❤⚘ E X I L E D P R I N C E ⚘❤ 🔥👑 ( LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) STORY & WRITTEN BY : MEERAH ⚘🕊 【THE ROYALTY LOVE ❤🌹】 【 BOOK ________4 📚🔥❤ 】 😂😂😂 TO BARI MU GA WANNAN SABUWAR DRAMAR YA ZA TA KARE 🤣🤣 SAKO GA MA SU YI SHARING LITTAFI BA TARE DA SANI NA BA ! * ALLAH NA GANIN KU IN NI BAN GANI 😴😴😴 * _______________________♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡______________________ { P A G E ............ 1 & 2🌹🕊} ▪SRORY 🔥 A hankali Malik ya mike ya na fadin " ki kontar da hankalinki , ina nan zuwa gobe " ya na gama fadar haka ya sauko wayar ya katse kiran haka ya ci gaba da latsa wayar shi , ya dan jima kafin ya kai wayar a kunne babu ko sallama ya ce " ina jiran ka Saudiya gobe , tare da Familyna " ya na gama fadar haka ya sauko wayar ya katse kiran ya mike tsaye kai tsaye stair ya nufa ya Haye ya koma bedroom din su ko da ya shiga dressing room ya wuce , ya shirya kayan su cikin trolley guda babba , ya fiddo ta ya ajiye bakin kofar sannan ya nufi bed din su ya haye ya na sauke ajiyar zuciya , ya lumshe idanunshi ya na a haka ya jiyo Muryar ta ta na fadin " yaya Zayd , gida za mu koma ? " ba tare da ya bude idanunshi ba ya ce " No , ke a nan za ki zauna , ni ma ba zan jima zan dawo " " what ? me ya sa ? ni gaskiya tare za mu tafi , ina so na ga su Ammie " ta fada kamar za ta yi kuka a hankali ya ware idanunshi ya juya su na fuskantar juna ya ce " ki yi hakuri Cutie ki zauna a nan , wlh idan ki ka bi ba zan samu nitsuwar yin aikin da ya mayar da ni , idan ki na nan hankali na zai fi konciya , ba zan so wani abu ya same ki tare da babyn mu ba " " ni gaskiya yaya Zayd tare za mu tafi , ka na bukata ta a kusa da kai , ni wlh ko ka tafi ka bar ni sai na bi bayan ka , in ya so na bace saman hanyar " " please my Cutie , kar ki raba min hankali gida biyu , kin ga ko kwana biyu ba zan yi ba zan dawo " a hankali ta juyo ta ba shi baya , kawai sai ta sakin mishi kuka ba tare da ta ce komai ba " ya salam !" ya furta cen kassan makoshi a hankali ya kai hannu ya janyo ta jikin shi ya hade bayan ta da kirjin shi ya ce " shikenan , rigimamiya kawai, mu tafi , amma wlh ba za ki fito bedroom din ki ba " wata yar karamar dariya ta yi dama ba kukan ta ke ba kawai dai ta san duk lokacin da ta ke mishi kuka ya na yi mata abun da ta ke so cikin sanyin murya ta ce mishi " Baby , na yi kewar Su Ammie sosai , da mama , da Nesi , da Aunty RIANNA , Aunty Tesnim ........ " cikin nitsuwa ya katse ta da cewa " uhm uhm , ki ce duk Saudiyar ma kin yi kewar ta " wata yar karamar dariya ta yi kafin ta ce " Eh , na yi kewar Saudiya sosai " a hankali ya matso ya manna mata kiss saman forehead kafin ya ce " su ma sun yi kewar ki my Cutie , now rufe ido ki yi barci " noke mishi kafada ta yi ta na fadin " ni ba barcin da zan yi , ina farin ciki Sosai za mu koma gida gobe " a hankali ya dan matso kusa da ita , murya kassa kassa kamar mai rada ya ce mata " okay , mu yi wani game din , har yanzu ban koshi ba " hararrar shi ta yi ta wutsiyar ido , tun kafin ta ce wani abu ya riga ta cewa " Matsalar wannan katon cikin naki na tare min hanyata " turo mishi dan bakin nan nata ta yi ta na fadin " ni ka daina ce min me katon ciki " " okay , okay , yanzu dai ba ni na sha , har yanzu yunwa na ke ji " hannu ta kai ta janyo duvet ta rufe jikin ta , har da kai , kafin ta ce mishi " no , ni barci na ke ji " marairaice mata murya ya yi ya na fadin " please my Cutie , wai kin ji wani dadi da ki kara ? Allah ji na ke kamar na kama da wuta , please ki yi wani abu a kai mana " wata yar karamar dariya ta yi , amma ba ta ce mishi komai ba shi ma bai ce mata komai ba ya janyo duvet din ya shige ciki shi ma sai da su ka gama buga wassan su , sannan su ka yi barci , har yanzu dai bai sauya ba da wannan muguwar sha'awar tashi , dan sai da ta dinga rokon shi ya kyale ta , ta na yi mishi magiya , sannan ya hakura ya bar ta , shi ma dan ya na tsoron ya ji wa Baby Nayel ne ciwo ya hakura , ba dan haka ba sai dai ta kwana ta rokon shi ba zai bar ta ba ▪BAYAN SALLAR ASUBA ⛅ tsaye Malik ya ke bakin kofar shiga parlourn , ya na sanye da wandon jeans black color , da T-shirt red color , ya daura wata jacket black color da ga sama , ya na tsaye sai faman duba watch din hannun shi ya ke ya na tsaye a haka Inaya ta fara sauko stair , ta na sanye da wata Abaya pink color , sai dan karamin hijab din ta white color dai'dai kirji , ga katon cikinta ya yi tsaye a hankali ta ke sauko stair din , tun da ta fara saukowa ya tsare ta da ido babu ko kiftawa har sai da ta karaso gaban shi ta tsaya , ta na shagwabe fuska , ta na faman turo bakin nan nata kamar ya ce zai yi mata kiss matse gera ya yi ya na nuna mata hanyar fita parlourn ya ce " wuce mu tafi , da wani katon cikinki kamar ball " murguna mishi baki ta yi ta na yi mishi hararrar kassa ido kafin ta daga kafa ta fice sai da ya kashe duk lamps din parlourn , sannan ya bi bayan ta su ka fita kai tsaye get din fita gidan su ka nufa , ta na gaba ya na bayan ta su na fitowa gidan ta ga motar shi bakin kofar an yi parking din ta , ga gateman nan tsaye geffen ta su na fitowa Malik ya bude mata kofar motar ta shiga a hankali , sannan ya juya ya yi wa gateman magana kafin ya juya ya nufi wajen driver ya shiga ya tada motar kai tsaye ya nufi airport su na isa , su ka shiga private jet din shi , lokaci guda Jet din ya daga ya nufi kassar Saudiya ▪AFTER SOME HOURS ▪MASARAUTAR SAUDIYA ❤ Misalin karfe 9 na safe , jirgin su ya sauka a kassar Saudiya tun da ya shigo kassar ya ga komai ya sauya mishi kamar ba Saudiyar da ya sani ba bai gama shan mamaki ba sai da ya isa bakin kofar Daular Saudiya a nan ya ga wasu status guda biyu na lions sun bude bakunansu , ga wasu Sword biyu gaban kawuna su , a takaice tambarin Daular Ottoman ne a kafe bakin kofar Daular Saudiya da ga gani kuma na zallar gold a haka Malik ya danne abun cikin zuciyar shi ya shiga Daular nan ya tabbatar da cewa Eh Aymane ba Al'heri ya ke shukawa ba , dan duk Daular ta ruguje garden din ta ya bushe kamar ba a taba yin ciyayi a wajen ba , duk ginin sun kwararabe da ga gani ba a kula da su a hankali Inaya ta tabo hannun shi ta na cewa " yaya Zayd , an ya nan gidan mu ne ? ba ka yi batan kai ba ? " murya a sanyaye ya ce mata " No my Cutie , ban yi batan kai ba , in sha Allah komai zai koma kamar da farko " ba ta ce mishi komai ba ta tsaya ta bin wajen da kallo ga jikin ta ya yi mugun sanyi duk inda motar su ta wuce sai an tsaya a na bin ta da kallo Malik kuwa kai tsaye part din MALIKAT HOUDA ya nufa ya yi parking din motar bakin kofar shiga part din ya na yin parking ya kashe motar ya kalli ta cikin glass din motar ya ga kowa ya tsaya waje guda su na kallon motar allamun su na jiran su ga wanda zai fito da ga ciki a hankali ya sauke ajiyar zuciya , kafin ya kai hannu ya bude kofar motar ya sauko da kafar shi guda , sai da ya dan jinkirta kafin ya fiddo gudar kafar ya fito da ga cikin motar duk wanda ke wajen sai da ya saki kuka lokaci guda ganin Malik ya dawo cikin masarautar shi kan shi sai da idanunshi su ka ciko da ruwa a hankali ya fara bin wajen da kallo , cen ya hango Azim ya tunkaro shi da mugun gudu ya na daga mishi hannu , ga idanun shi nan cike da ruwa haka Malik ya tsaya ya na kallon shi , har sai da ya kusa kawowa wajen motar ya yi tuntunbe ya fadi da gudu Malik ya nufe shi , ya na zuwa ya Zube saman guyiwowinshi ya tallabo Azim ya na fadin " Azim , ba ka ji ciwo ba ? " ina ko amsa mishi tambayar shi Azim bai yi ba , ya rungume shi ya na sakin kuka kamar karamin yaro a hankali shi ma Malik ya zagayo da hannayanshi a baya a Azim ya rungumeshi , da a ce zai iya yin kuka da ya yi shima sai da Azim ya gaji da kukan nashi sannan ya dago da ga jikin Malik ya na fadin " Ina ka shiga ranka shi dade ? ina ka tafi ka bar mu ? kai da kanka ka ce mu ne ahalinka amma shi ne ka tafi ka bar mu ? ba ka san irin kangin da mu ka shiga bayan tafiyar ka ba , na godewa Allah da ba abun da ya same ka , don Allah kar ka tafi ka sake barin mu a hannun wacen azzalumin mutum " ya fada ya na hawaye bibiyu a hankali Malik ya mike tsaye , sannan ya taimakawa Azim ya mike tsaye shi ma hannu ya kai ya fara gogewa Azim hawayen shi ya na fadin " kar ka damu Azim , in sha Allah babu inda zan je , ko zan tafi sai na cire ku da ga hannun wacen azzalumin " a hankali Azim ya gyada mishi kai ya na sakin wani dan karamin murmushin da har ya manta rabon shi da ya yi murmushi a hankali Malik ya juya ya nufi motar shi da sauri Azim ya mara mishi baya , su na isa ya bude gidan baya ya fiddo trolley din su Malik kuwa ya nufi geffen Inaya , ya bude mata kofar , sannan ya mika mata hannu ba musu ta daura hannun ta saman nashi , sannan ta sauko a hankali Azim na ganin cikin Inaya ya saki wani kyawatencen murmushi ya na yi wa Allah godiya cikin zuciyar cikin sanyin murya ya ce mata " ki shiga ina zuwa , su Ammie duk su na ciki " gyada mishi kai kawai ta yi , da ga haka ya manna mata kiss saman forehead ya raba ta geffen ta ya shiga cikin motar shi A hankali ta daga kafa ta fara takawa ta shiga part din MALIKAT HOUDA , Azim na biye da bayan ta janye da trolley bakin ta da Sallama ta shigo parlourn MALIKAT HOUDA , nan ta tardo MALIKAT INAS , MALIKAT AL'UMU , mama , Tesnim , Nesrine , har ita kan ta MALIKAT HOUDA Nesrine da mama na ganin ta su ka tashi da gudu su ka nufe ta , su ka rungume , su na sakin kuka wata yar karamar dariya Inaya ta yi ta na fadin " Ashhhhhh , kar ka ku ji wa babyna , ciwo " a tare mama da Nesrine su ka daga da ga jikin Inaya su na kallon katon cikinta Godiya mama ta shiga yi wa Allah cikin zuciyar ta , Nesrine ma haka sai sakin murmushi ta ke wani kyawatencen murmushi Inaya ta saki , ta nufi MALIKAT INAS da sauri ta na fadin " Ammie " da sauri MALIKAT INAS da MALIKAT AL'UMU su ka mike su na fadin " yi a hankali baby " cak ta tsaya ta na murmushi har su ka karaso wajen ta , su ka rungume ta sannan su ka shiga tambayar ta ya jiki , ya hanya gyada musu kai kawai ta ke ta na murmushi cen cikin hannun MALIKAT HOUDA ta hango wani baby , ya na barci sai jijiga shi ta ki washe baki Inaya ta yi ta nufi MALIKAT HOUDA ta na fadin " la mamie , baby ki ka samu ? " a tare duk su ka yi wata yar karamar dariya sannan MALIKAT HOUDA ta ce mata " ba na son shirme , na Nesrine ne " dan zaro idanu Ta yi kafin ta juya ta kali Nesrine , da ke tsaye ta na hawaye , irin kallon nan na tambaya a hankali Nesrine ta gyada mata kai ta na murmushi allamun Eh zama geffen MALIKAT HOUDA ta yi ta na fadin " mamie ba ni shi na rike " ta fada na mika mata hannu cikin zolaya Tesnim ta ce mata " wannan katon cikin naki zai bari ki dauke shi ? " " ni dai sai na dauki babyn Nesi " ta fada cike da shagwaba har da turo baki " karbi , ba za mu iya rigimar ki ba , ai dama dole ta ce sai ta rike shi , ba mijin ta ba ne " MALIKAT HOUDA ta fada ta na daura Baby saman hannayan Inaya da sauri Nesrine ta ce mata " yi a hankali kar ki murde min kan baby " hararrar ta Inaya ta yi ta na fadin " to ina ruwan ki , ai ni ma na kusa samun nawa babyn " ta kai karshen ta na murguna mata baki a hankali Nesrine ta karaso wajen ta , ta na fadin " ban babyna tun da haka ne " ta kai karshen ta na mika mata hannu da sauri Mama ta ce mata " Nesrine wai biye mata za ki yi , kin fi san halin ta " hararrar Inaya Nesrine ta yi kafin ta koma gefe ta zauna ta na tsuke fuska a tare kowa ya koma ya zauna kafin MALIKAT INAS ta ce " baby , ina mijinki ya yi ? ba tare ku ka zo ba ? " a hankali Inaya ta dago kai ta kalli MALIKAT INAS ta ce " a tare muku Ammie , ya ce akwai inda zai je yanzu ya dawo " a tare duk su ka yi hamdallah , sannan MALIKAT AL'UMU ta ce " baby , ya kamata ki je ki huta ko ? " noke mata kafada ta yi ta na fadin " ni tare da babyna zan tafi " da sauri Nesrine ta ce mata " wane babyn ? kam , wlh tun wuri ki sauke idanun ki da ga saman babyna , in ba haka ba na yi miki duka kawo ruwa " cikin nitsuwa Tesnim ta ce mata " Malik ko ya cire miki kai , gwara ki bi ta cikin ruwan sanyi ku rabu lafiya , dan in ta ce ta na son babyn nan ko mutuwa za ki ba abun da zai raba ta da shi " marairaice fuska Nesrine ta yi ta na shirin magana , ta ga Inaya ta miko mata babyn ta na fadin " amshi , barci na ke ji " da sauri Nesrine ta kai hannu ta karbi babynta ta na karba Inaya ta mike tsaye a hankali , ta na dafe da cikinta , ta ce " mama , barci na ke ji " ta kai karshen cike da shagwaba wani dan karamin murmushi ta saki ta na kallon ta , yau dai ga autar ta da ciki har ya kai watan haihuwa , ga kuma Nesrine da babynta , saura na Abdoul kadai ta ga burin ta ya cika , ga shi ko ta fara jiyo qamshin kamar Tesnim na da ciki a hankali ta mike ta nufi Inaya ta riko hannunta , ta na fadin " mu je ki yi wanka ki konta ki huta , Nesrine kawo kayanta bedroom di na " " bari zan kai " Tesnim ta fada , ta na mikewa ta nufi trolley din da Azim ya ajiye a wajen ta bi bayan su mama da su ka shiga corridor ( 🤔🤔 mama ba ki yi karya ba fa , ko ni na ga allamun ciki a jikin Tesnim , 🤣🤣🤣 ) ❤⚘ E X I L E D P R I N C E ⚘❤ 🔥👑 ( LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) STORY & WRITTEN BY : MEERAH ⚘🕊 【THE ROYALTY LOVE ❤🌹】 【 BOOK ________4 📚✍❤ 】 _______________________♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡______________________ { P A G E ________ 3 & 4 ✍💕🔥} ▪MALIK AYMANE zaune ya ke saman kujerar shi ta Gold ya na rike da wayar shi ya na latsa , haka zalika duk mutanan wajen kowa na harkar gaban shi , sai hira su ke yi su na dariya su na a haka Meli ya shigo da gudu babu ko sallama ya nufi Aymane da gudu , kai tsaye wajen kunnen Aymane ya nufa ya yi mishi rada a dubu dari Aymane ya mike tsaye har sai da ya saki wayar shi ta fadi kassa a tare duk kowa ya juyo ya na kallon Aymane da ke faman zaro idanu baki sake har su na hada baki su na tambayar shi lafiya ba su kai ga gama rufe bakunansu ba , su ka ga Aymane ya kai hannu ya damko wuyan Meli ya na fadin " karya ka ke , ba zai taba dawowa ba " murya a disashe Meli ya ke fadin " ranka shi dade , ba karya na ke ba , da ido na na gan shi zai shiga part din MALIKAT HOUDA " cikin bacin rai Aymane ya tura Meli baya har sai da ya fadi ya na shirin magana idanun shi su ka sauka cikin na Malik , ya na tsaye bakin kofar shigowa Fadar ya rike hannayan shi a baya a tare kowa ya mike tsaye ya na kallon Malik baki sake , wasu zuciyoyin su na bugawa cikin bacin rai Aymane ya ce mishi " me ka ke yi a nan ? " a hankali Malik ya daga kafa ya fara takawa ya karaso tsakiyar fadar ya na fadin " na zo karbar abu na , dama aro ne na ba ka " wata shegiyar dariya Aymane ya yi kafin ya koma saman kujerar Malik ya zauna , irin zaman nan na qasaita ya ce " ko da HICHAM BIN JAABAR ne zai fito da ga cikin kassa , ba isa ya sauke ni da ga saman kujerar nan ba , bare kai ragon banza " cikin bacin rai Malik ya ce mishi " kar ka kuskura ka kira sunan mahaifina " " na kira , na kira me za ka yi ? ,ko ba ka son na fadi sunan wanda ya haifi lusarin namiji kamar ka ? tun kafin na sa a cire maka kai , ka fice min da ga fada " a hankali Malik ya sauke ajiyar zuciya kafin ya ce " Aymane , tun ina yi maka cikin ruwan sanyi , ka sauka da ga kujerar nan " wani makirin murmushin geffen fuska Aymane ya saki , kafin ya juya ya kalli wani dogari da ke tsaye bakin kofar fadar , da hannu ya mishi allamun ya cirewa Malik kai ba musu dogarin nan ya tako gadan² ya na zaro takobi wai cire kan Malik lokaci guda Malik ya kai hannu baya ya fido gun ya juya ya harbe dogarin nan tsakiyar kai , nan take ya fadi kassa matace ba karamar razana Aymane da mutanan fadar su ka yi ba a hankali Malik ya juyo , ya saita kan Aymane ya na fadin " idan na ga dama , move guda zan yi na aika inda ka aika mahaifina , amma zan ba ka damar ci gaba da rayuwa , ka sauka da ga kujerar nan " cikin bacin rai Aymane ya mike tsaye ya na fadin " ba ka da ikon ce min na sauka da ga saman kujerar nan , kai da kanka ka bar ta , kowa ya na shaidar ka hakura da kujerar nan a bisa tsarin masarautar nan , duk Malik din da ya hakura da kujerar shi , ba shi da izinin komowa da sunnan zai koma saman kujerar shi , dan haka ba ka da ikon ce min na sauka " ya na gama rufe bakin shi ya ga Rafik ya shigo cikin fadar ya na fadin " as a direct descendant of Malik HACHIM bin JAABAR, he has every right to claim the tron ​​of his late father, even if he renounced him " " Gaskiya Rafik ya fada , dan haka malam ka tattara kayanka ka yi gaba " Fadin Diya ya na karasowa geffen Malik ya tsaya ya na sakin murmushi " No ! " Aymane ya fada da karfi ya na mikewa tsaye ya ci gaba da cewa " No , ba ka da izinin ce min na sauka , ba ka san irin famar da na sha kafin na hau saman kujerar nan , tun kafin ka shigo duniya na shirya hawa na kujerar nan ta Malik dan har yaron MALIKAT INAS na kashe , na kuma sace mahaifar ta dan kar ta samu wani babyn , amma wannan banzan uban naka ya auri kanwar Daddy , ta haife ka , tun ranar da ka shigo duniya , tawa duniyar ta ruguje , ni na sakawa part din Malik wuta shekara shidda baya kawai dan ka mutu na dawo na kashe Malik , amma wani ikon Allah dan banzan yaron nan ya rayu , okay na hakura , why za ka dawo ? me ya sa ba ka yi zaman ka a cen ba ? amma sai da ka dawo ka shiga tsakanina da burina , amma ban hakura ba ni na juya kwakwolwar Hakim ya harbi Malik saboda ya kassa kashe shi , ni na sa Rouksar zuba mata poison cikin abincinka , ni na saka ta sace ruhin MALIKAT AL'UMU , amma wacen banzar yarinyar ta ruguza shirina baki daya , why ba za ku bar ni na hau kujerar nan cikin konciyar hankali ba ? why ? , wlh ko da sama da kassa za ta nade , ba zan sauka da ga kan kujerar nan ba , ita ce burina a duniyar nan , tun da na taso da son zama saman wannan kujerar na taso , yanzu kuma da na hau ta shi ne za ka ce na sauka ? no , hakan ba zai taba yiyu ba " ya fada cike da bacin rai da allamun fasuwar rai ta kama shi duk mutanan wajen sai da su ka yi salati su na sauraron abun da Aymane ke fadi , bacin rai ya sa ya tonawa kan shi asiri da kan shi shiru Malik ya yi ya na sauraron abun da Aymane ke fadi , dole ya yi mishi ta wayo dan ya samu ya sauka da ga kan kujerar nan , Idan ya ce zai ta karfi , ba zai yi nassara ba , dole shi ma ya yi tunani kamar na su na mugaye , dole ya meda kwakwolwar shi irin tasu kafin ya samu Aymane ya sauka da ga kujerar nan , dama an ce mugu shi ya san makwontar mugu , cuta ce za ta dau cuta a hankali Malik ya sauke ajiyar zuciya , cike da nitsuwa ya ce "as the heir of Malik HICHAM bin JAABAR I have the right to claim the throne of my late father, but since you do not want to give in passively okay, Aymane Abdoul Mujeeb Me Nawfel HICHAM bin JAABAR I provoke you in a duel, the winner will ascend the throne of Saudiya and the loser will pay with his life " a dubu dari Rafik da Diya su ka kalli Malik su na zaro idanu , har su na hada baki wajen cewa " ka na jin abun da ke fada kuwa , hakan na nufin idan ka fadi kashe ka zai yi " cikin kwarin guyiwa Malik ya ce " Eh , na ji abun da na fada " ya na gama fadar haka Aymane ya bushe da wata shegiyar dariya har da tapi ya dafe ciki shiru kowa ya yi ya kallon shi kamar wani zarrare sai da ya tsagaita dariyar shi sannan ya dago ya kalli Malik ya ce " kai a ganin za ka iya kashe ni ? , ko ka kashe ni kamar ka kashe maciji ba ka cire kai ba , Okay na yarda , wane irin duel ka ke so mu yi ? " " Sword Duel " ya fada a takaice ya na kallon Aymane sake bushewa da dariya Aymane ya yi ya fadin " okay , na yarda , in dai ta haka ne kawai zan zauna saman wannan kujerar , na yarda , kai kuma ka shirya tarda tsohon mahaifinka , dan har yanzu ba a yi wanda zai ga bayan Aymane bin Abdoul Mujeeb , ko mutuwa tsorona na ke , bare kai ragon banza " " All right , tun da ka yarda fine , yau ranar monday , za mu yi shi a ranar Friday , amma kafin nan , da ga kai har wadanan mutanan fadar taka , ba ku da izinin shigowa fada da sunnan aiki , har sai mun kammala duel din mu , sannan da ga yanzu ka fita da ga Malik Aymane , ka koma Aymane , har zuwa lokacin da za mu kammala , a nada wanda ya yi nassara a matsayin sabon Malik " " okay " Aymane ya fada a takaice kafin ya sa hannu ya cire Alkyabar Malik da ke jikin shi ya ajiye saman chair din bayan shi , ya cire Rawanin kan shi ya ajiye saman Alkyabar , sannan ya juyo ya fara takawa ya karaso gaban Malik ya tsaya sai da ya kalle shi cikin ido sannan ya ce " mu zuba mu gani , shege ka fassa , Nawfel Hicham Bin Jaabar tun yanzu ka sa a shirya kabarin ka , da ni ne kai zan ce a yi shi nesa da na mahaifina dan kar ya ga wane irin lusarin yaron da ya haifa " ya kai karshen ya sakin wata yar karamar dariya ya raba ta geffen shi ya wuce ya na fita Malik ya saki wata yar karamar sheet da ya rike a hannun shi a baya nan take wajen ya fara zubar da jini a dubu dari Rafik ya riko hannun nashi ya na fadin " Inallillahi , ranka shi dade , why za ka ji wa kanka haka ? " a hankali Malkk ya sauke ajiyar zuciya ya na fadin " dole na yi hakan , if not zuciya za ta debeni , na buge shi " ya na gama fadar haka ya dago kai ya kalli mutanan fadar Aymane , wani mugun kallo ya wurga musu nan take su ka sha jinin jikin su cikin ba da umarni ya ce musu " idan ku ka yi one minute a cikin wajen nan , ka tabbatar gawarku ce za su fita " bai gama rufe bakin shi ba su ka tashi daya bayan daya da gudu su ka fice fadar , ta rage da ga Diya sai Malik sai Rafik su na fita Shi ma Malik ya juya ya fice fadar , ya na tafiya kamar zai tashi sama hannun shi na zubar da jini , ga idanun shi duk sun yi ja da allamun ya na cikin bacin rai kai tsaye part MALIKAT HOUDA ya nufa , babu ko sallama a bakin shi ya shigo parlourn nan ya tardo su duk su na zaune ban da Inaya da mama da su ka shiga Bedroom duk su na ganin shi kowane ya saki wani kyawatencen murmushi , MALIKAT INAS har da hawaye har sun tashi za su nufe shi , su ka ga Diya ya fado mishi a baya ya rungume shi ya na fadin " ni dama na san za ka dawo , tabbas za ka dawo , ai dama damuna a lokacin da a ka fi bukatar ta ta ke samuwa , kamar wata ka ke a sararin samaniya haskenka ya na mamaye duk duniya , na ji dadin ganin ka abokina , I have really missed you " ya na gama rufe bakin shi , Malik ya kai hannu cikin zafin nama ya medo Diya gaban shi , ya dunkule hannu ya kai mishi wani mugun bugu a face har sai da ya fadi kassa a tare duk mutanan wajen su ka razana , Nesrine har da sakin kara , lokaci guda babyn ta ya saki kuka kamar ya san abun da ke faruwa cike da bacin rai Malik ya ce mishi " ka na sane da abun da ke faruwa amma ka ki fada min , why ba za ka kire ni ka fada min halin da ahalina su ke cike tun kafin abun ya tsananta ? why Diya ? da yanzu RIANNA ba ta kire ta fada min ba shikenan haka Saudiya za ta dongwama hannun wacen azzalumin dan uwan naka " a hankali Diya ya dago kai ya mike tsaye , ya na fadin " lokacin da na samu labarin abun da ke faruwa , sai da na kira ka , amma ba ka dauki wayata ba , na tura maka text a na bukatar ka a Saudiya , amma ba ka min reply ba , asali ma blocked di na ka yi , shi ya sa na ja bakina , na yi shiru ba kyale ka , na tattare familyn ka na tafi da su Qatar , duk abun da ya faru laifin ka ne , da tun farko ba ka tafi ba da duk wannan ba ta faru ba " ya fada cikin bacin rai shi ma gaskiya Diya ya fada , duk abun da ya faru laifinshi ne , da tun farko ya tsaya , ya yaki Aymane da duk wannan abun ba ta faru ba ya na gama fadar haka ya fara jiyo kukan baby wani dan karamin tsaki Diya ya ja ya na fadin " dubi don Allah ka saka shi kuka " ya kai karshen ya na juyawa ya nufi Nesrine , ya kai hannu ya karbi babynshi , sannan ya juyo ya dawo gaban Malik ya shiga jijiga shi ya na fadin " Shiiiiiiiiii , calm down my baby ba abun da ya faru " a hankali ya dago kai ya kalli Malik ya na murmushi ya ce " tun kafin a rigani , bari na gabatar maka da Nawfel bin Abdoul Mujeeb , my baby " lokaci guda idanun Malik su ka ciko da ruwa , har wata nanauyar ajiyar zuciya ya sauke ya na kallon babyn babu ko kiftawa Diya na jin yadda ya sauke ajiyar zuciya , ya saki wani kyawatencen murmushi ya ce " ba za ka rike shi ba ? " ya fada ya na mika mishi babyn a hankali Malik ya dago hannayanshi har kerma su ke yi ya kai zai karbi babyn kamar wanda ya tuno wani abu , lokaci guda ya juya ya fita da gudu a tare su ka kalle shi har ya fita sannan Diya ya kalli babyn hannun shi ya ce " Oh sorry my baby , yanzu ya dawo kai da takwaran ka guda , duk gudun ruwanshi sai ya dawo ya dauke ka " sa ga haka ya juya ya koma geffen Nesrine ya zauna su ka shiga rarrashin babyn su haka kowa ma ya koma ya zauna , ya yi zugum sun rasa abun yi , wannan tashin hankali da me ya yi kama , su dan ba su ma ji abun da Aymane ya fada da sai sun dinga sumewa ▪AYMANE cike da bacin rai ya nufi part din Malik , kai tsaye a floor na biyu ya nufa dan a nan RIANNA ta ke , shi kuma tare da Hafsat a floor na uku , dan tun zuwan shi part din bai taba hawa floor na hudu ba , dan ya na rufe kuma babu wanda ya San ta yadda a ka rufe shi bare a bude shi babu ko sallama ya shigo parlourn ya kwallawa RIANNA kira kamar murya shi za ta fado da gudu RIANNA ta fito da ga Corridor , ta na tafe ta na ingishi da allamun kafar ta na ciwo , ga fuskar ta duk ta yi ja , ta na sanye da wata gown pink color ko veil ba ta da a kanta kai tsaye gabanshi ta karaso murya har kerma ta ke ta ce " ga ni , ka na bukatar wani abu ? " tsaya wa ya yi ya na kallon ta babu ko kiftawa sai da ya dauki one minute ya na kallon ta kafin ya daga hannu ya wanke ta da wani gigitacen mari har sai da ta saki kara ta fadi kassa cikin bacin rai ya tsuguna ya kai hannu ya shako wuyan ta ya na fadin " bayan ke na san babu wanda zai yi wannan aikin , why ? azabar da na ke miki ba ta ishe ki ba sai da ki ka yi abun da zai sani na kashe ki ? why za ki sa dan banzan dan uwanki ya dawo , har ya yi kokarin kwace min kujerar Malik ? " tattara duk karfin ta RIANNA ta yi , ta sa hannayan ta dukka biyu ta ture shi ya fadi baya da sauri ta mike tsaye ta na sakin murmushi ta na fadin " Akhie ya dawo ? " ta kai karshen hawaye na zubo mata ta na gama fadar haka ta ji hannun Aymane ya damko wuyanta ya na fadin " ya dawo , amma ba za ki samu ganin shi ba , da ga nan gawar ki ce za ta fita da ga part din nan , duk wanda ya yi kokarin shiga tsakanina da kujerar Malik , sai na ga bayan shi , ki jira shi ma dan uwan naki , zai tarda ki ranar Friday " " ka sake ni " ta fada murya a disashe dan a rarrabe ma ta fiddo hariffan ya na shirin magana ya ga an riko hannun shi a hankali ya juya ya ga ko wanene , kai tsaye cikin idanun Malik nashi su ka sauka ba karamar razana ya yi ba ganin wadanan hazel eyes din nashi , ga shi sun yi jazir dan bacin rai , har sai da Aymane ya saki wuyan RIANNA bai shirya ba ya na ganin ya sake ta ya yarfa hannu shi da karfi kassa , ya riko hannun RIANNA zai bar wajen da ita da sauri Aymane ya riko hannunta ya na fadin " she is my wife , ba ka da ikon tafiya da ita " Malik bai ce mishi komai ba , ya sa kafa ya tura shi har sai da ya fadi kassa ya na faduwa ya juya ya nufi lift ya na rike da hannun RIANNA , sai da su ka yi ido hudu da Aymane kafin kofar lift din ta rufe kai tsaye part din su ka baro , ya na janye da hannun RIANNA , ita ko ko gaban ta ba ta gani , kawai ta tsare shi da ido babu ko kiftawa ta na hawaye sai da su ka shigo parlourn MALIKAT HOUDA ba ta sani ba , kawai sai ganin ta yi ya saki hannun ta ya nufi corridor da sauri ta riko hannunshi , da karfi ya kwace shi ya nufi corridor ba ta hakura ba sai da ta sake kai hannu ta riko nashi ta na fadin " Akhie " ba ta gama rufe bakinta ba , ya juyo ya daka mata wata gigitaciyar tsawa ya na fadin " I say let me ! " da ga haka ya nufi corridor ya shige ya bar ta ta yi sumar tsaye da sauri MALIKAT INAS ta tasso ta rungume yarinyarta ta na sakin kuka a hankali RIANNA ta bude baki ta ce " Ammie , cewa ya yi na kyale shi " ta fada hawaye na zubo mata da sauri Diya ya ce mata " RIANNA , gwara ki kyale shi , dan yanzu bacin ran da ya ke ciki ko da marigayi Malik ne a gaban shi , zai iya yi mishi fiye da tsawan , dan idanunshi a rufe su ke , ba ku san abun da Aymane ya fada mishi ba a fada , dan haka ku kyale shi har ya sauko " da sauri RIANNA ta shige jikin MALIKAT INAS ta na sakin kuka har da zubewa saman guyiwowinta , ta na kuka bangaran Malik , kai tsaye corridor ya nufa , har ya wuce bedroom din da Inaya ke ciki ya jiyo Muryar ta , ta na fadin " Ashhhhhhh " cak ya tsaya , ko tunani bai tsaya yi ba ya tura kofar ya shiga babu ko sallama ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ ( LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) STORY & WRITTEN BY : MEERAH ⚘🕊 【THE ROYALTY LOVE ❤🌹】 【 BOOK ________ 4 📚✍💌 】 _______________________♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡______________________ { P A G E ________ 5 & 6 ✍💕🔥} cak ya tsaya , ko tunani bai tsaya yi ba ya tura kofar dakin ya shiga babu ko sallama nan ya gan ta zaune saman bed din mama , ta jingina bayanta a forehead din gadon , da ga ita sai bathrobe , ga hannun mama saman katon cikinta , sai murmushi su ke saki a tare ya na ganin haka ya ce " i'm sorry " ya kai karshen ya na shirin juyawa da sauri Mama ta ce " malam Zayd , ina kuma za ka je ? " shiru ya yi bai ce mata komai ba , ko motsi ya kassa ya na a haka ya ga mama tsaye gaban shi ta na fadin " dama ta ce ta na son ganin ka , Auta zan dawo anjima kin ji ? " gyada mata kai kawai Inaya ta yi , da ga haka ta sa kafa ta fito bedroom din ta janyo musu kofa ta na fita ko ya sakawa kofar security a hankali ya juya ya nufi bakin gado , ya zauna ya na kallon ta wani cool murmushi ta sakin mishi kafin ta ce " baby ka san wani abu ? " girgiza mata kai ya yi a sanyaye ya ce " sai kin fada " dan jinkirtawa ta yi kafin ta ce " babyn mu ya na motsi , yanzu na ji kafafunshi saman cikina " " da gaske ? " ya fada ya na daga mata gera gyada mishi kai ta yi da sauri ta na fadin " kawo hannunka ka ji " ta fada ta na kai hannu ta riko nashi ai ko wanda ke zubar da jini ta dago , " inallillahi , baby wa ya ji maka ciwo haka ? " ta fada cike da damuwa a hankali ya kwace hannunshi ya na cewa " kar ki damu , na zo wucewa ne , na bugi sword din wani dogari , kuma babu zafi ina zuwa " ya kai karshen ya na mikewa tsaye kai tsaye toilet ya nufa ya shiga , ko one minute bai yi ba ya fito ya na rike da towel ya na goge hannunshi , dai'dai ya karaso wajen sofa , ya tilla towel din a sama ya koma wajen ta , ya zauna bakin gadon , ya cire sneakers din shi ya haye saman gadon , ya konta ya tada kai da cinyoyin ta lokaci guda ya saki wata nanauyar ajiyar zuciya , har sai da Inaya ta yi wata yar karamar dariya ta na kai hannu saman kanshi , ta fara shafawa a hankali ya na a haka kawai ya ji wani dadaden qamshi , ya na isa cikin hancinshi a hankali a hankali slowly ya ware idanunshi , ya yi sama da su , kawai ya ga ashe ko pant ba za ta sanye da a hankali ya lumshe idanunshi ya sake bude kamar mai jin barci ba tare da ya janye idanunshi ba da ga saman vagina din ta ya ce " Cutie , ware kafafunki kadan " ba musu ta ware kafafunta , ta na fadin " me ya faru baby ? " ta fada dan ita a tunanin ta wani abu ya gani ai ko wani abu ya gani , ta na gama rufe bakinta , ta ji tongue din shi a cikin vagina din ta sai da ta zaro idanu ta kara danna kan shi a wajen dan ba ta shiryawa hakan ba murya a sanyaye ta ce " yaya Zayd ka bari please " a hankali ya zame tongue din shi ya matso a hankali kafin ya dago kai ya kalle ta ya ce " i'm sorry my Cutie " wani dan karamin murmushi ta saki kafin ta gyada mishi kai a hankali ya dawo geffen ta ya zauna ya riko hannunta ya ce " tell me , wane irin gift ki ke so na yi miki ? " cikin rudu ta ce " wane irin gift kuma ? na me ? " " ke dai kawai ki fada min , gift din da ke ki ke so " dan jinkirtawa ta yi kafin ta ce " ummmmm , Island " a rude ya ce " Island kuma ? " gyada mishi kai ta yi ta na fadin " yeah , Island , ai kai ka ce na fadi abun da ne ke so " ta fada cike da shagwaba " yeah , na ce ki fadi abun da ki ke so , amma ba abun da zan iya yi ba , ina kuma zan samo miki Island " " Nooooo , ni fa ba ka gane abun da na ke fada ba " " to , explain me , me ki ke nufi ? " ya fada ya na daga mata gera guda wani dan karamin murmushi ta saki kafin ta ce " let me explain to you , Cewa na yi mu samu kanmu a wani tsibiri da ke tsakiyar ruwa babu kowa kawai da ga ni sai kai a cikin wani katafaren gida kusa da ruwa, tare da kallon teku, da faɗuwar rana mai ban sha'awa " " ba dan ki gani abu a film ba za ki ce sai kin yi ke ma " ya fada ya na kai hannu ya dan zunguri kanta wata yar karamar dariya ta yi ta na fadin " It's a problem to have a dream ? ni kawai abun da na ke so kenan " ta kai karshen ta na turo dan bakin nan nata dan jinkirtawa ya yi kafin ya ce " okay , yanzu fada min , idan na cika mafarkin ki , me za ki ba ni ? " cike da zumudi ta ce " duk abun da ka ke so " " don't be sure , da gaske za ki iya ba ni abun da na ke so ? " " ya fada ya na daga mata gera guda a hankali ta gyada mishi kai allamun Eh " ko da kuwa ....... " ya rada mata karshen a kunne , ni dai ban ji abun da ya ce ba da sauri ta girgiza kai ta na marairaice fuska ta ce " no gaskiya ba zan iya ba baby , wai har yanzu ba ka bar maganar nan ba ? " " ta ya ki ke so na bari , idan kin shirya yi min zan saya miki Island din baki daya , na tafi na yi wanka " ya kai karshen ya na mikewa ya nufi toilet ya shiga jim kadan ya fito sanye da bathrobe , ya na fitowa ya wuce kai dressing room , kamar ko ya san kayan su na nan jim kadan ya fito sanye da wani wando Jeans black color , da T-shirt black color ita ma a hankali ya karaso wajen ta , kawai sai ya ga har ta yi barci bai yi kokarin tashe ta ba , ya janyo duvet ya rufe ta har zuwa kirji sannan ya manna mata kiss saman forehead kafin ya juya ya nufi kofar fita dakin security din ya cire sannan ya bude kofar ya fito kai tsaye parlour nan ya tardo su zaune sun yi zugum kamar an aiko da mutuwa cak ya tsaya ya na kallon su murya a sanyaye ya ce " lafiya ku ka zauna a haka ? mutuwa a ka yi ? " a tare duk su ka dago kai su kalle shi , ya na tsaye ya rike hannayan shi a baya a hankali ya bude hannayan shi ya na kallon RIANNA , da gudu su ka tasso ita da Tesnim su ka fada jikin shi , su na sakin kuka cikin sigar rarrashi ya ce " wlh in ba ku yi min shiru ba sai na koma inda na fito " da sauri RIANNA ta ce " shikenan , shikenan , mun yi shiru , ba kuka mu ke ba " " that's good , yanzu ku sake ni , kar ku karaya min baya " va musu su ka sake shi , su ka tsaya gabanshi har su na hada baki wajen cewa " i have really missed you " " ni ma na yi kewar ku over " ya fada cikin sanyin murya wata yar karamar dariya RIANNA ta yi ta na sakin kuka lokaci guda , na lura RIANNA kamar MALIKAT INAS ta ke , abu kadan sai ta saki kuka a hankali ya raba jikin shi , ya raba ta geffensu ya nufi MALIKAT AL'UMU ya rungume ta rungume shi tsam ta yi ta na fadin " na yi kewar ka sosai my baby " a hankali ya raba jikin shi da nata sannan ya nufi MALIKAT INAS tun kafin ya karaso ta nufe shi da sauri ta rungume shi ta na fadin " kar ka sake tafiya ka bar ni don Allah " cikin sigar rarrashi ya ce mata " kar ki damu Ammie , ba zan sake rabuwa da ku ba " wata yar karamar ajiyar zuciya ta sauke ta na murmushi a hankali ya raba jikinshi da nata ya juya ya kalli MALIKAT HOUDA cikin zolaya ya ce mata " wai ke tsohuwar nan har yanzu ba ki mutu ba ? " " karbi nan dan rainin hankali kawai , don Allah zo kashe ni in ka gaji da gani na " ta fada ta na matse mishi fuska dan tabe baki ya yi ya na kauda kai ya ce " ni tambaya ce kawai na yi " wata yar karamar dariya MALIKAT INAS ta yi ta na fadin " kai dai ka na son takurawa mamie , me ta yi maka ? ko dan ta na son ka shi ne za ka yi mata wannan shegantakar ? " " ai ni ban ce ta so ni ba " ya fada ya na kara shan tsami da ga haka ya ce musu " kun ci abinci ? ko ba ku jin yunwa ? " " Yanzu mu ke wa Inas mu koma part din mu , mu shirya muku abinci " fadin MALIKAT AL'UMU cikin nitsuwa ya ce mata " No , ba na son kowa ya bar part din nan , mamie bedroom nawa ne a part din ki ? " ya kai karshen ya na dawo da kallon shi kan MALIKAT HOUDA kai tsaye ta ce " bedroom takwas ne a ciki " gyada kan shi ya yi a hankali ya na fadin " okay , ba damuwa na san za su ishe ku kafin a gyara masarautar , ba na son ku fita bayan wannan azzalumin ya na cikin masarautar , duk wani abu da za ku bukata zan kawo muku " da sauri RIANNA ta ce " kai kuma fa Akhie ? " dan jinkirtawa Malik ya yi kafin ya ce " kar ku damu a kai na , kawai ina son na tabbatar ku na cikin koshin lafiya " " wacen Azzalumin kuma fa ? ya ce zau sauka da ga saman kujerar ? " MALIKAT INAS ta fada " Yeah , nan da Friday za mu sani " ya na gama fadar haka ya nufi hanyar fita parlourn ya fice da kallo su ka raka shi har sai da ya fita sannan MALIKAT INAS ta tasso ta riko hannun RIANNA ta na fadin " mu je ki sauya kayan nan " ba musu RIANNA ta bi bayan ta su ka shiga corridor bangaran Malik kuwa ya na baro part din ya shiga motar shi kai tsaye ya fice masarautar ▪AFTER SOME HOURS bai dawo masarautar ba sai karfe goma sha biyu na dare , ko ina ya tafi ? oho bakin shi da sallama cen kassan makoshi ya shigo parlourn MALIKAT HOUDA kamar aljana ta na zaune ita kadai cikin parlourn , ta na kallon waje guda a hankali ya karaso geffen ta ya zauna ya na fadin " me ki ke yi a nan ke daya ? " ba tare da ta kalle shi ba ta ce " nothing , kawai na kassa barci ne " " Da gaske , me ya faru ? tunanin me ki ke ? ko cikinki ke ciwo ? " a hankali ta girgiza mishi kai ta na dan karamin murmushi ta ce " uncle ne ya tsayar da ni , wai ya na son magana da kai " cikin rudu ya ce mata " ban gane ba ? " a hankali ta sauke nunfashi , ta lumshe idanunta kafin ta sake bude su , sun koma farare kal a hankali ta juyo ta kalle shi cikin a hankali ta bude baki ta ce " wai kai komai sai an kwatanta maka ne ? " ta fada da murya tak tak irin ta Malik HICHAM ba karamar razana Malik ya yi ba har sai da ya yi baya ya na zaro idanu ya na karanto kalmar shahada cikin zuciyar shi bushewa da dariya ta yi ta na fadin " wlh kai da momyn ka duk matsorata ne , dubi kamar ka ga wani aljani , ko da ya ke na mutu ashe dole ka ji tsoro , ba ni da isashen lokaci , kawai na zo na fada maka a kan ka yi hankali lokacin duel din ku , Aymane ba abun da ka ke tunani ba ne , ya ma wuce tunanin mutum , ba za ka iya kashe shi ba kai tsaye , dole ka fara kawo karshen sihirin shi , Idan ba haka ba ba zai mutu ba , ni kai na ban san inda ya boye karfin sihirin shi ba , da na je na kawo karshen shi , zabi guda gare ka , da ka samu dama ka cire mishi kai kawai ta haka ne kawai zai mutu idan ba haka ba tashin hankali da za ka gani da ga baya ya karfin tunanin mai tunani " ta na gama fadar haka ta sauke wata yar karamar ajiyar zuciya , ta ja wani dogon nunfashi kafin ta lumshe idanunta , ta sake bude su a hankali ya ga sun koma dai² a hankali ta juyo ta kalle shi ta ce " baby me ya faru ? " wata nanauyar ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce " ba komai " wani dan karamin murmushi ta saki sai kuma ta tsuke fuska lokaci guda ta na fadin " sai yanzu ka dawo , ni na yi fushi ma da kai " ta kai karshen ta na kauda kai " sorry Cutie , na tafi yin wani aiki ne " ya fada cikin sanyin murya turo dan bakin nan nata ta yi ta na fadin " baby yunwa na ke ji , tun tafiyar ka ban ci komai ba " " shikenan , me ki ke ki ci ? " da sauri ta ce mishi " irin abincin da ka ke min a US " ta fada ta na sakin wani dan karamin murmushi gyada mata kai ya yi kafin ya ce " okay , jira ni ina zuwa " da to kawai ta amsa mishi , da ga haka ya tashi ya nufi kitchen ya shiga da kallo ta raka shi har sai da ya shiga sannan ta saki wani dan karamin murmushi sai da ya dauki one hour a cikin kitchen din kafin ya fito ya na rike da wani tray kai tsaye gabanta ya karaso ya zauna a kassa saman carpet , sannan ya ajiye tray din a gaban shi ya na ce mata ta sauko ba musu ta sauko kassa su na fuskantar juna , ya fara ba ta abincin da kan shi sai da ta kammala sannan ya dauki tray din ya mayar da su kitchen sannan ya dawo parlourn ta na zaune saman sofa ya tardo ta , ta shafar cikin ta a hankali ya karaso wajen ta ya zauna ya na fadin " yanzu tashi ki je ki konta " shagwabe mishi fuska ta yi ta na fadin " ba tare za mu kwana ba ? " a hankali ya girgiza mata kai allamun a'a shiru ta yi ta na kallon shi babu ko kiftawa sai da ta dauki lokaci kafin ta ce " baby , amma akwai abun da ke damun ka ko ? " " me ki ka gani ? " ya fada a sanyaye " kawai na ga yanayin face din ka ya sauya ne " " ba zan miki karya ba , ina cikin damuwa , ba kadan ba , amma duk lokacin da na tare da ke na kan ji damuwata ta tafi , please don't leave me , kar ki tafi ki bar ni " wani dan karamin murmushi ta saki kafin ta rungume shi ta na fadin " mutuwa ce kadai za ta raba ni da kai " a hankali ya zagayo da hannayanshi a bayanta ya rungume ya na sauke ajiyar zuciya a hankali ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ ( LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) STORY & WRITTEN BY : MEERAH ⚘🕊 【THE ROYALTY LOVE ❤🌹】 【 BOOK ________ 4 📚✍💌 】 _______________________♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡______________________ { P A G E ________ 7 & 8 ✍💕🔥} Sai da ya dauki lokaci rungume da ita a haka kafin ya raba jikinsa da nata ya na ce mata " yanzu tashi ki je ki konta dare ya yi " marairaice mishi fuska ta yi ta na turo dan bakin nan nata ta ce mishi " please baby tashi mu je ni ba zan iya kwana ni kadai ba " ta kai karshen idanun ta na cikowa da ruwa kamar za ta yi mishi kuka a hankali ya sauke ajiyar zuciya kafin ya ce " shikenan , tashi mu je " ya fada dan ya san halin ta yanzu za ta yi zaune ta aza mishi kuka duk sai mutanan part din sun fito , gwara ya yi abun da ta ke so ko ya samu ya rabu da ita cikin lalama wani kyawatencen murmushi ta sakin mishi kafin ta mike tsaye ta na turo katon cikinta a hankali shi ma ya mike ya riko hannunta su ka shiga corridor , ya shiga bedroom din ta cikin sa'a ko babu kowa su na shiga ya saki hannunta ya juya ya rufe kofar ya saka mata security kafin ya juyo gare ta ya ce mata " let's go sleeping , i'm very tired " wata yar karamar dariya ta yi kafin ta ce mishi " baby , mu je na yi maka tausa mana " " uhm , da ni da ke wa ya fi bukatar tausa da wannan katon cikin naki " turo mishi dan bakin nan nata ta yi kafin ta nufi gadon ta Haye ta zauna a tsakiya ta yi irin zaman nan na bokaye shi dai bawan Allah ya na shan rigima , a ka je ta haifi mace kuma ta dauko wannan rigimar ta ta sai ya dinga bar musu gidan da wannan ya ya kare bare ya samu karama irin ta ya san kashe shi kawai za su yi wata boyayyar ajiyar zuciya ya sauke kafin ya tako a hankali ya zauna bakin gadon , ya kai hannu ya cire sneakers din shi sannan ya ida Hayewa ya jingina bayan shi a jikin forehead din gadon ya na kallon bayan ta sai turo baki ta ke slowly ya dago hannu ya daura saman bayan ta ya fara yi mata tafiyar tsutsa da yatsar shi tsakiyar gadon bayan ta wata yar karamar dariya ta yi kafin ta ce mishi " ni ka kyale ni fushi na ke da kai " ba tare da ya daina ba ya ce mata " da gaske za ki iya fushi da ni Cutie ? " dan jinkirtawa ta yi kafin ta ce " gaskiya ba zan iya ba , sai dai cikin wassa " cikin sanyin murya ya ce mata " i'm sorry my Cutie " a rude ta juyo ta na kallon shi ta ce " baby hakurin me ka ke ba ni ? " " abun da na yi miki lokacin da mu ke US " girgiza mishi kai ta yi a hankali kafin ta matso baya ta jingina bayan ta a jikin forehead din gadon sannan ta ce mishi " baby ni ba ka yi min komai ba " da sauri ya ce mata " no , na san na cutar da ke dayawa , kin zubar da hawayen ki saboda ni , na saka ki kukan da ban taba tunanin za ki yi shi ba a rayuwar ki , ga shi kuma nine silar wannan kukan , ban san abun da ya sa na kaurace miki a lokacin da ki ka fi bukata ta a kusa da ke , duk lokacin da na ga murmushi a face din ki sai na tuno wannan lokacin da ki ke zubar da hawayen ki , ban san ya a ka yi ki samu gourbin yahe min cikin zuciyar ki " wani cool murmushi ta saki kafin ta riko hannunshi , ta kontar da kan ta saman shoulder din shi ta ce mishi " because i love you , kuma na san duk abun da ka yi ka yi shi ne saboda ka na so na kuma ba ka son rabuwa da ni , amma komai ya wuce , saboda ga shi yanzu babyn mu ya girma kuma ba abun da ya same ni " cikin nitsuwa ya katse ta da cewa " no , har yanzu ina jin tsoro cikin zuciya ta , in a ka je na rasa ki kin san ba zan iya ci gaba ba da rayuwa kashe kai na kawai zan yi " slowly ta dago kan ta , ta kalli face din shi na dan lokaci kafin ta ce " idan ka tafi wa zai kula da babyn mu ? Diya ? Ammie , Aunty RIANNA , ? momy ? ka na ganin dukkan su soyayyar da za su nunawa babyn mu za ta kai taka ? please kar ka tsane shi a kan laifin da ba shi ya aikata ba , ko da kuwa wani za ka yi wa hukunci ni za ka yi wa tun da ni na ki yarda mi zubar da cikin " ta qarashe maganar idanun ta na cikowa da ruwa slowly ya girgiza mata kai kafin ya ce " no , laifi na ne , da a ce ban kusance ki ba da ba za ki samu cikin nan ba , da duk wannan ba ta faru ba " " baby , ka na nufin ka na nadamar duk lokacin da ka ke kusanta ta ? " ta fada a sanyaye kamar za ta yi mishi kuka da sauri ya juyo ya daura hannun shi saman face din ta ya ce " never , ko so guda , asali ma wadanan lokutan su ne ma fi mahimanci a cikin rayuwa ta , kuma su ke lokutan da su ka fi ko wane farin ciki a cikin rayuwa ta saboda a lokacin ne mu ke zama abu guda ni da ke , na ji kamar babu kowa a duniyar nan sai ni , sai ke " wani cool murmushi ta sakin mishi kafin ma ta ce mishi wani abu ya matso ya cabko lips din ta ya fara kissing din ta ya San in har ba hakan ba ya yi ba zai samu ta yi barci ba har ya tsere wata nanauyar ajiyar zuciya ta sauke kafin ta lumshe idanunta ta fara biye mishi a hankali ya sa hannu ya matso ta jikinsa kafin ya zame bakin shi da ga cikin nata slowly murya cen kassan makoshi ya ce mata " mu konta please , barci na ke ji " a hankali ta gyada mishi kai ta na sakin murmushi kafin ta gyada mishi da ga haka ta gyara ta konta shi ma ya konta ya janyo duvet ya rufe su har zuwa kugu kafin ya kai hannu saman cikinta ya fara shafawa a hankali wata nanauyar ajiyar zuciya ta sauke ta lumshe idanunta ta na jin wani sanyi cikin zuciyar ta ya na tsaka da shafa cikin ta kawai ya ji kamar cikin ta ya buge shi kadan a hannu gaskiya ya dan razana har zaro idanu ya yi kafin ya juya ya kalli face din ta , ta lumshe idanunta ta na sakin wani cool murmushi a hankali ya sauke ajiyar zuciya kafin ya ci gaba da shafa cikin ta , a hankali a hankali har barci ya yi gaba da ita shi kuma ya tsare ta babu ko kiftawa ya na jin barci ya dauke ta ya janye hannun shi a hankali da ga saman cikin ta kafin ya mike zaune ya sauko da kafafun shi ya kai hannu ya janyo sneakers din shi ya meda kafin ya tashi tsaye a haka ya fara takawa ya nufi kofar fita dakin ya fice abun shi ya na fitowa parlour ko ya tardo mama zaune ita kadai kamar aljana dan ba karya ya tsorata da ganin ta a hankali ya karaso tsakiyar parlourn ya tsaya , cike da kula ya ce mata " mama , wani abu ya faru ? ya na ga ki na zaune a ke kadai ? ko wani abu ki ke bukata na kawo miki ? " a hankali mama ta gyada mishi kai ta na murmushi ta ce " ba komai , kawai ina son yin magana da mahaifin su , amma Abyad ta ki hada ni da shi " cikin rudu ya matso ya na fadin " mama , ki na lafiya kuwa ? " " Eh ina lafiya , ko dan na ce ina son magana da malam ne ka tsorata , kar ka ji tsoro ina iya yin magana da mutanan da su ka mutu in har ruhin su bai yi nisa ba , haka ita ma Inaya ta na iya yi , idan Abyad ta janyo ruhin wanda mu ke son yi wa magana , amma yau sam ta ki yarda ta yi abun da na ce " a dan razane Ya ce mata " mama , ni wlh wannan abun duk ya fi karfin tunani na kawai ina shanye wa ne " a hankali ta gyada mishi kai kafin ta ce " na sani kar ka damu za ka iya tafiyar ka " ba musu ya fara takawa ya nufi kofar fita part din ya yi dan nisa ya jiyo Muryar mama ta na kiran shi cak ya tsaya ya juyo a hankali ya na tambayar me ya faru sai da ta saki wani dan karamin murmushi kafin ta ce " akwai sakon da malam ya ba ni na fada maka amma kullum sai na manta " " wani sako kuma mama ? " " ya ce ya gode da amanar shi da ka rike , ya na matukar alfahari da kai kuma ya na rokon Allah ya sa ka samu abun da ka ke so tare da matar ka ya na fatan za ku samu zuri'ar da za ku yi alfahari da ita kamar yadda ya ke alfahari da ku " shi dai kawai ya tsaya ya na kallon ta ya ma rasa me zai ce mata , kawai ya gyada mata kai kafin ya juya ya fice parlourn ya na juya abun da ta fada mishi cikin kwakwolwar shi ya na fitowa kai tsaye hanyar garden ya nufa , ya na zuwa ya tardo Diya zaune shi kadai kamar aljani babu ko tsoro Malik ya karaso wajen shi ya zauna ya na fadin " me ka ke yi a nan ? ina ka baro babys din ka ? " wani dan karamin murmushi Diya ya saki kafin ya ce " sun yi barci shi ya sa na fito na dan huta , takwaran naka mugun jaraba ce da shi sai mutane sun yi kwana ya tashe su da kuka " " uhm " Malik ya fada kafin ya lumshe idanunshi ya tafi duniyar tunanin shi kallon shi Diya ya tsaya ya na yi ya na sakin wani dan murmushi cen kuma sai ya ce " ka sani na yi kewar ka sosai , kullum in na yi sallat sai na saka ku kai da baby cikin addu'a , na godewa Allah da babu abun da ya same ka " ba tare da ya bude idanun shi ba ya ce " ni ma na gode da ka ceci ahalina a lokacin da su ka fi bukata ta , na san da ban tafi ba da duk wannan abun bai faru ba , wlh na yi nadamar tafiya " " no , kar ka yi nadamar lokacin da ku ka samu na farin ciki kai da ita , na san da ka san hakan za ta faru ba za ka tafi ba , amma tsotsayi ne , in ya wuni ba zai kwana ba , haka Allah ya rubuta za ta faru , kuma ta farun ni dai kawai fata na Allah ya sa ka yi nassara " " ko ban yi nassara ba don Allah ina son ka koma Qatar da family na , specially Cutie da Babyn mu , na bar maka amanar su don Allah kar ka bari wani abu ya same su ko da ba na raye " da sauri Diya ya ce mishi " in sha Allah kai za ka yi nassara , Allah ya na tare da ma su gaskiya , ba zai bari zalunci ya yi nassara ba " shi da Malik ya yi shiru bai ce komai ba amma har cikin zuciyar shi ya na fargaba a je bai yi nassara ba , shi ba ta saudiyar ya ke ba ta Cutie din shi ya ke , yanzu a ka je ya mutu ya za ta yi , babu wanda zai kula da ita da babyn su ya yi nisa duniyar tunanin shi ya jiyo Muryar Diya ya na fadin " ka san General Abdallah har US ya je neman ka ? " slowly ya bude idanun shi ya kalli Diya ya na daga gera ya ce " ya a ka yi ya san ina US ? " " ni na fada mishi , har General din US army General Aylan Jalaludeen su ka hada kai dan neman ka , musaman General Aylan ya ba da tukuyicin one million of American dollars ga duk wanda ya gan ka , amma shiru " cikin nitsuwa Malik ya katse shi da cewa " wait , General Aylan fa ka ce ? ina General Abdallah ya san shi ? " " ni ma ban sani ba , but ya ce mahaifin shi ya sani a Dubaï shi ya sa ya yarda ya taimaka wajen neman ka " " Diya , na hadu da General Aylan , har mu ka yi hira da shi " dan zaro idanu Diya ya yi ya na fadin " ban gane ba , ka hadu da shi kuma bai fada maka a na neman ka ba ? " shiru Malik ya yi dan ba shi da amsar da zai ba shi , kenan Aylan ya na sane a neman shi a Saudiya amma bai ce mishi komai ba , ta wani bangaran ta sanadiyar Aylan ne ya samu ya rage zafin da ya ke ji cikin zuciyar shi har ya karbi babyn shi , to why bai fada mishi abun da ke faruwa ba ? 🤔🤔 NI MA ABUN NAN YA DAURE MIN KAI , YA NA SANE KUMA YA YI SHIRU BAI CE KOMAI BA ? 🤔🤔 su na zaune a haka kawai su ka ga wata mota baka kirin ta nufi hanyar fita masarautar a tare duk su ka tsare motar da ido har sai da ta fita sannan Diya ya kalli Malik ya ce " Malik , Aymane ne fa , ina za shi je cikin wannan daren ? " cikin ko in kula Malik ya ce " shi ya sani " " a ka je wani abu kuma ya ke shirya wa ? please tashi mu bi bayan shi " " no , kyale shi , duk abun da ya shirya shi dan cutar da ni Allah ba zai bari ya yi nassara ba , kyale shi kawai " " amma M...... " bai kai karshen maganar shi ba Malik ya katse shi ya na daga mishi hannu allamun ya yi shiru ba musu Diya ya ja bakin shi ya yi shiru amma cikin zuciyar shi ya na jin ba abun kirki ba ne Aymane ke shirin yi ba , in abun kirki ne why zai fita a irin wannan lokacin ? sai dai kawai na ce Allah ya tsare Malik da ga sharin Aymane ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ ( LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) STORY & WRITTEN BY : MEERAH ⚘🕊 【THE ROYALTY LOVE ❤🌹】 【 BOOK ________ 4 📚✍💌 】 _______________________♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡______________________ { P A G E ________ 9 & 10 ✍💕🔥} ▪AYMANE 👺 Tuki ta ke yi cikin nitsuwa da ga gani akwai abun da ya shirya ya yi wajen one hour ya na wannan tafiyar kafin ya iso wajen wani kasurgumin Daji , babu motsin mutum bai rai sam sai dai tsintsaye da namun daji , har kukan tiger na ke jiyo wa amma shi ko tsoro babu ya ratsa ta dajin nan cikin motar shi ya yi ten minutes a haka kafin na ga ya tsayar da motar bakin wani katon dutsi a hankali ya bude kofar motar ya fito , kai tsaye dutsin nan ya nufa , nan na ga wata yar karamar kofa kamar cellar da ga kasan dutsin ko digon haske ba ya fitowa babu ko tsoro ya nufi kofar ya shiga babu ko sallama kamar da wassa kawai sai na ga wajen da mugun haske kamar safiya , wajen zallar dutse ne an yi zanen macizai a sama da mutane , ga wata wuta na tashi tsakiyar dutsen da wasu kwalabe zagaye da wutar hayaki na tashi da ga cikin su kai wajen ba zai iya kwatantuwa ba dan bai yi kama waje holy ba , da ga gani wajen tsafi ne in ba haka ba ya za a ce da ga waje na ga wajen duhu babu digon hasken da ke fitowa ta kofar ga shi kuma cikin da mugun haske kamar da safe , kai ni dai zuciya ta ba ta amince da wajen nan ba a hankali Aymane ya karaso gaban wutar nan ya sa hannu daya bayan daya ya fara cire kayan jikin shi ya na ajiye wa gefe sai da ya rage da ga shi sai short sannan ya zauna gaban wutar nan , ya yi irin zaman cin tuwo ya kai hannu ya dauki gudar kwalba ya sa yatsun shi biyu a ciki kafin ya fiddo su da wani abu ja a sama kamar jini , kai tsaye saman forehead din shi ya shafa wannan abun ya na shafawa ko ya shanye kamar bai shafa komai ba , a hankali ya meda kwalbar ya ajiye ya lumshe idanunshi ya fara karanto wani karatun mara dadin ji , a hankali wani dan karamin iska ya fara tashi a wajen a dubu dari ya ware idanunshi , ba karamar razana na yi ba ganin yadda idanun shi su ka koma na maciji , ma su ban tsoro ya tsare waje guda da ido kamar a film haka na fara ganin zanen macizan nan da ke saman dutsen nan sun fara fitowa kamar na gaske , daya bayan daya su ka nufi Aymane kawai sai su shige jikinsa su bace bat su na bacewa ko zanen ke fitowa saman fatar jikin shi , sannu sannu har sai da jikin sa ya cika da wadanan zanen sannan na ga ya ja wani dogon nunfashi ya lumshe idanunshi kafin ya sulale a wajen ko motsi ba ya yi ya na faduwa ko wutar nan ta gaban shi ta mutu ita kan ta , wajen ya koma duhu kamar ba a taba yin haske a wajen ba 🤧🤧🤧 NI DAI BA ABUN DA ZAN CE SAI DAI ALLAH YA KARE MANA MALIK , AYMANE YA WUEC ABUN DA YA KE TUNANI , MUGU NE NA GIDAN GABA , YANZU NI WANNAN ABUN DA YA YI BAN MA SAN KO MINENE BA , SAI DAI RANAR DUEL DIN MU GANI AMMA NA SAN BA AL'HERI NE BA , SAI DAI KAWAI NA CE MALIK ALLAH YA KARE KA DA GA SHARIN AYMANE DA MACIZAN SHI ▪AFTER TWO DAYS 🤧🔥 yau ta kama ranar Friday , tun karfe 6 a ka fara shirye²n duel din Malik da Aymane misalin karfe 8 kowa ya hallaci wajen da za a gabatar da duel din , a cikin garden a ka shirya yin duel din kowa na cikin masarautar sai da ya hallaci wajen , da mutanan fadar Malik , da kuma na fadar Aymane , har da su MALIKAT INAS , da Inaya ba rokon da su mama ba su yi mata ba a kan ta zauna , amma fir ta ki ta ce sai ta je a tsaye Malik da Aymane su ke tsakiyar garden din , su na fuskantar juna , Rafik na tsaye da ga tsakiyar su a gefe cikin nitsuwa ya fara magana ya na fadin " kun san yadda tsarin fada da takobi ya ke , ban da zalinci " cikin nitsuwa Aymane ya katse shi da cewa " ka ga don Allah ka ba mu waje mu yi mu wuce wajen , a sani na ka kashe ko a kashe ka shi ne tsarin wannan fadan , dan haka ka wuce ka ba mu waje " " za ka iya tafiya Rafik " Malik ya fada cikin sanyin murya gyada mishi kai Rafik ya yi kafin ya juya ya karbi Sword din da ke hannayan Azim da ke tsaye bayan shi ya mikawa Aymane guda , sannan ya mikawa Malik guda ya na fadin " Allah ya ba mai rabo sa'a " amma cikin zuciyar shi Malik kawai ya ke yi wa addu'ar samun nassara , da ga haka ya bar wajen ya koma wajen da a ka shiryawa ma su kallo ya zauna saman chair din shi geffen MALIKAT AL'UMU , ya na zama ko Aymane da Malik su ka fara fadan su a hankali MALIKAT AL'UMU ta juyo ta kalli Rafik ta ce " Rafik , wai fadan minene su ke yi ? " wani dan karamin murmushi Rafik ya yi ya na fadin " ranki shi dade , wanda ya yi nassara shi zai hau kujerar Malik " " Wanda bai yi nassara kuma fa ? " MALIKAT INAS ta fada dan jinkirtawa Rafik ya yi kafin ya ce " mutuwa zai yi " a tare su ka ce " inallillahi wa'ina illaihi raji'un , ka na nufin idan Malik bai yi nassara ba kashe shi Aymane zai yi ? " a hankali ya gyada mishi kai ya na fadin " ina jin tsoron hakan ranki shi dade , addu'a kawai za ku yi Allah ya ba shi sa'a , idan Aymane ya yi nassara za mu shiga babban tashin hankali dan babu wanda zai iya yin jayaya da shi a kan kujerar Malik " kalmar shahada MALIKAT AL'UMU da INAS su ka shiga jerowa , kenan kashe musu yaron su za a yi in dai bai yi nassara ba , nan take zuciyoyinsu su ka fara bugawa da karfi a hankali MALIKAT INAS ta juya ta kalli su Malik dai'dai lokacin da Aymane ya samu Malik a damtsen shi na dama ya yanke shi nan take ya fara zubar da jini har ya gangaro saman takobin hannunshi da sauri Inaya ta rumtse idanunta , ta na kauda kai gefe a hankali RIANNA ta riko ta , ta na fadin " ko mu koma ciki ? " girgiza mata kai Inaya ta yi ta na fadin " a'a Aunty RIANNA " da to kawai RIANNA ta amsa mata kafin su ci gaba da kallon su Malik wata yar karamar dariya Aymane ya yi lokacin da ya ji wa Malik ciwo a hannu ya na fadin " ya ,har ka gaji ? still yanzu ma mu ka fara " a hankali ya kai hannun shi na hagu ya riko sword din , dan ba karamin rauni ya samu ba , ba zai iya ci gaba da fadan da hannun damar ba wata yar karamar ajiyar zuciya ya sauke kafin ya nufi Aymane , shi ma Aymane da gudu ya nufo Malik sai dai kafin ya kai ga daga takobin shi , Malik ya juya ya ba shi baya ya caka mishi sword din shi a ciki har sai da ta fito mishi ta baya da sauri Malik ya juyo ya yi baya ya na kallon Aymane da ke zubar da jini ta bakinshi wata nanauyar ajiyar zuciya duk mutanan Malik su ka sauke MALIKAT AL'UMU da INAS su na yi wa Allah godiya cikin zuciyoyinsu da sauri Inaya ta mike tsaye ta na kallon Malik ta ce " ka cire mishi kai ! " ta fada da karfi har sai da hankalin kowa ya dawo gare ta Malik na jin hakan ya tuno abun da ta tabba fada mishi lokacin da ya ce wa Aymane su yi duel din na ya cire mishi kai ta haka ne kawai zai mutu tuno hakan ne ya sa shi nufar Aymane da sauri zai zame takobin shi sai dai kafin ya karaso ya ga Aymane ya zare takobin da kan shi ya tilla gefe ya na sakin murmushi " ka kashe ni , amma ba za ka iya ja da shi ba " Aymane ya fada jini na fitowa da ga bakin shi kafin Malik ya yi taku biyu , kawai ya ga skin din Aymane ta koma green scales na fito mishi kamar irin na maciji , idanunshi su ka koma irin na maciji bayan kalmar shahada ba abun da mutanan wajen da Malik su ke yi su na kallon Aymane da ya fara girma , ya na girma , ya na girma , ya koma dankareren maciji tsanwa shar , girman shi ya yi biyun macijin da Rouksar ta zama a word room wani irin razanannan kuka macijin nan ya yi tongue din shi na fitowa waje duk mutanan wajen sai da su ka saki kara , ma su tserewa na yi , ma su suma na yi MALIKAT INAS , MALIKAT AL'UMU da Rafik , RIANNA , Diya , bayan kalmar shahada ba abun da su ke yi da sauri General Abdallah ya kalli Sojojin shi da ke tsaye cen a geffen ya daga musu murya ya na fadin " Fire ! " da sauri Su ka fiddo gun su ka fara harbin macijin nan , amma ko ajikin shi , bullet din sai faduwa kassa su ke yi wutsiyar shi kawai ya sa ya buge duk sojojin da ke wajen su ka yi cen gefe su ka fadi shi dai Malik ya yi sumar tsaye bayan kallon macijin nan ba abun da ya ke yi , sai kalmar shahada da ya ke karantawa cikin zuciyar shi , ya na kallon macijin nan cikin ido dan shi ma macijin Malik ya ke kallon ya na tsaye a haka kawai ya ga........ ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ ( LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) STORY & WRITTEN BY : MEERAH ⚘🕊 【THE ROYALTY LOVE ❤🌹】 【 BOOK ________ 4 ❤✍💌 】 _______________________♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡______________________ { P A G E ________ 11 & 12 ✍💕🔥} ya na tsaye a haka kawai ya ga Inaya kamar ta fado da ga sama tsaye a gaban shi , kayan jikin ta duk sun koma baki kirin , gashin ta ya yi black sosai , ga shi kuma ya yi kwari kamar an yi kitso , idanunta sun koma bakake kirin ko digon fari babu , har wani bakin hayaki ke tashi da ga saman rigar ta da gashin ta , wani abun mamaki kuma cikin jikinta ya bace bat kamar ba ta taba yi ba a hankali Malik ya bude baki ya na shirin magana ya ga wani haske ya fito da ga jikin ta ya yi cen gefe dan nesa kadan wata irin muguwar bugawa zuciyar shi ta yi wata Inayar ce kuma daban , amma wannan kayan jikin ta duk farare ne , har gashin kan ta fari ne kal , idanunta sun koma farare kal har wani haske su ke yi kamar torch , ita ma dai cikin ta a shafe ya ke babu allamun pregnancy a tattare da ita cikin wani harshe da ban san irin shi ba mai sanye da bakaken kaya ta cewa dayar " Abyad ki koma , idan wani abu ya same ki dukka mu uku ba za mu rayu ba " girgiza mata kai Abyad ta yi ta na fadin " Aswad , ba za ki iya yin fada da shi ba ke kadai , ki bari na taimaka miki " " Ki fara fitar da Malik da ga wajen nan " Aswad ta fada gyada mata kai kawai Abyad ta yi , kafin ta tako da gudu ta nufo Malik da ya yi sumar tsaye , ta riko hannunshi ta bace bat tare da shi sai ga ta tsaya gaban su MALIKAT AL'UMU rike da Malik sakin hannunshi ta yi , ta na shirin juyawa ya riko hannunta ya na fadin " Cutie , kar ki tafi " a hankali Abyad ta juyo , ta kwace hannunta a hankali , wannan karan da harshen Hausa ta ce " kar ka damu ba abun da zai same ta , ka zauna a nan , idan wani abu ya same ka , ita ma za ta cutu " ta na gama fadar haka , ta yi taku uku baya , ta na fuskantar su , ta fara motsa lips din ta a hankali a hankali wani farin hayaki ya fara tashi tsakanin su , ta dago hannun ta , ta fara yin sama da shi , shi ma hayakin nan ya fara yin sama sannan ta daina motsa lips din ta , ta sauko hannun ta kafin ta juya da gudu ta na juyawa Malik ya tako da sauri ya na fadin " Cutie ! " , sai dai ya na iso wajen hayakin nan ya yi baya da sauri ya ji kamar ya bugi bango a rude ya tsaya ya na kallon hayakin nan , ya mika hannun shi , kawai sai ya ga ya tabo abu kamar ya taba bango cikin fitar hayaci ya fara kai wa hayakin nan bugu , ya na fadin " Cutie ! Cutie ! " da sauri Diya ya riko shi ya na fadin " Ka kontar da hankalin ka , ba abun da zai faru da ita bangaran Abyad kuwa , kai tsaye geffen Aswad ta dawo ta tsaya ta na fadin " ya za mu yi da shi ? " a hankali Aswad ta yi sama da hannu ta , sai ga wata katuwar Sword baka kirin ta fito a ciki , ba tare da ta kalli Abyad ba ta ce mata " kar ki damu , zan yi maganin shi " ta na gama fadar haka ta nufi macijin nan da gudu da sauri ya juyo da wutsiyar shi zai kai mata bugu , kawai sai ta bace bat sai ga ta tsaya a bayan shi , ba tsaya bata lokaci kawai ta caka mishi sword din hannun ta a baya wani irin razanannan kuka macijin nan ya yi , a dubu dari ya sa wutsiyar shi ya buge ta , wata yar karamar kara ta saki ta na yin cen gefe ta fadi " Cutie ! " Malik ya fada da karfi ya na zaro idanu lokacin da macijin nan ya buge ta , sa karfi ya shiga kai wa hayakin nan bugu amma ina , ba kuma zai iya zagaye shi ba dan hayakin ya raba masarautar biyu , babu ta hanyar wucewa lokaci guda Abyad ta bace , sai ga ta tsugune geffen Aswad ta na fadin " ba ki ji ciwo ba ? " " a'a " Aswad ta fada ta na kokarin tashi da sauri Abyad ta mike tsaye , ta na kallon macijin nan ya na kokarin cire sword din Aswad da ke bayan shi a hankali ta mika hannunta , kamar da ga sama wata farar bow ta fito cikin hannunta a hankali ta kai dayan hannunta , ta fara jan zaren bow din nan kamar ta na shirin tilla kibiya sai da ta ja shi har karshe kafin ta saki , kawai sai na ga wata farar Arrow ta fito ta nufi macijin nan da mugun gudu ta soke shi a jiki wani marayen kuka macijin nan ya saki dan ba karya ya ji zafin hakan lokaci guda Abyad ta bace bat , ta koma gaban macijin , ta kara jan bow din nan ta harba mishi kibiya , ta sake bacewa ta koma bayan shi , ta harba mishi wata arrow a baya , yanzu ma ta sake bacewa ta koma dayan geffen ta sake harba mishi arrow , sai da ta harba mishi har guda hudu kafin bow din hannunta ta bace wani marayen kuka macijin nan ya saki , kafin ya nufe ta gudu , duk da ya galabaita dan har idanun shi sun fara rufewa , jikin shi ya yi sanyi ya na isa ya sa wutsiya , kafin ta bace , ya matse ta a cikin wutsiyar shi ya daga ta sama , ya buga ga kassa da mugun karfi har kura na tashi da mugun gudu Aswad ta tasso , ta nufi Abyad ta Zube saman guyiwowin ta , ta talabo ta , ta na fadin " Abyad , Abyad , ki na ji na ? " murya a disashe ta ce " ina jin ki , ba abun da ya same ni " da sauri Aswad ta mike tsaye , cike da bacin rai , ta bude baki ta yi wata razananiyar kara ta na kallon macijin nan nan take wata bakar guguwa ta tashi da karfi ta fara mamaye macijin nan , a hankali Aswad ta daga kafa ta shiga cikin guguwar nan , ta tsaya cak waje guda a hankali ta mika hannunta , da sauri Sword din ta da ta caka mishi a baya ta fito ta koma cikin hannun ta wata razananiyar kara macijin nan ya saki lokacin da sword din ta fita da ga jikin shi da sauri ya nufi Aswad cike da bacin rai , sai dai kafin ya iso gare ta , ta bace bat cikin guguwar nan cak ya tsaya ya na juyi ya na kuka ya na neman Aswad sai da ya share one minute a haka , babu Aswad ya na a haka ya ga kawai ta fito da ga cikin guguwar nan cen sama dai'dai tsawon shi , kamar an tillo ta , ta daga sword din ta sama ta raba macijin nan gida biyu har jininshi ya watsun mata a fuska nan take ya fadi kassa rabi ya yi gefe , rabi ya yi dayan gefe non take gudun guguwar nan ya kara , sai kururuwa ta ke yi wani razanannan sauti na fitowa da ga ciki sai da ta yi wajen good one minute ta na wannan sautin kafin ta bace bat tare da macijin baki daya wata nanauyar ajiyar zuciya Abyad ta sauke ita da Aswad a tare , ta tashi da gudu ta nufi Aswad wani dan karamin murmushi Aswad ta saki kafin ta bude mata hannayan ta , ta na isa ta shige jikin ta a hankali farin hayakin nan da ta tare su Malik da shi ya fara yin kassa har ya bace shi ma ya na bacewa ko sai ga Inaya tsaye a wajen , ta na sanye da kayan ta na farko , idanun ta sun komo dai'dai har wannan katon cikin nata a hankali ta fara bin wajen da kallo ta na tambayar kanta me ta ke yi a nan cen ta hango su Malik tsaye , sun yi cirko² su na kallon ta babu ko kiftawa sun ma rasa abun da za su ce , da a ce wani ne ya ba su labarin abun su ka gani yau , da wlh sai su ce mishi ba shi da hankali , amma da idanunsu su ka gani , kowa ya shiga yi wa Inaya ayar tambaya ban da Malik ta na ganin shi ta saki wani cool murmushi ta fara takawa a hankali ta nufe shi ya na ganin ta fara takowa ya sauke wata nanauyar ajiyar zuciya har zai daga kafa kawai ya ga ta tsaya cak , kawai sai ya ga wajen da ta ke tsaye ya jiqe kamar an watsa mishi ruwa wata irin muguwar murdawa cikin ta , ya yi mata har sai da ta saki wata razananiyar kara ta na dafe shi da hannayan ta a dubu dari Malik ya yi kanta ya na fadin " Cutie , me ya faru ? " amma ko jin shi ba ta yi sai kara ta saki , ta nunfashi sama sama da sauri su MALIKAT INAS su ka nufe su dan sun ga allamun kamar naquda ce ta ke , ga shi kuma ta zubar da ruwa hakan na nufin haihuwa za ta yi MALIKAT INAS na karasowa wajen Malik ta ce mishi " mu kai word room , haifuwa za ta yi " dum ya ji gaban shi ya fadi , tun kafin wani ya yi magana , ya sa hannayan shi biyu ya dauke ta cak sai kara ta ke saki ya nufi word room da ita sai cije lips din shi ya ke dan ba karamin zafi hannun shi na dama ya ke yi mishi ba , ga shi ko sai zubar da jini ya ke amma a haka ya daure ya nufi word room da ita , tun a reception ya shiga kwallawa su doctor kira dama cikin word room din akwai mace likita me karbar haihuwar matan masarautar da gudu wata nurse ta tafi office din ta , ta kira ta ta na fitowa ta cewa Malik " yi sauri ka shiga da ita dakin cen " ta fada ta na nuna mishi wani daki da sauri ya nufi dakin , har su MALIKAT INAS sun bi bayan shi , doctor ta ce musu " a'a ku tsaya a nan , shi ma yanzu zai fito " ta kai karshen ta na nufar dakin da Malik ya shiga ba musu kowane ya zauna saman waiting chair , kowane da addu'ar da ya ke yi cikin zuciyar shi bangaran Malik kuwa , ya na isa cikin dakin kawai ya kontar da ita saman gadon jinya dai'dai lokacin da doctor ta shigo ta na fadin " za ka iya fita " ta fada dai'dai lokacin da wasu nurse guda biyu su ka shiga da gudu har ya juya zai fita ya ji ta riko hannunshi da sauri ya juya ya na kallon ta , a hankali ta girgiza mishi kai hawaye na zubo mata ya na shirin yi mata magana doctor ta ce " please ranka shi dade ka fita " ko sauraron ta ba ya yi ya dawo wajen Inayar shi ya sunkuyo ya ce mata " ki kontar da hankalin ki ba abun da zai faru , kin ji ? " ya na gama fadar haka ya jiyo Muryar doctor ta na fadin " ka fita don Allah " cikin bacin rai ya dago ya ce mata " babu inda zan je , ku yi aikin ku kawai , idan ba za ki iya ba ki fice min da ga nan " ba dan ta so ba ta ja bakin ta ta yi shiru wata yar karamar kara Inaya ta saki , ta na kuka ta ce " kar ka saki hannuna don Allah " a hankali ya dago hannunta da ke cikin nashi ya manna mishi kiss ya na fadin " ba abun da zai faru , ina tare da ke " ba ta amsa mishi ba kawai ta saki kara ta na lumshe idanun ta har wani dago kai ta yi kafin ta koma , ga wata uwar zufa da ta karayo mata , kamar an watsa mata ruwa cikin sanyin murya doctor ta ce mata " ki kontar da hankalin ki , ki dinga jan nunfashi a hankali , ki na saukewa " ba musu Inaya ta ja wani dogon nunfashi har kirjin ta na yin sama sai dai maimakon ta sauke kawai sai ta saki kara ta na kara matse hannun Malik a cikin nata da sauri ya daura dayan hannun nashi saman kumatun ta ya na fadin " Cutie , Dube ni kin ji ? " ba musu ta juyo ta kalle shi idanun ta duk sun yi ja sai hawaye ta ke ta marairaice fuska da sauri ya sauke forehead din shi saman nata ya na kallon cikin idanunta , murya cen kassan makoshi ya ce mata " ba abun da zai faru da ke okay ? " da sauri ta katse shi da cewa " yaya Zayd mutuwa zan yi , da zafi " ta kai karshen ta na kara sautin kukan ta cikin sanyin murya ya ce mata " ba abun da zai same ki , ki daina cewa mutuwa za ki " ya fada kamar zai yi kuka har wasu hawaye ke zubo mishi wanda shi kan shi bai San da su ba karan farko da na ga hawayen Malik , ko a lokacin da Daddyn shi ya mutu bai yi hawaye ba wata yar karamar kara Inaya ta saki ta na janye forehead din ta , ta kauda kai gefe , da karfi ta cije lips din ta kamar za ta fashe su da sauri Malik ya kalli doctor ya ce " wai har yanzu ba ku fiddo mata wannan abun ba ? " " don't worry , ga kanshi nan na fitowa , ranki shi dade , last working , ki turo da karfi " doctor ta fada ta na kallon Inaya da sauri Inaya ta shiga girgiza mata kai idanunta a lumshe da sauri Malik ya daura hannunshi saman kumatunta , ya juyo da face din ta , ya sauke forehead din shi saman nata murya kassa kassa ya ce " okay , zan kirga zuwa uku , da ga nan ki ka dogon nunfashi ki sauke , kin ji ko ? " a hankali ta gyada mishi kai allamun Eh " Okay , one , two , three let's go " wani dogon nunfashi ta na sakin wata siririyar kara karfin ta sauke wata nanauyar ajiyar dai'dai lokacin da kukan baby ya gauraye wajen wata nanauyar ajiyar zuciya Malik ya sauke ya na fadin " Alhamdoulilah " cikin zuciyar shi har lumshe idanunshi ya yi ya na sakin murmushi kamar shi ya yi aikin ya na bude idanunshi ya ga Inaya ta yi tsit kamar an yi ruwa an dauke Dum ya ji zuciyar shi ta buga da karfi , a dubu dari ya kai hannu ya fara jijiga ta ya na fadin " Cuti , Cutie , please ki bude idanunki , Cutie , please ki bude kar ki min haka mana " da sauri Doctor da ke rike da babynsu ta karaso wajen ta na fadin " ka kontar da hankalinka , ba mutuwa ta yi ba , suma ce ta yi " ta na gama fadar haka ya ga ta sauke babyn hannun ta saman kirjin Inaya ta kontar da kan shi saitin zuciyarta wani irin sanyi ne ya ji lokacin da idanunshi su ka sauka saman babyn , kyakyawa da shi fari kal kamar ka taba jini ya fito har wani ja ya yi , ya na kama tak da Malik kamar an tsaga kara , sai dai idanun shi a rufe su ke sai in ya bude mu ga kalar su da sauri Nurse din da ke tsaye a baya ta ce " Doctor , ina ga Twins ne " cikin rudu Doctor ta ce " Twins kuma ? " ta na gama fadar haka ta dauke babyn ta juya ta mikawa nurse din ai ko da gaske Twins ne dan ga kafafun shi nan su na son fitowa , ya kuma a ka yi haka bayan baby ta kai ya ke fara fitowa da sauri Malik ya ce mata " Doctor me ya faru ? Twins ne ? " Doctor ba ta ce mishi komai ba ta na aikin ta kawai sai ganin ya yi ta na rike wani babyn a hannun ta amma ko motsi ba ya yi Dum ya ji zuciyar shi ta buga , kenan da gaske Twins ne ? ga shi shi ma namiji ne slowly Doctor ta dago ta kalli Malik , cikin raunin murya ta ce " i'm sorry bai zo da rai ba " ta fada dan ta san ba karamin abu zai sa baby ya fito ta kafafu ga shi ko motsi ba ya yi hakan na nufin ya jima da ya mutu a cikin ta ba ta sani ba Dum Malik ya ji zuciyar shi ta buga har wani lumshe idanu ya yi ya na fadin " inallillahi wa'ina illaihi raji'un " kassa kassa ta daya bangaran ya ji dadi da ba ta cikin hayacinta ta haihu da yanzu in ta ji babyn ta guda ya mutu zuciyar ta bugawa kawai za ta yi , a hankali ya sauke ajiyar zuciya kafin ya dago ya mikawa Doctor hannayan shi a kan ta ba shi babyn ba musu ta daura mishi babyn a hankali ya dago shi , ya yi mishi addu'a sannan ya yi mishi kiss saman forehead din shi ya na a haka kawai ya jiyo sautin kukan wani babyn , cak ya tsaya ya na zaro idanu , ga shi dai sautin ba ya kama da na farko wata nanauyar ajiyar zuciya ya sauke ya na lumshe idanunshi a hankali kafin ya sake bude su , ya dago kai nan ya ga Doctor rike da wani babyn , sai wuntsila kafafu ya ke , ido a rufe ya na kuka da karfi bai san lokacin da ya lumshe idanunshi ya na yi wa Allah godiya cikin zuciyar shi a hankali doctor ta matso rike da babyn ta ce mishi " congratulation it's a girl , ranka shi dade Triplets ne ta samu " sai da ya sunkuyar da kai ya mannawa babyn hannunshi kiss saman forehead sannan ya dago ya kalli Doctor ya ce " ba na son maganar nan ta fita da ga dakin nan , kar Wanda ya san MALIKAT Triplets ne ta haifa , ko ita kanta kar ku fada mata , ki dauki babyn cikin sirri ki bizine shi " dan zaro idanu ta yi ta na fadin " ran ka shi dade , ba za a yi mishi jana'iza ba ? " bai ce mata komai ba ya juya a hankali ya kontar da babyn saman gadon da ke bayan shi sannan ya juyo ya kali doctor ya ce " zan yi mishi jana'iza , amma ba na son kowa ya san da maganar nan , da ga ni sai ku ukun nan , na roke ku don Allah , dan son annabi kar ku fitar da maganar nan , na san ba za ta iya jure wa ba idan ta ji wannan maganar , ni na godewa Allah ma da ba ta cikin hayacin ta ya shigo duniya , na roke ku don Allah kar ku bari wani ya san wannan maganar , ya zama sirrin mu na mudu hudun nan sai Allah " a hankali Doctor ta gyada mishi kai kafin ta juya ta karbi dayan babyn ta ce " in sha Allah , Twins ne MALIKAT ta haifa , nurse ? " a tare su ka ce " twins ne ta haifa " wata boyayyar ajiyar zuciya Malik ya sauke , ya na shirin magana Doctor ta riga shi cewa " za ka rike shi , ko mu tafi ? " bai ce mata komai ba ya dago hannayan shi a hankali ya mika mata ba musu ta daura mishi babyn a sama nan take ya kara sautin kukan shi ya na wuntsila Kafafu kadan ya kubcewa Malik da sauri Doctor ta karbe shi ta na fadin " Nurse , ku je a yi wa mai martaba dress , ya samu rauni a jikin shi , ku kontar Da hankalin ku , zan kula da komai " ta fada ta na juyawa da babyn hannunta , gudar nurse din ta na rike da namijin sai da ya sunkuyo ya mannawa Inaya kiss a saman forehead din ta , sannan ya kai bakin shi saitin kunnen ta ya yi mata rada kafin ya mike ya juya ya bi bayan nurse din nan su ka baro dakin , ya ma kassa kallon dayan babyn nashi dan ya na jin zafi cikin zuciyar shi ba kadan ba , amma ba komai haka Allah ya so kuma duk abun da ya yi dai'dai ne ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ ( LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) STORY & WRITTEN BY : MEERAH ⚘🕊 【THE ROYALTY LOVE ❤🌹】 【 BOOK ________ 4 📚✍💌 】 _______________________♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡______________________ { P A G E ________ 13 & 14 ✍💕🔥} su na fitowa kawai ta ga Malik ya yi gaba abun shi , ya nufi su MALIKAT AL'UMU da ke zazzaune sun yi zugum su na ganin shi su ka mike a tare su na tambayar ta sauka lafiya gyada musu kai kawai ya yi kafin ya ce " za ku iya komawa part din ku , doctor ta ce ta na bukatar hutu " ya kai karshen ya na shirin takawa da sauri MALIKAT AL'UMU ta taro shi ta na fadin " me ta samu ? mace ko namiji ? " slowly ya juya ya kalli MALIKAT INAS , cikin sanyin murya ya ce " Nayel & Nailah " wani kyawatencen murmushi MALIKAT INAS ta saki har hawaye na zubo mata da sauri RIANNA ta ce " Akhie Twins ne ta samu ? " gyada mata kai ya yi a hankali kafin ya juya ya fice word room din ran shi fari tas kamar an yi mishi albishir da gidan Aljanna a haka su ma su MALIKAT INAS su ka baro Word room din , kowace ta nufi part din ta na asali shi ma Diya da Nesrine su ka koma part din su , haka Abdoul da Tesnim Rafik kuma ya nufi fada ya bude ta , ya kira duk wani na fadar ya fada mishi ya dawo Ranar Friday za a sake nada Malik Nawfel Hicham Bin Jaabar bangaran Malik kuwa kai tsaye part din MALIKAT HOUDA ya koma , babu ko sallama ya shigo parlourn , nan ya tardo ta zaune , sai faman addu'a ta ke yi ta na ganin shi ta sauke ajiyar zuciya ta tashi da sauri ta nufe shi ta na fadin " masoyina , ba abun da ya same ka dai ko ? Allah na gode maka " wani dan karamin murmushin geffen fuska ya sakin mata kafin ya ce " kin ga , ki daina kira na da masoyinki , so ki ke papi ya tardo ni , ya ce na kwace mishi matar shi " wata yar karamar dariya ta saki ta na fadin " kai dai ka sani , mara kunya kawai " " shikenan , bari na yi wanka , zan yi miki albishir me dadi " " shikenan , ina jiran ka , mai martaba " ta fada cikin zolaya bai ce mata komai ba ya nufi corridor ya shige bedroom din Inaya ke ciki , kai tsaye toilet ya wuce bai ce mata komai ba ya nufi corridor ya shige bedroom din Inaya ke ciki , kai tsaye toilet ya wuce dan ya yi wanka jim kadan ya fito sanye da bathrobe bed din ya nufo ya zauna , ya zauna a baki ya kai hannu ya bude bedside drawer ya fido A box sannan ya ajiye a sama , sannan ya bude ya fiddo wata yar takarda hannu ya sa ya rabata gida biyu , ya fido wata yar karamar allura irin ta dinki ta na da wani siririn zare blue a hankali ya kai allurar nan wajen yankar da Aymane ya yi mishi , ya fara yi wa kanshi dinki , ya na lumshe idanunshi , ya na cije lips din shi na kassa dan ba karamin zafi a dakwai ba amma a haka ya yi wa kan shi dinki , ya yi dressing wajen , sannan ya tashi ya nufi dressing room jim kadan ya fito sanye da Trouser black color , da T-shirt sky blue , sai wasu sneakers farare a kafafun shi , ya daure wanan smooth hai din nashi a baya , sai tashin qamshi ya ke , sannan ya nufi kofar fita bedroom din ya fito kai tsaye part din ya baki daya ya baro , ya nufi hanyar Fada bakinshi da sallama cen kassan makoshi ya shigo Fadar , nan ya tardo duk mutanan fadar shi , su na zaune su na ganin shi kowane ya saki murmushi ya na mikewa tsaye su na gaishe shi cike girmamawa sai da ya karaso tsakiyar fada sannan ya juya ya kalli side din su tsayawa ya yi ya kare musu kallo na dan lokaci kafin ya ce " na ji dadin ganin ku cikin koshin lafiya " a tare duk su ka saki wani kyawatencen murmushi su na fadin suma sun ji dadin ganin shi a raye dan sunkuyar da kai ya yi kafin ya dago ya ce " okay , zan so ku fara shirye shiryen nada sabon Malik ranar Friday , sannan Dalil ( sabon Sarkin bayi ) zan so ka mayar da bayinka part din su , sannan gobe ka sa su je part din Malik su kwashe duk kayan da ke ciki za a zuba sabi , duk wani abu da ke bukatar gyara a cikin masarautar nan har ma wajen ta kawai ku aiwatar , kar ku damu da adadin kudin za a kashe , Idris ( shi ne sabon me kula da dukiyar Daular ) ka bude bankin masarautar , na ba da dama a fitar da kudin da su ka dace dan ganin an kyara masarautar , amma abu na farko da na ke son ku fara shi ne cire min wadanacen banzan status da a ka kafa min bakin Daula , General Abdallah , duk mutanan Fadar Aymane da ke hannun jami'an ka , ku yi executed din su kawai , ita kuma Hafsat a mayar da ita wajen mahaifiyar ta , sannan ku shirya min zama da yan JARIDA a matsayin Mr president ba Malik ba ran monday " ( Idan ba ku manta ba tun farko na ce muku Malik shi ne shugaban kassar Saudiya , kuma duk wata maganar administration a hannun shi ta ke , hakan na nufin shi ne sarki kuma president din kassar Saudiya , mutanan Fadar shi kuma duk yawwancin su ministers ne ) " an gama ya shugaba " su ke fada a tare sannan su ka shiga jero mishi addu'a cikin zuciyarshi ya ke amsa musu da Ameen kafin ya juya ya sa kafa ya baro fadar tafiyar shi ya ke cikin konciyar hankali ya na bin Daular da kallo , a haka har ya karaso cikin word room kai tsaye dakin da ya kai Inaya da farko ya nufa , kawai sai ya ga babu kowa a ciki da sauri ya juya ya koma reception ya na tambayar matar shi cikin nitsuwa Wata nurse ta ce mishi " an sauya musu daki , su na cikin room 5 " bai bata amsa ba ya juya ya nufi room 5 , babu ko sallama ya tura kofar ya shiga ya na idanunshi su ka sauka saman ta , ta na konce saman gado ta na sanye da wata gown blue irin ta ma su jinya , idanunta a lumshe da allamun barci ta ke ko har yanzu ba ta farka da ga sumar ta ba kusan gadon ya ga wani dan cradle tsayin shi daya da gadon Inaya a ciki ya hango babys din su konce a ciki , an dunkule su cikin wani towel , Macen pink , Namiji kuma blue , Ita dai Nailah idanunta a rufe da allamun barci ta ke , Nayel kuma idanunshi na bude ya na kallon ceiling , idanunshi Tak tak irin na Malik wato hazel wata nanauyar ajiyar zuciya Malik ya sauke kafin ya tako a hankali kamar barawo ya karaso gaban su tsayawa ya yi ya na bin babys din shi da kallo kamar ya hadiye su ya na a haka kawai ya ga idanun babyn sun juye kamar yadda a ke juya PAGE din littafi su ka koma farare kal kafin su dawo dai'dai wani dan karamin murmushin geffen fuska ya yi murya cen kassan makoshi ya ce " idanun momynka ka dauko " ya na gama fadar haka ya tako a hankali wajen shi , har kai hannu zai daukar babyn ya tsaya cak ya na kallon Tambarin masarautar a wuyan babynshi ya so ya duba hannun Nailah , amma ya san tunda a ka yi wa Nayel ba makawa ita ma an yi mata lokaci guda kawai ya ji ranshi ya baci da sauri ya janye hannunshi ya juya da sauri ya fice dakin kai tsaye office din doctor din da ta karbi haihuwar Inaya ya wuce babu ko sallama ya tura kofar office din ya shigo ya na fadin " wa ya ba ku izinin yi wa babyna tambarin masarautar nan ? " a hankali Doctor ta mike ta na fadin " ranka shi dade b..... " ba ta kai karshen maganar ta ba ya katse ta da cewa " ki ba ni amsar tambaya ta kawai " " MALIKAT AL'UMU " ta fada a takaice bai ce mata komai ba kawai ya juya ya fice office din , kai tsaye word room din ya baro ya nufi part din MALIKAT AL'UMU ya na taku da sauri , duk yanayin face din shi ya sauya da allamun ranshi ya baci babu ko sallama ya shigo parlourn MALIKAT AL'UMU ya na kiran " momy ! , momy ! momy ! " ya ke fada da karfi ya na tsaye tsakiyar parlourn da sauri MALIKAT AL'UMU ta fito da ga corridor a rude ta ke fadin " lafiya ka ke min irin wannan kiran ? me ya faru ? " cikin bacin rai ya ce mata " momy , why za ki ce a yi wa babyna tambarin masarauta ? , why ? " " zo mare ni Nawfel , mare ni na ce don Allah " ta fada cikin tsare gida wani dan karamin tsaki ya ja ya na kauda kai gefe kafin ya ce mata " momy , ni fa ban bada izinin yi wa babyna wannan abun ba , why za ki min haka ? " " saboda yaron Malik ne , kuma dole a yi mishi tambarin masarauta , kar ka ce za ka goge shi , wlh za ka ji musu ciwo ka ga har yanzu ba wani kwari ne da su ba " " momy ba na son abun da zai hada babys di na da wannan masarautar , that's why na yanke shawarar komawa US da su bayan nadin Malik " dan zaro idanu MALIKAT AL'UMU ta yi ta na fadin " what ? ban gane ba , kamar ya za ka koma US da su ? ka na nufin ba za ka zauna ba ? " cikin sanyin murya ya ce mata " yeah , ba zan zauna ba , ni dama ban dawo da Niyar zama ba , kuma in sha Allah Next Friday zan koma US , dalilin da ya sa ban bada izinin yi mishi tambarin masarautar nan ba , amma kin je kin ce a yi mishi , gaskiya momy ban ji dadin haka ba " a hankali MALIKAT AL'UMU ta nufi Sofa , ta zauna ta na kallon shi fuska a marairaice ta ce " yanzu tsakani da Allah Nawfel komawa za ka yi , tun da komai ya wuce ka zauna cikin familyn ka mana " a hankali ya tako wajen sofar ya zauna geffen ta murya a sanyaye ya ce " momy , ba zan yi miki karya ba , these months that I spent there were the best of my entire life, I felt free, without any pressure, just her and me , na ji dadin zamana a cen fiye da komai , please kar ki ce za ki tsayar da ni , i promise duk bayan sallar Azumi za mu dinga dawowa mu yi babbar sallat a nan , just let me go please " shiru MALIKAT AL'UMU ta yi ta rasa abun da za ta ce mishi , ita ta na farin cikin komai zai dawo dai'dai , amma ya ce zai koma , zai sake barin su a hankali ta sauke ajiyar zuciya kafin ta ce " kujerar Malik kuma fa ? wa zai hau ta yanzu ? " " Diya " ya fada a takaice " ka sani Diya ba zai iya hawa kujerar nan ba , in da ma a ce Abdoul ne da zai iya hawa " " na sani momy , amma shi za a nada , dan na san Bayan shi babu wanda zai iya rike min ahalina , na san zai kula da masarautar nan kamar yadda ni zan kula da ita , na yarda da Diya fiye da rayuwata , ba dan shi ba da yanzu ban san inda zan tsinci kai na ba , ba dan shi ba da ba zan taba haduwa uncle bare har ya ba ni auren Cutie , duk wani abun al'heri da ya same ni cikin rayuwata shi ne sila , shi ya sa na yarda da shi fiye da rayuwata , he is my best and ONLY friend's , He is my Brother not my Cousin , dan haka ya na da ikon hawa kujerar Malik " wani dan karamin murmushi MALIKAT AL'UMU ta saki kafin ta ce " ka tabbatar shi ne abun da ka ke so ? " " na tabbatar momy " ya fada kai tsaye " shikenan , amma kar ka fadawa kowa maganar nan , har ranar nadin " " okay momy " ya fada ya na mikewa tsaye da sauri MALIKAT AL'UMU ta ce mishi " ina kuma za ka tafi ? " " ina son na ga babyna kafin mu tafi mosque lokacin sallat ya yi " da to kawai ta amsa , da ga haka ya sa kafa ya fice part din har ya nufi hanyar word room a ka fara kiran sallat , kawai sai ya juya ya nufi mosque dan ya yi sallat bayan sun yi sallat , Diya ya ja hannunshi ya nufi part din shi da shi , sai tambayar shi Malik ya ke me ya faru , ya sake shi amma ko sauraron shi Diya ba ya yi , su ka shiga part din shi sai da su ka shiga cikin dayar bedroom sannan ya saki hannunshi , ya meda kofar ya rufe , ya saka mata security Malik na ganin haka ya ce mishi " wai lafiya ka kawo ni nan , ina son na je na ga babys di na , ka wani kawo ni nan har da rufe kofa " cikin sanyin murya Diya ya ce mishi " please , ka tsaya akwai wata magana da na ke son mu yi " wani dan karamin tsaki Malik ya yi ya na fadin " magana ba za ka iya yi min ita ba a mosque sai ka kawo ni har nan ? , wlh ba ka da hankali , ban hanya na wuce " ya fada ya na nufar kofar dakin da sauri Diya ya riko hannunshi ya janyo shi bayan da karfi ya na fadin " please Nawfel , ka tsaya wlh maganar mai mahimanci ce , don girman Allah ka tsaya " ya fada ya na marairaice fuska wani dan karamin tsaki Malik ya yi ya na fadin " okay , ina jin ka , amma yi sauri " wani dan karamin murmushi Diya ya yi kafin ya gyada mishi kai a hankali ya lumshe idanunshi a fara motsa lips din shi kamar ya na karanto wani abu a hankali skin din shi ta fara sauya launi , ta koma wani launi shi ba green ba shi ba yellow ba , scales su ka fara fito mishi , nan take skin din shi ta koma irin ta maciji , a dubu dari Diya ya bude idanun shi dai'dai lokacin da ya koma wani babban maciji , amma yanayin jikin shi da tsawon shi duk dai'dai yanayin jikin shi Diya ne da tsayin shi , sai wutsiyarshi a baya ta na motsi " inallillahi wa'ina illaihi raji'un " Malik ya fada da karfi har ya na yin baya ya fadi , ya na zaro idanu ya na kallon macijin da Diya ya koma zuciyar shi na duka uku uku , ganin abun ya ke kamar a mafarki a hankali ya bude baki lips din shi har kerma su ke ya na fadin " Diya ! " ya furta lokaci guda ya na gama fadar haka ya ga A hankali skin din macijin nan ta sauyawa , sannu sannu har ya bace Diya ya dawo tsaye a hankali ya zauna a kassa ya yi irin zaman cin tuwo ya sunkuyar da kai murya a sanyaye ya ce " na je na kira ka mu tafi mosque dan lokacin sallat ya yi , amma ban gan ka ba a part din MALIKAT HOUDA , shi ne da na tambaya , a ka ce min ka na part din MALIKAT AL'UMU , na je part din zan shiga na jiyo Muryarka ku na magana da MALIKAT AL'UMU , na ji abun da ka fada mata , ka yi hakuri na boye maka wannan sirrin tsawan shekaru , just na rasa yadda zan iya fada maka ne , na san duk lokacin da ka san ya na ke ba za ka taba ci gaba da yarda da ni ba , that's why ya bunne abu na , amma bayan na ji abun da ka fadawa MALIKAT AL'UMU shi ne na yanke shawarar fada maka " " ya Salam " Malik ya fada cikin zuciyar shi , ka fin ya bude baki ya ce " kai , kai ma tsafi ka ke yi ? kamar Aymane ? " da sauri Diya ya dago kai , nan Malik ya ga hawayen da ya ke zubar wa da sauri ya ce mishi " No , ba na tsafi , duk zaman da mu ka yi da kai ka taba gani na na yi wani abu mai kama da tsafi ? " a hankali Malik ya girgiza mishi kai allamun a'a kafin ya ce " ta ya a ka yi ka ke zama wannan abun kai ma , kenan ka na sane da Aymane shi ma ya na zama hakan ? " ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ ( LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) STORY & WRITTEN BY : MEERAH ⚘🕊 【THE ROYALTY LOVE ❤🌹】 【 BOOK ________ 4 📚✍💌 】 _______________________♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡______________________ { P A G E ________ 15 & 16 ✍💕🔥} dan jinkirtawa Diya ya yi kafin ya ce " tsinuwar macijiya ce a kan ahalin Abdoul Mujeeb , lokacin da mahaifin mu ya hau mulkin masarautar Ottoman ya yi kokarin kara fadada girman masarautar , akwai wani fili da ga bayan masarautar , kawai sai ya ce a sanyo shi cikin Daular , a yi sabin gine² a cen , ashe wajen snake's nest ne , lokacin da ya samu labarin wajen gidan macizai ne kawai sai ya tura a kashe duk macizan , haka ko a ka yi , amma abun da ba su sani ba , sarauniyar macizan mayya ce , kafin ta mutu sai da ta tsinewa Ahalin Abdoul Mujeeb , duk yaran da zai haifa za su zo rabi maciji , rabi mutum , kuma haka a ka yi , ba Aymane kadai ba , duk yaran Abdoul Mujeeb mu na iya komawa wannan macijin da ka gani na koma yanzu , amma na Rouksar daban ne , dan duk lokacin da idanunta su ka koma na maciji a ka yi katari wani ya kalli cikin su , to sai ya koma status har sai ta yi mishi kiss sannan ya dawo dai'dai , shi ya sa ma mu ke kiran ta da Medusa , ina da shekara 17 na fara komawa wannan macijin , abun ya yi matukar ban tsoro , da na fadawa Daddy shi ne ya ke ban labarin yadda a ka yi na zama macijin , da na ji hakan kawai na ji na tsani masarautar , shi ya sa ma na daina zama cikin Saudiya baki daya , na koma UK da zama , idan na gaji na tafi Dubaï ko Jordan ko Asia , tsakanin wadanan gariruwan hudu na kammala karatu na , shi kuma Aymane nashi macijin daban ya ke shi ma , saboda shan jinin mutum ya ke , mutanan ma sai mata , ba yin da Daddy bai yi ba dan ganin Aymane ya daina shan jini amma ya kassa , har ya kai ya gogawa Rouksar shan jini , ba tare da sanin shi ba , ga shi kuma ya koyo yin tsafi , da ya ga abun ya fara gagara shi ne ya tura shi kassar Rouma wajen wani babban masanin tsafi dan ya cire wannan macijin da ke jikin Aymane , amma ya kassa asali ma tsafin shi sai karuwa ya yi , babu yadda ya iya ya sa mishi ido har ya girma a haka , ba zan maka karya ba , lokacin da Aymane ya yi kokarin kashe ka shekara bakwai baya , ina sane , saboda na zo wucewa na ji ya na maganar , dalilin da ya sa ma na shigo masarautar Saudiya a ranar dan na cece ka , amma ina shigar ta kai ne mutum na farko da na ci karo da shi , ba karamin sanyi na ji ba ganin ka a raye , shi ya sa ma na hakura na bi ka Nigeria , saboda ina tsoron Aymane ya cutar da kai idan ya samu labarin ka na raye , na san ka manta amma ni na sani , duk lokacin da ka je kai wa papi Ziyara a Daular Ottoman kai da Tesnim , sai Aymane ya yi kokarin kashe ka , amma bai taba yin nassara ba , akasin da a ka samu , duk lokacin da ka ke zuwa Daular ni ba na nan , shi ya sa ba ka san ko ni wanene ba ranar da mu ka hadu , tun lokacin da na sauke idanu saman Baby na san ta na da aljanu , na san kuma Malik ya shiga jikinta ya ce maka dole sai ka fara karaya tsafin Aymane sannan za ka iya kashe shi , ko kuma ka cire mishi kai , ni na san inda Aymane ya boye sihirin shi , amma ba zan iya fada maka ba , saboda a jikin RIANNA ya boye shi a ranar da a ka yi auren su , hakan na nufin sai ka kashe RIANNA , shi ya sa na ja bakina na yi shiru , bare kuma ba ni da tabbacin za ka yarda da ni , mistake daya a ka samu Aymane ya koma maciji a gaban ka , da ni ma ba zan fada maka ba saboda ya na daya da ga cikin abun da ba na son tunawa a cikin rayuwa , dalilin da ya sa ma na yi bincike a kan yadda zan cire macijin da ke jikina , kuma Alhamdoulilah ya na fita a hankali ta hanyar karatun kur'ani da sallar dare dan macijin ba ya son adini , da farko girman shi ya kai irin na Aymane , ka yi hakuri na boye maka wannan abun tsawon shekaru but i don't know how to explain you , i'm just afraid idan na fada maka ka ji ka tsane ni ba zan iya jure hakan ba , I'm so sorry " ya fadi na karshen kamar zai yi kuka sai da ya dan jinkirta kafin ya ci gaba da fadin " lokacin da a ce ka sha poison , lokaci guda na san da Rouksar ce , dan ita kadai ke da poison , ba rokon da ban yi mata ba a kan ta ba ni antidote , ka yi hakuri har alkawari na yi mata idan ka tashi za ka aure ta , amma fir ta ki , ta na cewa idan ta ba ni kashe ta zai yi , na tambaye ta wa amma ta kassa fada min saboda ya rufe bakin ta da tsafin shi , sa'ar mu guda aljanun Baby sun tashi , ba dan haka sai dai ka mutu dan antidote din poison din ta , yawunta ne that's why ma ka ga mahaifinmu bai wani damu da mutuwarta ba saboda ya san wacece ita , haka ma Aymane ya yi kokarin ya ja mishi birki lokacin da ya hau kujerar amma ya yi kokarin kashe shi , shi ya sa ya ja bakinshi ya yi shiru dan ba abun da zai iya yi , ka yi hakuri ahalina ya cutar da kai dayawa , please ka samu wani gurbin a zuciyar ka ka yahe min , na san ko na mutu ruhi na ba zai samu salama ba idan ban fada maka gaskiya ba " wata nanauyar ajiyar zuciya Malik ya sauke kafin ya mike tsaye , ya na kallon Diya da ya tsare shi da ido ya na hawaye a hankali ya tako gaban shi ya tsaya , sannan ya mika mishi hannu wani cool murmushi Diya ya saki kafin ya dago hannun shi a hankali ya daura saman na Malik kafin ya mike tsaye ya na mikewa tsaye Malik ya kai hannu ya goge mishi hawayen shi ya na fadin " ni wlh na zata wata babbar magana ce za ka min , kawai dan ka yi zaune ka min kuka ne , ko dadi ya yi maka yawa ne ? " " ta ya za ka min irin wannan maganar bayan abun da na fada maka " a hankali Malik ya janye hannayan shi , kamar wanda bai san komai ba ya ce " me ka fada min , ni ban ni abun da ka fada ba " ya kai karshen ya na nufar kofar fita dakin da sauri Diya ya riko hannunshi ya na fadin " kar ka tafi ba ka ce min komai ba don Allah " a hankali Malik ya juyo ya ce mishi " don Allah malam tun dazu ka kawo ni nan ka tsaya ka na min kuka kamar wani karamin yaro , ni fa ina son na je na ga babys di na " " ka na nufin ba ka ji abun da na fada maka ba ? " Diya ya fada cikin rudu " yeah ban ji ba , ban kuma gani ba , zan iya tafiya yanzu ? " wani cool murmushi Diya ya saki dan ya gano abun da Malik ke kokarin yi a hankali ya saki hannunshi ya na fadin " shikenan tafiyar ka , ni barci ma na ke ji " " na gode " Malik ya fada a takaice kafin ya juya ya cire security din kofar ya fice ya bar Diya nan tsaye ya na sakin murmushi dama ya jima ya na son ya fadawa Malik wannan maganar amma ya rasa ta ina zai fara , amma yau ya samu kwarin guyiwar fada mishi , kuma ya ji dadi da Malik bai dauki abun wani iri ba , ya san da wani ne zai yi mishi wani kallon daban har ya yi kokarin kashe shi , amma Malik ko ajikinshi , shi ya sa ya ke Alfahari kasancewar shi dan uwa kuma amini ga Malik ▪MALIK bakinshi da Sallama ya shigo room din da Inaya ke konce , nan ya tardo ta zaune saman gadon , ta na rike Nayel wata nurse na gwada mata yadda za ta ba shi nono , Nailah kuma har yanzu ta na barci da allamun ita ma ta gaji har ya karaso wajen ba su lura ba , a hankali ya yi musu gyaran murya ya na fadin " za ki iya tafiya " ba musu nurse din nan ta fice ta ba su waje ta na fita ya janyo chair ya zauna bakin gadon ya na kallon Inaya ta na ganin ya zauna ta turo mishi dan bakin nan nata ta na shirin magana ya riga ta cewa " no please kar ki min wannan shagwabar taki a gaban babyn mu " ai ko sai da ta yi mishi shagwabar ta na fadin " ka ce mishi ya sake ni , zafi na ke ji " " ki bari idan ya ishe shi zai saki " ya na gama fadar haka ko babyn ya sake mata nipple wani dan karamin murmushi ta saki ta na kallon shi a hankali Malik ya kai hannu ya dauki babynshi , wani dan karamin murmushin geffen fuska ya saki lokacin da idanunshi su ka sauka cikin na babyn shi ya na a haka ya jiyo Muryar Inaya ta na fadin " la baby , da gaske murmushi ne ka ke ? " ta fada ta na dan leko face din shi a hankali ya dago babyn ya kai bakinshi wajen kunnen babyn ni dai ban ji abun da ya ke fada ba sai da ya gama sannan ya sauko babyn ya kalle ta ya ce " ba za ki gane ba , i'm just Happy to day , specially da ba abun da ya same ki " marairaice mishi fuska ta yi ta na fadin " amma yaya Zayd ba za mu sake samun wani babyn ba ko ? wlh sai da na ji kamar zan mutu sai da na dinga ganin wutar lahira " maganar ta ba karamar dariya ta so ta bashi ba amma ya danne kayanshi ya saki wani dan karamin murmushin geffen fuska ya na fadin " don't worry , Nayel & Nailah sun ishe mu , bayan su ba kari " wani cool murmushi ta sakin mishi kafin ta ce " ta gaske Nayel ka saka mishi ? " a hankali ya gyada mata kai allamun Eh wani kyawatencen murmushi ta saki har da dariya , ta na kallon shi rike babynsu " dubi har ya yi barci " ya fada ya na nuna mata Nayel da ya yi barci a cikin hannunshi murmushi mai dan sauti ta yi kafin ta ce " ba dole ba , ya na cikin hannun Daddyn shi dole barci ya dauke shi " bai ce mata komai ba ya ci gaba da kallon Nayel , sai zuba mishi surutu ta ke amma ba ya ma jin ta tuni ya tafi duniyar tunanin shi ya na a haka ya jiyo Muryar ta ta na fadin " baby , ina gudan babyn mu , ban gan shi ba " Dum ya ji zuciyar shi ta buga har dan zaro idanu ya yi da sauri ya dago kai ya na kallon ta , sai da ya dauki lokaci kafin ya ce " wane baby kuma bayan Nayel ? " a hankali ta girgiza mishi kai ta na fadin " baby , ni Nayab na ke cewa " wannan karan har wani dishi dishi ya gani , ya a ka yi ta san sunan da ya yi mishi huduba da shi , dan tabbas sunnan Nayab ya saka mishi a hankali ya bude baki Muryar shi har kerma ta ke ya ce " Cutie , Nayel ne ba Nayab ba " da sauri ta katse shi da ta na girgiza kai kamar za ta yi kuka ta ce " baby , ni baby uku ne a cikina , ina gudan babyn , ina jin Muryar shi ya na kira na , in wassa ka ke ka bari please , ni ka kawo min baby na " duk inda hankalin Malik ya ke sai da ya bi ya tashi ya ma rasa ya zai yi , ya a ka yi ta san da Nayab , bayan ya na da tabbacin ba ta cikin hayacinta lokacin da ya shigo duniya , in ma doctor ce ta fada mata ya a ka yi ta san sunan shi Nayab bayan shi bai fada mata ba ya yi nisa duniyar tunanin shi kawai ya jiyo Muryar mama ta shigo dakin ya na sallama a hankali ya sauke ajiyar zuciya kafin ya juya ya na amsa mata sallamar ta Inaya na ganin ta ta saki kuka ta na fadin " mama , ki ce mishi ya fiddo min babyna , ina jin shi ya na kira na , amma wai ya ce shi bai san maganar me na ke ba , ni baby uku na haifa ba guda ba , ku medo min da babyna " a hankali Mama ta rungume ta ta na fadin " Auta , duba ki gani " ta fada ta na nuna mata Malik da ke rike da Nayel cikin rudu Inaya ta kalle su kafin ta juyo da kallon ta kan mama cikin sanyin murya mama ta ce mata " kin dai gani , mijin ki ne kuma ya na rike babyn ku , ga guda kuma a konce , ki na tunanin da a ce uku ne ba zai fi ki farin ciki ba , amma kin gani baby biyu ne , kawai tunanin ki ne ya ba ki hakan " cikin kukan nata ta katse mama da cewa " amma mama ina jin kukan shi , ina jin shi ya na kira na " a hankali mama ta girgiza mata kai ta kai hannu ta fara goge mata hawayenta ta na fadin " tunanin ki ne kawai , please ki kontar da hankalin ki kin ji auta ? wannan su kadai ne babyn ku a yanzu sai wanda za ku samu a nan gaba , ai ki na so ko ? " wata yar karamar dariya ta yi kafin ta ce " mama da gaske biyu ne ba ? ba uku ba ? " " no biyu ne Allah ya Albarkaci auren ku da su , ko ba ki son su ? " da sauri ta ce " mama ina son babyna mana , fiye da komai " " har ni ? " su ka tsinci Muryar Malik ya na fada a tare su ka juya su na kallon shi , ya tsare su da ido wata yar karamar dariya ta yi kafin ta ce " ina son ka fiye da tawa rayuwar " gyada mata kai ya yi a hankali kafin ya mike ya kontar da babyn saman gadon shi dan ya yi barci , sannan ya dago ya ce musu " yanzu na dawo " ya kai karshen ya na juyawa zai fita har ya kai bakin kofar mama ta ce mishi " tsaya don Allah ina son na yi magana da kai , auta yanzu na dawo " ta kai karshen ta na sakin Inaya ta mike ta bi bayan Malik su ka fita ita kuma Inaya ta koma ta konta sai da su ka yi dan nisa da dakin sannan su ka tsaya mama ta ce mishi " na sani Triplets ne ta haifa , ban ga laifin ka ba dan ka boye mata dan kar ta cutu , amma ina jin wani abu wanda ba zan iya fada maka ba " cikin rudu ya ce mata " ta ya a ka yi ku ka san uku ne bayan ni da doctor da nurse biyu ne kawai mu ka san triplets ta haifa , ko ita na yi mamakin yadda a ka yi ta san Triplets ne " " Muryar shi ta jiyo , haka ni ma na jiyo Muryar shi ta haka ne na gane su uku ne ta haifa , but zan so ka koma wajen doctor ka tambaye ta ina babyn ka ya ke in ba ta gan shi ba za ta iya samun sukuni ba , haka za ta yi ta jin Muryar shi " wani dogon nunfashi ya ja ya na saukewa a hankali kafin ya ce " ki yi hakuri mama , ba zan iya ba , na san in ta ji labarin shi ba za ta iya jurewa ba , shi ya sa na boye wannan maganar , ke ma ina rokon ki don Allah kar ki fada mata " " amma ya ka ke so ta yi Muryar shi da ta ke ji ? " " zan san yadda zan yi " ya na gama fadar haka bai jira amsar ta ba ya raba ta geffen ta ya wuce a hankali ta juya ta bi shi da kallo na dan lokaci kafin ta juya ta sauke wata yar karamar ajiyar zuciya sannan ta koma dakin Inaya ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ ( LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) STORY & WRITTEN BY : MEERAH ⚘🕊 【THE ROYALTY LOVE ❤🌹】 【 BOOK ________ 4 📚✍💌 】 _______________________♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡______________________ { P A G E ________ 17 & 18 ✍💕🔥} ▪AFTER TWO DAYS wani katon waje ne cike da chairs red color dukkan su , su na kallon wani hall a saman hall din akwai wata doguwar table shinfide da wani tissu white color , an jera drinks kala² a sama da Mic guda 11 a gaban kowace kujera , amma na gaban farar chair din nan ya fi kawatuwa , bayan table din akwai wasu chair guda biyar a geffen , biyar a geffen hagu sai wata babba fara kal ta alfarma a tsakiyar su wajen duk zagaye ya ke da Sojoji , kowane rike da gun ya daure fuska , ga wasu yan JARIDA zazzaune saman chairs din nan , sai wasu manyan cameras wajen hall din nan cen na hango Diya zaune saman kujerun da ke saman Hall , da Rafik , da General Abdallah , Idris da Hussein a geffen dama , a geffen Hagu ma akwai wasu biyar zaune saman chair din da allamun wadanan su kuma ministers ne wajen ya yi tsit ba ka jin komai su na a haka Malik ya shigo wajen ya na sanye da wasu suit Farare kal ma su mugun kyau , ya saka wasu sneakers farare kal a kafafun shi , ya daure wanan smooth hair din nashi a baya , ya na taku cike da Izza wasu sojoji guda uku na biye da bayan shi ya na shigowa wajen kowa ya mike tsaye , har su Diya , nan take kowa ya shiga yin tapi , dan duk mutanan wajen ba karamin dadi su ka ji ba ganin shi a haka har ya karaso saman hall din nan , ya nufi chair din Fara , da sauri wani soja da ke tsaye baya ya karaso zai janyo mishi chair a hankali Malik ya daga mishi hannu , ba musu ya koma ya tsaya hannu ya sa janyo chair ya zauna , sai da ya zauna sannan kowane ya koma ya zauna su na kallon shi cike da nitsuwa ya fara magana cikin wata zazzakar murya ya na fadin " Assalamualaikum wa rahmatullah wa barkatuhu , My name is Nawfel Hicham Bin Jaabar , na ji dadin ganin yadda ku ka hallaci wannan zaman , kafin mu fara abun da ya kawo mu , zan so mu bude taron nan da addu'a , mai girma Rafik , bismillah " ya fada ya na dan kallon Rafik ba musu Rafik ya mike tsaye ya fara jero musu addu'o'i su na amsa mishi da Ameen , sai da ya kammala sannan ya koma ya zauna saman chair din shi ya na zama Malik ya ce " Alhamdoulilah , na san kowa a wajen nan ya san matsayina a cikin kassar nan tamu mai albarka , na san kuma kowa ya san abun da ya faru last seven months da ba nan , bayan hawan Aymane Bin Abdoul Mujeeb kujerar Malik , da farko zan so na gabatar da sakon ta'aziyata ga ahalin da su ka rasa 'ya'yansu , ina me kara ba ku hakuri , in sha Allah wannan shi ne na karshe da izinin ubangiji , Tabbas ni na hakura na sauka da ga kujerar Malik , amma ba wanda ya yi tunanin Abun da Malik Aymane zai aikata , a lokacin da na samu labarin abun da ke faruwa a cikin masarautar na yanke shawarar dawowa dan na rushe wannan bakin mulkin nashi , kuma cikin yardar ubangiji na yi nassara , ga duk al'umar Saudiya da ke sauraro na a wannan lokacin , zan so ku sani , ni Malik Nawfel HICHAM bin JAABAR na dawo kan kujerata ta Malik , kuma in sha Allah zan ci gaba da kula da kassar Saudiya kamar yadda mahaifina Malik HICHAM BIN JAABAR ya kula da ita bisa gaskiya da kyakyawar zuciya , da ga yanzu duk wani mai laifi za a yanke mishi hukunci dai'dai abun da ya aikata bayan kwakwaran bincike , mai gaskiya kuma a ba shi gaskiyarshi , duk wasu makarantu da a ka rufe za a bude su , a ci gaba da bawa yaranmu karatun da ya dace , da ga Maza har zuwa Mata , I'm sorry ba ni da isashen lokacin sauraron tambayoyin ku , amma ministers za su amsa muku , ina yi wa kowa fatan al'heri , Allah ya mayar da kowa gidanshi na lafiya , Thanks a lot " ya na gama fadar haka ya mike , da sauri su ma yan JARIDA su ka mike su na kokarin su nufe shi amma sojoji sun tare su , a haka har Malik ya sa kafa ya fice wajen , ya na fitowa sai saman wasu dankareren motoci ma su nunfashi duk black , cike a wajen , na yi kokarin kirga motocin amma gaskiya na kassa sai ka ce companyn buga mota dan wajen cike ya ke da motoci ga kuma motocin sojoji kamar su ci kan su , ga kuma sojoji cike da harabar wajen 200 ma Albarka , kowane rike da gun Malik na fitowa duk sojojin wajen nan su ka tsaya cak waje guda , da sauri wani ya nufi wata dankareriar mota Fara kal dan duk cikin motocin nan fara guda tak na gani sai motocin yan JARIDA , a haka sojan nan ya sa hannu ya bude mishi gidan bayan motar hannu ya kai cikin aljihun wandon shi , ya fiddo wasu glass bakake ya saka a idanun shi , maimakon ya shiga motar nan da soja ya bude mishi kawai sai ya raba ta geffen ta ya wuce , ya ci gaba da tafiyar shi ya nufi hanyar fita wajen , duk inda ya wuce sai sojojin nan sun daga kafa su na sara mishi ko sannu bai ce musu ba , a hankali ya dago hannun ya cire button din Jacket din suit din , ya fida jacket din ya yadda a kassa ba tare da ya tsaya ba ya kai hannu ya fido kassan farar shirt din shi da ya soke cikin wandon shi , ya kai hannu cikin dayan aljihu ya fiddo wata bakar face mask , ya saka , ya sa kafa ya fice wajen shi kadai duk mutanan wajen sai da su ka yi mamaki baki sake , sun ma rasa abun da za su yi , su bi shi ko kuwa ? kawai dai sun tsaya su na bin shi da kallo har ya fice bangaran Malik kuwa kai tsaye hanyar Daular Saudiya ya nufa da kafa , duk inda ya wuce sai ya jiyo Muryoyin mutane su na ta yabon shi , dan taron da su ka yi yanzu on live ne kowa ya na kallo ba karamin dadi ya ke ji ba jin yadda mutane ke yabon shi , wasu na jefa mishi Albarka , wasu na jero mishi addu'a kai abun dai Masha Allah , ya amshi sunan shi na Malik dan kowa cikin garin Saudiya ya shaide shi ya na tsaka da tafiyar shi kawai ya karaso wajen wani plaza , cak ya tsaya ya na bin plaza din da kallo , ya na nan yadda ya bar shi bai sauya ba , lokacin guda ya saki wani cool murmushi ya na kallon plaza din dan a wannan wajen ne ya hadu da Diya for the first time a haka dai ya ci gaba da tafiyar shi hannayanshi na cikin aljihun wandon shi , har yi dan nisa kawai ya jiyo Muryoyin wasu samari da ga bayan shi su na fadin " ranka shi dade ! " su ka fada da karfi cak ko ya tsaya , kafin ya ci gaba da tafiyar shi ba tare da ya juyo ba ya na haka kawai ya ga wasu samari guda hudu a gaban shi kamar sun fado da ga sama sun tare mishi hanya daya da ga cikin su ya na ce " ku yi hakuri mun tsayar da ku , ni sunana Adel , tun mu na wancen layin ne mu ka hango ku , to na cewa abokai na mai martaba Malik ne , amma sun ki yarda , shi ne mu ka biyo ku dan mu tabbatar " a hankali Malik ya dago musu hannu ya nuna musu kunnenshi kafin ya yi musu kwatancen shi kurma ne kuma makaho , ba zai iya magana ba " wayo , ba ka gani kuma ka ke tafiya kai daya ? ina dan jagoran ka ? dama dama yanzu akwai security a masarautar da tuni an yi gaba da kai " daya da ga cikin su ya fada a hankali ya girgiza musu kai allamun ba shi da Adel ne ya kalli abokanshi ya ce " kun ga , bari mu raka shi ni da Hadi , kun ga zirga²r da a ke a masarautar nan ya dawo kamar da farko , kar a je mota ta buge shi , ku/ku koma shop , ba za mu jima " ba musu biyun su ka raba ta geffen Malik su ka koma inda su ka fito su na barin wajen wanda ya yi magana da farko ya riko hannun Malik ya na fadin " mu tafi " ba musu Malik ya bi shi su ka tafi tare da wanda ya kira Hadi sai sun karaso wajen da a dakwai kwana sai su tsaya su tambayi Malik wace kwana za su yi , sai ya girgiza musu kai ya na nuna musu gaban su allamun su ci gaba ba musu su ke yin hanyar , a haka har su ka karaso bakin kofar Daular Saudiya , ba tare da sun kawo komai a ransu ba sai da su ka zo dab da kofar shigar sannan Malik ya kwace hannunshi ya na fadin " okay , na gode sosai da rakiya , rike wannan " ya fada ya na cire face mask din shi ya daura saman hannun hadi sannan ya cire glass din shi ya daura saman hannun dayan ya na fadin " na gode , amma na san hanya , zan ci gaba da ga nan , see you next time " ya kai karshen ya na shiga Daular ya bar su nan sun yi sumar tsaye sai da ya shiga sannan ya su ka juyo su ka kalli junan su baki sake su na zaro idanu , wata yar karamar kara su ka saki da dariya a tare kafin Adel ya ce " sai da na ce muku Malik ne amma ba ku yarda ba " wani dan karamin murmushin geffen fuska Malik ya saki dan ya jiyo abun da ya ce , da ga haka ya ci gaba da tafiyar shi har ya iso part din MALIKAT HOUDA bakin shi da sallama ya shigo parlourn MALIKAT HOUDA , nan ya tardo ta zaune tare da MALIKAT AL'UMU da mama da Nesrine , MALIKAT AL'UMU na rike da Nailah , MALIKAT HOUDA kuma ta na rike da Junior ( 🤣🤣🤣✌ gaskiya sai dai mu kira shi da Junior dan ni mutum guda na bawa wannan sunnan wato MALIK NAWFEL HICHAM BIN JAABAR , MY NUMBER ONE 🤣✌ ) MALIKAT INAS kuma ta na rike da Nayel bai ce musu komai ba ya nufi corridor ya shige , kai tsaye bedroom din da Inaya ke ciki ya nufa dan dama ita ya zo nema ya na shiga ya gan ta konce tsakiyar gado , ta dunkule waje guda , idanunta na bude da sauri ya nufi gadon dan a nashi tunanin wani abu ya same ta , ya na isa ya zauna a baki ya na fadin " my Cutie , me ya faru ? ciwo ki ke ? " a hankali ta dawo da kallon ta gare shi , ta saki wani dan karamin murmushi ta ce " yanzu fa na tashi da ga barci , ko one minute ba a yi ba da na bude ido " a hankali ya sauke ajiyar zuciya kafin ya ce " to me ya faru ? ko wani abu ki ke so ? fada min zan je na kawo miki " girgiza mishi kai ta yi ta na fadin " yaya Zayd ba na bukatar komai a yanzu , kawai ina son na huta , jikina duk a mace ya ke " a hankali ya sunkuyar da kai ya manna mata kiss saman forehead ya na fadin " okay my Cutie , konta ki huta , dama na zo na fada miki ran Friday za mu tafi Makkah , da ga nan mu koma gidanmu na US " wani dan karamin murmushi ta saki murya a sanyaye ta ce " da gaske yaya Zayd , za mu tafi Makkah ? " gyada mata kai ya yi a hankali ya na cewa " har Madina sai mun biya , da ga nan mu tafi Dubaï mu yi shopping sannan mu komawar US " har ta saki wani dan murmushi sai ta marairaice fuska ta na fadin " baby , please tell me , baby nawa na haifa ? don Allah ka fada min , wlh hankalina duk ya ki konciya , da na lumshe idanu sai na dinga jiyo Muryar shi " wata yar karamar ajiyar zuciya ya sauke , a sanyaye ya ce mata " Cutie , me ki ke so na ce miki yanzu ? " a hankali ta mike zaune , ta jingina bayanta a jikin forehead din gadon , ta riko hannunshi ta na fadin " ka fada min gaskiya mana , zan fi jin dadin ka fada min gaskiya ko me zai faru hakan zai sa na ji sanyi a zuciya ta , ko dai babyn bai zo da rai ba ? " ta fada ta na dan marairaice fuska sai da ya dauki lokaci kafin ya ce mata " i'm sorry my Cutie , na yi tunanin in na boye miki hakan ba za ki ji zafin rashin ba , amma gaskiya ne Triplets mu ka samu , sai dai namijin na biyu bai zo da rai ba , I'm sorry " wata nanauyar ajiyar zuciya ta sauke kafin ta lumshe idanunta , ta fara zubar da hawaye da sauri ya fara goge hawayen ya na fadin " kin gani ko , shi ya sa na ki fada miki , ga shi yanzu ki na kuka " a hankali ta girgiza mishi kai ta na fadin " ba komai baby , Allah zai ba mu wani , ko ba komai yanzu zan daina wannan tunanin , amma please ina son na ga Nayab , ina so na ga in ya na kama da Nayel din mu " ta kai karshen ta na ware idanunta a sanyaye girgiza mata kai ya yi a hankali kafin ya ce " i'm sorry my Cutie , amma tun ranar a ka yi jana'izar shi , bayan ni da doctor da nurse biyu sai mama ba wanda ya san wannan maganar , ko je dan kin matsa ne na fada miki , ki yi hakuri don Allah " a hankali ta sakin mishi kuka ta na fadin " yanzu ka hana ni ganin babyna , why za ka yi haka , da ka bar ni na gan shi mana " " i'm sorry my Cutie , wlh ban yi hakan dan na cutar da ke , please ki daina kukan nan wlh b....... " bai kai karshen maganar shi ba kawai ya ga ta koma Aswad lokaci guda ta na daga mishi da karfi ta ce " ka daina ce min na yi shiru , babyna ne ba nata ba , why za ka ce a yi jana'izar shi ba tare da na gan shi ba " ta fada har wani sama gashin ta ya yi kamar a na hura shi da iska ba karamar razana Malik ya yi ba , har sai da ya mike tsaye ya na karanto kalmar shahada wasu yawu ma su daci ya hadiye kafin ya ce " please my Cutie, calm down , please , i'm sorry " ya na gama fadar haka kawai ya ga ta saki kuka , wasu bakaken hawaye na zubo mata , ta na fadin " ka kawo min babyna na gan shi , ka kawo min shi na gani " ta fada a sanyaye kafin ta lumshe idanunta a hankali , nan take jelar gashinta ta zubo saman shoulder din ta wata nanauyar ajiyar zuciya ta sauke kafin ta ware idanunta a hankali shi ma nanauyar ajiyar zuciya ya sauke ganin idanunta sun dawo dai'dai a hankali ya zube saman guyiwowinshi ya riko kunnuwan shi , ya na fadin " i'm so sorry my Cutie , just na yi tunanin in na boye miki hakan ba za ki ji zafin mutuwar Nayab ba , ban yi tunanin hakan zai cutar da ke ba , i'm sorry , please forgive me , please " ( in na gane wani abu 🤔🤔🤔 Nayel shi ya dauko Abyad , Nayab kuma ya dauko Aswad , yanzu da babu Nayab Aswad za ta koma jikin Nailah1 ko kuwa ? ) wani dan karamin murmushi ta sakin mishi kafin ta mika mishi hannu a hankali ya mike tsaye ya riko hannunta , ya zauna bakin gadon " babu komai , na gode baby , na san duk abun da ka yi ka yi shi because you love me , kuma ba ka son abun da zai cutar da ni , ko ba komai na so na ga Nayab , amma tunda kai ka gan shi , ni ma kamar na gan shi ne , so it's okay now " ta kai karshen ta na sakin mishi wani dan karamin murmushi murmushi shi ma ya sakin mata kafin ya kai hannu ya fara goge mata bakaken hawayen Aswad ya na fadin " kin sani , ya na kama sosai da Prince , kamar an tsaga kara , ba abun da ya baban ta su " murmushi kawai ta yi mishi kafin ta koma ta konta ta na fadin " ni yanzu barci na ke ji baby , kuma in na tashi ina son ka shirya min diner da kanka " " duk abun da ki ke so sarauniyata " a hankali ta lumshe idanunta ta na sakin murmushi , ta na a haka ta ji saukar lips din shi saman kumatunta ya manna mata kiss sannan ya mike ya na fadin zai dawo zuwa anjima gyada mishi kai kawai ta yi ba tare da ta ce komai ba da ga haka ya sa kai ya baro bedroom din har zai fita parlourn MALIKAT HOUDA ta yi saurin ce mishi " da ka tafi da ita ma zai fi , ka zo ka wuce mutane ko sannu babu " slowly ya juyo ya kalle ta ya ce " ke dai tsohuwar nan kin shiga rayuwata wlh , sai na yi maganin ki nan gama , kar ki damu ki na gani zan zo na dauke ta na tafi da ita ai dama tawa ce ba taki ba , ci gaba da shiga harkata sai na rataye ki , tsohuwa kawai " ya kai karshen ya na juyawa ya fice abun shi baki sake MALIKAT HOUDA ke kallon shi , har sai da ya fita sannan ta dawo da kallonta kan MALIKAT AL'UMU da ke rike da jikanta ta ce " kin dai ji abun da yaron ki ya ce ko ? kuma ba ki ce mishi komai ba ? wata yar karamar dariya MALIKAT AL'UMU ta yi ta na fadin " to mamie ya zan yi ? na isa na shiga tsakanin mata da mijinta , um um ku yi dramar ku cen nawa ni dai kallo kawai " a tare duk mutanan wajen su ka yi dariya har ita MALIKAT HOUDA , ba karya tun lokacin da Malik ke karami ya saba sosai da MALIKAT HOUDA , dan bayan ita babu wanda ya ke yi wa wassan kaka da jika , ita ma bayan shi ba wanda ta ke yi wa irin wannan wassan , jinin su ne ya hadu tamkar ita ce kakar shi ta gaskiya bayan ba shi da hadi da ita ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ ( LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) STORY & WRITTEN BY : MEERAH ⚘🕊 【THE ROYALTY LOVE ❤🌹】 【 BOOK ________ 4📚✍❤ 】 _______________________🕊✍🕊✍🕊✍🕊✍🕊✍🕊✍🕊______________________ { P A G E ________ 19 & 20 ✍💕🔥} Bari na dan takaice labarin , a ranar Friday a ka yi duk wasu shirye shiryen dan sake nada Malik , amma wani abun mamaki kawai sai ya ce shi bai dawo dan ya zauna saman kujerar nan ba , kawai ya dawo ne dan ya kwace ta da ga hannun Aymane kuma ya yi nassara , yanzu kuma zai nada wanda ya cancenta sa wannan kujerar bayan shi , da ga haka ya nada Diya da kanshi a matsayin Malik , kuma babu wanda ya yi mishi ja , har ya kammala , sannan ya nada Abdoul a matsayin na hannun daman Diya , nan ma babu wanda ya yi mishi ja a haka har a ka kammala taron , kowa ya koma part din shi a misalin karfe takwas na dare duk ahalin Malik su na cikin parlourn shi na part din shi a floor na uku dan har yanzu bai bude floor na hudu ba a haka ya sanar da su zai koma US dan dama ziyara ce ya kawo musu yanzu lokacin komawarshi ya yi RIANNA ta sha kuka ta rokon shi ya zauna amma fir ya rufe ido ya ce ta yi hakuri shi dai sai ya tafi babu yadda su ka iya haka su ka yi mishi bankwana su na yi mishi addu'a Allah ya tsare shi tare da Familyn shi , su na fadin sun yi kewar shi sosai , ya ce duk ranar Friday su dinga zuwa a nan parlourn a karfe takwas su yi video call ya ga in kowa ya na cikin koshin lafiya da ga haka har karfe goma sha biyu na dare ya yi kowane ya koma part din shi bayan sallar asuba misalin karfe 5 , su ka raka Malik da Inaya da Twins din ta har airport , su na yi musu bankwana , da ga nan su ka shiga jet din su ya daga ya nufi US THE END ............ 🤣🤣🤣🤣🤣🤣✌✌✌✌✌✌ WASSA NA KE ▪AFTER FOUR YEARS ▪UNITED STATE OF AMERICA ( WASHINGTON DC ) wani kyakyawan yaro ne ya sauko stair , Fari kal da shi kamar ka taba jini ya fito , ya na da kananan idanu Hazel , ga dan karamin hancin shi a tsaye , da bakinshi , lips din shi red color shape din na sama kamar heart , ya na da smooth hair ya zubo mishi bayan keya , sai wasu kananan da su ka zubo mishi a gaban goshi har zuwa wajen eyebrow , ga tambarin masarautar Saudiya a wuyanshi ya na sanye da wandon Jeans white color , da T-shirt blue color , ya daura wata jacket a sama White color , kafafun shi na cikin wasu sneakers Navy blue , da gani renon madara da ice cream da gudu ya ke sauko stair din ya na wata yar karamar dariya kai tsaye parlourn gidan ya nufa nan ya tardo Malik zaune saman sofa ya na faman latsa laptop din gaban shi , ya na sanye da wandon jeans Blue da polo white color , ya na nan dai bai sauya ba , sai dai har yanzu bai tara gemu ba , smooth hair din nan nashi ya kara tsawo duk da ya na rage shi , ya bazun mishi a baya , ya na aikin shi cikin konciyar hankali a haka dan yaron nan ya nufe shi , ya Haye sofar ya na fadin " Daddy , tashi mu tafi , ice cream na ke so " ya fada cike da shagwaba ba tare da ya kalle shi ba Malik ya ce " Prince , ba ka ga aiki na ke yanzu ba , ka bari har zuwa yamma sai mu tafi , ka tafi ka yi barci please , Princess na cen na hutawarta kai ka na nan " noke mishi kafada Prince ya yi kafin ya haye saman bayan shi , ya na tura shi wai ya sauka su tafi , ya na fadin " No , No , No , ni yanzu na ke son ice cream , kuma yanzu za mu tafi , ka tashi mu tafiiiiiii " wani dan nunfashi Malik ya sauke kafin ya sa hannu guda ya sauko shi da ga saman bayan shi ya na fadin " please my Prince , ka bari at least na gama aiki na , sai mu tafi " ai ko ya na gama fadar haka Prince ya Zube a kassa ya na sakin kukan shagwaba , ya na harba kafafu har sai da sneakers din shi su ka fice , ya na fadin " Ni ice cream na ke so , mu tafi mu sayo ice cream " har da wasu hawayen iskanci ya ke kamar da gaske sarai Malik ke jin shi amma ya share shi , dan ya saba da rigimar Prince , da ya tashi dauko momyn shi sai da ya wuce , gwara ya share shi , dan in ya ce zai biye mishi yanzu zai yi frog jump , ya san ba karamin aikin Prince ba ne ya ce sai ya yi frog jump sannan zai hakura da ice cream din , dama dama Princess ita ta dauko miskilancinsa , shiru da ita in har ba tabo ta ka yi ba , sai ka rantse ba ta cikin wajen akwai wata rana da su ka taba fita da PRINCE su ka manta da ita cikin bedroom din ta , amma a haka su ka je su ka dawo ta na cikin bedroom din ta , ta na konce ta na barci ya na a haka kawai ya ga Prince ya sa hannu ya ture laptop din shi har sai da ta fadi kassa ba tare da ya bar kukan shagwabar shi ba cak Malik ya tsaya ya na zaro idanu , kamar ya tashi ya yi kuka shi ma ya ke ji dan jarabar Prince wani dan karamin kukan kura ya yi kafin ya tashi a zafafe , ya dauki Prince ya juya ya na kallon kofar Kitchen ya na fadin " Cutie ! Cutie ! Cutie ! " ya ke kwalla mata kira da karfi cikin nitsuwa na ga Inaya ta fito da ga kitchen din Masha Allah , Gaskiya ba karamin kyau ta kara ba ta cika ta yi bul bul abunta , da ga gani ta samu hutu , har wani haske ta yi kumatu sun fito , gaskiya US ta zauna mata ta na sanye da wando palazzo pink colour , da wata t-shirt blue , amma da ga gani ta Malik ce dan ta so ta yi mata yawa a haka har ta karaso cikin parlourn , a sanyaye ta ke fadin " baby , lafiya ka ke min irin wannan kiran ? " mika mata Prince ya yi ya na fadin " rike yaron ki ! " cikin rudu Inaya ta kai hannu ta karbi Prince da ke ta faman turo dan bakin nan nashi irin nata ta na karbar shi ta juya ya dauki laptop din shi da ta fadi , da wayoyin shi , sannan ya juyo ya kalle ta ya ce " na bar muku gidan , na san sai kun kashe ni za ku huta , da ke da yaron ki ku na neman ku saka min hawan jini wlh , da daddare ban huta ba , da safe ban huta ba , gwara na tafi tun kafin ku kashe ni " ya na gama fadar haka ya juya ya nufi kofar fita parlourn ya fice wata yar karamar dariya Inaya ta yi dan ta san yaron nata ya tsula tsiyar tashi , sai da ya fita sannan ta dawo da kallon ta saman shi ta na fadin " me kuma ka yi wa Daddyn naka ? " cike da shagwaba Prince ya ce mata " Cutie , ni fa kawai na ce mishi ina son ice cream ne , shi ne ya yi fushi ya tafi , ni ke ce mishi ya dawo , na bar ice cream din , ina son zama tare da Daddyna " ya kai karshen ya na sakin kukan gaske wannan karan ita dai ta tsaya ta zuba mishi ido ya na hawaye bibiyu , kamar ba shi ya tukarawa baban nashi ba har ya tafi , yanzu kuma ya na kuka dan ya tafi , ta tafi duniyar tunanin ta kawai ta jiyo Muryar Malik ya na fadin " wa kuma ya taba min babyna ? " a tare ita da Prince su ka juya su ka kalli saitin kofar parlourn ya na tsaye ya na sakin wani dan karamin murmushi , dama ba tafiya ya yi ba , laptop din shi ne ya kai cikin motar ya runo ashe ya manta file din shi , shi ne ya dawo zai dauka , ya jiyo Prince na kuka da sauri Prince ya diro da ga jikin Inaya ya nufi Malik ya na sa isa ko Malik ya sa hannayan shi biyu ya dauke shi , cikin sanyin murya ya ce " I'm sorry my Prince , bari mun tafi sayan ice cream din , now stop crying please , kai ma ka san ba na son ganin kukan ka " wani dan karamin murmushi Prince ya saki kafin ya kai hannu ya fara goge hawayen shi , ya kontar da kan shi saman shoulder din Malik , ya lumshe idanunshi , da alamun barci ya ke ji , Inaya na ganin ya lumshe idanunshi ta san to na barcin ne su ka sauko mishi , " baby , ina ga barci ya ke ji , ka kai shi bedroom din shi yanzu ina zuwa " ta fada ta na juyawa ta koma kitchen ba musu ya nufi stair ya Haye , kai tsaye bedroom din Prince ya shiga bedroom din ta hadu gaskiya , komai na cikin ta blue ne , har gadon , da carpet , ga ta ko cike da kayan wassa , har da su play station , dan wani lokaci tare su ke game din su shi da Malik kai tsaye saman gadon shi Malik ya kontar da shi , sannan ya zame jacket din shi , ya ajiye gefe , ya sauko ya manna mishi kiss saman forehead , kassa kassa ya ce " i love you my baby " cikin magagin barcin nashi ya ce " i love you too my Daddy " wani cool murmushi Malik ya saki kafin ya sake ce mishi " konta ka huta , in ka tashi sai mu tafi sayan ice cream , mu biya park , okay ? " wani dan karamin murmushi Prince ya saki kafin ya gyada mishi kai , ya juya mishi baya ya kai hannu ya janyo Teddy din shi , ya rungume janyo duvet Malik ya yi ya rufe shi har zuwa kirji , sannan ya sauko da ga saman gadon , ya kashe lamps din dakin , Sannan ya fito ya na fitowa ya ci karo da Inaya taa shirin shiga dakin da sauri ya sa hannu ya toshe mata baki ya yi baya da ita , su ka shiga nasu bedroom din , sannan ya meda kofar ya rufe ya sa mata security cikin rudu ta ce mishi " lafiya ka min irin wannan janyowar ? " a hankali ya tako ya tsaya gaban ta , sai dai ya kare mata kallo da kyau sannan ya kai hannu ya ja mata hanci ya na fadin " dubi don Allah yanzu kin bata min yaro da wannan rigimar taki " hmmm , kamar dama jira ta ke kawai sai ta sakin mishi kukan shagwaba har da bubuga kafafu a kassa bai ce mata komai ba kawai ya sa hannu ya yi sama da rigar ta ya fidda mata ita , ya hade bakin su waje guda ya fara kissing din ta ai ba shiri ta yi tsit , ta na karbar sakon shi , nan take ita ma ta shiga mayar mishi da martani , ta zagayo da hannayanta a wuyan shi a hankali ya yi baya da ita , su ka fado saman bed din su , ya sa hannu ya fara raba ta da kayan jikin ta , har sai da ya meda ta naked , sannan ya zabe bakin shi da ga cikin nata bai dire shi ko ina ba sai saman nipple din ta , nan take kawai ya gama fita hayacin shi , specially yadda ya ke jin hannun ta saman kanshi duk ta gama birkice mishi lissafi Ita kanta tuni tuni ta tafi , dan dama a kusa ta ke , ta yi tunanin janyowar nan da ya yi mata dan su buga game ne , wai sai ta ga ya ja mata hanci shi ya sa ta sakin mishi kukan shagwaba 😴😴😴 NI KAM BARI NA JUYA HAR KU GAMA NA DAWO , DAN ABUN YA FARA FIN KARFINA ▪AFTER SOME HOURS 💫 Misalin karfe 5 na yamma , a tare duk su ka shirya su ka tafi park , dan Malik ya san in ba su tafi ba tom Prince ba zai kyale shi ba , ita dai Princess cewa ta yi ba za ta je ba , ta zauna tare da maid din su , ba irin rokon da Malik bai yi mata ba su tafi , da ga karshe ta sakin mishi kuka, ba dan ya so ba ya hakura ya kyale ta a haka su ka nufi park din Malik ke yawan kai Su , ba kowane ne ba sai park din da ya hadu da Aylan , kullum a zuciyar shi ya na tunanin zai sake ganin shi , amma tsawan shekara hudu yanzu kullum ya zo ba ya ganin shi har ya cire rai ma , bayan ya yi parking din motar su , su ka fito su ka shiga park din , shi dai prince tun da su ka shigo baki ya ki rufuwa , sai dariya ya ke , ita kuma Inaya ta biye mishi , da allamun na yarintar sun dawo mata shi dai Malik kallon su kawai ya ke ya na murmushi su na a haka kawai ya ga Prince ya kwassa da gudu ya nufi wajen wani me sayar da halawar auduga da sauri Inaya ta bi bayan shi ta na fadin " Prince , yi a hankali don Allah kar ka bace mana " bin bayan su Malik ya yi ya na kiran sunan Prince shi dai Prince ko jin su ba ya yi dan halawar ta yi mugun shiga ranshi , sai da ya iso sannan ya tsaya ya na fadin " Uncle , ina son halwar nan " ya kai karshen ya na nuna mishi mai pink color ya na gama fadar haka ya ji Nihal ta riko hannunshi ta na fadin " Prince , next time in ka na son abu ka fada min ba tserewa za ka yi ba , a ka je ka bace fa ? " cikin yar shagwaba ya ce " i'm Sorry Cutie , please saya min halawa " ya na gama fadar haka Malik ya iso wajen ya na fadin " Prince , why za ka tsere ? dubi yadda ka gajiyar da momyn ka " wani dan karamin kukan shagwaba Prince ya yi mishi ya na fadin " ni halawa na ke so , pleaseeee " ya kai karshen ya na dan marairaice fuska ya na rufe bakin shi Malik ya ji wayar shi ta fara ringing , hannu ya kai cikin aljihu , ya fiddo ta , sannan ya kai hannu cikin gudan aljihun ya fiddo bandir din dollars , ya mikawa Inaya ya na fadin " kar ku bar wajen nan , yanzu na dawo " da to kawai ta amsa mishi kafin ta kai hannu ta karbi kudin shi kuma ya juya , kai a sunkuye ya fara takawa ya nufi hanyar fita park din ya na latsa wayar shi ya yi nisa kadan , kawai ya ji ya bugi mutun da karfi , har sai da ya saki wayar shi , ya yi gaba kamar ya yi tuntunbe sai dai bai fadi ba wata yar karamar ajiyar zuciya ya sauke kafin ya duka ya dauki wayar shi , kawai ya ga screen din ya tarwatse baki daya , ta mutu wani dan karamin tsaki ya ja , kafin ya juyo ya na fadin " I'm sorry na....... " ai maganar da bai kai karshen ta ba kenan ya dan zaro idanu ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ ( LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) STORY & WRITTEN BY : MEERAH ⚘🕊 【THE ROYALTY LOVE ❤🌹】 【 BOOK ________ 4📚✍❤ 】 _______________________🕊✍🕊✍🕊✍🕊✍🕊✍🕊✍🕊______________________ { P A G E ________ 21 & 22 ✍💕🔥} wani dan karamin Murmushi Aylan ya sakin mishi kafin ya ce " kai ma an koya maka tafiya ka na latsa waya ? " ya kai karshen ya na dukawa ya dauki tashi wayar shi ma wata nanauyar ajiyar zuciya Malik ya sauke kafin ya ce " General , sai yau Allah ya sake hada ni da kai " " Kennan nema na ka shiga yi " Aylan ya fada ya na meda wayar shi cikin aljihun shi , ya juyo da kyau su na fuskantar juna wani dan murmushi Malik ya yi kafin ya ce " Eh , dole na nema ka " cikin nitsuwa Aylan ya katse shi da cewa " Why ?" " akwai tambayar da ta tsaya min a rai tsawan shekaru , kuma na san kai kadai za ka iya ba ni amsar ta , amma sai yau Allah ya sake hada ni da kai " wani murmushi mai dan sauti Aylan ya yi kafin ya nade hannayanshi a kirji, ya daga mishi gera guda ya na fadin " me ya sa ban fada maka a na neman ka a Saudiya ba ko ? " dan zaro idanu Malik ya yi ya na kallon shi , ta ya a ka yi ya san tambayar da zai yi mishi kenan ya yi nisa duniyar tunanin shi ya jiyo Muryar Aylan ya na fadin " maganar ta na da tsawo " da sauri Malik ya katse shi da cewa " please tell me " " shikenan tun da ka matsa , it's true na san da a na neman ka , kuma har da ni cikin neman ka , har kyauta na bayar ga duk wanda ya samo ka , lokacin da na ji labarin halin da familyn ka ke ciki na yi kokari wajen ganin na taimaka musu saboda General Abdellah abokin mahaifina ne , na so na tura jami'an tsaro na Saudiya dan sauke Malik da ga kujerar , sai da ga baya General ke kwatanta min in na yi haka kamar na haddasa yaki ne tsakanin Saudiya da US , nemo ka ne kadai solution din mu , that's why ma na bayar da kyautar ga wanda zai samo ka dan ka koma Saudiya in da a ka fi bukatar ka , a ranar da mu ka hadu na ga damuwa sosai a tattare da kai , ga kuma halin da familyn ka ke ciki , ba zan so na kara maka wata damuwar ba , that's why na yanke shawarar yin shiru , na fara tambayar ka abun da ke damun ka , na ga in zan iya taimaka maka , na san indan ka samu nitsuwa kai da kanka za ka nemi sanin halin da familyn ka ke ciki " wata nanauyar ajiyar zuciya Malik ya sauke , sai da ya dauki lokaci kafin ya ce " na gode , i don't know how zan yi maka godiya " cikin nitsuwa Aylan ya katse shi da cewa " please , ba sai ka yi min godiya .... " " no , in ban yi maka godiya ba na san sai Allah ya kama ni , ko ba komai kai ka kawo nitsuwa cikin rayuwa ta " ya kai karshen ya na rungume Aylan ba shiri wani dan karamin murmushi Aylan ya yi kafin ya rungume shi shi ma , ya na dan bubuga bayan shi a hankali sun dauki lokaci a haka kafin su raba jiki da murmushi a face din shi Malik ya ce " please , mu je na gabatar maka da familyna " " ka ce ba kai kadai ba ka zo wannan karan ? " wata yar karamar dariya Malik ya yi ya na gyada mishi kai ya ce " yeah , ni da Cutie da Prince , my son " gyada mishi kai Aylan ya yi kafin ya ce " okay , ina jiran ku " gyada mishi kai shi ma Malik ya yi kafin ya juya da sauri ya koma wajen da ya baro su Inaya ya janyo su su ka dawo wajen da su ka bar Aylan sai dai ya na dawo ya neme shi sama da kassa ya rasa , ya kalli hagu , ya kalli dama babu Aylan babu mai kama da shi wani dan murmushi Malik ya saki kafin ya cewa Inaya " ina ya tafiyar shi , mu tafi kawai " da to kawai ta amsa mishi , shi dama PRINCE bai san abun da ke faruwa ba ya na ta shan halawar shi , sai wajajen Magriba sannan su ka baro park din , shi ma sai da su ka biya pastery su ka sayo cake da ice cream sannan su ka koma gida ko da su ka koma , Malik ya yi sauri ya yi wanka ya yi alwala ya fice ya tafi mosque Inaya kuma ta ja Prince ta yi mishi wanka , kafin Malik ya fito ita ma ta shirya shi dan kullum tare su ke tafiya mosque haka su ka tafi su ka bar ta ita kadai cikin gidan , ita ma wanka ta yi ta yi alwala sannan ta fito ta gabatar da sallar ta , sai bayan sallar isha Malik da Prince su ka dawo cikin gidan ▪WASHE GARI ⛅⛅ ▪PRINCE 👑❤ a hankali ya ke sauko stair , ya na tsalle , ya na sanye da wani Trouser black color , da wata sweater Red color , da sneakers farare a kafafun shi , duk in ya yi tsalle sai gashin kan shi ya yi sama ya na gama sauko stair din Malik ya shigo parlourn ya na sallama Prince na ganin shi ya nufe shi da gudu ya na fadin " Daddy , tun dazu fa na ke jiran ka , har na yi fushi " ya fada cike da shagwaba a hankali Malik ya sa hannu ya dauke shi ya na fadin " I'm sorry my Prince , tell me kun gama shiryawa mu tafi ? " da sauri Prince ya ce " yeah , kai kadai mu ke jira , na matsu na ga Ammie , da mamie , da mama , da Uncle " ya fada cike da shagwaba ( hmmm , ko da ga ina ya dauko wannan shagwabar ? 🤔🤔 ) " okay , where is your mom ? " Malik ya fada " wait " Prince ya fada kafin ya juya ya kalli Stair ya ce " Momyyyyyyyyy ! " ya fada da mugun karfi sai da Malik ya lumshe idanunshi ya na fadin " Prince slowly mana , ka fasa min kunne " ya na gama fadar haka Inaya ta fara sauko stair ta na sanye da wata Abaya fara kal mai mugun kyau an yi mata zanen flower kamar rainbow , ta yafa veil din ta fari shi ma , ta na sanye da wasu sneakers pink color a kafa , ta na rataye da wata yar bag pink color ita ma ta na rike da hannun Princess , gaskiya babyn ta hadu kamar na sace ta na gudu , fara kal da ita har ma ta so ta fi Prince haske , sak balarabiya , ta na kama da Malik kamar an tsaga kara , har idanunsa Hazel , kamar dai Prince ta na sanye da wata gown pink color har kassa , sai wata yar jacket white color , mai mugun kyau , fuskarta a daure kamar dai ta Malik a baya , sai ka ce ba ta iya dariya ba tun da ta fara sauko stair Malik ya tsare ta da ido babu ko kiftawa , sai magana prince ke yi mishi amma ba ya jin shi a hankali Prince ya kai hannu saitin fuskar Malik ya kyasta mishi yatsu ya na fadin " Daddy , tun dazu ina maka magana ka kyale ni , sai kallon momy ka ke kamar ba ka san ta ba " a hankali Malik ya sauke ajiyar zuciya dai'dai lokacin da Inaya ta karaso gaban shi ta na fadin " mu tafi ko ? " gyada mata kai Malik ya yi a hankali ya na murmushi kafin ya riko hannun Inaya , ya juya su ka fita parlourn , su ka fito harabar gidan , su na fitowa sai saman motar Malik , kai tsaye ya budewa Inaya wajen mai zaman banza , ta shiga sannan ya daura Princess saman kafafunta , ya rufe motar ya zagayo ya bude wajen driver ya shiga tare da Prince ya zaunar da shi saman cinyoyinshi ya yi tukin a haka har su ka bar gidan su ka nufi hanyar Airport ❤⚘ E X I L E D P R I N C E ⚘❤ 🔥👑 ( LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 🕊💕 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) 💕🕊 STORY & WRITTEN BY : MEERAH ⚘🕊 【THE ROYALTY LOVE ❤🌹】 【 BOOK ________ 4 📚✍💌 】 _______________________🕊✍💕🕊✍💕🕊✍💕🕊✍💕______________________ { P A G E ________ 23 & 24 ✍💕🕊} 【 THE LAST PAGE 🤧❤🕊 】 ▪DAULAR SAUDIYA 👑🔥 zaune MALIKAT AL'UMU ta ke cikin parlourn tare da MALIKAT INAS sai murmushi su ke saki su na a haka RIANNA ta shigo ta na sallama ta na fadin " Ammie , momy mu tafi sauran ten minutes jirgin su ya sauka " ba ta jira amsar su ba ta juya ta fice da sauri ta na sakin murmushi a tare MALIKAT INAS da MALIKAT AL'UMU su ka fito part din , su na fitowa sai saman wasu motoci a jere bakin part din , a tare su ka shiga motar da ke gaban su , su na shiga motocin su ka tada su ka bar masarautar da mugun gudu su ka nufi airport a jere motocin su ka shiga airport , kai tsaye wajen saukar jirgi su ka nufa , sannan su ka yi parking , daya bayan daya su ka fara sauko motocin , Diya da Nesrine su ka fito da ga cikin motar su tare da Junior din su RIANNA kuma ta fito da ga cikin motarta tare da mama da MALIKAT HOUDA MALIKAT AL'UMU da MALIKAT INAS kuma cikin mota guda sannan Abdoul da Tesnim su ka fito cikin mota guda tare da wata kyakyawar yarinya a shekaru ba za ta wuce 3 or 4 years ba , kyakyawa ce gaskiya kamar an tsaga kara da Abdoul dan ta na kama tak da shi , sai dai ta dauko farin Tesnim dan kamar ka taba jini ya fito ta ke har wani ja ta yi ta na ganin MALIKAT AL'UMU ta nufe ta da gudu wani cool murmushi MALIKAT AL'UMU ta saki kafin ta durkusa ta dauki yarinyar nan , a hankali duk su ka karaso wajen motar su MALIKAT AL'UMU su ka tsaya da sauri MALIKAT HOUDA ta ce " wai har yanzu ba su iso ba ? " wata yar karamar dariya duk mutanan wajen su ka yi kafin Diya ya ce " mamie , mu ma duk mun matsu mu gan su " har ta bude baki za ta yi magana su ka jiyo karar jirgi a tare su ka kai kallon su wajen da su ka jiyo sautin su na fadin Alhamdoulilah cikin zuciyoyinsu a hankali jirgin nan ya sauka , ya tsaya ya na fuskantar motocin su sai da ya yi two minutes a haka kafin kofar jirgin ta bude a hankali a tare Malik da Inaya su ka fito da ga cikin jirgin Malik ya na dauke da Prince duk jikin shi ya yi sanyi allamun barci ya ke a tare duk su ka nufe su su na yi musu barka da zuwa , da sauri MALIKAT INAS ta kai hannu ta karbe shi nan ta ga ashe barci ya ke , amma duk da haka sai da ta karbe shi , MALIKAT AL'UMU kuma ta karbi Princess hannu Inaya da ga haka su ka shiga rungumar juna , specially Diya , da ya rike Malik sai da RIANNA ta shiga ce mishi ya sake mata dan uwa ita ma ta rungume shi , ita dai Inaya tun da ta rungume mama ba ta sake ta ba har kowa ya hakura ya bar ta dan sun San yadda kewar uwa ta ke da ga su ka shiga motocinsu su ka bar airport din su ka kama hanyar Daular Saudiya ko da su ka isa kai tsaye Diya ya wuce da Malik building din shi tare da Abdoul MALIKAT INAS kuma ta tafi part din su da Prince tare da MALIKAT AL'UMU da RIANNA da Tesnim Inaya kuma ta bi mama tare da Nesrine su ka nufi part din MALIKAT HOUDA tare da Junior ▪MALIK tsaye ya ke a cikin parlourn part din shi a floor na uku sai bin wajen ya ke da kallo kamar bakwon shi ya na a haka ya jiyo Muryar Diya a bayan shi ya na fadin " mu tafi ka yi wanka , ka huta , amma gaskiya abokina US ta zauna maka , ka na cen ka na shan dadinka ka kyale ni nan da aiki " wani dan karamin murmushi Malik ya yi ya na fadin " ai ni zuwan tsaye na muku , dan gobe zan yi gaba da Cutie " ya kai karshen ya na fara takawa ya nufi corridor cikin rudu Diya ke ce mishi " ban gane ? " ko sannu Malik bai ce mishi ba ya shige corridor sai da ya shiga sannan Diya ya juyo ya kalli Abdoul da ke tsaye gefe ya ce " har yanzu dai na miskilancin nan su na nan " wata yar karamar dariya Abdoul ya yi ya na fadin " ai miskilanci a jininshi ya ke , ba zai taba fita ba , ba banza Allah ya hada shi da wadda ba ta iya rufe bakin ta ba " " hmmmm , mu tafi mu ba shi wuri " Diya ya fada ya na nufar lift ba musu Abdoul ya bi bayan shi su ka baro part din , dan Diya nashi part din daban ya ke , ko so guda bayan tafiyar Malik bai taba shiga building din ba , saboda wannan building musaman na Malik nz , shi ya sa ya yi nashi part din daban , amma mai floor biyu , sai in Malik na shirin zuwa sannan ya ke sa a bude shi a gyara part din , amma floor na hudu sai Malik ya zo da kan shi ya bude shi dan babu wanda ya san ya ma a ka rufe shi bare a bude sai Malik , dan a ganin shi sirrin da ke cikin wannan floor na nashi ne shi kadai , saboda a nan ne ya ga dare mafi mahimanci a rayuwar shi , a nan ne ya zama cikaken mutum dan haka ba wanda ke da damar shiga floor din , idan kuma za su koma US ya sake rufe shi , bayan shi da Inaya ba wanda ya taba hayo shi , har prince kai tsaye Malik kuwa bedroom din shi ya nufa , ya na isa ya wuce kai tsaye Toilet sai da ya share good one hour a ciki kafin ya fito daure da towel a kugunshi ya na fitowa idanun shi su ka sauka saman ta , ta na zaune tsakiyar gado , ta jingina bayan ta a forehead din gadon ta na rike da wayar shi ta na latsawa wani cool murmushi ya saki kafin ya karaso wajen gadon , ya zauna a baki ya kai hannu ya kwace wayar shi ya na fadin " ta ya a ka yi ki ka san ina nan ? " ya kai karshen ya na ajiye wayar shi saman bedside drawer wani kyawatencen murmushi ta sakin mishi ta na fadin " tracker na saka maka a jiki, ba ka sani ba ? " daga mata gera guda ya yi ya na fadin " Oh , da gaske ? " " sosai ma kuwa " ta fada ta na kauda kai gefe a hankali ya matso , ya kai hannu ya janyo ta a hankali jikinshi , murya kassa kassa ya ce mata " kin zo ko a dai'dai lokacin da ya dace " " wane lokaci kuma ? " ta fada cike da shagwaba har da turo dan bakin nan nata a hankali ya kai bakin shi saitin kunnen ta ya yi mata rada wani dan karamin murmushi ta saki kafin ta zagayo da hannayan ta a kugunshi ta kara shigewa jikinshi ta na fadin " kai dai ba ka gajiya baby , yanzu fa mu ka zo ka bari mu huta mana " " idan mun je cen mun huta " ya fada ya na yin kassa da zip din abayar ta cikin rudu ta ce mishi " ina kuma za mu je baby ? " " Honey Moon " ya fada a takaice ya na cire mata Abayar jikinta ya ajiye gefe a rude ta ke ce mishi " Honey Moon kuma baby ? ka manta da Twins ko ? " a hankali ya kai hannu ya balle mata bra din ta ya na fadin " ina tune da su , wajen Ammie da RIANNA za su zauna , mu kuma , mu tafi inda za mu huta , na kula da Big babyna " turo dan bakin nan nata ta yi ta na fadin " ni ka daina kira na da big baby , kuma ba ka fada min inda za mu je ba " bai ce mata komai ba har sai da ya raba ta da bra din ta ya ajiye gefe sannan ya ce " it's a surprise " har ta bude baki za ta yi magana kawai ta ji ya sauke lips din shi saman nata a hankali ta sauke ajiyar zuciya kafin ta lumshe idanunta ta fara biye mishi ita ma ▪AFTER SOME HOURS a zaune duk su ke a dining room din part din Malik su na yin diner , MALIKAT AL'UMU , MALIKAT INAS , mama , Diya , RIANNA , Tesnim , Nesrine , Junior , Inaya , Abdoul , Yarinyar wajen Tesnim da shi kan shi Malik duk su na zaune saman dining room sai cin abincin su su ke su na hira su na dariya gwanin burgewa cen na hango Prince konce saman Sofa , ya na rike da phone din Inaya ya na latsawa Haka ita ma Princess ta na rike da waya geffen shi ta na latsawa a hankali ya sauko da kafafun shi ya mike tsaye ya fara takawa cike da izza ya karaso wajen Malik , ya kai hannu ya dan bubuga cinyar shi a hankali Malik ya juyo ya kalle shi ya na fadin " what happening my Prince ? " " Daddy , wannan lion na ke son ka saya min " ya fada ya na nuna mishi screen din wayar hannunshi da murmushi a face din ta MALIKAT INAS ta ce " My prince , me za ka yi da lion kuma ? ba ka tsoron ya ji maka ciwo ? ko dai Teddy ne ? " tsuke fuska Prince ya yi cike da dakiya ya ce " ba Teddy ne ba , Lion din gaske ne kuma sai an saya min " a hankali Inaya ta daura hannun saman kan shi ta na fadin " Prince , ba fa lion din gaske ba ne Teddy ne , ba ka gani da kyau ba " " to momy ai ni lion din gaske na ce ina so , ba Teddy ba , Daddy ka fada mata mana " ya kai karshen ya na dawo da kallon shi kan Malik da sauri yarinyar da ke zaune saman cinyar Tesnim ta ce " Uncle , ni ina son Teddyn " wata yar karamar dariya MALIKAT AL'UMU ta yi ta na fadin " ke dai Pretty , duk Teddyn da gare ki ba su ishe ki ba " ta na gama rufe bakin ta Prince ya marairaice fuska kamar zai yi kuka ya na kallon Malik ya ce " Daddy " a hankali Malik ya kai hannu ya dauki Prince ya daura saman cinyar shi , ya na fadin " da ka tashi dauko rigimar momynka sai da ka fita , me za ka yi da lion don Allah ? kuma lion ba ya cikin dabobin cikin gida , bari zan sayo maka Dog or cat wane ka fi so ? " " Lion " ya fada a takaice " ya salam " Malik ya furta a hankali cikin zuciyar shi kafin ya ce " okay , zan siya maka , kafin mu koma US , shikenan ? " da sauri Prince ya girgiza mishi kai ya na fadin " Yeah , that's why i love you more than momy " da sauri Malik ya rufe mishi baki ya na fadin " yi shiru kar ta ji " ya na gama fadar haka ya jiyo Muryar Inaya ta na fadin " na ji ai , kuma na yi fushi da kai kar ka sake min magana " ta na gama fadar haka ta tashi ta nufi corridor sai da ta shiga sannan Malik ya bude bakin Prince ya na fadin " ka gani ko ? to ai yanzu sai ka tashi ka je ka bata hakuri tun da ka bata rai " ba musu prince ya sauko ya bi bayan momyn shi da ga haka su ka ci gaba da cin abincinsu , su na hira har sai da su ka kammala sannan kowa ya tashi ya nufi part din shi , MALIKAT INAS kuma ta ja Twins ta tafi da su Malik da Diya kuma su ka zauna a parlour sai da Diya ya tashi ya na yi wa Malik sai da safe ya tsayar da shi ya na cewa " please ka sa a shirya min Helicopter gobe wajen karfe 10 ko 12 haka " cikin rudu Diya ya ce mishi " Helicopter kuma ? akwai inda za ka je ne ? wai kai ba ka iya zama waje guda ? ka san sunan da a ke kiran ka da shi ? THE EXILED PRINCE , babu wanda bai san wannan sunnan ba cikin Saudiya " " yeah I'M AN EXILED PRINCE , I bought the island of Palawan in the Philippines three years ago , ina son mu tafi ni da ita , ta ga gidan da na yi mana a cen " dan zaro idanu Diya ya yi ya na fadin " noooo , you're serious , yanzu Island guda sukutum ka saya ? " gyada mishi kai Malik ya yi ya na fadin " yeah , har da gidaje ma a sama dan yanzu haka a na cikin gina na ukun , ni dai ka yi abun da na sa ka please , kar ya wuce karfe 12 please " " nawa ka saye ta ? a sani na Island din Palawan ita ce No 1 a cikin jerin wajajen Tourism , ta ya a ka yi ka saye ta ? " " five hundred millions of American dollars na yi cinikin ta , that's why su ka yarda , akwai kuma wata private Island a Thailand cikin archipelago din Koh Samui da a ka saka a kasuwa last year , ita ma na saye ta " shi dai Diya ya tsaya kawai ya na kallon shi , ya ma rasa abun da zai ce wa Malik " okay , zan sa a shirya muku duk abun da ya dace , Allah ya kiyaye hanya , Hope dai ba za ku jima ba ? " mikewa tsaye Malik ya yi ya na fadin " don't worry , just one week ne za mu yi mu dawo , kar ka fadawa kowa maganar tafiyar nan please " " okay , sai da safe " " sai da safe " Malik ya fada ya na nufar corridor , Diya kuma ya nufi lift kai tsaye bedroom din su Malik ya koma , ya shiga ya ga Inaya konce da ga ita sai underwear har ta yi barci wani cool murmushi ya saki kafin ya taka ya shiga toilet ya yi wanka sannan ya fito ya shirya cikin kayan barcin shi kafin ya nufi bed din ya haye a haka har barci ya yi gaba da shi shi ma ▪WASHE GARI ⛅⛅ A hankali ta ware idanunta ta na karanto addu'ar tashi da ga barci ta na gama karantawa ko ta jiyo Muryarshi ya na fadin " sarauniyar barci , sai yanzu a ka tashi ? " wani cool murmushi ta saki kafin ta mike zaune ta kontar da kan ta saman bayan shi ta na fadin " barka da safiya baby " " barka , yanzu tashi ki je ki yi wanka ki zo ina jiran ki yi sauri please " da to kawai ta amsa mishi kafin ta mike ta sauko da kafafun ta kassa ta nufi toilet ta shige jim kadan ta fito sanye da bathrobe har ta nufi dressing room ta jiyo Muryar shi ya na fadin " ga su na fiddo miki " ba musu ta nufo shi , har ta kai hannu za ta dauki kayan , ya taro ta ya na fadin ta bari zai saka mata da kan shi ba ta yi mishi musu ta tsaya ya saka mata kayan kamar wata baby , ya feshe ta perfume sannan ya kai hannu saman bedside drawer ya dauki bowl din fruits salad din da ya hada mata da kan shi ya ba ta wani cool murmushi ta saki ta na fadin " na gode sosai baby , kamar ko ka san abun da ke cikin rai na " daga mata gera guda ya yi ya na fadin " da Gaske ? " a hankali ta gyada mishi kai allamun Eh " shikenan , cinye ina zuwa " ya fada ya na tashi ya fice dakin ba musu ta fara shan fruits salad din nan , sai da ta shanye dukka sannan ta ajiye bowl din saman bedside drawer ta haye saman bed din ta konta , kamar ba yanzu ba ta tashi da ga barci ten minutes bayan konciyar ta Malik ya dawo cikin dakin ya na ganin ta konce ya saki wani cool murmushi ya karaso bakin gadon ya zauna ya kai dan bakin shi saman forehead din ta ya manna mata kiss ▪AFTER SOME HOURS ( misalin karfe 6 na yamma ) ▪ISLAND OF PALAWAN ▪INAYA konce ta ke tsakiyar wani lafiyayen gado mai mugun laushi , ya na shinfide da wata bedsheet white color , ta na sanye da wata bathrobe pink color a hankali ya motsi ta na kokarin tashi , da kalmar shahada a bakinta ta farka kafin ta ware idanunta a hankali slowly ta mike zaune ta na bin wajen da kallo , gaskia bedroom din ya hasu ba kadan ba , a cen geffen hagunta , kawai sai ta ga teku , ya yi wani blue mai mugun kyau , ga rana ta zo faduwa , kun dai san yadda yanayin sky ya ke idan rana ta zo faduwa , musaman wajen su karfe 6 din nan abun ya na da matukar kyau , ga wani dan balcony nan , an saka mishi wasu chair gwanin burgewa , sai wata yar karamar chair kamar table karamar stair makale da karyar balconyn sai a lokacin ta fara jiyo wata music mai dadi na tashi cikin bedroom din ta na tsaka da juye juyen ta kawai sai ta ga wall din glass da ke fuskantar bed din ya rabu gida biyu , ya zuge kan shi gefe da gefe sai ga Malik a tsaye ya na kallon ta ya riko hannayanshi a baya da ga shi sai short ta na ganin shi ta sauke wata yar karamar ajiyar zuciya ta sauko da gudu da ga saman gadon ta nufe shi ta fada jikinshi ta na fadin " da farko na zata mafarki na ke , amma da na gan ka na tabbatar ba mafarki na ke ba " wani dan karamin murmushi ya saki kafin ya ce " mafarkin ki ne ya zama gaskiya " murmushi mai dan sauti ta yi kafin ta dago da ga jikin shi ta na bin wajen da kallo , tamkar gidan da a ka fiddo da ga cikin film haka ya ke dan musaman duk walls din gidan na glass ne , ga wasu tsadadun fournitures farare kal da a ka kawata shi da su a hankali ta dawo da kallon ta gare shi , kafin ta yi magana ya yi sauri kai hannu saman lips din ta ya na fadin " mu je ki gani " ba musu ta bi bayan shi su ka iso saman balconyn nan murmushi mai dan sauti ta yi ta na fadin " baby , it's so beautiful , don Allah ko cikin film mu ke ne ? " " ba film ne ba zahiri ne , wannan shi ne gift din da na yi miki alkawari last five years , da zan iya ba ki fiye da wannan ma da sai na ba ki dan kin yi min komai a rayuwa my Cutie " dan zaro idanu ta yi ta na kallon shi , ita ko a lokacin da ta fada mishi hakan cikin wassa ne , ba ta yi tunanin zai dauki abun serious ba , bare ya yi abun da ta ce , ita ba ta ma san gift din minene ya ba ta , kawai ya tambaye ta wane irin gift ta ke so ta ba shi amsa ta yi nisa duniyar tunaninta kawai ta ji ya raba ta da bathrobe din jikin ta , ya bar mata underwear kadai , ya ajiye bathrobe din saman chair a gefe , da sauri ta ce mishi " baby , ba ka tsoron wani ya gan mu a haka ? " a hankali ya sa hannu ya dago ta , da sauri ta zagayo da kafafun ta a kugunshi , hannayanta kuma a wuyan shi , murya kassa kassa ya ce mata " babu kowa a wajen nan da ga ni sai ke , sai Allah , sai wacen mai idanun mage da ta tsare mu da ido " ( 🙄🙄🤭 ba dai ni ka ke cewa mai idanun mage ba ko ? ) wata yar karamar dariya Ta yi ta na fadin " baby , where is our Twins ? " " su na wajen Ammie da RIANNA , babu kowa a wajen nan da ga ni sai ke " " to yanzu me za mu yi " ta fada ta na daga mishi gera guda a hankali ya fara takawa ya nufi yar table din nan kamar stair a bakin kariyar balconyn ya haye sannan ya ce mata " close your eyes " ba musu ta lumshe idanunta ta na sakin murmushi " kin shirya ? " ya fada cikin sanyin murya " na shirya " ta fada duk da ba ta san abun ya ke shirin yi ba ta na gama fadar haka kawai ta ji sun yi sama , wata kara ta saki ta ware idanunta dai'dai lokacin da su ka tsunduma a cikin ruwan Tekun a tare su ka dago ta na janye kafafun ta da ga saman kugun shi , amma ba ta janye na wuyan shi ba ta wata yar karamar dariya , shi kuma ya zagayo da hannayanshi a kugunta " ya ? da dadi ? " ya fada ya na daga mata gera guda wata yar karamar dariya ta yi ta na gyada mishi kai , kafin ta juya ta kalli rana har ta shige kadan a ke iya gani , da murmushi a face din ta ta ce " it's so beautiful " ta na gama rufe bakin ta ya daura da cewa " right , it's beautiful , but you are more beautiful " wata yar karamar dariya ta yi kafin ta kai lips din ta saman nashi ta yi mishi kiss kafin ta juya ta ci gaba da kallon rana ta na shigewa tsayawa ya yi ya na kallon ta babu ko kiftawa cikin zuciyar shi ya na fadin " Thanks uncle , na gode da wannan farin cikin da ku ka ba ni , Rest in peace uncle " ya na gama fadar haka ya ga ta juyo ta na kalle shi ta na sakin wani cool murmushi ta daga mishi gera guda allamun minene bai ce mata komai ba ya matso da face din shi ya cabko lips din ta ya fara yi mata hot french kiss idanu a rufe a hankali ta sauke ajiyar zuciya kafin ta lumshe idanunta ta fara mayar mishi da Martini , ta na cusa hannun ta guda cikin gashin shi , gudan kuma ta yi kassa da shi kai tsaye cikin short din shi ta saka shi ta damko dick din shi ba shiri ya zame bakin shi da ga cikin nata dan ta tabo wajen da ke yi mishi kaikayi cikin wata siririyar Muryar shi ya ce " kar ki saki , keep please My Cutie " wani cool murmushi ta sakin mishi ta na fadin " ai dama ban ce zan saki ba " a hankali ya cije lips din shi na kassa ya na kallon ta da idanun nan nashi da su ka yi jazir , sai shafar mishi dick ta ke ta na kara birkice mishi lissafi lokaci guda ya kai lips din shi saman nata ya ci gaba da kissing din ta , har ya raba ta da bra din jikin ta bai sani dan ta gama fitar da shi hayacin shi da allamun duk sun manta a cikin teku su ke , bare ko yanayin wajen gwanin burgewa ga wata music na tashi ai dole sha'awar shi ta motsa a hankali ya zame bakin shi da ga cikin nata , ya na wani lumshe ido kamar mai jin barci , murya cen kassan makoshi ya ce mata " mu koma ciki " gyada mishi kai kawai ta yi kafin ta fiddo hannunta da ga cikin short din shi ta sakalo wuyan shi , ta zagayo da kafafunta a kugunshi a hankali ya juya da ita a jikin shi ya nufi wani stair da ke bakin ruwan , wanda zai sada ka da balcony , ya haye ya koma cikin bedroom din da ita kai tsaye saman bed ya dire ta , ya sa hannu ya cire mata pant din jikin ta , sannan ya fidda nashi short din , ko wassa bai tsaya yi ba kawai ya shige ta wata yar siririyar kara ta sakin mishi ta na kankame shi , ta daga kafafun ta ta daura saman bayan shi , hakan ko ba karamin dadi ya yi mishi , nan take ya gama fita hayacin shi baki daya , ita kanta bayan kukan dadi ba abun da ta ke yi mishi , har ce mishi ta ke ya ci gaba kar ya bari , da ga ya ga sambatun nata sun fara kauce tunanin shi , kawai ya sai ya cabko lips din ta ya na yi mata kiss kar ta fadi abun da ya fi karfin shi 🤣🤣🤣 ah ni abun ya fi karfi na gaskiya , na yi nan na ba su waje 😂😂 Amma gaskiya ina son na ga karshen game din nan ku tsaya na koma sai da ya ji realizing a jikin ta sannan ya tsaya ya zame bakin shi da ga cikin nata , ya na sakin murmushi a hankali ta bude idanun ta , ba su sauka ko ina ba sai cikin nashi da sauri ta dago ta na neman ta cabko lips din shi , amma sai ya yi baya kadan ya na fadin " madam ya isa haka , tashi mu je mu yi sallat " girgiza mishi kai ta yi ta na fadin " ka tsaya mu gama mana " ta fada murya cen kassan makoshi a sanyaye da allamun har yanzu ita ma a hannun ta ke a hankali ya matso da face din shi kusan face din ta ya na kallon cikin idanunta ya ce " tashi mu je mu yi sallat , ma ci gaba da ga baya " da sauri ta ce mishi " baby pleaseeeee " ta fada ta na marairaice mishi murya wani cool murmushi ya saki ya na fadin " since when i asked you to sucked me but kin ki yi min , sai ke ki na so ni na yi miki , yau nima ba zan yi ba " ya kai karshen ya na kokarin fida dick din shi da ga cikin vagina din ta da sauri ta taro shi ta na fadin " zan yi maka " cak ya tsaya ya na kallon ta ya na murmushi ya ce " you promise ? " gyada mishi kai ta yi ta na fadin " yeah , i promise , idan mun yi wannan zan yi maka " " kamar yadda ki ke shan sweet za ki min ? " ya fada ya na daga mata gera guda ita kanta sai da maganar shi ta bata dariya , amma sai ta saki wani kyawatencen murmushi ta saki ta na fadin " sosai ma kuwa my lolipop " ta fada ta na kashe mishi ido guda ( 🤣🤣abun da ya sa ta kashe mishi ido guda saboda sunan nan na My lolipop da ta kira shi da shi , shi ne sunan da ya yi Saving din numbar shi a cikin wayar ta da larabci kafin ya tafi Makkah da Malik , shi ya sa RIANNA ta kassa fada mata me hakan ke nufi 🤣🤣🤣🤣 GASKIYA MALIK YA CIKA DAN LOVE 10000000000% ) wani dan karamin murmushin geffen fuska ya saki kafin ya hade forehead din su ya na kallon cikin idanunta , ya fara sucked din ta a hankali ya na fadin " Mrs Nawfel , My Cutie , My crush , My first and last love , Madubin zuciya , tauraruwa da ke haskaka fadin duniya har zuwa duniyar mars , ya ke Sarauniyar zuciyata , na fada miki wani abu ? , ko wace safiya kashe ni ki ke da salon soyayyar ki , Um , ga wannan muguwar zumar taki mai dadi , sai dai kawai na ji kaina a duniyar sama jannati ina yawo cikin gajimare , Allah ki na kaso yarinyar nan , Allah dadin ki karshe ne , ke makura ce My Cutie , duk cikin matan duniya ke kadai ki ka iya mulkar zuciyar Nawfel Hicham Bin Jaabar , wayoooooo Allah dadin Cutie zai ....... " ai ba ta bari ya kai karshen maganar shi ba ta cabko lips din shi ta fara yi mishi kiss dan ta ga allamun ba ya cikin hayacin shi , ga sambatun nashi idan ya fara sai ka rantse hura mishi a kunne a ke dan dadi kuma duk bai San ya na yi ba , dama jira ta ke ya fara wuce gona ta taro shi a haka su ka ci gaba da shar-holiyar su , sai ta gaji da kissing din shi sannan ta saki lips din shi ya ci gaba da zuba mata sambatun dadin nashi ni kuma na tattara takarduna , na ba su waje su ji dadin rayuwar su , na yi gaba dan da sauran labarai ___________________HAPPY ENDING ✍🕊___________________ Alhamdoulilah ! Alhamdoulilah ! Alhamdoulilah ! GODIYA TA TABBATA GA ALLAH , DA YA BA NI DAMAR KAMMALA WANNAN LITTAFIN CIKIN AMINCIN SHI , NA GODE SOSAI DA IRIN GUDUN MAWAR DA NA SAMU DA GA GARE KU ♡ MY COMMENTS ♡ WANNAN LITTAFIN NA EXILED PRINCE YA NA DAYA DA GA CIKIN ABUN DA NA KE ALFAHARI DA SHI A RAYUWATA , WANNAN SHI NE LITTAFI NA BIYU DA NA RUBUTA , DUK DA KIRKIRAREN LABARI NE , AMMA NA GA ABUBUWA DAYAWA A CIKI , ZALINCI , CIN AMANA , KIYAYA , SON ZUCIYA , MAKIRCI KALA KALA , AMMA BA SU YI NASSARA BA A KAN SOYAYYA , DAN LABARIN SOYAYYAR MALIK DA INAYA YA YI MATUKAR BURGE NI , NASU TARIHIN SOYAYYAR DABAN YA KE , 🤣🤣 BA ZAN YI KARYA BA GASKIYA LABARIN NAN YA YI MATUKAR BURGE NI , WASU WAJAJEN INA DARIYA NA RUBUTA SU , WASU KUMA INA HAWAYE NA RUBUTA SU , MUSAMAN WAJEN DA MALIK YA CE SAI SUN ZUBAR DA CIKIN PRINCE , WAJEN NAN SAI DA NA YI HAWAYE , DA KUMA WAJEN DA DIYA KE GWADA MISHI MACIJIN SHI , NA SAN BABU WANDA YA YI TUNANIN HAKA AMMA SAI MALIK YA NUNA MISHI KAMAR BAI GA KOMAI BA , ABOTA IRIN TASU BA A KO INA BA ZA A SAME , WANNAN ZUCIYAR TA MALIK BA A KO INA ZA A SAME TA BA 🤣🤣🤣 GA KUMA UWAR SHAGWABAR MU A GEFE 🤣🤣 SAI DA MALIK YA MALLAKA MATA SAUDIYA BAKI DAYA BA TARE DA YA SANI BA 🤣🤣 YARINYAR NAN TA IYA KASHE MUTUM WLH 🤣🤣 DUK LOKACIN DA NA ZO WAJEN DRAMAR TA DA MALIK SAI NA YI DARIYA YANZU DA A CE AYMANE BA YI KOKARIN KASHE MALIK BA A LOKACIN DA YA KE 24 YEARS DA BA ZAI HADU DA DIYA BA , BA ZAI JE NIGERIA , BA ZAI HADU DA MALAM BA , BARE HAR YA BASHI AUREN INAYA 🤧🤧 GASKIYA BAN JI DADI DA LABARIN NAN YA KAMMALA , NA SO MU CI GABA DA SHI 🤧🤧 NA GA INA DRAMAR INAYA ZA TA KAI 🤣✌ WAI WA YA KE TUNE WAJEN DA TA CE MISHI YA BA TA NONO TA SHA 🤣🤣 SAI DA NA KAMMALA PAGE DIN INA DARIYA 🤣🤣🤣🤣 🤣🤣 GA KUMA DRAMAR MALIK DA KAN SHI , WAJEN DA TA KE MISHI DAN ISKA 🤣🤣 🤣🤣 NI DAMA NA SAN WANNAN SHIRUN NASHI BA A BANZA BA , GASKIYA MALIK YA CIKA ROMEO , 🤣🤣 INAYA BA TA JI DA SAUKI A HANNUN SHI , DA CIKI MA BAI KYALE TA BA 🤣🤣✌ 🤣🤣 DA WAJEN DA YA YI WA SU ADEL KARYAR SHI MAKAHO NE 🤣🤣 WLH WAJEN NAN YA KASO NI KAMAR ME 😂😂 ALLAH MALIK NAMIJIN DUNIYA NE 😂 KU DUBA HAR ISLAND FA YA SAYE KAWAI DAN YA DINGA TAFIYA HONEY MOON DA INAYA , BA ISLAND GUDA BA HAR BIYU MA 😂 😂😂 GASKIYA YA BURGE NI , NA SARRA MISHI NAWFEL HICHAM BIN JAABAR , DA TILA GA MALIK HICHAM BIN JAABAR , JIKAN MALIK ABDOUL LATIF BIN SAUD DA MALIK ABDOULAZIZ BIN SAUD DAYA YA KE BABUN NA BIYUN SHI A DUNIYA 😂😂 GASKIYA IDAN NA CE ZAN FADA MUKU IRIN DARIYAR DA NA SHA SAI MUN KAMMALA BOOK DIN NAN 🤭🤭 KAI ASHE FA YA IDA 😓😓😓 GASKIYA ZAN YI KEWAR MALIK , DA INAYA , DA PRINCE DA PRINCESS 😍❤🔥🔥 THE PERFECT ROYAL FAMILY 😍👑🔥 GASKIYA NA GODE SOSAI DA IRIN GUDUN MAWAR DA NA SAMU , DA KUMA KARBUWAR DA KU KA YI WA BOOKS DI NA , WASU SUN SHA CE MIN WANNAN SHI FIRST PAID BOOK DIN DA SU KA TABA SIYA , NA JI DADIN HAKAN GASKIYA NA GODE SOSAI , ALLAH YA BAR ZUMINCI ALLAH YA KARA MANA SON MANZON SA 🥰🥰 AMMA INA DA TAMBAYA GUDA 🤔🤔🤔🤔🤔🤔🤔 A GANIN KU YAKIN KUJERAR MALIK YA KAMMALA ? DAN FA KAR KU MANCE AYMANE YA AURI HAFSAT KUMA HAR DA CIKIN SHI A JIKIN TA A LOKACIN NA SAN HAR TA HAIFE SHI MA , GA SHI KUMA TWINS TA HAIFA MACE DA NAMIJI ITA MA , GA KUMA KIYAYAR DA KE YI WA MALIK YA KASHE MAHAIFINTA YA KUMA KASHE MIJINTA KU NA TUNANIN BA ZA TA SAKAWA BABYS DIN TA BA KIYAYAR MALIK SABODA SHI YA KASHE AYMANE ? GA KUMA JUNIOR GA UWA UBA PRINCE CIKAKEN MAGAJIN KUJERAR MALIK KU NA GANIN IDAN SUN GIRMA BA ZA SU YI YAKI A KAN KUJERAR NAN BA GA KUMA PRETTY A TSAKIYAR SU , YA ZA TA KASANCE IN PRINCE DA JUNIOR DUK SU KAMU DA SOYAYYAR TA ? GA KUMA YARON AYMANE A GEFE NA SAN KUMA YA GADO MACIJIN UBAN SHI GA ABYAD DA ASWAD A JIKIN PRINCE DAN SUN SAN YAKIN BAI GAMA BA SHI YA SA SU KA DAWO A JIKIN PRINCE A KA JE KUMA YARINYAR AYMANE TA KAMU DA SON PRINCE SHI KUMA PRETTY YA KE SO A KA JE NAYAB BAI MUTU KUMA FA ? A KA JE YA DAWO YA KUMA DAWO A MATSAYIN MAKIYIN NAYEL ? A KA JE YA HADU DA PRINCESS KUMA YA KAMU DA SON TA ? YA KU KE GANIN DRAMAR ZA TA KASANCE NI DAI NA CE HMMMMMM , INA GA BAN GAMA DA FAMILYN NAWFEL HICHAM BIN JAABAR BA , DAN YAKIN KUJERAR MALIK YANZU YA FARA DA GA ALKALAMIN AMEERA ABDOULAYE ✌💕 A.K.A MEERAH 🕊🔥 【 THE ROYALTY LOVE 🕊🌸💕 】 ✍✍✍✍ FREEDOM OF WRITERS ✍✍✍✍ PEN IS MORE THAN SWORD ✍✍✍✍✍ GA DUK ME BUKATAR YIN MAGANA DA NI KAI TSAYE ZAI IYA TABO NI TA WANNAN NUMBER +22798999753 WHATSAPP ONLY THANKS A LOT ✌ LUV U SO MUCHHHHH ❤❤❤❤❤❤❤❤❤❤❤ PEACE 🕊🍃