannan ta nutsu!tana kada kaihawaye suka cika idonta ta matse su tayi sauri tashare tace Allah sarki duniya. Kamar su hadiyetacikin gidan sunata kawo mata cima kala kala.bayan sun gaisa hajiya hajjo tace haba mama.meyasazakice bazakiyi aureba?ga dan uwanki kamar yayihauka akanki.yakamata ki duba. Duk yayi baqin jini gun matarsa dagaji ana maganartahau fishi ba gaira ba dalili,,don Allah mama kiyitunani akai.aliyu yadade yanasonki.ta sunkuyar dakaitace inna ai matarsa tana sonsa,bai kamata yajawoabinda zai tarwatsa gidansaba.ni wlh tawa mai sauqice tunda amina bataso kawai ya haqura..hajiya gaje tace bazai haqura ba.tunda Allah bai haramta masabaki amince masa kisha mamaki.tadan kada kai kudaiyihaquri inna!yaya ali nawa ne ko ban auresaba.kidaiyitunani kinji mama?zamuyi farin ciki idan kin amince!tace to.nan tayi sallar la'asar suka kama hanya dadirebanta.haka suka qara ganin danliti yanata bilayi.tsince tsince kan titi.duniya kenan.babbarmakaranta.suka wuceshi.kafin takwas da rabi na daresuna abuja! Harya zuwa yanxu da mama tayi nisa a zariya ya alibai daina damunta da magiya ba.kusan kullum saiyakirata yagaya mata kalaman dayake ganin zaisatasamu nutsuwa dashi.itakuwa karatunta batawaiwaye.haka bata damu tasan kowaba indai bamaganar karatuba.matar aure sak!kowa yadauketa domin jikin littafanta da hand out duk (mrsal'ameen)tasanya saida tashafe shekara daya batadaqawa ta zama ayi hira.mutane dayawa sun buqacineman aurenta,amma in suka bincika sai a gayamusutana da aure.saboda iya takunta.yanxu suna shekarata biyu kuma suna tare da wata zainab gida daya.amma ko wacce da dakinta Allah yasani duktsawon lokacin zainab na matuqar kaunar mama.dukda cewar tasan ta girmeta saidai rashin samun hadinkan mama yasata cijewa.illa iyaka su gaisa yar asalinkatsina ce tanada kokarin kamun kai.saudayawatanazuwa aron text books.din mama don zumunci ya qullu amma ina!mama bata maida hankaliba.Yau litinin sunada masaniyar zasu (practical)ofishinbabban likita a fannin da suke karantawa.wataucutattukan dasuka shafi kai.duk sun hallara acikinclinic din dake cikin babban asibitin koyarwa nashika.su goma sha biyu ne cif!amma likita bai riga yaisoba.saboda haka mama tace zataje takai wani (assignment) kafin likitan yaxo.zainab tace karki tafikusha bam bam sakeena.kinsan doctors dinnan basuda sauqi.balle wannan bamu taba ganinsaba.tacekarki damu zainab bazan dadeba.kin karba idanlokacin yawuce ta juya ta fita ta wata kofar.kamarhadin baki ya bayyana ta kofar gabansu.ya wuce su zainab yafada ofis din.wannan ya tabbatar musushine DR SAIFULLAHI.Da aka turasu gunsa.nandanan hankalin zainab yatashi gashi batada numbanmama bare taqirata.hakanan tabi ayari suka shige ofisdin sukayi gaisuwa.ya sauqe gilas yaqare musu kallosannunku fa likitoti.duk suka fara murmushi gabansu ya rage faduwa da alama zaiyi sauqin kai.amma dukda haka hankalin zainab tashe yake. Ya miqo musu farar takarda yace musu write urnames here!wato su rubuta sunayensu.nafarko yaamsa yarubuta ya miqa wa dan uwansa amma mamabata dawoba.ya karbi takardar ya duba yana shirinajiyewa zainab tace sorry sir!akwai sauran daya batashigo ba.taje kai assignment sir.yadan tabe baki yace ko?may b assignment yafi mata wannan muhimmancishisa bata damuba.jiki na rawa tace no sir!yanxu zatadawo.mujirata kenan?tadan sunkuyar dakai tace sorrysir! Ya numfasa yace well mu bama jira haka qa'idartake.saboda mu masu ceton raine mai ceton rai kuwabaya jiran kowa kuna iya zama.kowa ya nemi wajen zama suka kewayesa yafara daga (files) kenan mamata murda kofar cikin sanda da tsarguwa tashigo.zainab taruntse ido tace thank god.!ta tako ahankali ta tsaya a gaban tebur din tace morning sir!yadago a hankali ya dubeta.kai!ta maza kawai yayiamma jiyake kamar zai zube a qasa,Ya zura mata ido,,tamkar yadda ta daskare a tsayesai dai iya takun mama yasa tayu kamar bata tabaganinsaba.tayi dan yaqe sorry sir!nakai assignmentne,pls sorry sir!ya wani sauqe numfashi bironsa nacoge bisa kuncinsa yace gaskia ba haka akeyi ba!bahaka akeyiba ni yakamata ki fara gani kafin ki tafi!.tace sorry sir! yace zauna takoma kusa da zainabtazauna tace nagode!sauran students na mamakinabunda yafaru.kalamansa na farko kwarai yabasudariya sai dai ba'ayi wa oga dariya.shiyasa suketayiacikin cikinsu.zainab ta rada mata anfa rubutasunaye.don haka suna miqewa tace sir!ni ban rubuta sunana ba ya zuba mata ido yace nasani ki zaunakawai.ta zauna a sanyaye.aka fara kiran masu ganinlikita kowacce tambaya sai yace makararriya bamuamsa!ya kuwa ji amsa.dan ko ajikinta fes take budebaki ta turance shi.duk yadda yaso ya rikirkitata.har akafara musu dariya.anan suka kai qarfe dayan rana lokacin tafiyansu yayi.Mama tasake fadin sir!my name...yace owk myname? AL'AMEEN SAIFULLAHI LAFAI.Tace sir inanufin bansa sunanaba.yace bazaki rubuta sunankibakinxo latti wannan shine horonki kinxo latti.ya juyakujera yace zaku iya tafiya.duk suka fice zainab tarada mata karta fito ta tsaya ta bashi haquri su gyarota.yasan duk sun fita amma yanaji cikinxuciyarsa tana nan.yasake wawan numfashi ya juyosuka xubawa juna ido..kafin yace mafarki nake kogaske sakina?idanunta suka tara kwalla.damuwa tabayyana qarara a fuskarta.kuma ta rasa yadda zatayikawai saita juya zata fita.ya sanyaya murya ya kirata sakeena?ta tsaya kyan !kafin ta juyo fuskar nan babuannuri.yace zoki rubuta sunanki.ta tako a hankali tatsaya a gaban teburin ta rubuta sannan tafice cikinsauri.ya lalubi kujera a hankali ya zauna fadi yakecikin ransa mafarki ko wasa? yadauko takardarsunayensu.sakeena uwais malami! Ya runtse ido tamau..kirjinsa yaci gaba da dokawainnalillahi wainna ilaihi rajiun.sakeena? yatashi da sauriyabar ofis din ya shiga wani ya murda kofa.da lawalke zaune shi kadai yana rubuce rubuce..ya dubeshi famurmushi kai likita ya akayi ne?ya zauna hankalitashe idanuwa sun kada yace yau naga abun mamaki dr lawal!ya zura masa ido cikin patients da akaturama?yace students aka turamin yau kuma nagasakeena acikinsu! shikansa saida ya girgizasakinarka?ita dr lawal gaba daya na rude ta maxanayi kar yaran su gano ni.amma bakaji bugunxuciyataba .yace dakata!a wani yanayi kaganta?da alamar akwai aure?yace matsalata kenan.bansankoda aurenba.wani abin mamaki yanda ta nunatamkar bata taba ganina ba.dan Allah?yace wlh todaaure kenan.ya yamutsa fuska kadaina gayamin drlawal please!ya zura masa ido baki sake kafin yacekai likita ka nutsu kanada abun yi ne intanada auren? ya dubi zoben alqawarinsu yace zan bincika da alamasa'a ce tadawo dani qasar nan sha Allahu sakeenatadawo gareni.Dr lawal ya numfasa!yace to Allah yasa idan kumatabada aurenta muke wannan maganar astagafurullah! katashi ne?bai amsaba yaga ya miqe yabar ofis dinyabishi da kallo ya xabga tagumi a ransa yace munshiga uku!meya dawo da yarinyar nan zata wargazamana oga?ofis dinsa yakoma tunani ya isheshi.yazanyi da rayuwata yau idan sakeena nadaaure?menene yasa ta nuna min halin ko inkula?hakanyanuna tanada aure?yayi saurin kauda wannantunanin no ba haka bane ai hawaye ya taru a idontame wannan yake nufi? yakada kai gaskia bansani ba aina zansamo gaskiayar lamarin?abufa yarikicewa al'ameen yakasa sukuni gida da ofis.har cikin bacciyake ganin mama gaban teburinsa tana fadin morningsir!kafin sati ya zagayo ya sukurkuce.haka al'amarinyake gun mama.gaba daya nutsuwa ta matatsuntsu.tun aninta yaya zatayi da al'ameen takaudaduk wani alaqa dazata shiga tsakaninsu inbata karatuba? Haka kuma abin na bata mamaki ganin har a ka'abatayi addu'a karya sake hadata dashi gashi sun hadunme hakan ke nufi?tambayar na hanata bacci.hakakota dauko hotonsa take kasa kallo saboda tsoronkarya bata amsa.zainab kanta ta lura sakeenanadauke da wata damuwa.a yan tsakanin nan tana yawan zama shiru cikin mota kafin ta qaraso gida.kocikin aji tarage bada yawan amsoshin da datakebayarwa.abin yadameta sai dai bazata iya tunkararsakeenaba ganin ba fuska.kuma tana kwarjini.kamarko wacce litinin yau ma tazagayo clinic din masufama da larurin kai qananan yara.ranta bace tashigo gun.zainab na lura da ita.tunda suka shigo bata yardasun hada ido da al'ameen ba.dan ko gaisuwardasukayi cikin jam'i bata tankaba.ya tura musutakarda yace kowa yasa hannu wato signing Bayan sun kammala aka fara shigo da masu jinyayariyar sunanta sakeena ahmad file nata na tsakiayasa aka dawo dashi sama albarkan sunan akafarakiranta bayan mahaifiyar yarinyar taqare bayanintaakan ciwon yar(convosion) kasen cewar zuwansuclinic nafarko.sunja tsawon lokaci tana amsa tambayoyi daga dr.tashin farko mama yafara jefawatambaya,sakeena tunda sunanku daya kezaki faracewa wani abu!karo na farko datayi masa duba tadauke kanta.da turanci suke magana.ki bayyanamana me ake nufi da suma? da abinda ke kawota?tayishiru kamar bazata tankaba bawai dan bata saniba sai dan jin haushin fara kiranta da yayi.ganin ya zubamata ido yasa tafara zazzago masa bayanai yadda yakamata.yace bai gamsuba.wazaiyi bayani wandayawuce na mama?ya kallesu daya bayan daya inafatadai da likitoti nake magana?93-duk suka amsa yes sir"banda mama yace to kuyimagana mana kuna nufin kunfi yarda da sakeena?Suka fara sosa keya suna kallon juna ya tabe bakiyace wannan son kai ne'su kayi yar dariya mama takirne zainab ta daga hannu tace sir zan dan kara yacego ahead ta kara wasu yan bayanan masu kama dana mama ya dube ta yace muntafi mun dawo ke nan kunfini gaskiya to bari mu ci gaba kar mu bata lokaci ko?yaci gaba da bayanai da tambayoyi har lokacin tashiya yi karfe daya daidai suka sallame shi tare dayimasa godiya cikin karfin hali ya nuna zainab yace tatsaya yana son ganinta na minti daya kawai duk suka fice suka barta tana yan mazurai gaban ta nafaduwa.sun dan jima shiru yana wasu yan nazari kafinya dubeta yace ke ce zainab tace yes sir yaceuhm...ko kina da alaka da sakeena tace eh sir gidanda muke ma daya ne,94-yace good don Allah ko kin san tana da aure kobata da shi? tace uhmm..toni dai gaskiya ban sankomai game da ita ba amman da alamu tana da auredon jikin littattafan ta ma ni kan ga tana rubutawakoga wannan pharmacology din ma na ta ne"ta mikamasa ya bude shafin farko ya duba "mrs al- amin? Ya tambayi kansa ya dube ta da sauri kin taba ganinsaya zo gunta tace wallhy ban sani ba ta kan sami bakiamma da yake ba wata mu'amala take da kowa bashiya sa ba zan iya tantancewa ba ko yana zuwa yasauke numfashi yace zainab idan bazaki damu ba kigaya min inda kuke ki kuma bar min littafin nan tace shi ke nan sir nan take taba shi adirea ta bar masalittafin ta fice dauke da wasi wasi mai yawa cikinranta,ta tabbata oga ya kamu ne to amma zai shaguduma muddin ya tinkari sakeena fargabar ta dayace karbar littafin nan a hannunta mece ce manufarhakan?Allah yasa ba amfani zai yi dashi ta wata hanyar ba don ya cimma burinsa yasa jawo matabakin jini su daina gaisawa da sakeena babu abindabata sakawa ranta ba. Haka mama ta sha jinin jikintatunda taga. al-ameen ya tsaida zainab sai dai batafargaban komai don ta san zainab bata san kamai baa game da ita ba shi yasa hankalinta kwance ta isa gida tayi fakin motar ta cikin inuwa ta fito ta budebangarenta ta shige ta mayar da kofa ta kulle bayangabatar da sallah ta danci abinci ta maida kai bisa filotana ta sakar zuci game da sake haduwar ta da al-ameen, a haka barci ya sace ta har zuwa uku da rabita farka ta nufi bayi ta fito da alwala ta gabatar da la'asar daga nan ta kawo azkar ta dora kai tsayelittatafanta ta kwaso don yin wasu aiyukan gida daaka basu cikin wayar ta take. Ta birauzin ta yanargizo duk ta kosa ta gama don karfe biyar take dawata lakcar Babu zato taji an kwankwasa kofar ta ta dago kaita dubi kofar tace ana zuwa ta karasa dan rubutun datake yi ta taso ta murda makulli ta bude kofa gaban taya yanke ya fadi tabi mutumin dake tasye da kallo tadafe kirji tace inna-lillahi wa inna ilaihir raju'un tace niya ce ni kuma nace Assalamu alaikum ta hadiye miyau da kyar taamsa sallama dole yace zan iyashigowa? Ta tsaya jim kafin ta koma gefe ta bashiwuri ya shigo ita kuwa tana daga tsaye a bakin kofabata motsa ba shi ma bai zaunaba ya zuba mata idoyace ya karatu tace lafiya yayi dan murmushi yace ".mrs al-ameen ke nan ta kara dubansa a razane amma ta kasa cewa komai ya kara matso ta ya sake fadinkin taba ganin aure babu zoben alkawari? Ya nuna nayatsan sa kinga nawa nan bai taba rabuwa da yatsanan ba saboda muhimmancinsa sannan ban tabaganin inda mata ke gudun mijin bs idan da amana airuwa za zai dafa kifi ba mama ya kamata ki maida zoben ki kafin mu ci gaba da tambayar bayan rabuwa!Ya laluba aljihun sa ya fiddo shi cikin gidan sa yabude ya ciro shi tun daga lokacin. Idanuwan ta sukafara tara kwalla kirjinta kamar zai tsage tana tsayesototo har ya kamo yatsunta da zoben yake ya maidashi mazauninsa shi kan sa kwallan ne cikin idonsa yayi ta maza ya hadiye su yayi murmushi yacegodiya ta tabbata ga Allah daya nuna min wannanrana amma zai fi kyau ki zauna sakeena inji kalamanbakin ki, tace Al-ameen kazo ka tafi yace in tafi waisakeena laifin me nai miki ki ka daina so na ne tacenace ka zo ka tafi yace bazan tafi ba sakeena sai kin gaya min dalilin da yasa ki ke amfani da suna na amatsayin mijinki alhalin ba kya sona ki gaya min inji, ta zuro masa ido kwalla suka fara zuba" ni nayiamfani da sunanka?ya daga littafin dake hannunsashafin farko yace mene ne wannan? Idan kuma kinamusu ki kwaso gaba daya (texs book) din ki dahandout a duba takara razana rashin gaskiyarta yabayyana karara bakinta ya mutu kwalla suka ci gaba da zubo mata ya sanyaya murya yace. Sakeena kinsan ina sonki munyi wa juna alkawurra masu damaban taba tunanin zaki yaudareni ba har kwanan gobekuwa ba na kawo hakan a raina ni na san yanzu kinwarke kin dawo cikin hayyacinki sosai tunda har ki kagane ni ne mijinki,amma me yasa da aurenki ya mutu ba ki nemeni ba ki ka barni ina wahala? Nayi rantsuwako ki duke saboda tsufanki sonki bazai shafezuciyata ba kuma zan karbe ki a matsayin matardana fi so a rayuwata. Dubi. Zoben nan sakeenagirman dana karayi yasa ya yi min kadan ammasaboda ba zan iya rabuwa dashi ba na kai shi aka yanka min na kara bude shi ina sa shi a haka dubenisakeena har yanzu al-ameen dinki ne sak babuabinda ya sauya kar kiji nauyi ko kunya kin kini abaya wallahi ban daukeshi a matsayin laifi ba muddinki ka amince min zan baki mamaki!, Ta goge kwallata ce banyi aure ba al-ameen karuwanci nayi kuma da diro har ciki na haihu cikin dana zubar kuwa ban sanadadinsu ba me za kayi dani me zai sa in ne mekabayan cin amanarka,amanarka kuma ta cini me zakayi da kazama irina? Ni abar kyama ce ni kaina nasan ni najasa ce balle wani,koba ka jin warin.... Ya daka mata tsawa ya isa haka sakeena ta cebai isa ba dole in bayyana maka ko ni wace ce don katabbatar da cewa babu abin sha'awa a tattare danikyan dan maciji gareni idan kai ba ka jin warin danake ji ni na san ina yi kuma....bai san lokacin da yaciro hannunsa ba ya dalla mata mari duk suka dauke wuta ita da shi,tana tallabe da kunci ta zuba masa idoya nuna mata yatsa fuskar nan kaman gobara yace kidaina ci min fuska sakeena....!ya kasa kara komai saiya kama hanya ya fice cikin sauri ta sulale kasa batasan lokaci da ta fasa kuka ba ji tayi an rungumeta tamurya mai sanyi na fadin sakeena! Sakeena mene ne ta cira kai ta dubi mai magana Zainab ce ke tallabe daita ta kasa magana sai kuka takeyi hankalin zainabyayi mummunan tashi don taga shigowa da fitar Dr al-ameen cikin ranta. Tace na shiga uku Allah yasa bani na haddasa wannan fitinar ba hakan yasa ta damukwarai taji musabbabin kukan da mama takeyi, ta kwashi lokaci tana rarrashinta kafin ta shawo kantatayi shiru amma hawaye basu daina sauka basakeena kina cikin damuwa ni tuntuni na san hakaamma Allah ya zuba miki zufin ciki na kasance inamatukar kaunarki sakeena zan si ki gaya min keketsakaninki da Dokta yake neman wasu bayanai da suka shafe ki, Ta goge kwalla ta kadai kai tace ke yatambaya tace gaskiya ni ce amma na gaya masa kinada aure harna bashi littafinki da ki ke rubuta sunanmijinki don ya tabbatar kiyi hakuri in ni na haddasamiki wannan fitinar sakeena banyi zaton zai zoba donna tabbata gaskiya na gaya masa tace bakiyi laifi ba zainab hasalima shi ne al-ameen din....98-Ta kara dubanta a razane what? Nan da nan tagaggauta tuna baya ranar da ta fara shigowa ofishinirin razanar da suka yi na ganin juna da yaddasunanta ya zauna bakin sa haka tabbas ya fadicikakken sunansa sunji, ta sake dubanta tace damaoga ne mijinki sakeena ? Kai amma kinyi sa'a me yasa ki ke gudunsa kuma da alama kun dade rabonkuda juna tace ban aure shi ba zaina amma munyisoyayya ta ban mamaki mishkilar da aka samu ita ceboyayyen labarina wanda ya tilasta min maida kainadodanniya ga kowa musamman da namiji, cikintausayi tace Ayya koda ban sani ba na tausaya maku ta goge hawaye haka idan kika ji baza ki so in rabikowa ba rayuwa ta za tafi min kyau ni kadai dongudun abinda kaje ya dawo" ta kara rungumota tace kidaina kuka sakeena rayuwa ita shirin Allah ce dukyadda ya tsaro maka baka iya tsallakewa yanzu bagashi ya wuce ba? Tace ai ya dawo tunda al-ameen ya dawo rayuwa ta ni kuma bazan iya auren sa ba ke kosabo dame shi ya miki laifin? Ta kada kai bari kiji agurguje take nan ta bayyana mata yadda rayuwarta takasance a baya Tuni zainab ke kuka har da shashekatace sakeena kinga rayuwa Allah ka rabamu dasharrin mutun da aljan tace amin zainab to kin ga ina ni ina aure? ba komai nake gudu ba gori yanzu al- ameen ya daukeni ya hada da matarsa idanbatakwarai bace duk ta yadda zatayi ta binciko asalinazata yi don ta muzguna min ba zai yuwu ba zaina bazan iya jurewa ba dole in nemi. BAKIN CIKI 3***9 yace karki damu zainab duk inda take yau zandawo da ita bazatabar karatunta saboda ni ba!ya juyaya fada mota kai tsaye ya dauki hanyar kaduna yatabbata bata wuce gidan yayanta Abdurrahman ko datambaya zai kai kansa gidan tunda yasan anguwar. Awannan lokacin ita mama ke shiga get din gidan yayi fakin ta fito jaye da jakarta ta kwankwasa kofa akabude takwararta ce tabude nan da nan ta rungumetaanti mama oyoyo tace oyoyo name sake ina su ihsansai gasu sun kwaso a guje suka rungumeta dukkansukayan islamiyyar da suke zuwa ne a jikin su tace haladaga ismaliya kuka dawo yanzu suka amsa eh safiyya ta fito daga kicin ta tarbeta maraba da doktakece haka da almuru ina fatan dai lafiya tace qalaumatar yaya suka wuce da jakarta cikn daki basugama gaisawaba aka kira sallah duk suka tashi yinalwala ta kai raka'a daya ta jiyo muryar yayanta yanafadin naga motar mama a waje ta zone safiyya ta amsa ta zo gab da magariba magariba lafiya tacehaka dai tace wai gobe ma abuja zata wuce yayi danmurmushi yace mama manya kwadayin ganin abbane ya motsa tana ina tace tana sallah ne suka wuceshima yayi alwala yayi sallar ya fito ya samu mama afalo da y'ayanta bayan sun gaisa ya tambayeta babu karatue kika baro school tace eh dan break mukasamu gobe da jibi shine nace bari inje inga Abba yacekin kyauta amma abba ya hanaki ki tuko mata zuwawani gari ko?me yasa baki kira an turo miki direbaba?kuma ance gab da magariba kika iso tace sorryyaya na kosa in taho ne yau din don in kwana biyu a can, 104- yayi yar dariya yace to Allah ya kaimun gobenlafiya sai in nemi mai tuka miki motar muje cin abinciko duk suka nufi tebur inda safiyya ta shirya gara kalakala suna cin abinci suna hira mai gadi yayi sallamaya shigo yace ana sallama da mai gidan babu batalokaci ya aje cokali ya fita yana tsaye jikin motar sa daga wajen gate yaya Abdul rahman yayi sallama yaamsa ya dan zura masa ido kamar ya taba ganinfuskar ka gane ni yayayace kamar na san fuskar dadaewa yayi dan murmushi yace al ameen ne ya kamabaki kana nufin dokta. Ni ne yaya yace ikon AllahAllah bisimillah shigo da motar yace kafin nan yaya ina fatan sakeena na nan gidan? ya numfasa yace tananan shigo,yasa mai gadi yabude get ya shigo da motarsa.ya jagoranceshi zuwafalon gidan.gaba daya suka shigo da sallama.hankalinsu ya koma kan bako.zumbur mama ta miqe dafe daqirji ta zaro masa ido jim! Sannan ta zura da gududaki hawaye na fita.safiya ta cika da mamaki.a haka suka wa baqon sannu da zuwa suka gaisa.yara masuka gaisheshi.suka dauki abincinsu suka wucedakinsu.ita kuwa safiya kicin tashiga ta hado wa bakokayan kusa da baka.yayinda suke gaisawa da yayaabdulrahman.amma mamaki ya ishen fa.wai yaya ne?takenan ya fede masa biri har wutsiya.yayan yace Allah mai girma da daukaka.tsarkakakken sarki maishirya yadda yaso.inbanda abin mama meye na boyemin?zan mata dole ne?saidai in nuna mata abundayakamata idan ta dauka ya yi mata kyau.idan batadauka ba laba'asa.amma zancen tabar karatu mabaitasoba.105.Yace nima abinda nagani kenan.don me zatabarkaratunta? hankalina yatashi dana koma akace tataho.shiyasa nabiyota inbata haquri.ta komamakaranta bazan zama sanadiyyar rasa komainataba.nasan ina matuqar sonta zanci gaba da jurewakuma bazanyi dana sani ba!idan na mutu akan sonta.pls yaya ka kirata na roketa,tazo mukoma kardare yayi.gobe in Allah yakaimu taje lakcasdinta.bana ma so abba yaji.maganarnan .don karya cezai tilasta mata.yaya yayi shiru jim! ya sauqenumfashi ina zuwa.ya miqe ya bita dakin.tana ta rusakuka kamar an aiko mata da mutuwa.duk ta dagawa safiyya hankali ta riqeta tanaso tamata bayani ma yagagara.sai fadi take ni bazan aureshi ba.yazaunagefenta yace to wayace dole ki aureshi?da kikazo nankika rufe min abinda yafaru.kina ganin shinemafitarki?to shima baya biyoki bane donya tilastamiki aurensa!soyake yamai dake makaranta.kici gabada karatunki.saboda haka kitashi kije ki sauraribaya ninsa..idan harkika yarda kika koma makarantanamiki alqawarin ko abba bazaiji maganar nan,Na miki alqawarin ko abba bazaiji maganarba.balleyasan al'ameen na numfashi.tashi kije sharehawayenki.safiya ta goge mata tace dama wannan nematsalar?to ta wuce tunda shima ya haqura.miqe kijekarki barshi zaune.ta yunqura da kyar ta mike sukabita da kallo.yayanta ya numfasa ya dubi safiyya data zabga tagumi yace idan kuwa har mama bata yarda taauri al'ameen ba lalle babu wanda zata aura aduniyarnan!tace ko?yace gaskia safiya yadda mamataso al'ameen banjin antaba soyayya irin tasu.keqarshen abin dubi yanda akemata kallon ta lalaceshibai damuba.zanso su daidaita da al'ameen saboda ina sha'awarsu tare.tace ubangiji ya sa hankalintayadawo jikinta tagane muhimmancin auren da zatayiya amsa da amin.salalau salalau tashiga falon tayitsaye kanta na qasa tana share hawaye.ya zuba mataido jim!kafin yace ki zauna mana. Yace nima abinda nagani kenan.don me zatabarkaratunta?hankalina yatashi dana koma akace tataho.shiyasa nabiyota inbata haquri.ta komamakaranta bazan zama sanadiyyar rasa komainataba.nasan ina matuqar sonta zanci gaba da jurewakuma bazanyi dana sani ba!idan na mutu akan sonta.pls yaya ka kirata na roketa,tazo mukoma kardare yayi.gobe in Allah yakaimu taje lakcasdinta.bana ma so abba yaji.maganarnan.don karya cezai tilasta mata.yaya yayi shiru jim!ya sauqenumfashi ina zuwa.ya miqe ya bita dakin.tana ta rusakuka kamar an aiko mata da mutuwa.duk ta dagawa safiyya hankali ta riqeta tanaso tamata bayani ma yagagara.sai fadi take ni bazan aureshi ba.yazaunagefenta yace to wayace dole ki aureshi?da kikazo nankika rufe min abinda yafaru.kina ganin shinemafitarki?to shima baya biyoki bane donya tilastamiki aurensa!soyake yamai dake makaranta.kici gabada karatunki.saboda haka kitashi kije ki sauraribaya ninsa..idan harkika yarda kika koma makarantanamiki alqawarin ko abba bazaiji maganar nanba.Na miki alqawarin ko abba bazaiji maganarba.balleyasan al'ameen na numfashi.tashi kije sharehawayenki.safiya ta goge mata tace dama wannan nematsalar?to ta wuce tunda shima ya haqura.miqe kijekarki barshi zaune.ta yunqura da kyar ta mike sukabita da kallo.yayanta ya numfasa ya dubi safiyya data zabga tagumi yace idan kuwa har mama bata yarda taauri al'ameen ba lalle babu wanda zata aura aduniyarnan!tace ko?yace gaskia safiya yadda mamataso al'ameen banjin antaba soyayya irin tasu.keqarshen abin dubi yanda akemata kallon ta lalaceshibai damuba.zanso su daidaita da al'ameen saboda ina sha'awarsu tare.tace ubangiji ya sa hankalintayadawo jikinta tagane muhimmancin auren da zatayiya amsa da amin.salalau salalau tashiga falon tayitsaye kanta na qasa tana share hawaye.ya zuba mataido jim!kafin yace ki zauna mana.106-Ta nemi wuri ta zauna ya numfasa ya karamatsowa gareta ya sanyaya murya yace sakeena nasan na tafka kuskuren daukar hannu na mareki inarokonki ki yafe min kuskuren danayi amma ina so kisanu ba laifi na bane miyagun kalaman da ki ke jifarkanki dasu sune kunnuwa na baza su iya ji ba, zuciya ta baza ta iya daukar girman kalaman da bakinki yakefurtawa ba maganganun sunyi muni a ido sakeenadon girman Allah kar ki sake danganta kanki da irinwadannan kalaman don ba su kamace ki ba maganata gaba da nake so ki sani sakeena itace tun farko nine nayi sanadiyyar rushewar komai naki burin ki dana iyayenki shine ki zama likita Amma na cusa miki sona ki ka dauki dukkan ra'ayinaki ka bar wanda su abba suka shirya miki ba ki dawani buri face aure na nayi ruwa nayi tsaki dole kikirani in dawo muyi aure kafin ki fara karatunki ki kaamince min a karshe wani ya sami damar dagulalissafinki ya rushe komai ya lalace ni ne silar rugujewar komai naki sakeena saboda haka a yanzuba zan sake zama sanadiyyar barin karatun ki ba.Ta goge kwalla ta dube shi na yan sakwanni kafintace na amince ya sauke numfashi yace na godeamma ina so in roki alfarma guda biyu bata dainakallonsa ba tace zan amsa maka idan masu yuwuane yace ki amince zaki bar zobe na a yatsanki kiamince zaki ci gaba da amfani da suna na a matayin mijinki da gudu wani hawayen suka zubo bisakuncinta ita kanta bata san dalili ba haka murya takerawa tana fadin suma na amince maka idan har bazaka taba nuna kai ne al-ameen ba da sauri ya amsabazan nuna ba i promise yau babu wanda zai sani drlawal ne kadai. Ya sani kuma zan kwabe shi ya rike min sirri amana,108-tace shike nan", zamu iya tafiya yanzu tace bariin tambayi yaya suka mike tare shi ya zauna a kujeraita ta wuce kiran yaya. Yaya abdul-rahman yaso sukwana da sassafe suyi sammako amma al- ameen yanuna ya fison su tafi saboda haka dole ta bar motar tagoben direbansa zai kawo mata suka kama hanya karfe takwas saura yan mintoci sun jima shiru a motababu wanda ya tanka shi al-ameen bakin ciki ne yacunkushe zuciyarsa yana tunanin yadda zai sarrafarayuwar ba tare da abinda yake so ba alhalin yanaganinta kusa dashi ita kuwa mama tausayinsa ne yahana mata magana harga Allah ta san al-ameen karfin hali yake yi kawai shiyasa bata so sake haduwarsuba sauke numfashin da yayi shi yaja hankalintazuwa gareshi ta dubeshi yana kada kai gwanintausayi jikinta ya kara sanyi tayi shiru tana tunaninme zata ce masa? Ya dan sanyaya ransa jim kadanta sake dubansa tace yaranka nawa kamar daga sama ya ji tambayar don haka ya dan dubeta sukahada ido ta yi dan murmushi shi yasa shima ya daukekansa yana murmusawa kafin yace yarana dozin Ido waje take kallon sa kai dokta dozin fa ka ce ?sunyi yawa ne tayi yar dariya tace naji abin ne kamarna debo su a kasuwa don Allah yaranka nawa yacebiyu ne....ta yi fit ta katse shi Ameer da Ameera ko?Ya dan dubeta ya kadai kai waleed da waleeda tace azatona mafarkinka kullun ka sami ameer da ameera me yasa ka sauya ra'ayi tai masa susan inda yakemasa kaikayi kai tsaye yace kin san yadda mafarkiyake. Ba kasafai yake zama gaskiya ba,109.Ta sunkuyar dakai shiru shima shirun yayi kamarbazai tankaba.sannan yace tun ranar dana daina jinmuryarki a waya na tsinci kaina cikin wani hali dabazan iya misaltawaba sakeena!da taimakon Allah dataimakon mamina nasamu yar nutsuwa.hankalina yadaidaitu akan qaddarar data sauqo min.bayan narasa ki nakoma rasha.can na kwashe shekara hudu banwaiwayi gidaba.sai dai inkira waya.a cikin shekara tabiyar goggo ta rasu mafarin zuwa na gida kena(inbakumanta ba goggo itace kakarsa daya fara haduwa damama a kofar gidanta farkon littafin)shima saidan nakwashe sati biyu nasamu zuwa.iyakata minna wajensu daddy nayi sati daya adaddafe nacezankoma.mami tace bazan komaba saina fidda mataraure.nace banda wadda nakeso alokacin suyi minuzuri zuwa wani lokacin.109-ta sunkuyar da kai shiru shima shirun yayi kamarbazai kara tankawaba sannan ya ci gaba tun ranardana daina jin muryanki a waya na tsinci kaina cikinwani hali da bazan iya kwatanta shi ba sakeena dataimakon Allah da taimakon mamina na sami yarnatsuwa hankalina ya daidaitu akan rungumar kaddarar da ta sauko min bayan na rasaki na komarasha can na kwashe shekaru dudu ban waiwayi gidaba sai dai in kira waya acikin she kara ta biyar Allahya dauki ran gwaggo mafarin zuwana gida ke nanshima sai da ta kwashe sati biyu na sami zuwa iyakata minna wajen su dadi nayi sati daya a daddafe nace zan koma mami tace bazan koma ba idan har banfidda matar aure ba nace banda wacce nake so alokacin suyi min hakuri zuwa wani lokaci Duk suka hade min kai sukace atabau basuyardaba.akan dole na basu zabi,,dan na farantamusu.ba ayi kwana ukuba dady yasamo min yarabokin kasuwancinsa a suleja sunantaruqayya.dakansa yadaukeni yakai ni gidan.tsakani daAllah ruqayya batada makusa amma saboda hankalina ba a kanta yakeba naji raina yanabaci.zucita namin sake sake akan alqawuran danadauka miki.wlh sakeena bantaba kawo wa rainakindena sonaba cikin raina.shiyasa nakasa kallonruqayya a matsayin matar dazan aura.saidai bandenabin umarnin su daddy ba har akasa mana rana.cikin watanni biyu aka daura aure.batare da munfahimcijunaba.saboda rashin kulawa irin nawa.dukda nasanita ruqayya nasona.kumatana iya qoqarinta wajennunamin ta amince dani bawai hadamuakayiba.tausayi takeban idan na kalleta na tuno babualamar sonta cikin zuciyata.110 Bawai rashin sobane yahanani rabarta a matsayinmatata ta sunna ba.a a tausayin danakeji shikehanani aganina ban mata adalciba.idan natabata alhalibabu soyayyarta a zuciyata.abun yadamen kamaryadda na lura itama tanada damuwa cikinzuciyarta.amma son xuciya ya hanani magance matsalar.ruqayya nada kunya kuma duk abinda ta lurainaso zata ce gashi basai na tambaya ba.munkwashe sati biyu a haka nafara shirye shiryenkomawata rasha.saidai su mami sunce inbar musu itaanan dan indinga waiwayen gida akai akai.darendazan koma bansa ruqayya a idonaba.amma naga duka kayana ta kimtsa min cikin jaka sai da jikinayayi sanyi danaga jakan tsaf ashirye.Na fita naje wajen su mami nayo hira na dawo misalintara da rabi na iske ruqayya tanata rusar kuka cikindakin,duk iya sallamata bataji shigowata ba.nimaganin banji motsintaba yasa na tura qofar naleqa.gaskia gabana yaafadi ayadda naganta.dasaurina qarasa na zauna gefen gadon nayi kiranta ruqayya! take naga ta dauke wuta taqara tusa kai a filo nacemeyafaru? ta amsa ba komai.nace babu komai ayitarafsa komai? kigayamin danna tabbatar bani na batamikiba..tayi shiru nace tashi ki zauna.nanda nan tabiumarni na.gayamin abunda yasaki kuka.ta sunkuyardakai idan ka tafi yaushe zaka dawo?na zura mata ido saboda mamakin wai tafiyata ce tasata kuka.atunani na da xama na da rashinsa duk zai iya zamadaya agunta ashe ba haka bane. To mezaisa nakasazama adali agareta? Tausayinta ya lullubeni idanuwa na suka tarakwalla bansan lokacin danakai hannu na kamotabanace ruqayya!ta dibeni da kyar muka zurawa juna idotsawon lokaci kafin ince shi ne kadai matsalarki?taamsa dakai.nayi murmushi nace ai bazan dadeba komutafi tare? tace aiba ka shirya hakanba ko?nace hakane kiyi haquri sai na sake dawowa.kinji?ta kallenitanadan murmushi tace nayi!tundaga lokacin natabbatarwa ruqayya cewa kyakkyawar tarbiyarta tajawo mata wani matsayi a zuciyata! daren dazan tafiyazama daren da ban taba mafarkinsaba da ita.natafinabarta cikin wani yanayi da bazan iya gayamiki ba.ko ni na dade ina juyayi nakasa mance ruqayya daalherin dake tattare da ita.amma duk sanda na runtseido ke nake gani.wata guda bayan tafiyata ruqayyatafara rashin lafiya gwaje gwaje ya tabbatar tanadauke da juna biyu.al'amarin yadaure min kai ikonAllah kenan.zuciyata ta qara sanyi akan qaddarar al'amarinmu.kuma na tabbata su mami na rokon Allahakaina.cikinta na wata shidda .112.Taqi samun lafiya saboda haka na wuce da itarasha.tasami ishasshen binciken da sakamakonsayadagawa kowa hankali.cancer aka samu amahaifarta nida kaina saida na zubda kwalla.sabodatausayinta.nan na barta a asibitin danake aiki hartahaihu gaban kwararrun malamaina.dukda haka dakyar aka samo ranta.babynmu kuwa qaton gaske ba indayabaro ni sakeena.ta waya mukayi maganar sunadasu mami nace sunan yaro abdulrasheed.su nanmahaifin ruqayya.abin yabasu mamaki saida mami tatambaya donme bansa sunan dadyba?na nuna matakawaici nayi dan faranta mata rai.bayan ta warware a asibiti muka dawo gida nigeria akayi shagalinsuna.aikuwa iyayenta sunyi murna akan sunandanasa kaya akwati akwti abbanta yayo masa nannabarsa nakoma rasha.tana samun kulawa a gidansutare da shan magunan cutar dake jikinta.wanda likitotidani kaina na tabbatar hatsari ne sake haihuwarta nan gaba dalilin dayasa kenan muka shirya planning doledan ceto lafiyarta.bamu rasha bamu nigeria sabodakwarewata a fannin daya shafi kai,Ko'ina ana gayyata ta muna zamanmu lafiya daruqayya tsawon shekaru takwas ba a yiwa waleedkani ba saboda tasoron abinda kaje ya dawo kuma balaifi kulawar da take samu ya taimaka kwarai wajeninganta lafiyar ta a gaskiya ruqayya mace ce takwarai saboda a dalilinta ne na gane hali yana sawa a so mutum ko a tsane shi zama na da ita ta samar mindukkan farin ciki iyakar kokarinta kuma na gamsu datarbiyarta amma koda sau daya na kasa furta kalmarso gareta duk lokacin dana dubi fuskarta da nufintabbatar mata da soyayyata gareta sai in ga fuskarbata wadda nake mafarki kullun bace,kwatsam cikin wani hukuncin na ubangiji wani cikin ya bayyana ajikin ruqayya,tun kowa bai sani ba daga ni sai ita nacea zubar dashi don kar sa mi matsala nan gaba ammamezai faru ruqayya tace atabau bata san wannanzancen ba raina ya baci a zatona hakan zai sa ta barina aiwatar da abinda nake ganin zai tsirar da lafiyar ta Sai daii abun mamaki Ranar dana diro kasar na sha fada wajen mami kwaraita nuna min bacin ranta saboda halin ko in kula da nanunawa ruqayya dalilin da yasa kenan dana koma nakira ta daki na ta sameni ta zauna bakin gado gadadaya ta rame sai katon ciki gabanta na kare matakallo na kada ka nace saboda Allah ruqayya kin ga yadda ki ka dawo kiri kiri ki yi wasa da rayuwarsaboda me? Ta kare min kallo kafin tace me zai saAllah ya bamu kyauta muce ba ma so me yasa zakudage akan cewa wannan cikin zai iya zama ajalinakuna nufin kun fi wanda ya bani cikin sanin abinda yadace,114-da sauri na katseta ruqayya...."Itama ta katse nizan mutu koda cikin nan koba bu shi muddin kwanakina suka kare dokta amman ka dauki karan tsana kadora min akan laifin da bani nayi shiba nayi zatonzaka tausayamin ka dauki laifin ka dora wa kankaganin komai ya faru daga gareka ya fito sai ka juya bin baya ka nuna min tabbas hadamu akayi Allah yayi aurenmu badan ka so ba,, ban san lokacin da narufe bakin ta ba nace ba haka bane ruqayya pleasekar ki dauki maganar nan ki kai ta in da bai dace banasan nayi kuskure ki yafe min don Allah idonta yacika da kwalla tace ya wuce dokta kullum burina in faranta maka rai don kar kogin soyayyar da yacinyeka ya samu damar hallaka rayuwarka gaba dayana zura mata ido dauke da mamaki na ce ya akayikika sani? Tace iya taban labari tun lokacin zamantaa waje na jegon waleed tun daga ranar na kara azamabana fashi kuma ba na sanya akan duk wani Bakin ciki daka shiga Barin cikin nan yana daya daga cikinhanyoyin. Dana zaba na faranta ranka dokta na sankona mutu idan ka kalli abinda na bari zakaji dadi harka tuna yi min addu'a ka taso kai kadai cikin gidankubai kamata ace kaima ka rayu da Da kwaya daya batace ina ji ina gani a kashe maka karin da Allah ya baka ina fatan kaima zaka dubi uzurina ka dainaganin laifina? Kai ban taba jin kalaman da suka ratsani ba tun rabuwar mu dake sai a ranar ban san tsawonlokacin dana kasance rungume da ruqayya ba idokuwa taf da hawaye kaunarta na ratsa ko'ina a jiki naduk da ban iya furta mata ba na tabbata son ta ya kamani baki na ne kawai ya kasa fadi,115-mun raba dare muna. Faranta wa juna rai washegari nayi shirin tafiya. Sakkwato in da zan gudanar dawasu aikin fida cikin kai burina in hanzarta kammalaayyukan da zanyi a nan sai in dauketa mu komarasha tare don ta haihu a can wata kila a dace tatsallake siradi, sai dai shirin ubangiji yana gaba da mu a ranar da na wuce sakkwato a daren na sami wayana kai ta asibiti nakuda ta zo hankalina ya tashikwarai da gaske ga shi tiyata biyu ke gaba na daya adaren zamu shiga dayan kuwa sai da safe ni dai aikinnan nayi ne kawai Allah dai ya bada sa'a bamu fito basai karfen biyun dare ina fitowa na kunna waya ta mami na fara nema cikin daran nan jim kadan naji tadauka nace mami yaya ruqayy,?tace ruqyyaalhamdulilahi ta haifi ya mace wajan sha biyun dare tadai ji jiki amma an gode Allah tunda da gata a kwancetaba bacci na sauke numfashi nace lallai Allah abingodiya ne to Allah ya kara mata lafiya ya amfana abinda aka samu tace amin yaushe. Zaka dawo na cein sha Allahu gobe zan dawo muna fitowa aikin dazamuyi tayi min kyakkywar addu'a muka kashe wayana kwanta na kasa barci ina tunanin kalaman ruqayyaina sallar asuba na sake kira mami ta hadani da itamuryar ta a shake tayi min sallama na ansa cike da fara'a mai jego to ya jikin ki tace lafiya lau kintabbata? Tace zazzabi ne kawai ke damuna nace zaibari in sha Allahu ya bebina ina fatan dani take kamatace kuma shi ke nan kai kadai zaka cinye gidan?Nayi dariya sosai nace kina kishi ke nan to ya zakiyiidan na cinye gidan.... tace me kuwa amma idan aka raba ai zai fi amisali in na mutu baza ka rinka ganin me kama daniba Nace yanzu me ya kawo maganar mutuwa bayankin fimu gaskiya Allah ya nuna mana ikonsa tayimurmushi tace hakane to yaushe zaka dawo naceyau yau din nan da yardar Allah badan ma aikin gaggawa zamuyi ba dana biyo jirgin karfe bakwainazo na ganku tace Allah ya kawo ka lafiya na amsada amin mun jima muna waya ta ita tana min dariyawai. Bebyn tayi kama da ita,karfe takwas muka shigatiyata banmance wa akwai wani mutum ne da wasujijiyoyinsa ke hardewa ta bayan ke yarsa suka dinga haifar masa da matsaloli masu yawa awowi bakwaimukayi kansa muna aiki don bamu fito ba sai karfeuku na yamma na hanzarta sallar azahar na dan kirala'asar ta karasa yi itama na mika ta kai tsaye wayata na zaro na kunna na nemo lambobin ruqayya najitaa kashe saboda haka ns nemo ta mami hankalinta a. Tashi naji muryarta kamar mai kuka tace al-ameentun dazu nake neman wayarka a rufe ya mata ka tahojikin ruqayya ya rikice bata san halin da take ciki ba,jiki na ya dauki rawa nan da nan zufa ta fara ketojikina ban jin na cewa mami wani abu ba kashe wayarkawai nayi na bazama wajan abokan aiki na na gaya musu halin da iyalina ke ciki take nan suka kai ni filinjirgi yan mintoci ya rage jirgin danayi bukin ya tashilokacin na cika ya kwashe mu ya aje minna ya wuceabuja tundaga nan na dauki shata har asibitin inatambaya aka nuna min dakin haihuwa na doshi dakingaba na bai daina faduwa ba da ka ganni kasan bana cikin natsuwa mami na fara hangowa,117-kamar kuka take yi na rage sauri ina zare idosannan na gane kowa na wajen kuka yakeyi na matsana zurawa mami id nace mami da dago ido ta dube nita kara fashewa da kuka ya jikinta sai ga dadi tare daabban ta suka fito daga dakin na nufi gunsu inatambaya don su ma babu alamar natsuwa a jikin su abban ruqayya ya kamo kafada ta ya jawo ni gefeyace kayi hakuri al- ameen ruqayya babu ita kaina yasara yayi gingirin duk da na saba ganin mutuwa iri irisai yau naji ta sabuwa zuciyata ta buga komai nawaya daina aiki tsawon lokaci ina kallon abban ta bancekomai shi yaja hannu na. Zuwa dakin dadi ya biyo bayan mu tana rufe bisa gadon ta yasa hannu yabude min fuskarta na kafa mata ido yanzun nan tacika da kalmar shahada al-ameen don Allah kayihakuri kayi imani da hukuncin ubangiji Inji abbanta,,innalillahi wa inna ilaihi rajiun..gabadayanarikice kamar ba likita ba.nidai bansan yaddaakayiba aka dawo da gawar gida nakasa mata wankakamar yadda shariah taso sai su mami ne sukamata.ina rungume da waleed,shima kukayakeyi.mami tace inje inyi mata addua kafin afita da ita.nashiga dakin nasameta tsaf cikin likkafanintatamkar ka kirata ta amsa.nadauki kanta nadaura bisacinyoyina nafara addua.muryata na rawa ido na zubdahawaye.bansan lokacin dana goce da sumbatu ba,fadinake haba ruqayya,meyasa zakimin haka?saidanafara sonki zaki tafi ki barni? kinmin adalci kenan? yanxu ya kikeso nayi da raina?dady ya dafani yacekayi shiru da bakinka al'amin.taso haka ya isa!nadubeshi hawaye na sauqa nace haba dady wannanwani irin abune? narasa sakeena sannan narasaruqayya ma kenan?ku tausayamin mana.118Baice komaiba yadauke kanta daga jikina yanadeta waje daya,sannan yakamoni ya fiddo niwaje,yatura aka fito da gawar.mutane maqil!sukasallaceta nadauketa da hannuna nasa akabari akabinne abinda nakasa mantawa kenan.ya rinqa firgitaniidan natuna dasafe munyi waya da ita.nakasa kallon jinjirar data bari ga waleed naqara raunana min xuciyada tambayoyinsa.su nanta aka maidawa bebin danhaka muke kiranta waleeda.babu inda tabarmahaifiyarta.tananan yanxu shekararta daya darabi,nikuwa tun lokacin nakoma rasha nabar waleedwajen mami.ita kuwa waleeda tana hannun umman ruqayya.idan kinganni nigeria to gayyotani akayi waniaikin dabazan wuce sati biyu ko wata guda ba.gabadaya nasamu rauni acikin xuciyata agame damaganar aure ko soyayya.dukda nasan nafaramanyanta yakamata nasake aje mata.amma banatunanin hakan.abisa dalilin dani kaina nasan ba hujjabace a wajen ubangiji,119Amma Allah yagani na jarabtu wajen kewarruqayya.da kayan sonki danakasa sauqewa shekarada shekaru.kuma inayin addua ina rokon Allah idanyasake bani mata yabani wacce zuciyata zatasotakarna sake tafka kuskuren danayiwa ruqayya.saibayan ta mutu nake gayamata kalmar so.kwatsam! Nasami takardar gayyata indawo inyi aikin wata shidaanan asibitin zariya.musamman saboda ku yan koyonaikin dakuma yawan samun matsaloli lalurar datashafi kwakwalwar yara.bantaba tsammanin zansakehaduwa dakeba sakena.saigashi cikin satin farkodana shiga office.Allah yahadani dake.nayi murna da farincikin dana manta rabon da inyi irinsa.don azatonaAllah yakarbi adduata.saboda yasan babu macendanakeso tamkarki..ya numfasa tareda shafa zufardata karyo masa,yaci gaba da fadin.koda yake nayiimanin bakomai kakeso yake zama alheriba.wata qilaakwai abunda Allah yaboye agame damu shisa nakasa samun aurenki.nagode Allah tunda ya tsamoki daga qangin sharri.ubangiji yadada tsaremu dagasharrin masu sharri. Ya dubeta tana share kwalla yace kukan me kikeyi?tace mutuwar ruqayya naji tamkar nasanta.Allahyajikanta.yace amin summa amin! tace haryanxuwaleeda tana suleja?yace tana can waleed ma yanazuwa hutu yadade acan har hutun yaqare.ta numfasatace Allah amfanasu yace ameen.sukayi shiru suna ratsa tsakiyar zariya haryakawo gida.yayi fakin.tadubeshi daidai lokacin dashima ya dubeta.tacenagode ina fatan zaka yafemin.yace me kika min?tace shikenan saida safe.ta bude murfin motar tafitoyana kallonta bai iya tankawa ba.yabude nasa murfinyafito yasake dubanta yace dazaki ban numbarki dakin taimakamin ko gaisuwa mudinga yi.tagyaratsayuwa tace kada muyi hakadakai babanwaleed.alfarma biyu ka nema.kakuma gayamin naamince.toyanxu zaka karya alqawari.ya kada kai yacesakeena.....ta katse shi saida safe baban waleed tajajakarta ta tura get ta shiga ta nufi bangarenta tana budewa zainab ta tura qofar ta shigo.sakeena kindawone?tadub eta da murmushi bake kika turamin dr ba?yana iya daku!ta tura qofa tashige,120.zainab tana dariya to ko kefa? saboda Allahakanme zaki bar karatunki?ta jefar da jaka tazaunagefen gado bazaki gane bane zainab.medaki shiyasaninda yake masa yoyo.nisanta ta da dr shine zamanlafiyata.tazauna kusa da ita ta sanyaya murya tacedon Allah intambayeki?tace tambaya naji.tace tsakani da Allah bakison dokta?ta zura mata ido jim kadantace meyasa zakimin tambayar kurilla?kiban amsakai tsaye zan fahimta sakeena.tace to aikobangayamiki ba kinsan amsar tambayar zainab shinaso afarko kuma shine a qarshe.idan kuwa hakanebaikamata ki cutar da kanki ba.kimanta da komai ki amince masa adaura muku aure.tace zainab kenan tona gode da kulawarki.tamiqe tana fadin don Allah kiyitunani karki bari dr yaqara kubucemiki.Ta juya ta bar dakin mama tayi shiru kanta sun kuyeduk gabobinta suka mutu,zainab ta sake fadowadakin. Ta firgita sakeena haba sakeena ki taimakibawan Allah nan koya sami natsuwa ko kin san haryanzu yana waje ta kara zaro ido banganeba doktayana waje kin kuwa san zai iya kwana a nan don hankalinsa ba a jikinsa yake ba ta sauke numfashitace na shiga uku ta mike da sauri ta fita zainab tabita kansa na kife bisa sitiyari ji kawai yayi an budemurfin motar ya dago kai ya dube ta ya zura mata idobaki sake ya kasa fadin komai ta gyara tsayuwa tacebaka san dare ke kara yi ba Ta juya tabar dakin,mama tayi shiru kantasunkuye.duk gabobinta sun mutu.zainab tasakefadowa dakin harta firgitata,sakeena!haba sakeena!kitaimaki bawan Allah nan kozai samu nutsuwakinsan haryanxu yana waje.ta qara zaro idobanganeba? dokta yana waje.kinkuwa san zai iya kwana anan,don hankalinsa baya jikinsa.tasauqenumfashi tace na shiga uku!ta miqe da sauri tafita.zainab tabita.kansa na kife kan sitiyeri ,ji kawaiyayi anbude murfin motar.yadago kai ya dubeta yazura mata ido baki sake,yakasa fadin komai.tagyaratsayuwa tace bakasan dare ke qarayiba?ya sauqe numfashi yace zantafi.tace yakamata kasan yanayingarin ko?yace hakane saida safe.tace Allah yatashemu.ta rufe masa murfin mota ya tayar yasakedubanta kamar yagayamata sirrin zuciyarsa ya tunamata baya,amma yariga ya dauki alqawari dan hakayadake kawai.yadaga mata hannu ya wuce.itama tana daga masa saida yabar haraban wajenm tadawo dakiba kwari ajikinta.batama san tawuce zainab tsayeba.Ta maida kofar ta rufe ganin haka yasa zainab itamata wuce nata bangaren ta kyaleta tayi tinani akanabinda take shirin aikatawa.kwanciya tayi bisa gadotunani ya isheta labarin daya bata kawai yakanta cikinranta.ta tausaya masa ta lalubo hotonsa ta zura masaido bata lokacin da kwalla ya zuba mata ba daren nan bata runtsa ba saboda tsabar tausayin al'ameen dayaransa.haka zalika lamarin yake ga al'ameen tundaya koma gida yakira wayar mami yasheda mata dukyadda sukayi da mama.ita kanta ta girgiza.sai daibatada abinyi illa tabashi haquri ya dangana..tundayace bayaso abbanta yasani dan karya takuramata.wanda hakan baisan abunda zaijanyoba.haka yakwana yana juyi da tinanetinane.kamar yabar garin yakeji.dasafe a ofis ya iskemutumin dr lawal.yazauna shiru yana kallonsa.drlawal yakada kai yace ai mukam mun shiga uku!tundasakeena ta dawo mana!yanxu shikenan haka zamu kasance a susuce?dafa ba yanxubane kasanalameen din yanxu ba yaro bane.122Yaja tsaki ina ruwan so da shekaru? yace waitsaya baku daidaita bane?ko tana da aurene?yacelabari ne mai tsawo ashe yaron nan asiri yamatasaboda taqi yarda dashi ya lalata mata rayuwartayakuma qi aurenta.ya rabata da iyayenta.ya ajiyetakamar dadiro.cikin wahala da kazantatciyar rayuwa abin babu dadin ji sai dai Allah yakawo qarshenabin.asirin ya karye.ance yananan yana hauka afandogari.amma ingaya maka har haihuwa sukayidashi saida yaron yashekara goma sha biyu yamutu.da wannn fa take ganin ita abar kyamace.tagaggaya min maganganu masu qona zuciya.wai harda tarkata kayanta ta gudu tabar karatun.tagudu harkaduna nabita na lallasota nace indan tanine tayihakuri na haqura.ya ce haba!bai kamata kayi hakabaai ita abar tausayi ce kuma dakai yadace ku zaunazaman aure.don wancan BAKIN CIKIN Yazama tarihi! HAUSA Novels BOOK BAKIN CIKI 3***10 Yace ita batayi wannan nazarin ba.amma tunda hakane sai mu mutu gwaraye!dr lawal yace a a Allahyasauqa kamutu gwaro nizanje nasameta.da sauriyace karka je dr lawal alqawari nadauka mata koabbanta bazaijiba.to saboda me?bayan kana sonta?yace bana so tabar karatunta dr lawal.kaga tunfarko abbanta karatu yaso tayi nazo na tusa matasoyayyata har wancan shirin ya russhe.yanxu kumatayi nisa sai inqara rusa shi? ka kyaleta kawai zandaure har zuwa lokacin dazan koma abina.daga nanbazata sake ganinaba.ina ganin hankalinta zai kwantataji dadin karatunta.ya numfasa yace Allah yazaba mana mafi alheri.yace amin zan qarasa ofis.tosai kafito yamiqe yafita yabar dr lawal yana girgizakai.kwana 7 suncika litinin tazagayo wa al'ameen adaddafe.domin gani yake kamar yashekara da zuwayanda nigeria tamasa zafi.komai akan qarfin haliyakeyi.amma hankalinsa nakan mama.ko yau da wuri yazo ofis dan ya ganta kozaiji dadi aransa.kowa yazoya tarar dashi ne azaune a ofis yanata fama da (laptop),A hankali masu jinya suka cika wuri masu raba(folder)suka rarraba kamar kullun sababbin zuwa susuke ganin baban likita kuma mutun hudu ake bokinko wane wata saboda dadewar da ake wajan bincikeakan kwashe sama da awa biyu ana ganin mutumdaya, dalibai suka iso cikin ayari kaman yadda suka saba suka kutsa kai ofishinsa. Bai iya dauke idon saga kallon mama ba hasalima wani banzan kyau tayimasa ga rigar likitocin ta kara mata kwarjini bayansun gama sa hannu kowa ya zauna aka fara karatugaba daya ya tasa mama da tambayoyi kuma idonsabaya daukewa akan na ta koda bada ita yake magana ba ma'ana dole ne duk bayan yan sakwanni ya dubiinda take zaune anan suka kai karfe daya kamaryadda suka saba suka sallame shi kowa ya ficemama na tsaye rungume da wani (file) a hannunta yazuro mata ido jim kafin yace yaya dai ta matso ahankali ta dora masa file din hannunta akan tebur ta juya da sauri tabar ofis din ya bita da kallo ya rasa mezaice har ta fice ya jawo file din ya bude ya daddagetakardun dake ciki daya bayan daya ya karanta kafdin su sakamakon gwaje gwajen da aka yi mata ne aegypt kansa ya daure mene ne nufinta na kawo masafile din yakasa warware dalilin... -Amma a hakikanin gaskiya kai zan kawo mawa don ka gani a matsayinka na mijin da na yanke shawarar mika wa amanta Allah ya tsare ni dokta ba'a sami cutar komai ba a jiki na zaka iya hakuri dani a matsayin matarka ba tare da tunanin na taba haihuwa a waje ba tsawon sakwan biyar yayi zuru yana kallon a idanuwanta jajur taf da kwalla murya dishe ya ce idan zolayata ki keyi ki bari sakeena please kar ki yi wasa da rayuwa ta kwalla suka zubo bisa kuncinta tace ba wasa bane dokta zainab tayi kokarinta ta gaya min gaskiya haka abokin ka dr lawal zuwansa uku gidan nan yana jawo hankalina akan abinda ya sameni ba hujja bace ta kin yin aure na kuma tabba ta ko abba yaji wannan maganar zai so mucika wa juna alkawari shi yasa na hakura na yi niyya cikin raina da yardar Allah baza mu mutu gwauraye ba muddin zaka kare min mutuncina wajen danginka kayi min alkawari ya dafe kirji idanuwansa sama yake fadin Alhamdulillahi Allah na gode maka da ka nuna min wanna rana dana dade ina mafarkin zuwanta kawai gani tayi ya zaro waya ya nemo wasau lambobi ya kara wa kunnensa tayi zuru tana kallon sa dukkansu kwalla ke bin kuncin su jimawa kadan ya fara fadin wa'alaikumus salam mamina albishirinki sakeena ta amince mami sakeena ta yarda zata aure ni tace godiya ta tabbata ga Allah ka gaya mata muna godiya yace zan gaya mata mami zan kira dadi in gaya masa ya fara shiri tayi yar dariya tace Allah sarki dan gidan dadi to shi ke nan sai mun ganka ya kashe waya ya dubeta sukayi wa juna kuri na tsawon lokaci yai dan murmushi yace sakeena har,126Yace sakeena har abada asirinki a rufe yake.kuma zaici gaba da zama a rufe har qarshen rayuwarki.duk wanda ya nemi ya tona miki sai naga iyakarsa.ina mai tabbatar miki qarshen sa zai zama tamkar na danliti.karkiyi kokanto ko kadan tunda ga fuska har zuciyaata alameen dinki ne wanda kikasani.ta kada kai tace bashi bane al'ameen dina saurayine,wannan kuwa harda furfura!ya fashe da dariya yana tambaya furfura?ina furfurar take? itama ta fara dariya gatanan ina gani bisa kanka!Allah sarki dr na ya tsufa!yace sakeenarfa?ai ita ma ta canza.taci gaba dayi masa dariya.yana kallonta kwalla suka taru masa ya numfasa yace Allah nagode maka da dr lawal da zainab.dasuka dage da farin ciki na ya dawo.sakeena kigayamin ranar da za'a daura mana aure tun kafin a tasheni daga baccin nan! 126Yace sakeena har abada asirinki a rufe yake.kuma zaici gaba da zama a rufe har qarshen rayuwarki.duk wanda ya nemi ya tona miki sai naga iyakarsa.ina mai tabbatar miki qarshen sa zai zama tamkar na danliti.karkiyi kokanto ko kadan tunda ga fuska har zuciyaata alameen dinki ne wanda kikasani.ta kada kai tace bashi bane al'ameen dina saurayine,wannan kuwa harda furfura!ya fashe da dariya yana tambaya furfura?ina furfurar take?itama ta fara dariya gatanan ina gani bisa kanka!Allah sarki dr na ya tsufa! yace sakeenarfa?ai ita ma ta canza.taci gaba dayi masa dariya.yana kallonta kwalla suka taru masa ya numfasa yace Allah nagode maka da dr lawal da zainab.dasuka dage da farin ciki na ya dawo.sakeena kigayamin ranar da za'a daura mana aure tun kafin a tasheni daga baccin nan! Yace sorry ba baraka yadace infara tambayaba ya umma dasu ameera?tadanyi shiru jim kadan ta dubeshi ido ya kawo kwalla tace umma ta rasu dokta.....yace what?innalillahi wa inna ilaihi rajiun.ciwo tayi?ta goge kwalla tace BAKIN CIKI Ne yakasheta dokta!umma takasa jure ganin halin qasqancin dana shiga.shisa bana son tunata.hankalina tashi yake tun lokacin shima abba yasamu matsalar paralise.andai samu yanxu hannun yana dan aiki amma baya tafiya a keke ake turashi.yace subhallahi Allah ya jikanta ya mata rahama.ta amsa ameen.ya miqo mata hankici share hawayenki kiyi haquri kinji?ta share fuska yana qara bata hakuri.sundan jima shiru kafin yace pls kidena damuwa insha Allahu abba zai warke idan har akwai yiwuwar hakan sai inda qarfina ya qare.ta numfasa nagode hira ta tsunke labarin bayan rabuwa sukeyi.kiran magruba dole ya miqe sukayi musayar lamba,yafito ta tako masa zuwa gaban motarsa.ya bude ya shiga,sannan yace to sai munyi wayako?tace ina sauraronka.ya qara zuba mata ido yace i love u! tace mee too!yace so much?tayi murmushi ta tura hularsa gaban goshi tace so much!ta juya tabar wajen tana waigensa.bakinsa har kunne yabar wajen, 128.tana karasowa ta iske zainab tana mata dariya.taja ta tsaya meyabaki dariya?ta daga gira ta kama kugu hannu biyu so baya tsufa,sai dai masoyan su tsufa kinga oganmu baki har nan?ta nuna da hannayenta mama tayi murmushi tana kada kai ke mayya ce zainab,wato ido kikasa mana ta window? zangayamasa.tace karki hadani da oga kisa ranar monday ya kasheni da tambayoyi.tana dariya ta tura qofarta tana fadin barinyi sallah.akwai abincifa kixo muci,tace sai na shigo ina jiranki kowacce ta nufi bangarenta.sannan suka hadu cin abincin karo na farko da mama ta gayyoto zainab saboda jin dadin shawarwarin data bata,har suka taimaka wajen dawo mata da farin cikinta. Haka al'amarin yake wajen dokta yana fitowa masallaci wayan dr lawal ya kira yagaya masa yana gida cikin yan mintoci dabasu fi ashirinba ya isa gidan.yana fitowa yaga dr al'ameen ya nufosa baki har kunne ya rungumesa.ya dubesa yaya dai likita?yace Allah yasaka maka da mafifi cin alheri!ya ware ido sosai yace amin likita meya jawo min wannan kyakkyawar addu'ar?yace ta amince dr sakeena ta amince zata aureni!ah haba?yace gaskia nake gaya maka,bansan irin godiyar dazan makaba dr lawal.ya numfasa yace yazame mini dole in taimaka maka.don na tabbata fadi kawai kake bazaka iya haqura da itaba.nima ngd Allah data dubi girmansa ta amshi rokona!nagaya mata bakai kadai zata kasheba. Allah kadai yasan mutanen dazasu mutu idan ta bari sonta ya wargaza mana kai.ko ba gaskia ba?abin ya dameni da yawa.koda kace kar insake mata magana najika ne kawai amma tunani yana kan yadda zanyika auri sakeena.muma hankalinmu ya kwanta.so yaushe tace zamusha bikin?ya rungumeshi yana fadin.bazan taba mantakaba a rayuwa dr lawal.yace to nima nagode.suka dubi juna fuskokinsu cike da annuri to yaushe zamusha bikin?yace tace wata uku amma gaskia yayi yawa munbarshi a sati uku.yayi dariya dr love!watau ku kuka sanya wa kanku rana koh? tsokanarka fa nake dakaji na tambayeka.ya zura masa ido yana yar dariya.wlh madam na fama da iya shegenka.to miye dan musa rana?ya tabe baki hannayensa cikin aljihu babu komai sa'ido ne kawai irin na lawal mushiga muci abinci.ko sakeena ta baka?yace banceba dr lawal.karka min sharri.suka shige ciki sunawa junansu dariya.dr al'ameen na fadin ranar sati zamu wajen abbanta a abuja shima sati uku zamu gaya masa.bakuda kunya shima sai kun nuna masa kun kosa?suka fado falo suna kyalkyala dariya.ah madam kenan!ta yunkura ta tashi tana murmushi oga ne dakansa?ashe yana dariya haka abokin naka?tana tambayar mijinta dr lawal.yace kingano kenan?ai sirrin zuciya a tambayi fuska.ko?yace hakane mana ke me kika fahimta kan fuskarsa?130.Tace wataqila sakeena ta janye gudumar data daga!yace shisa nake sonki mairo.akwai ganewa ingayamiki har sunsanya wa kansu rana!tace ahaba dai!?kace biki ya kusa.yace sati uku kinkuwa san akwai sonkai aciki suna nufin sun kosa.takama baki wai!maganar tafi qarfina.wannan tsakaninku ne.dokta ka zauna akawo ruwa ko?yazauna yana fadin kungama sharrin?toya yarana.tace suna lafiya tun dazu suke sallah yace yayi kyau.tace to congrats! muna murna Allah sa ayi damu yace amin madam.ta wuce yayinda dr lawal ke zama kusa dashi.kai mugun maasharranci ne wlh.yace rantse da Allah baka kosaba?ya zura masa ido yana dariya yace yo see! nasan bakada abin cewa nidai ina roqon likita pls nd pls karka manta wa wani almakashi acikin kai.arinqa ajiye sakeena a kofar tiyata.ya bashi hannu suka tafa suna kyayatawa kasamu ni dayawa dr lawal.amma ba komai gidanka naxo.maryam ta fito da tiren kayan abinci ta nufi tebur ta jera musu.sunata yankar dr al'ameen.yazaiyi?sai dariya kawai dan sunfishi baki.shiyasa yace wa dr lawal duk ka bata madam da sharri Allah shiryeku.ahaka suka gama cin abincin takwas da rabi yabar gidan yakoma nasa.can yayi sallar isha'i yayi wa Allah godiya ya rokesa daya nuna masa ranar dazai ganshi da mama a matsayin matarsa.yayi shiru ya rufe idonsa.wayarsa tayi qara ya dauka dadinsa ne.yamayar masa yanda akayi.dadi ya lullubesa.yasa musu albarka tare da fatan Allah nuna musu wannan rana da zata zamar musu abin tarihi a rayuwarsu.bai iya bacci ba dan daya rufe ido mama yake gani tana tura hularsa tana fada masa so much! ranar asabar akan hanyarsu ta zuwa abuja.kaduna suka tsaya makarantar da waleed yake (TURKISH INTERNATIONAL SCHOOL.)inda yake karatunsa makarantar kwana ce ta yaran masu kumbar susa.suna zaune falon karbar baqi aka kawo musu shi.ya rugo ya rungume babansa murna kamar ta kasheshi.mama tayi zuru tana kallonsu tana murmushi daka ganshi kaga al'ameen..ya dago shi suka zurawa juna ido dady yaushe kazo?yace banwani dade ba dama nace kar a gayamaka sai naxo kaganni suprise ko?yace amma kaje kaga waleeda?yace sau daya naje Allah sau daya naje ya tura baki a shagwabe gaskia ba haka akeyi ba .ba haka akeyi ba dady.ya fara dariya ya kama kunnuwansa biyu sorry.i'am very sorry abdul kayi?ya qara rungumeshi i miss u dad.yace nima haka yarona! ya dagoshi ya dubi mama ta zura musu ido tana murmushi.har wasu kwallan da batasan dalilinsuba suka taru.dadi wannan fa?ya dubeshi ya numfasa mominku ce saura sati uku adaura mana aure kana sonta?ya zura mata ido tamkar yadda take kallonsa ina sonta dady wlh tanada kyau kamar balarabiya! suka fashe da dariya mama ta jawoshi jikinta ta rungumeshi.tace nima inasonka kaima kayi kama da larabawan my beloved son.ya kwashe da dariya yace harda waleeda?tace sosaima.131Yace sister nane tana can suleja wajen kakarmu.zakije ki ganta?tace daganan can zamu wuce ya miqa mata yatsansa promise?ta jawo shi ta rungume al'ameen ya sauqe numfashi ya zura musu ido yana murmushi..ta dago ta dubeshi to nagode tunda kana sona kaga zamu zauna cikin farin ciki kenan koh?ya amsa da kai dady kuzo ku dauken ranar daurin auren.yace ai bakuyi hutu ba waleed kasan makaranta bazata bariba.kayi haquri inkunyi hutu kai tsaye zariya zan wuce dakai wajenta.yace waleeda zataje bikin?yace wai meyasa waleeda tazamo kishiyarka?to ita bazata jeba shikenan? gaba dayanku sai anyi hutu inkaiku.yadan saki fuska.mama tadauko wata farar leda ta miqa masa duk wannan naka ne.ya karba ya dudduba.kwalayen biskit da cukulet kala kala wanda yakeso.ya dubeta yana dariya momy na gode!tayi murmushi nima nagode.dr al'ameen yace bari mu wuce koh? muna sauri muje muga waleeda kar dare yayi sai mundawo.sukayi sallama da waleed kamar zaiyi kuka.hakanan suka tafi suka zuciyarsu cike da tausayinsa.shiyasa mama tayi shiru a mota tsawon lokaci sannan ta numfasa waleed kamar kayi kaki dokta!133Yayi dan murmushi Allah ko? tace har muryarku iri daya.ga shagwabar gado.ya kyalkyale da dariya yace.haka kema zaki haifa min ameer da ameera.ta watso masa harara,tace kai ka sansu.yace ashe kingane.kullum na rufe idona su nake gani.suna tumurmusani uhm...mafarkina yakusa zama gaskia.Allah kaban ameer da ameera ta tsatson sakeena wannan shine babban burina.ta zura masa ido harya tsargu yajuyo ya dubeta suka hada ido.yayi murmushi yadauke kai.itama tahauyi cikin ranta tana tayashi addu'ar Allah ya cika masa burinsa.suna tafe suna hira nanda nan suka iso suleja mama tana ganin yanda yadauki babban titi tace ina zamu? yace wajen waleeda mana!tace gaskia inajin kunya dokta.mu wuce kawai watarana na ganta.yace kunya?ina alqawarin dakika dauka wa waleed?tadan runtse ido ya salam.ta dubeshi ta ci gaba sai kuma muje kace musu ni wa?yace mominsu waleed ofcourse!cike da damuwa tace aikaji.sai ace banda kunya harna biyoka ganin yarka.ya karkace kai yace salo!to idan baki biyoni ba waza ki biyo?ta zura masa ido harya gaji yace tsaya kiji karewa cemusu zanyi kece nafara so rashinki yasa na auri ruqayya..tace kaga tun anan ansami matsala kana fadi zanyi baqin jini. Da dai....yanxu zakice bazakije kiga waleeda bako? ta bishi da kallo haka shima yasa mata ido jim! sukayi shiru kafin tace muje dokta amma ka taimakeni dan Allah karka basu labarin daya wuce.yayi dan murmushi yana tada mota fuskarki kamar na mara tsoro can cikin zuciyarki kamar farar kura.ga tsoro ga ban tsoro.tace muje a tsoron aini nasan menakeyi.yace nine bansani ba ko?tace wuuu! banfada ba Allah huci zuciyar mai gida. Da wutsiyar ido ya kalleta in banda abinki gidansu ruqayya ai gidan mune aminin dady fa.yadda yake abbanta nima abba nane tace nima abba nane.har kofar gidan kowa na kokarin kare kansa yayi horn mai gadi yabude suka gaisa ya ajiye motar a wajen ajiye motoci.suna tsaye kofar gidan dr al'ameen yana kwankwasawa yana mata dariya ganin yadda ta tsaya tamkar marar gaskia.jimawa kadan aka bude.ah! oyoyo dadin waleed yana murmushi yace anti niima sauqar yaushe?tace dazu dazu tafe kake da baquwa? yace wlh kuwa wai tanaso tazo taga waleeda.bakinta har kunne tajawo hannunta suka wuce ciki.tana mata sannu da zuwa.har kujera takaita.tace zauna inkira umma.suka zauna dr alameen yace antin ruqayya ce tana aure a kano.tace akwai fara'a sai gasu sundawo.anty ni'ima na riqe da hannun waleeda tana taka qasa dabas dabas.saboda kiba,rugu rugu!da ita.ga gashi kamar buzaye.mama ta zura mata ido ai batasan lokacin data tashi ta runguma yarinyarba saboda sha'awa data bata.bayan angaisa anty ni'ima takawo musu ababen sha.hajiyar ke tambaya hala wannan itace sabuwar mominsu waleeda?Yana yar dariya yace itace hajiya munje makaranta taga waleed shine tace sai na kawota 135-wajen waleeda hajiya tace madalla ya ya kyau Allah ya sanya alkairi yace amin yayin da mama ta kara sunkuyar da kai tanayi wa waleeda wasa ita kuwa tamkar ta taba ganin ta fariya kawai takeyi mata ya sunanta anti ni'ima ta tambaya yace sakeena sunanta tace sakeena ta dan yi shiru ka na ta kara fadin dadin waleeda ko dai sakeenar da marigayiya ta taba ban labari ne duk suka kalli juna sannan ya tambaya ta taba. Baki labarin wata sakeena ce tace ya dade da ta gaya min ka so wata yarinya sakeena amma Allah bai yi auren ba ta auri wani itama iya ce ta bata labarin irin son da kake mata haka ne? Yayi murmushi yace haka ne anti ni'ima ga ta kuma mun sake haduwa hajiya tace haka shirin ubangiji yake matar mutun aka ce kabarinsa ina fatan dai yanzu babu wani sai da na ko sakeena taja mayafi ta rufe fuska suna ta mata dariya kunya ta hana mama sakewa sha biyu rana suka bar gidan da alheri mai yawa da hajiyar taba mama waleeda kuwa harda kukanta da taga sun shige mota sun tafi sun barta, suna tafe suna labarin gidan irin kyakkyawar tarbar da akayi mata abin ya faranta mata rai kwarai da gaske bayan wucewa awa daya. Suka iso maitama gab daza su shiga gidan take cewa kasan wani abu ban fa gaya wa abba komai a kanka ba kamar yaya tace kawai gaya masa nayi zan zo weekend so na ke abba ya sha mamaki yace ai kuwa zai sha mamaki na bazata ma kuwa ba shi kadai ba kowa ma ya ganni zai saki baki yau , kin kyauta da baki fadi yayi horn aka bude musu get suka sulala ciki tace munyi sa'a yaya na gida ga motocinsa nan a jiye yace good al-ameen sa'a ke nan... mu je ciki asa mana rana yarinya balarabiya ta bakin waleed" ta ballo masa harara tace wace ce yarinyar yayi yar dariya ya bude murfin yana fadin Allah na tuba duka kwaya nawa kike ita ma ta fito gara dai da kace Allah ka tuba ta wuce yabi bayanta yana dariya suka tsaya bakin kofa tace ka tsaya anan zan dawo in shigo da kai yace ba laifi ina jira ta shige tana kwarara sallama duk suka amsa mata daga babban falo can ta wuce da sauri suna mata oyayo ta fada jikin abba da murna sanna ta juya. Wajen yayanta da anti amina duk ta gaishesu kana ta mike tsaye tace kun san wani abu duk suka zuba mata ido abba ya bata amsa sai kin fadi mama na tace duk ku rufe idanuwanku akwai abin mamaki dana taho muku da shi yayanta ya aje jarida yace idan kin ka nuna mana shirme sai na balla kafarki tana dariya tace na yarda to kun shirya mun shirya a rufe ido ina zuwa ta fice suna mata dariya abba yace ai sai mu rufe mu bude muga abin mamaki duk suka rufe suna dariya jimawa kadan suka shigo tare da al-ameen ya tsaya saitin daza su ganshi sosai yana ta murmushi tace kuna iya budewa duk suka bude kowa ya yi ido hudu da al-ameen dif yake dauke wuta ya zubo masa ido anti amina ce ta fara magana dokta ko ba shi bane mama tace gashi nan dai abba wanene a tsaye yaya ka gane shi yaya yace al-ameen abba ya miko hannayensa biyu yace zo nan al-ameen zo in taba ka in tabbatar da ba mafarki na ke yi ba ya tako da sauri bakinsa har kunne ya zube,137- gaban abba ya rungume shi yana fadin 鈥渢sarki ya tabbata ga allah ashe zan sake ganinka al- amin?鈥� Ya jima yana rungume da shi.sanna ya dago shi suka duba juna. abba ya numfasa ya sake fadin 鈥渉aba al- amin kuma sai zumunci ya yanke? Babu kai babu labarin dadinka?鈥� Ya-ce 鈥渒a yi hakuri abba. Tunda na ba kasar nan ban dawo ba. Sai da na kusan shekara biyar. Duk abubuwan da suka faru ban dawo ba. Sake haduwarmu da sakeena take gaya min har umma Allah yayi mata rasuwa kai kuma ga lalurar da ta same ka banji dadi ba Abba ubangiji Allah ya jikanta yayi mata rahama hannayensa biyu bisa kafadarsa ya amsa amin summa amin ina fatan su alhaji duk suna nan lafiya ya juya suka gaisa da yaya soja da anti amina yayi masu. Gaisuwar umma nan da nan aka baibayeshi da kayan ciye ciye dana sha kala kala ya jika mako shinsa da ruwan sanyi yace ashe haka al'amura suka faru abba wannan wane irin zaluncine da rashin imani, Abba ya kada kai yace ka bari al-ameen ai munga tashin hankali yarinyar nan ta dawo tamkar mahaukaciya a gari kowa yana ganin kamar rashin biyayya ce ta jawo mata lalacewa da kaskanci ashe ba haka bane ka ganta nan Allah ne yasa tana da sauran shan ruwa a duniya hankalin al-ameen ya kara tashi yace subahanallah Allah karabamu da sharrin shadan suka amsa da amin yace shine wannan zai zama dalilin da* tace ba zatayi aure ba sati uku muna artabu abba da kyar abokin na ya shawi kanta. Inda harna ce na hakura suka zuba mata ido kafin abba yace haka ne kuma nima na kyale ta ta zaba abinda tafiso dan hankalinta ya kwanta sai dai tun lokacin na sani dole wannan kudirin na ta ya tashi domin bani da wani buri da ya wuce in cika maka alkawarin dana daukar maka to Alhamdulilahi,138.tunda itama ta gane gaskia,nakuma tabbatar batada wanda takeso face kai.saboda haka duk lokacin daka shirya kazo adaura auren dafatan bazaka samu matsala da iyalinka dake gidaba.yayi murmushi yace ai babu iyalin abba banganeba.ta rasu abba shekara daya da rabi kenan.yace ayya Allah yamata rahma yasa duk musulmi suna kyakkyawar matsayi.yace amin abba.kowa yayi masa gaisuwa,,,,,suna suka ci gaba da tattaunawa.mama tace abba bakaga yaronsaba.yakusa tsawona.al'amee n yasaki baki yana kallonta,,yayinda abba ke fadin ah lalle ba shakka,su nawa ne?tace su biyu ne,abdulrasheed da ruqayya.sunan mamanta aka samata.abin tausayi abba tana haihuwarta ta rasu.tausayi yakama kowa sunata mata addu'a.al'ameen na amsawa haka suka wuni hira salloli kawai ke tadasu.dare yayi aka kai al'ameen masauqi.farin ciki kamar ya kashesa.shine mutumin dazai iya sharewa mama hawayenta.cikakken labarin abinda yasameta dayaji ya qara masa tsantsar sonta.bashida wani buri daya wuce ya mallaketa ta hanyar sunna.don ya tabbatar mata da cewa Allah baya zalunci kuma bayason mai yinsa.washegari qarfe tara suka bar abuja dauke da albarka mai tarin yawa daga wajen abba.suna shigowa suleja mama ta tunada waleeda.tadan dafa qirji Allah sarki waleeda kamar mu koma mu daukota.yace kinsan rigimar waleeda kuwa? bazaki iyaba nake gayamiki kukanta sai hajiya.139.Tace haka kake gani,badon karatu ba dana daukota.Allah taban sha'awa,jiya saidanayi mafarkinta.kukan da take lokacin dazamu tafi.yace ba waleeda kika gani ba ameera ce.ta ballo masa harara yasan hararar yakesha shiyasa yaqi waigowa ya rinqa yar dariya.ya qirqiro waka.yana rerawa idan da rai da rabo!.......al'ameen zaisamu ameer da ameera! mai harararsa yadena!...takada kai tana dariya Allah ya shiryeka!yace ameen.sannan yace na fahimci kinfison waleeda akan waleed,lalle zakuyi rigima dashi dan kishiyarsa ce.tace naga alama komai saiya tambaya yaji ko anyi mata shi ba a yimasaba? tace ba komai nasan yadda zanbi dasu yace ko? kana shakk ne?uwace fa! yayi murmushi yace uhm....naqosa inganki mama.tace bari gatse dama sunan kenan! yace godiya nake!dai dai lokacin daya dauki hanyar minna.idanuwa waje tace yaya haka?yace haka dinne.dan Allah ina zamu?yace yanda kika nuna ni suprise haka zan nuna ki mamakiyos!ta langume kai amma bakada kirki mesa zakamin haka?yace mesa? tambaya kike?any way....kinma riga kinba kanki amsa tunda kikace banda kirki.rashin kirkin ne yasa zan nunawa kowa cewa alqawarin Allah baya tashi.fuska yamutse tace wayyo Allah na!yace ke yasu!?ta numfasa bata bashi amsaba.yafara mata dariya yana karawa don a gaskia tanajin kunyan su mami balle kuma dady. Ganin abin yadameta sosai yace to miye abun damuwar keda zaku zauna nan bada dadewa ba.kinsan cewa ko bajima ko ba dade zaku zauna tare.tace ai da sai a bari na dolen yazo saboda Allah fa! Yace gaskia bazan iyaba kiyi haquri kawai muje kisha kunyar a yau.kinji ko bebina?tace naji sir! yayi dan murmushi yace thank you mah!suka ci gaba da hira kala kala.har suka isa minna.kai tsaye yadauki hanyar anguwarsu.tace tsaya bansaya wa mami komai ba.gayamin abinda tafi so?yace idan kinaso ki burge mami kisaya mata carrot.cucumba,da kankana.to muje insaya mata.yace karki damu munayin kwanar can akwai masu fruit.yana maganar suna shiga kwanar sai gasu birjik!yayi parking duk suka fito mama ta kwasa kamar banxa gaba daya akace dubu daya.alameen yazaro zai miqa tace anyi ba ayiba kenan.nice zansaya mata bakaiba kokai kace?yakama kunnuwansa tuba nake wannan jan idon?tayi murmushi harmai fruits na tayata.ta zaro dari biyar biyar sabbi dal ta miqa masa akasa a boot.suka wuce alameen na tsokanarta hajiya mama kenan kinfara raina min wayau!tun jiya kike kashe min kudi,karfa ki maidani mijin hajia?tace sai me? yace sai ni baban ameer da ameera.tayi dan tsaki ta kyaleshi yana mata dariya.sunyi fakin harabar ajiye motoci,suka fito shima ya ajeta waje kamar yadda tamasa.yashiga ciki tare da sallama.maminsa na dakin dady.daga can ta amsa sallamarsa.ya qarasa ciki da fara'a maraba da bokan turai!.inji mami yace mamina!ya tsugunna gabanta yadafa guiwowinta.ta dafashi tace ya aiki?yace mungode Allah mamina!141,ya juya kan dady dadina!yace nidai ansaba min son kai.ai de ba haka akeyi ba!yadawo gunsa yana dariya yace dadina albishirinka?yace goro fari yace to duk ku taso muje falo in nuna muku wani abu.meye shi? mami ta tambaya.dady yace miye naki na tambaya taso muje kawai.suka nufi falo.yauwa! to ku rufe idanuwanku!kuma dai?inji mami.kedai rufe dadi yafada suka rufe ido suna dariya.yace minti daya yakoma waje da sauri ya kamo hannunta tana fisgewa yashigo da ita.ya tsaidata gabansu.kunya kamar ta nutse qasa yace kuna iya budewa yanxu..alokaci guda suka bude duk sukayi mutuwar tsaye.dadi yafara fadin sakeena! taja mayafi ta rufe kai.mami kuwa da saurinta ta rungumeta.Allah sarki sakeena! ashe Allah zai hada fuskokinmu?kwalla suka cika idon mami.mama kuwa ta goce da kuka.mami ta dagota hannu biyu menene abin kuka sakeena? don Allah ki dena.wannan ranar farinciki ce.dan na tabbata dan tilon dana zaisamu farinciki data dade dayin qaura daga jikinsa.karki damu da komai kisaki jikinki kamar da kinji ko?ta durqusa qasa baba ina yininku? haryanxu yana mamaki lafiya qalau sakeena.haka shima alameen idanu suka dauki kwalla.yace ashe har umma ta rasu.mami ta kamota sukazauna a 2 sitter,tana rungume da kafadarta tace munji rasuwar ummanki amma rashin jin dadin abinda kikayiwa alameen shiya hanamu zuwa gaisuwa.kuma bamu gaya masaba.karkiga laifinmu sakeena.Allah kadi yasan wahalar da mukasha kafin musamu mu ceto ransa. Allah kadai yasan yan kudaden da muka batar dan neman taimakon addu'ar Allah ya cire mishi sonki.muka samu son yasuma.dan kuwa suma yayi tunda gashi daga ganinki ya farfado.kiyi haquri sakeena wannan al'amari duk cikin rashin sani akayi.ta silale qasa tasake durqusawa wlh babu komai mamii.idan kuwa dame laifi ni yakamata nabada haquri dan angayamin dakanki kikazo rokona.kina bani haquri amma naqi sauraronki nima ku yafemin,,,,,ta jawota ta rungumeta karki damu sakeena.wannan wani qaddararren al'amarine daga Allah.babu mai iya kauda shi.amma dayake bakida hakki gashi ubangiji yabayyana komai....shikuma yaga makomarsa.to Allah ya jiqan hajiya halima.kidage dayi mata addu'a ita kadai ce ribarki gareta.kinji?ta dago tana amsawa dakai tana share kwalla!dady ya numfasa munyi farin ciki da ganin wannan rana.muna masu tsananta godiya ga Allah ta'ala mafificin dukkan komai.saboda haka muke roqonsa ya karemu daga dukkan sharri.yakuma jikan hajia halima ya yafe mata dukkan kurakurenta.143Suka amsa amin summa amin, bayan dadi ya gama addu'oinsa alameen ya dubi mami yace ina iyata?tace suna can bayan gida suna hira.ya miqe yana fadin barin kirasu suga sakeena ta.ta dawo mami tace yakamata.yashige kicin kofar dazata sada shi da waje.mami ta dubi mama tace inaa fata komai ya dai daita?biki kawai zamu shako?ta sunkuyar dakai dadi yace kema kinsan bazata iya fadaba.ki bari ya shigo muji daga bakinsa,,,,sai ga hayaniyarsu dasu iya suka shiga tafa hannu suna sallami lalle matar mutum kabarinsa.suka zauna gefe suka gaisa.iya tace ubangiji yanuna mana ranar auren nan.suka ce amin.al'ameen yazarce da fadin musha rawa ko iyata?baki har kunne tace sosai kuwa dan iya.Allah dai yanuna mana lokacin lafiya.anata raha suka bar falon.ladi ta tafi takawo musu ruwa da abinci.mami ta gyara zama tace yadai? ya ake ciki? nafa kosa..yayi yar dariya yace komai dai dai mami.kinga tun jiya muka baro zariya muka tsaya kaduna makarantar su waleed.mukaje suleja gun waleeda yar rigima.muka wuce abuja gidan abba.bakuga yadda ya karbeni ba murna da farin ciki ba a bayani.ya rungumeni yana kwalla.yanxu maganarku muke jira yace ko yaushe nashirya nazo adaura mana aure ai baza a bata lokaciba ko dady? bakin mami har kunne tana fadin masha Allah! dady yace me za a jira?Mu ai a shirye muke in sha Allahu gobe zan tafi abujar mu sasanta dole in durkusa in nemi afuwa zan karbi lambarsa da adres kafin ku tafi Allah ya shige mana gaba ya kore dukkan fitina suka amsa amin al- ameen ya zarce da fadin amma dadi karya wuce sati uku ayi komai a gama kowa BAKIN CIKI 3******11 kunga kuma zan sami wata shida anan abin zai yi daidai suka yi dariya mami tace gaskiya ne sati uku ai sun wa duk shirin da za'ayi kai Allah ka nuna mana lfy, murna cike da zukatansu bata misaltuwa mami kamar ta hadiye mama ta tasa ta a daki suka ci abanici tare bayan sallar azahar sukayi shirin tafiya haka ta baza mata kaya kala kala tun daga sutura zuwa kayan shafe shafe tace ta zafi duk wadanda ta keso ta cire kunya ta zabi yan tsiraru Al-ameen na taya ta shine ma ya jido mata kayayyaki masu yawa dadi ya kwala wa mami kira ta tashi ta fita mama ta dubi al- ameen tace wai ka manta da tsarabata ne yace ina sane kyale ki naiy in gani komawa zakiyi dasu ta dan shagwabe fuska kai dokta saboda Allaj baka san kunya ba maimakon ka taimake ni, ya zuba mata ido maimakon ka taimakeni ya maimaita a shagwabe tayi yar dariya tace don Allah in ta shigo ka gaya mata gani ma na shigon me za'agaya min mama ta sunkuyar da kai ya fara dariya yana fadin wai tsaraba tayo miki shine ta bari a mota tana jira ni in gaya miki wanda ya siyo abu ba shi yake daukowa ya bada ba? Mami ta dafa ta tace Allah sarki sakeena kyale shi karya gadi din so yake ya manna miki laifi dame dame kika kawo min cike da kunya tace fruit ne kawai mami tace Allah yasa da karot ciki suka kalli juna suna dariya akwai mami ta ce to shine ki ka ki gaya min abinda na ke ta marmari kwana biyu ban ciba ta yunkura da sauri tacr bari a kwaso miki shi ma ya mike yabi bayanta mami ta bisu da kallo tana dan murmushin jin dadi jim kadan suka dawo daddauke da ledojin guda uku manyan gaske mami taji dadi sosai tana sa albarka sannan ta mika wa mama rafar kudi dubu ashirin tace wannan dadinku yace in baki tasa hannu ta karba tana kada kai haka da yawa mami to nagade Allah ya saka da alkairi tace amin sakeena al-ameen yace mun gode mami bari inje wajen dadin mu za mu wuce ya wuce suka zauna jiran fitowarsa basu dade ba suka fito tare mama ta zamo daga kujera ta tsunna tayi godiya yace ba wani abu Allah ya sauke ku lafiya tace amin suka rankayo waje al-ameen ya daga murya yace iya ta na wuce suka fito tare da ladi sukayi masa sallama sannan suka karasa wajen mota sai da suka bar get suka koma cikin gida suna masu addu'ar sauka lafiya ,, lafiyar kuwa suka sauka cikin yarda ubangiji ya sauketa gida ya taimaka kwaso mata kaya zainab ta fito ta tarbe su bakinta har kunne tace ga amarya ga oga shirin yayi yace kin ci ziro zainab kuma baki da sa'a da kin fada daidai Allah kadai ya san yawan ladarki tace sir zan gyara ga amarya ga ango....yace kin makara". Zai wuce ta karbi kayan hannunsa no sir ai ba wani sai ogan mu yana yar dariya yace kinyi gaskiya zainab kina damaki ashirin tace"thank yau sir mama tasa musu baki har wata godiya ki ke yi ki na kware baki kar kiyi karatu yarinya ki jira bonus" ta bude kofa suna dariya dr al-ameen ya ce ina ruwanta zainab ta amsa nima shi na gani ke ko tukuicin baki bani ba amma kina sawa oga ido suna tsaye tsakar daki ya laluba aljihunsa ya zaro dubu biyar ya mika mata karbi wannan ki kyaleta kawai sai mun hadu gobe -tana dan murmushin jin dadi jim kadan suka dawo daddauke da ledojin guda uku manyan gaske mami taji dadi sosai tana sa albarka sannan ta mika wa mama rafar kudi dubu ashirin tace wannan dadinku yace in baki tasa hannu ta karba tana kada kai haka da yawa mami to nagade Allah ya saka da alkairi tace amin sakeena al-ameen yace mun gode mami bari inje wajen dadin mu za mu wuce ya wuce suka zauna jiran fitowarsa basu dade ba suka fito tare mama ta zamo daga kujera ta tsunna tayi godiya yace ba wani abu Allah ya sauke ku lafiya tace amin suka rankayo waje al-ameen ya daga murya yace iya ta na wuce suka fito tare da ladi sukayi masa sallama sannan suka karasa wajen mota sai da suka bar get suka koma cikin gida suna masu addu'ar sauka lafiya ,, lafiyar kuwa suka sauka cikin yarda ubangiji ya sauketa gida ya taimaka kwaso mata kaya zainab ta fito ta tarbe su bakinta har kunne tace ga amarya ga oga shirin yayi yace kin ci ziro zainab kuma baki da sa'a da kin fada daidai Allah kadai ya san yawan ladarki tace sir zan gyara ga amarya ga ango....yace kin makara". Zai wuce ta karbi kayan hannunsa no sir ai ba wani sai ogan mu yana yar dariya yace kinyi gaskiya zainab kina damaki ashirin tace"thank yau sir mama tasa musu baki har wata godiya ki ke yi ki na kware baki kar kiyi karatu yarinya ki jira bonus" ta bude kofa suna dariya dr al-ameen ya ce ina ruwanta zainab ta amsa nima shi na gani ke ko tukuicin baki bani ba amma kina sawa oga ido suna tsaye tsakar daki ya laluba aljihunsa ya zaro dubu biyar ya mika mata karbi wannan ki kyaleta kawai sai mun hadu gobe.............. - Takarba mama na fadin ok mun gane dama da mun ganki da manyan maki mun san na coge ne yace eh ba komai zainab tayi dariya tace na gode sir sai ka fito ta wuce tanayi wa mama dariya yayi mika yana salati sannan ya zauna a kujera ta ware ido tace zama naga kayi kar in zauna tace gida ya kamata kaje yace korata ma kike yi ta kada kai ba haka bane zai fi kyau kowanne mu ya samu yay wanka ya huta kafin magariba ta karasa ya munfasa yace haka ne yi hakuri don Allah sai ina ganin kamar an daura ne unguwa muka je muka dawo ta ware ido iye eh wallahi kiris ya rage in fada katifar nan in kwanta fuska yamutse tace wasa ka ke kin san Allah bada wasa nakeyi ba a dai bar kaza cikin gashinta miko min ruwa in sha in gudu,,Tace sai dai in karbo maka wajen zainab ka sha na firij dina babu sanyi yace to barshi kawai bari in tafi ya zubo mata ido suka kalli juna yai dan murmushi tace mene ne ya mike yana fadin nothing sai munyi waya ko ta kada kai a ranta race dokta ke nan ya wuce tanataka masa tana fadin ina sauraronka tara kashi har mota suka y irin sallamar sa suka saba yaja mota ya wuce ta tako a hankali daki irin son da ala- ameen yake mata shi yasa take jin kanta ita wata ce ta shige wankanta ta fito ta sauya kaya ta kwaso littatafanta ta baye a kasa ta fara karatu tana yi tana zuba hamma barci ne sosai yake son kamata gashi yamma tayi babu kyau yin barci a wannan lokacin don haka ta aje littafinta yunkura zata tashi da nufin fita wajen zainab suyi hira ko barcin ya fita idonta, wani sauti mai dadi ya fito wayarta alamun sakon ya shigo ta dubi wayar kawai ranta ya kwao mata zakin zuciyar tane tasa hannu ta dauko tana dan murmushi ta bude sako amma sai taga sunan yaya ali dake rubuce kamar haka, Assalamu alaiki ya kanwata sai yau nayi saranda na sauke hannayena daga rokon soyayyarki a yau na yarda na amince kin sami gwarzo jarumin da nake da yakinnin zai shaer miki hawaye tamkar yadda nake zaton zan miki shine nake da tabbacin zai rike ki babu gori balle mugun kallo ko zargin kin taba yin wata mummunar rayuwa a. Baya amma ina so ki aje a ranki wallahy wallahi!!! Wallahi!!! Al-ameen bai fini sonkiba sai dai zanyi hakuri ne saboda ke shi kika fi so a gunsa duk farin cikin ki yake to nima ina son farin cikin ki mama shi yasa na ke son abinda kike so ina muku fatan alkari tare da tayaku murnar sake haduwa da juna,,Yanyaki aliyu!! Hawaye kawai taji ya goce mata saboda. Tausayin yaya ali to doka tagumi tana kalubalantar kanta me yasa nake zama butulu akan son da yaya ali ke nuna min laifi na ne meyasa ban yarda. Na aure shi ba tun kafin mu sake haduwa da dokta ta goge kwalla ta kada kai abin ya dame ta kwari ta rasa inda zata sa ranta taji sanyi sai kawai ta nemo lambobin sa ta kira bugun farko taji muryarsa yana mata sallama murya na rawa take fadin don girman Allaj yaya ali kayi hakuri ka yafe min.. 148-yace mama kuka ki keyi me yasa tace dole inyi kuka yaya ali don ban taba sanin ni butulu bace sai yau komai ya faru laifina ne kamar yaya laifinki komai bana Allah bane tace laifina ne me yasa ban aure ka ba tun kafin mu sake haduwa da al-ameen kuma ni nasan kana sona fiye da tuna ni na me yasa na zama butulu akan soyayyar da kake nuna min ya numfasa ya dan kada kai yace saura reni da kyau mama ai yanzu mu ba yara bane dai dai gwargwado mun yi hankali gane komai shirin Allah ne ni nayi imani sabo dani ba mijin ki bane shi yasa aurenmu bai yuwuba alkawari ne sai kin auri al-ameen shi yasa Allah ya sake hada ku wallahi bana BAKIN CIKIN auren ki da shi illa iyaka ina ciwon rasa abinda ni nake so.. Abinda na rubuto miki a sakona har cikin zuciyata haka yake Allah ne shaida na saboda haka ki manta komai ke yar'uwata ce ta jini abar alfaharina a ko'ina kar ki sake zubda hawayenki idan har kin yarda kin amince da abinda nake fadi kin yarda? Ta sauke munfashi wasu kwallar suka sauko bisa kuncinta tace na yarda da kai yaya ali ya ce to share hawayenki tasa bayan hannu tana sharewa kafin tace na share ya yi dan murmushi yace zamanin kuka ya wuce har abada da yardar Allah farin ciki muka fuskanta babu waiwaye yanzu gaya min ranar da kuka fara ganin juna duk a sume kuka fadi ko yasa dariya ta kubce mata ta cw wane irin suma yaya ali ah ya baza ku suma ba saboda murna ai so ba karya bane kanwata,,, , 149-tace hakane amma ina mai tabbatar maka shi din ma Allah ne yayi dole sai na aure shi wallahi da da gaske nake bazanyi aure ba sati uku muna dauki. Ba dadi har na bar makaranta saboda shi daga baya muka sasanta saboda abokinsa ya cika min ido yace baki kyauta ba kuma da kin zalunci kanki akan aikin banza don nayi rantsuwa kina son al-ameen to alhamdulilahi tunda Allah ya gyara komai sauranmu shan biki ko? Yayi dan murmushi ta sunkuyar da kai kin yi shiru. Tace me kake so in ce ki gaya min ranar shan shagali mu fara shirye shirye tace kaji yaya ali baku. Ne masu sanyawa ba yace eh gaskiya ne dama abba ya gayawa su baba za'a zo asa rana da zarar sun turo ni zan bada shawara kar asa da tsawo yaci gaba da dariya yaya ali ke nan yace ba dai kunya ki ke ji ba na sani to shi ke nan bari in kyaleki ki huta sai mun hadu a gida ko to shi ke nan Allah ya kai mu lafiya.. Yace amin suka danyi shiru jim sannan tace yaya ali ya amsa ina jinki ta sanyaya murya tace indan na gaya maka wata magana zaka yarda yace me zai hana tace ina sonka yaya ali ya yi jim shiru kana ya numfasa yayi dan murmushi yace to na gode ki gaida min angonki tace zai ji...bata karasa amsawa ba taji ya kashe wayar ta runtse ido tana mai da numfashi kwalla suka tsatso mata tayi sauri ta goge su ta jawo filo ta jin gina shiru tsawon lokaci sannan ta kada kai tace a fili Allah sarki yaya ali Allah ya kara maka dan gana haka zalika yaya alin jikinsa ya yi mugun mutuwa ya dade yana sakar zuciya sai dai kalmar da mama ta furta. Masa tayi masa dadi kuma ya tabbata duk lokacin daya tuna zaiji sanyi a ransa, 150- TABBATACCEN ALKAWARI duk inda ka duba kofar gidan uban dawaki jama'a ne kwatsam babu masa ka tsinke motoci kuwa sun tasar ma bakin babban titi zan so mai karatu ya tsamo mutum daya cikin wadannan daruruwan mutanen ku kwatanta irin FARIN CIKIN da yake ciki a halin yanzu kuma a wannan rana mai dimbin tarihi cikin rayuwarsu sanye yake cikin wani farin lallausan yadi yar ciki da wando hadi da mulun malun hula fara da farin takalmi. Fari hakan zai tabbatar da yanayin da yake ciki koba ka kalli fuskarsa ba,idan ka kalleta kuwa kai kace gonar auduga ne a haske da walwaki da annuri wajen kwatance,Ayi kurum ke nan tabbas shirun shine zaifi domin kwatancen bazai yuwu ba tsaye yake jikin wata makekiyar jeep yayin da wasu rukuni na manyan lokitici daga ko ina gida da wajr suka zazzagaye shi domin dai akwai wasu jajjayen kunnuwa su uku gab da za'a daura auren dr lawal ya sake ketowa da wasu tawagar bakin likitocin a matsayinsa na mai tarbar baki al-ameen ya tarbesu kusan dama sune kawai dr al-ameen yake zaton basu iso ba tawagar likitoci ne da wasu ma'aikatan jinya daga sakkwato ana ta musabaha baki yaki rufuwa kowa ka kalla ka san yana cike da farin ciki daga ciki kuwa waliyyai ne ke ta shirye shiryen gabatar da daurin auran cikin dan kankanin lokaci alhaji basiru ya mika amanar sakeena a hannun alhaji nuhu waliyyin dr al-ameen akan sadaki dubu hamsin... -nan da nan masu. Shela suka hau aikin su wasu tsofafin mata suka fara rangada guda makada da mabusan marafan lafai suka dirfafi ango rerawa suke yi abin sai wanda ya gani kwarai suka birge bakin turawan da ke tare da ango shiyasa suka zaro wayoyinsu suka fara dauka baya ga haka ga makadan nufawa nan birjik kowa na gwada basirarsa da kwarewar sa duk inda ango yake takawa kuwa kudi ne kawai yake zubdawa marokan da mawakan na kwashewa daga nan ma'aikatan hotel din da a ka kwaso daga minna da kaduna suka fara raba wasu manyan fararen ledoji guda biyu ake mikawa kawanne mahaluki dake wajan koda almajiri ne al-ameen ya bada umarnin a basji kamar yadda akaba kowa leda daya kayan kwalama ne dangin abubuwan da ake yi da fulawa watau (snacks) nama kala kala akwai na kaza rago da shanu jus iri iri da robar ruwa, dayar ledar kuma abinda rabonka ya tsaga domin dai babu abinda ba 'a raba ba,, Agogon bango da na hannu da wayoyin hannu dardumar sallah kai harda takalma da huluna turare masu zafi banda kana nan abubuwa irin su tawul hankici birorin rubutu da littafan addini da sauran abubuwa zaiyi wuya ka bude jakar ka ka sami kyauta kasa da iri bakwai can kuma sai ga wasu kananan yara suna raba wata yar karamar jaka mai ban sha'awa bakin jakar a tsuke take in ka bude ka sha dariya domin babu komai cikinta face SACET SACET NA PARACETAMOL nan. da nan abokai suka kaiwa ango don ya ganewa idanuwansa lallai yau shagalin na likitoci ne yana karba ya kwashe da dariya turawan wajrn na taya shi su kansu. Abin ya basu al'ajabi har daya daga cikinsu yace lallai wanda yayi kyautar nan yana da basira hakan yasa al-ameen ya duba sunan take nan yaga (CUT CEE BARAKA) ya kada kai yana yar dariya yace best friend din ta ce aka ci gaba da dariya tare da annashuwa mai yawa...... .idan muka shiga daga cikin gida kuwa ita uwar gayyar kusan can ake kankat.wajen ado tayi canji sama da talatin tun kwanaki uku dafara shagalin bikin.dole tasa domin angonta yasa mata kaya akwati goma sha biyu.ita kanta dataga kayan ciki saida suka girgizata.musamman kit din na kayan karas.mai karatu nabarka da tunanin ya suke?kusan yanxu abubuwa sun kawo karshe.tunda anfara neman amarya ana zagawa da ita gun manya dan su samata albarka.inna saude ke riqe da mayafinta.sasan gidan aka zaga da ita.iyaye suka tofa albarkacin bakinsu.daga qarshe akajata falon abbanta.inda gabadaya yayunta suke zaune shi.suna shigowa ta wuce jikinsa,yawan shekarunta bai hanata gaucewa da kukaba.shikuwa abban farin ciki! yasanya shi zubda hawaye.yau autarsa zata tafi gidan mijinta hartakai ga bai iya cewa komaiba.sai yayunta ke mata fada tareda sawa auren albarka.kamar wasa sai yazama dakyar aka banbareta daga jikin abba.takoma dakin ummanta takifa kai ciki.kukan rashin ummanta takeyi.jitayi anzauna kusa da ita muryar yaya ali taji yana fadin kiyi haquri kitaso mama!kowa yashiga mota ke kadai angonki ke jira!nanda nan tadago ta dubeshi duk idanuwa sun kode jajir!sun qara fitowa waje. 153.yasake fadin pls.ki kwantar da hankalinki ki taso a fita dake,,kin san hanya ba kyau ko?batace komaiba.ta tashi zaune ya miqa mata hankici yace share hawayenki!ta karba ta share ya gyara zaman mayafinta ya rufe mata fuska.sannan yakamo bakin mayafin yajawo ta falo.inda su anty amina ke tsaye cirko cirko.yace gatanan na fiddo da ita.ku muje nizan sata a mota.ya wuce anata musu dariya.wasu na guda.makekiyar jeep din sabuwa fil!itace angon ya tanada don amaryarsa.yaya ali yasanya ta aciki.inna saude da baraka tare da zainab da anty amina suka take mata baya cikin motar.gabadaya motoci suka tashi aka jera kamar an rako shugaban qasa.sun iso minna karfe biyar da rabi na yamma.akwai wasu kosassun dawakai guda goma dake jiran isowarsu.akan mahadar dazata shiga dasu anguwarsu..amarya da zainab suka hau biyu.sauran takwas din kuwa ango da abokansa cikinsu harda turawan da sukazo daga rasha.gaba daya sun daura alkyabba da rawani na alfarma.musamman alkyabbar amarya tafi kowacce ado.sai wanda ya gani suka tankaya makada da mabusan sarakunan lafai na gaba da bayansu suna qayata sha'anin.motoci na biye dasu ga jama'a suna tafiyar qasaita anata dauka da kamarori kala kala.tafiyar minti talatin takaisu get din gidansu.mami ta fito ta tarbi amarya da turarenta mai shegen qamshi.tana fesa mata anata rangada guda.sannan takamo hannunta suka wuce gida sauran ayari suka take musu baya.sashi na musamman aka warewa amarya da yan uwanta.babu abinda babu na nau'in abinci dasu kala kalar kayan sha.sun cika wani dan matsakai cin sito.sai abinda kake sha'awa zaka debo kaci. BAKIN CIKI 3***12 bayan anci abinci sallar la'asar aka gabatar data riskesu a hanya.bayan magrib da isha'i motoci suka sake kwashesu sai gidan amarya.wanda layi biyu kacal ne a tsakaninsu.dukiya taji jiki.irin dukiyar da aka zubawa mama agidan sai ka rantse da Allah baza a kwanta a kabariba.shikansa tsarin gidan abin kallo ne.bayan yan rakiya sungama bawa idonsu abinci.motoci suka sake dibansu suka maida wajen mami.amarya kawai aka bari dan bawa ango damar hutawa da amaryarsa.ganin basuda isashen lokaci suma gobe lahadi zasu koma zariya.karfe tara ya raka bakinsa hotel dindaya kama musu.shikuma yadawo gida cike da zumudi maras misaltawa..ita kuwa amarya tuni tayi wanka saboda zafin datakeji.tasake caba ado ta qame tana ta zuba qamshi.kawai sallamarsa taji cikin dakin gabanta yayi mugun faduwa.ta amsa masa tanajan mayafi.yatako a hankali yazo gaban gadon ya zuba mata ido.tsawon lokaci sannan ya sauqe numfashi..yazauna gefenta ya duqa sosai.yaleqo fuskarta suka hada ido.tayi murmushi tasadda kanta qasa yayi dariya yace amarya kenan.yadauke mayafin ya zura mata ido.yayin da yake juyo fuskarta gareshi.ta dubeshi tana murmushi kafin tace sannu da zuwa!yace kezanyiwa sannu kin iso lafiya?tadan murmusa lafiya lau.yace to alhamdulillahi.dukkan godiya ta tabbata ga Allah.daya nuna mana wannan rana dabamu taba mafarkin zatazoba.155.ya lalubo yatsanta ya runtse cikin nasa ya nisa sannan yaci gaba abinda nakeso dake shine ki kwantar da hankalinki muyi zama na amana wannan zama dazamuyi bana soyayya bane zalla a'a harda ibada.mudauka hanyar aljanna muke nema.ina fatan zaki zama mai bani hadin kai har qarshen rayuwarmu.ta dubeshi ido taf kwalla.tace insha Allahu zaka sameni mai sadauqar da rayuwata a gareka.tareda bin umarninka muddin bai sabawa shari'ah ba.kwalla suka sauqa bisa kuncinta ya zura mata ido sosai.yadan kada kai.meya kawo hawayen? yayi sauri yajawota jikinsa.no pls bansan dalilin wannan kukanba.murya shaqe tace farin ciki dokta! bantaba tsammanin zansamu nutsuwa kamar daba.azatona rayuwata tagama rushewa.amma sai gashi kanata hidima dani tamkar zaka auri.......yayi wuf ya rufe bakinta.bana sonji.kawai kiyi shiru idan bazaki fadi alheri ba.ta zuba mishi ido shima nasa sun fara kadawa.ya share mata hawaye.kinga tashi muje muyi alwala muyi sallah shine zaifi mana kyau.yaja hannunta yakai bayi fara yi ki fito.tayi ta fito.shida ya shiga sanda ya watsa ruwa tukun yayi alwar ya fito.ya jagoranci sallar raka'a biyu tareda miqa godiya ga Allah........ya juyo gareta tana miqe kafafunta saboda gajiya.yace in kwanta? tace kwanta mana waya hanaka?nazaci za a min irin na rannan ne a koreni inaji ina ganin abinda nakeso.tayi yar dariya.mesa baka mantuwa?yayi lum da ido!yace sharp brain.!ya qara bata dariya tace ai yanxu ban isaba,,,kayi kwanciyarka mai gida... .kawai taga ya yada kai bisa cinyoyinta kunya ta kamaata.ta kauda kai daga kallonsa.yasa yatsansa yamaida fuskarta.yace kalleni mana.mekike nufi da kauda kai?ta yamutsa fuska tace ina na kai shi? yayi dariya.wai naga har paracetamol kuka raba wai ku doctors ko?tace babu ruwana aikin baraka ne.tace alqawari ta dauka sama da shekaru biyar dole ta cika.gashi nima tasaka min ajaka dazu dazasu koma.yace kuma wlh ta birge har dr begas yasarawa basirarta.sai dai kun mance baku rubuta dose ba yakamata agayamana nawa nawa zamu sha?tayi dariya ai yawuce dokta.in,miqo maka kasha?.kawo min.tace to dagani.ya manne ido daya yace nanfa daya.ta watso masa harara.yayi murmushi.yace kinajin yunwa ko?takada kai.yace aikuwa ko bakiji yunwa dole kici tsarabata..tace dole?yace yazama wajibi ne yau inshayar dake madara inji manzon Allah.kinga kuwa dolene tayi shiru tana kallonsa kamar yadda ya zubamata ido.karfe biyar na asuba da kwata taji ana bubbugata a hankali tabude ido taga fuskarsa dafda tata.yasa mata ido za a iya tashi koda sauran gajiya?taja mayafi ta rufe fuskarta yayi dariya.yasa hannu ya yaye rufuwar.ta mulmula ta dirqa tadayan side din tafada bayi.yanata dariya sannan yanufi sallaya yatada kabbarar sallah.157.yayi nafila kana yakawo farali.kafin ya kammala tafito ta kintsa ta daura hijab.ta fara sallah.sai da ta kammala tsaf harda azkar din safe.sannan ta juyo ta dubi inda yake.yana kwance bisa shimfida.yasa hannu yayi kiranta.ta miqe ta nufi gunsa ta zauna gefe sannan tace ina kwana? yatashi zaune yabita da kallo yace qalau na kauna kefa?tace nima yace da kyau!kinsan wani abu?ta girgiza kai.to rufe idonki.tayi murmushi ta rufe.cike da annuri.ya tura hannu qasan filo ya zaro dan mukulli.yakamo hannun damarta ya damqa mata.bude ki gani.ta bude ta bishi da kallo dan mukulli nagani.yace hausawa sunce yaba kyauta tukuici.wannan shine tukwaicin kyautar kanki daki ban jiya.wata yar mota ce kiyi maneji.kanta yayi gingiri gin dokta shine......ya nuna mata alamun tayi shiru banson ji ok?ta wuce jikinsa ta qnqame.ban cancanci wannan ba dokta!don Allah kadaina wahalar da kanka akan......ya daka mata tsawa akanme? nace akanme? ta gigice cikin kuka ta kasa magana yace wallahi! wallahi!!wallahi!!!idan kikasake aibanta kanki ayau zan barmiki qasarnan.sai ranar da kikayi hankali zandawo.kina jina?haba!jiya jiya fa kika min alqawari? kina nufin abaki ne kawai?to wlh bazan dauka ba.bazan jure jin lBAKIN CIKIN Lafazinki susa min hawan jini ba.kin gane? tafada jikinsa ta qanqamesa sautin kukanta na ratsa kunnuwansa.shiyasa zuciyarsa taci gaba da tafarfasa..don baison jin kukanta sam.haka kuma bayaso taci gaba da aibata kanta.abinda yafii tsana da kyama kenan.dan haka ya kyaleta taci gaba da zubda hawayen.amma yadda ta qara qanqamesa kamar zata shige jikinsa.shiya tabbatar masa da lalle haquri take bashi dukda bata furta da bakintaba. hakan yasa fushinsa yadinga sauqa harya rabu da zuciyarsa.yabar masa tausayin amaryarsa kawai..ya tallafo kanta yasauqe numfashi ya sassauta murya.tun ranan da Allah ya hada ni dake ya manna min matsanancin sonki a zuciyata har rana mai kamar yau. Banji sassauci ba.duk wani abu dakikaga nayi a halin yanxu dama shiryayye ne.tunda mafarki nane kawai yazama gaskia.karkiyi mamakin irin tarairayar da zanmiki cikin zaman da zamuyi.kiga kamar shekaruna sun wuce hakan.ni a wajena dole inyiKARA'IN Soyayyarki.duk abinda na shirya mana a farko sai na nuna miki.tunda ubangiji ya nufeni da mallakarki.idan kuwa shekaru basu hanani dawowa yaroba.banga dalilin dazai hanani aiwatar da abunda nayi niyyaba.don faranta ran wacce ta faranta mini,,,,,ya dago fuskarta idanuwa sunyo jajuz.yaci gaba pls kidena kona zuciyata da zafin hawayenki.ta zura masa ido na tuba dokta!yayo dan murmushi amarya bata lefi. Kota kashe dan masu gida.tace gara da kace wai.ya goge hawayenta baki yarda ba? yanxu ki kamo waleed ki yanka ai babu abinda zanyi.illa in miqo miki waleeda itama ki yanka duk cikin nishadin amarci ne.159.tace Allah ya tsareni nazaama mahaukaciya kenan!ba amaryaba.karka sake min irin wannan misalin ya lakucr hancinta nima karki sake min asaran hawayenki.tace idan bakason hawayena kadaina min hidima..ya dubeta yace uhmm....to shikenan nadena.tamiqa masa yatsanta promise? yace bawani promise.karkiyi mini wayau maman waleen.ta watso masa harara.yafara dariya ai gaskia kisan nanda watanni tara zuwa goma zaki haifi ameer ko ameera.kinga kuwa hidima takama babab waleed da waleeda uba awajen ameer da ameera.ta shagwabe fuska takai masa duka a kirji.ya kece da dariya yakwanta a filo yana kallon shagwabar datake masa.zaka dace da roqo tace masa wannan irin kirari?yace eh bandeji haushiba..tayi dariya ta lallabo jikinsa nagode dokta Allah qara budi na halas!ya tallafota ameen bebina.abinda kawai nakeso ki rinqa fadi kenan kinji?tayi far da ido insha Allahu.good sai gari yawaye muje kiganta tana motor park.ta dada shigewa jikinsa double thank sir!sir sis!?babu sir a wannan gidan daga darling sai cweethrt sai honey. Sai sugar da mazarkwaila.ta fashe da dariya tana kada kai.yaci gaba da nishadantar da ita tuntana ji har bacci mai dadi ya saceta.shikuwa farin ciki ya hanashi bacci gani yake tamkar a mafarki.wai yau shine tare da sakeena?kana ya aje numfashi yace Allah nagode maka. I60.qarfe takwas da rabi wayarsa dake silent take hasko wa alamun ana kiransa.yasa hannu yadauka mami ce take kiransa..yayi sauri ya amsa sannan tagayamasa direba nanan zuwa da abinci safe.yayi godiya suka kashe wayar.ya dubi mama dake kokarin tashi zaune na tasheki koh?tayi lum da ido takada kai dama yakamata intashi.kiyi me?tace inyi wanka inshirya.kafin baqi su fara zuwa.yace gaskia ne mami ne takkira waya wai direba nanan zuwa da abinci kafin ya iso jekiyi wankan tace to.ta sauqa tashiga bayi ta tsalo wanka tadawo baya dakin.taci gaba da shirinta.kafin wani lokaci tahade kanar sarauniya.tafar a gyaran gado kenan taji sallamarsa shima yahade.da jar shadda mai duhu suka zubawa juna ido sannan tayi murmushi tajuya taci gaba da aikinta.ya matso yakama yana tayata.yana fadin kinkalleni ki dauke kai.banyi kyau bane? tace aidama kai mai kyau ne dokta!rudewa nayi nakasa magana.ko?kamar yadda nima na gigice? aida kika waigo kiris ya rage na zube qasa.sai kuma kika dauke kanki.tace ashe na taima keka?yayi yar dariya kintaimaki kanki dai.kamar yaya?idan nazube.a sume zaki iya kwasata? tafara dariya Allah yashiryeka dokta!wayarsa taqara haskawa daga can inda take yashe .yasa ta miqo masa tana fadin mami ne kuwa.yakarba da sauri yadanna ok. Hello mami!tace wai ina kake ne tun dazu?naketa kira?yace ayya yi haquri mamina wanka nashiga.tace to direba na waje fiyeda minti talatin wai baku fitoba.ai baiyi maganaba mami mai makon yataba kararrawa? sun ciki shirme mutanen nan wlh. yakashe wayar yayo waje mama ta biyoshi harwaje.yana zaune yatasa kuloli gaba sunata zuba hirada mai gadi.ganin dokto yasa duk suka miqe sukanufosa sukayi gaisuwa bai amsaba yafarafada.meyasa kuke haka?donme aka manna waccarqararrawar? kudaina maida kanku yan qauye gaku a birni..suka ce tuba muke dokta!yayi guntun tsakiyakama hannun mama suka wuce ma'ajiyar motoci.Da ita direba ya lallaba ya kwashi kayan abincin.maigadi yataimaka suka shigar falo suka fito.mama tadubeshi bansan dokta na da fishiba! shima ya dubetahaushi yabani wlh.ni banso mutum yarinqa qasqantar da kansa saboda wani.kawai yazo ya latsa kararrawako bacci nake zan sauraresa.ko uzurin kansa balle namami amma sun tasa kuloli gaba kuma hadda magajiya biye masa..ta qara matse yatsunsa Allah hucizuciyar wakilin marafan lafai.ya zura mata ido yanasoyayi dariya.yaushe kuma kika ban wannan rawanin.? tace dama can haka kake bawani sai kai babanwaleed da waleed ameer da ameera.ya bushe dadariya dai dai lokacin dasuka tsaya gaban motaranrufeta da tamfol,yace badan karki sake kukabadana qara wata kyautar motar.!tayi dariya wannan mata isa.tunda fushin dokta ya sauqa.buqata ta biya danshine farin cikina.yabita da kallo yarasa me zaicesaboda dadin kalamanta.yajawo ta jikinsa Allahyayimiki albarka.tace amin.toga motarki.ta ware idotace oh my god.!yasa hannu ya kwashe tampoldin.idonta ya nuna wata tsaleliyar farar mota.akallakudinta zai kai miliyon biyar.162.hannayenta bibbiyu ta rufe bakinta da wasa kakekoh?yace duk yadda kikace.tayi kwal kwal daido.kwalla na neman zubowa.ya murtuke fuska idankika bari hawayen nan ya zubo Allah zanyitafiyata.kinji na rantse.batasan lokacin datarungumeshi ba amma takasa magana tasan tanayi zatayi kuka.sai shi ke fadin zanso kice wani abubebina.don kalamanki nasanyani nishadi.tadago tadubeshi bayan ta tabbatar ta shanye hawayenta.banida kalaman godiya dokta! wlh na rasa mezance.kagayamin me zance dan Allah.?yakamohannunta yace zo muje kici abinci wata qila inkin qoshi ki tina me zakice.ta kwace hannunta tanazagaya motar kamar yar qauye..tasa bakinta tasumbaci motar.yakawo kuncinsa saura ni.shima tasakar masa babu wani noke noke.tace ngd ngd.ngddokta. Iluv u soo much iluv u yace nima haka murnarta isa haka yar shagwaba nafara jin yunwafa.tayi murmushi Allah ya temaki wakili muje kaci abinci yagirgiza kai yace wannan nadi yamin kina fasa min kaigaskia.tafigi hannunsa suka wuce tana waiwayarmotarta.yace kina tafe kina waige idan kikaci da bakiAllah bazan dagaki ba.a shagwabe tabe Allah motarne tacika kyau.! shima ya maimaita a shagwabe.ta fara dariya jitayi ya ciccibota ya sure ya na bari kigani kada kijamin ina tsakiyar angwanci.gabadayakunya ta kamata. yakashe wayar yayo waje mama ta biyoshi harwaje.yana zaune yatasa kuloli gaba sunata zuba hirada mai gadi.ganin dokto yasa duk suka miqe sukanufosa sukayi gaisuwa bai amsaba yafarafada.meyasa kuke haka?donme aka manna waccarqararrawar?kudaina maida kanku yan qauye gaku a birni..suka ce tuba muke dokta!yayi guntun tsakiyakama hannun mama suka wuce ma'ajiyar motoci.Da ita direba ya lallaba ya kwashi kayan abincin.maigadi yataimaka suka shigar falo suka fito.mama tadubeshi bansan dokta na da fishiba!shima ya dubetahaushi yabani wlh.ni banso mutum yarinqa qasqantar da kansa saboda wani.kawai yazo ya latsa kararrawako bacci nake zan sauraresa.ko uzurin kansa balle namami amma sun tasa kuloli gaba kuma hadda magajiya biye masa..ta qara matse yatsunsa Allah hucizuciyar wakilin marafan lafai.ya zura mata ido yanasoyayi dariya.yaushe kuma kika ban wannan rawanin.? tace dama can haka kake bawani sai kai babanwaleed da waleed ameer da ameera.ya bushe dadariya dai dai lokacin dasuka tsaya gaban motaranrufeta da tamfol,yace badan karki sake kukabadana qara wata kyautar motar.!tayi dariya wannan mata isa.tunda fushin dokta ya sauqa.buqata ta biya danshine farin cikina.yabita da kallo yarasa me zaicesaboda dadin kalamanta.yajawo ta jikinsa Allahyayimiki albarka.tace amin.toga motarki.ta ware idotace oh my god.!yasa hannu ya kwashe tampoldin.idonta ya nuna wata tsaleliyar farar mota.akallakudinta zai kai miliyon biyar.162.hannayenta bibbiyu ta rufe bakinta da wasa kakekoh?yace duk yadda kikace.tayi kwal kwal daido.kwalla na neman zubowa.ya murtuke fuska idankika bari hawayen nan ya zubo Allah zanyitafiyata.kinji na rantse.batasan lokacin datarungumeshi ba amma takasa magana tasan tanayi zatayi kuka.sai shi ke fadin zanso kice wani abubebina.don kalamanki nasanyani nishadi.tadago tadubeshi bayan ta tabbatar ta shanye hawayenta.banida kalaman godiya dokta! wlh na rasa mezance.kagayamin me zance dan Allah.?yakamohannunta yace zo muje kici abinci wata qila inkin qoshi ki tina me zakice.ta kwace hannunta tanazagaya motar kamar yar qauye..tasa bakinta tasumbaci motar.yakawo kuncinsa saura ni.shima tasakar masa babu wani noke noke.tace ngd ngd.ngddokta. Iluv u soo much iluv u yace nima haka murnarta isa haka yar shagwaba nafara jin yunwafa.tayi murmushi Allah ya temaki wakili muje kaci abinci yagirgiza kai yace wannan nadi yamin kina fasa min kaigaskia.tafigi hannunsa suka wuce tana waiwayarmotarta.yace kina tafe kina waige idan kikaci da bakiAllah bazan dagaki ba.a shagwabe tabe Allah motarne tacika kyau.! shima ya maimaita a shagwabe.ta fara dariya jitayi ya ciccibota ya sure ya na bari kigani kada kijamin ina tsakiyar angwanci.gabadayakunya ta kamata. ta rufe fuska da hannayenta tana salati.ya diretaa falon.ko nauyi batadashi ashe fafa lolo ce..ta watsomasa harara tace gemai gemai dakai dokta?yace tome akayi?ai na gayamiki sai anyi kara'i.ta girgiza kaihakane?to saura kara'in cin abinci.bismillah zaunasuka ciyar da juna cikin annashuwa.qarfe goma da rabi suka koma daki ya tsinci missed cal goma cikinwayarsa.yadanna yaga gabadaya dr lawal.ya dafe kaina shiga uku! ta dafe kirji da akayi me? yace missedcal goma sakeena yau na mutu wajen drlawal..tawangame baki maza kira karya sake kira.yakwashi sauri yana kiran layin yaqi dauka shima saidaya kira sau uku yana tuqi sannan ya dauka.danAllah malam karka dami mutane!ya kashe wayarsayabar dr alameen da salati.ya take mota dan kankaninlokaci yakaishi hotel din.yana shiga dakin yakamakunnuwansa yana i'am very sorry.! very sorry!!verysory!!! Suka fara masa dariya.dr will dake malami ne agaresa yataso ya riqesa manta dasu sun mantaangwanci kakeyi.yace thank you sir!ya bubbugakafadarsa bawani abu ya amarya?ya amsa lafiya lautake.yace dakyau.zamuje mu gaisheta daga can saimu wuce dan karmu rasa jirgi.yace yes sir!ina fatankunci abinci?yace munci yabi sauran duk suka gaisa.yana zuwa wajen dr lawal ya ballo masaharara.sai ya tsugunna yace ina kwana baba lawal?Dariya ta kubce masa.sauran ma dabasu san meyaceba suka kama dariyar ganin dr lawal yakai masaduka.yace masa bafa kai kadai ne mai mataba.mumamunaso muje mugansu.sannan soyayyar nan ba afi mu iyawa ba. yayi dariya yace nayarda na amsa laifinaamin haquri.yayi shiru yana kallonsa murmushi yayiyana fadin kun shirya mutafi? munshirya ango.ya juyaya tambayi sauran da turanci duk sun shirya sukafirfito da jakukunansu.suka rankaya wajen amarya.tasawo hijabi ta fito suka gaisa.minti goma kacal sukayi cikin gidan suka fito dr lawal da dr alameen sukakaisu filin jirgi suka tashi zuwa legos.inda zasu tashizuwa rasha.shikadai yadawo gida domin dr lawalyadau hanyan zariya.gidansu yaja birki ya tsayaharsuka gaisa da baki haryana tsokanar baraka inafata kema kin kora paracetamol din.?tace ai wannan dole ne over dose ma nayi saboda inada likitoci.yafitoyana dariya suna tayashi.ya wuce shashin mami sukagaisa yazarce na dadi suka gaisa daga nan yaketambayarsa yaushe zasu wuce?yace bayan sallarla'asar.tare suka bar gidan a motar dadin yamasarakiya wasu harkokinsa.sukuwa yan rakiyar amarya mami tasa aka maida su wajen mama don kammalawasu al'adu.bayan sallar azahar dadi yadawo da doktalokacin baki sungama shiryawa komawagidajensu.godiya maiyawa da kyaututtuka suka samugun mami da dadi.haka dokta yanuna farin cikin saakan karamcinsu.bus din kamfanin dady mai daukar mutum talatin ita ta kwashesu suka bar mama nakwall. BAKIN CIKI 3***13 Yasa mata ido ko yanzu din ma idanuwan na ta tamsuke da kwalla ya girgiza kai yace karki dami. Kankinasan kina da masaniyar ajali sauka yake kodasababi ko babu da zarar kwanakin suka kare shi kenan an gama magana fatan mu kullum Allah yasatana cikin hasken kabari tace amin yasa yatsansa ya goge kwallar daya sauka kucinta please ya wuce ina.Fatan kin shirya zuwan ameera kafin in koma da saurita dube shi har da zame hannunsa a kafadarta yakece da dariya harda tureni tace me ka sani dole intoreka yace to ai ba ni na fara fadiba mami ce ta kosaitama ta sami takwara ita din ma bata sani ba kam!bai taba ganin irin wannan hararar ba yasa yake ci gabada kwasar dariya -mai da wukar mai jego duk ni kadai wannankallon please rage in sami na gobe ta make shi tanadariya ko tausayina ma babu abin don bakaga yaddajini ke zuba a jiki na bane take nan jikinsa kuma yayila'asar ya sake kamota yace Allah sarki bebina toAllah ya kara miki lafiya ina ganin ya kamata mu binciko dalilin yawan zubar jinin idan akwai yuwuwarmagance matsalar sai a tareta da gaggawa kogaskiya ne kara a bincika yace sha kurumin kiwannan dole ne tsakani da Allah ina son Ameera takada kai tana kallon sa ai na san baza ka daina fadiba yace "Thanks God da kika san haka yabi bebinsa da kallo sannan ya sumbace shi yace ko dadina Allahda ikonsa yayi yar hamma cike da fara'a yace"yausee" shi ma ya amsa ya kara sumbatar sa yace "whata sweet dady! Ta tabe baki tana kallon sa sun shararihira har mami ta dawo ciki tayi kwanciyar ta tabarsusuka kwana hira Washe gari aka sallameta bayan ya gama tattaunawada likitocin mata watau(gynea doctors) akan matsalarta wanda suka tabbatar masa akwai yuwuwartaimakon da za'a bata amma sai wani cikin ya samusun koma gida baki suka ci gaba da zuwa daga ko'inasuna ganin bebi yayin da angon karni ke ta shirye shiryen walimar suna adalilin bai fara aiba tukyna yasami damar zirga zirgarsa yadda yake so har zuwagobe suna kafin yamma gida yayi tankam da bakitundaga lagos har arewacin mu nan tun daga lokacinhidima ta kankam zuwa washe gari da ya kasancecikar suna hajiyar ruqayya mata sami zuwa a ranar dauke da alkairi mai yawa anci an sha a sunansaifullah an bar arziki inda yake Rana ta biyu sai da aka gyarewama jego ko ina sannan baki sukafara tafiya rukuni rukuni anti rabice kadai ta kwana hudu ta warwaregajiya sosai kana ta koma innasaude ke kula da wankan jegontahartayi arba'in tana je tana katatuta kwashi alheri mai yawa sukakoma tare da mami aka bar mamada dan bebinta maryam ta samomata yarinya zata kai shekara shabiyar tare suke zuwa makaranta tazauna mata da ameer a motasaboda ya ruka samu yana shannono isasshe to Allah ya raya shiya kwao Ameerar da ke ta fatansamu nan gaba -BAYAN. SHEKARU BIYAR. Satinda ya wuce ne akayi shagalin bikinnadin wakilin marafan lafai wandaakayi a fadar mai martaba sarkinlafai wannan yana daya daga cikinabubuwan da suka kawo shi wakilinmarafan kasar nan watau DR AL- AMEEN dalili na biyu don tafiya daiyalansa sakamakon makarantardaya samo wa mama taci gaba dazurfafa iliminta shi yasa bayanbikin nadin suke ziyarar bankwanatare da ban gajiya ga wadan dasuka sami halartar bikin nadin tunsha biyun rana suke garinfandogari da yaran su Allah daikonsa mama ta iske yan uwantada yawa suma sun zazzo ganin gidairinsu danlami dake sakkwato gakuma yaya ali da iyalansa shi yasafarin cikinta ya karu sukayi ta hirabar bayan sallar la'asar abubuwadangin abinci da kudade ta kawowa kawun nan ta da matansu Ta fito suna tasa mata albarka yayaali na dauke da karima(ameera)yar shekara daya da rabi dokta yabude mota yaran suka zauna gidanbaya da hafastu mai kula dasu yayaali ya mika mata ameera ya rufekofar yayin da mama ke shiga gabata zauna itama yaya ali ne ya rufemata kofar ta dubi shi tanamurmushi na gode yace Allah yatsare tace amin gaba daya sukayisallama da al-ameen sannan yashiga mazauninsa ya tada motasuka wuce ta dube shi tun kafinsubar layin tace ranka ya dade zakakaini wani gida nan bayan tashayace kina so muyi dare dai yau Aawallahi bazama zanyiba kawaigaisawa zamuyi in fito mantawanayi da muka fito wajen inna damun wuce yace ok amma donAllah sharp sharp kin san yanayinhanyar tace Allah shi taimakimarafa ya dan dubeta Dungurugunkuma? -tace me ya rage gaba kadanmurabus zai yi ya bar maka gadonyace har naji sanyi da kikacemurabus tsoran bakin ki nakejikinsan wakilin ma ke ki ka faranada min kawai naji dadi yace waiza'a min sarautar wakilin marabatayi murmushi tace bakawai baneakwai cancanta shima yaga dacewara tattare da kai yace uhm..kinsabafasa min kai wakiliyar marafanlafai ta dubi shi tana yar dariya daidai yana tsayuwa kan mahada indashagon danliti yake da Ameeara tafasa kara ta firgita kowa duk sukajuya suna tambaya lafiya hafsatutace ameer ne ya ja mata gashi Mama ta nuna shi kafara ko waime ya hadaka da gashinta nekullun sai kaja mata dadinsu yayidariya yace baki ganin shi baya dashi al'ajabi abin ke bashi ya ganshizalau zalau yana lilo ko dadina taceba wani muguntace da wasuidanuwansa kamar na agolannufawa, dokta ya saki baki suwaleeda nata masa dariya jim yanakallonta kafin yace ke maimaitaabinda ki kace kamar wa? Ta faradariya ai kaji abinda nace tace okdama idan bana nan zama ki kekina yankar min dadi akan wannanyar rigimar yar taki ko to dadinabin idon nufawan aka gani akarude ta tabe baki Allah shi kyautameye a idon zai bata amsa ke nanwani. Tsoho ya dauki hankalinsa dayake buga glass din tagarsa kumada alamun taimako yake nema nanda nan tausayi ya. Kamashi ya zuge glass dinyace sannu baba kaitsaye yace ataimaka min da kudi inci abincitake nan yasa hannu aljihu ya zarodari biyar ya mika masa ya wuceda sauri ko godiya babu tabbatuwarbabu hankali ke nan ya kada kai yamaida glass sama yana fadinALLAHU AKBAR ALLAH mungodemaka ki wannan kyakkyawanmutumin da gani yana da zubi dafulani ko ina yan'uwansa suke sukabarshi ya lalace haka yanzu hakaidan kika bibiya matsalar karamaceamma saboda rashin kulawa yasata girma shiru bai. Ji tabashi amsaba fuskarta na can tana kallon indatsohon yabi ya taba ta ta waigo anatse ta dube si ta ina zamu bitace ka hau titi kabi dama ya hautiti yana mamakin yadda jikinta yamace haka shi yasa bai gama hawatitinba ya tambaya yanaga kamarbaki tare damu Tayi dan yake ta kada kai kaga tsohon nan... Ya katseta bashi nake gaya miki ba abin gwanin ban tausayi ko ina yanuwansa suka barshi yana yawo tsirara? Gaba daya kayan jikinsa ba su rufe al'aurarsa ba mtsw.. Ya ja tsaki ta kara kada kai. Tace hummm..... A zatonka tshone ko?da kyar in zai girme ka tsabar rashin tsoran Allah ya maida shi haka banganeba tace a takaice shine DANLITI... Yayi shiru yana dawo da tsohon cikin kwakwalwarsa nan kwanar zaka shiga yaji tana fadi yasaki siginal ya fada har suka ja birki kofar gidan maman fati ba wanda yace wani abu game da danliti ta kalli gidan yana nan yadda yake sai dai akwai mutane a. cikinsa ta dubeshi tace kaga wancan gidan ciki ya ajeni ya rinka cin zarafina ya murtuke fuska yace donme kikace in kawoki nan tace zan gaida maman fati ne matar da ta rinka taimaka min da abinci da sutura harma da kudi.yace ina ne gdan -ta nuna na wanda zuke tsayegabansa yace maza ki shiga nimakice ina gaisheta ta wuce da sauricikin gidan ta bar dokta zuciyarsana tafasa baya son ganin gidanamma idonsa yaki daina nunamasa shi yan mintoti kalilan mamata fito tare da maman fafi cikinmurna har kunne tana fadin inayaran suke, gasu nan a mota tadan duka suka gaisa da al- ameensannan mama ta bude mota ta gayara duk suka gaisheta ke mamahar kinyi uku tace ga sunan kumakina gani lallai ba shakka Allah yaamfana miki su tace amin nagodetace nike da godiya wannan irinhidima Allah yasa bata gama rufebaki ba al-ameen ya miko wasukudade yace ki kara mata ta amsata mika mata zasu kai dubu gomabaki sake ta karba tana godiyamama ta shige mota tana fadin tosai wani lokaci Allah ya sauke kulafiya na gode da zumunci mamaAlhaji nagode yace ah muke dagodiya yaja mota tana daga masuhannu Sun hau titi sosai bakin al-ameen amace yake mama ta dube shi tacekana mamaki ko ya numfasa yaceke dai bari lallai Allah yayi gaskiyabaya zalunci baya son mai zalunci"anyway"mu koma can inda kikaraina min wayau ki kace ido kamaragolan nufawa ko? Tace na shigauku yau yace sosai kuwa tunda kintaba dadina tace ayi min afuwa abari idan na samu abba na sai karama kace ido kamar agolan fulaniyace ke ki kasan wannan idan ma Agolan KATSINAWA ne "idon't care" tace wayyo Allah tubanake yi Allah ya taimaki wakilinmarafa Baban waleed da waleedauban Ameer da Ameera' yayai yardariya yace ga tsoro ga neman fadaeh ba komai muje a hakan yacekin san wani abu gaskiya nextweek zamu tafi tace ayya na zacizamu jira waleed kaga sati nasama za suyi hutu kuma hutunkarshen shekara ne yana da tsawozaiji dadi idan ya kasance taredamu ya dubeta yana murmushinaji maman yara ina fatan rokonaya karbu ya kamo yatsunta yamatse yace babu wani rokon ki daba zai karbu ba a waje na muddinnafi karfinsa karki manta kina gabada dukkan abinda na mallaka hakakuma idan kin dake iyayena dukduniya bani da abinda na fi sokamarki raina yana kaunarkisakeena babu abinda zaki nema awajena in hana ki insan karshenmagana? Daya yau na zama Drsakeena kawai ta tuntsire da dariyakai dokta na wannan shinebanbarakwai yace namiji da sunansakeena ai duk cikin so ne tace nayarda domin nima na shagala dayawa kaga idan na dubi abba nayana tafiya da kansa na tuna iringagarummar gudummawar da kabayar Allah ya taimake mu sai injikamar in mika wuyana ince kayanka kullum gani nake ayyukanasunyi kadan ya dubeta ya yimurmushi ya kara matse yatsuntayace kiyi shiru kawai karki sanirusa kuka tayi yar dariya yajahannun bakinsa ya sumbata yace "ILOVE YOU" tace ME TOO ya dubetaSO MUCH ta kai hannu zata turahular sa ido waje tace kai na turerawanin wakilin yace aikaji dadi yahadani da aiki dole sai na nadafarin. Nan bisa kai idan zan shigajama'a - tace kuma yayi gaskiya fa shirawani ai musulunci ne kuma yanakara kima da kamala dadin dadawayana yiwa dokta na kyau yace banson zakin baki tura shi kawai kigaya min inji dadi tasa hannu tatura hular goshi tace SO MUCH shike nan? Yaran suka ji sun daukidariya a bayan mota waleeda hardatafi ameer ya mike ya ziro kansaya kama hular dadi gyara hularkakaji suna ta dariya yace gyara mindadina momin nan bata ji ko yagyara masa yana fadin ido kamaragolan nufawa suka kece da dariyatace oho dai dara taci gida yacedadina kayi shuka a idonmakwarkwa bai dai gane karinmaganar ba dariya kawai yake yi azatonsa dadinsa ya rama ne shiyasa mama ke ci gaba dayi masudariya motarsu na cilla gudu a titi.ALHAMDULILLAHI sai muce Allahya sauke su lafiya a wannan tafiyada wacce zasuyi zuwa rasha sati nasama haka nima ina godiya gaAllah daya bani ikon kammalawannan fararren labari zanyiamfani da wannan dama in rokiaddu'a wajen bayin Allah mutaimaka da addu'a ga yan'uwanmumusulmi wadanda suka tsinci kansucikin irin wannan musiba damakamatansu, TAKU HAR KULLUM YAR MUTAN KAGARA KARSHE ALLAH HADAMU A WANI LITTAFI. COMPILED BY ESHAAT SMILER HOM OF HAUSA NOVELS DOCUMNTS WASPP08066360176 FOR MORE